es
Feedback
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

Ir al canal en Telegram

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

Mostrar más
2 293
Suscriptores
+224 horas
+77 días
+2930 días
Archivo de publicaciones
Karbala ba labari bane na wani tarihi da ya ruga ya shuɗe , gamammiyar makaranta ce mai cike da iznar da duk ɗan Adam yake bu
Karbala ba labari bane na wani tarihi da ya ruga ya shuɗe , gamammiyar makaranta ce mai cike da iznar da duk ɗan Adam yake bukatar komawa gareta har ranar tashin ƙiyama. Tabbas Karbala fitila ce mai haskaka rayuwa. ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

LABARAN KARBALA DA ASHURA (61H) . -Isowar Umar bin Sa'ad Karbala A ranar 3 ga watan Almuharram shekara ta 61 bayan hijira , Umar ɗan Sa'ad ɗan Abi Waƙkas ya iso filin karbala da rundunarsa mutu dubu huɗu wani ƙaulin dubu Talatin , bisa umarnin Gwamnan Kufa Ubaidullahi ibnu Ziyad cewa in ya kashe Imam Hussaini (a.s) zai bashi Mulkin garin (Raiy) . - Shirye-shiryen Rundunonin Banu Umayyah A safiyar yau ne sansanin Annakhilah ya zama sansanin sojojin Umayyawa don yaƙar Imam Hussain (a.s), an bada umarnin kaddamar da rundunoni kamar haka : 1. Naɗa Shammar bin Zhul-Jaushan al-Kilabi ya jagoranci bataliyar mayaƙa 4,000 sannan ya nufi Karbala nan take. 2 . Bawa al-Husayn bin Namir al-Hamsi jagorancin bataliyar mayaƙa 4,000 tare da garzayawa Karbala nan take. 3. Sanya Ka’b bin Dalha ya jagoranci bataliyar mayaƙa 3,000 sannan ya nufi Karbala nan take. 4. Naɗa Mudayir Al-Mazini ya jagoranci bataliyar mayaka 3,000 sannan ya nufi Karbala nan take. 5. Naɗa Nasr bin Harsha ya jagoranci bataliyar mayaƙa 3000 sannan ya nufi Karbala nan take. 6. Naɗa Yazid bn Rikab jagorancin bataliyar mayaka 2000 da garzayawa zuwa Karbala nan take. 7. Sanya Shabath bin Rabi’i ya jagoranci bataliyar mayaƙa 2000 sannan ya nufi Karbala nan take. 8. Naɗa Hajjar bin Abjar ya jagoranci bataliyar mayaka dubu daya da gaggawar zuwa Karbala. 9. An umarci Al-Jaafi ya zauna tare da wata rundunar tsaro da ta ƙunshi mayaka dubu a kewayen gadar kogin Sarat (arewacin Kufa) , don hana kabilar Azd da Hamdan kaiwa Imam Hussain (a.s) ɗauki a Karbala. 10- Suwaid Al-Munqari zai ci gaba da kula da harkokin tsaro a Kufa. Dukkanin rukunin sojojin suna ƙarkashin kwamandan Sojoji Umar Ibn Sa'ad Ibn Abi Waqqasn L ne. Wasu daga fitattun bataliyoyi masu dauke da makamai da suka taka rawa wajen kashe Imam Hussain (a.s.) , kuma sun yi raunuka da dama a jikin Abul Fadl Al-Abbas (a.s.) lokacin da ya kutsa su . 1. Jar Bataliyar Dailam Ta ƙunshi mayaka dubu 4, kuma Shammar ne ke jagorantarsu, waɗanda suka fito daga garin Rayy suka zauna a Kufa, sun kasance maƙiya Ahlul Baiti (a.s) kuma sune rabin mutanen Kufa. Masu kula da al'amarin tsaron cikin gida a gwamnatin Ibn Ziyad, kuma sun taka rawa wajen kashe Muslim bn Aƙil (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) , sannan sun riƙe manyan muƙamai na gudanarwa a garin Kufa . Sun kasance masu sa ido a kusa da kufa , domin katse duk wani ɗauki da za'a iya kawowa Imam (a.s) a kwanakin farko , daga bisani kuma suka shiga Karbala suka yi yaki har aka kashe Imam Husaini (a.s). 2. Busasshiyar Bataliya , Sham : Ita ce bataliyar Al-Hosayn bn Numair al-Homsi L , mutum ne da jami’an leƙen asirin (Rum) suka horar da shi ta hanyar (Sargon) mutumin Rum, wanda shi ne wakilin gwamnatin Rum a Gwamantin Mu’awiya L . Malaman tarihi sun haɗu akan cewa ; Sargon ne ya bawa Yazidu shawarar kashe Imam (a.s.) koma ya masa umarnin hakan , wannan busasshiyar bataliya wata bataliya ce ta musamman wacce Gwamnatin Rum ta horar. Dukkansu sun haɗu don su kashe jikan Manzon Allah (saww) da baida mataimaka , ba sojoji ba mayaƙa face mutanen da basu wuce 80 ba . السلام على المقتول صبرا 😭 ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 3/Almuharram/1444H - 21/7/2023 Miladiyya. https://t.me/tafarkintsiratv

"شَهْرُ الشُّجُوْنِ" هَلَّ شَهْرُ الشُّجْوْنِ فَوْقَ الْبَرَايَا جَدَّدَ الْحُزْنَ وَالْبُكَا وَالْبَلَايَا يَا هِلَالَ الْحَرَامِ حَرَّمْتَ قَلْبِيْ طِيْبَ عَيْشٍ وَرَغْدِهِ بِالرَّزَايَا يَا هِلَالَ الْحَرَامِ أَوْجَعْتَ قَلْبِيْ وَسَرَى الْوَجْعُ فِي الدِّمَا وَالْخْلَايَا كَيْفَ لَا بَعْدَ ذَبْحِ نُوْرِ فُؤَادِيْ فِيْكَ ذَبْحًا كَالْكبْشِ يَوْمَ الضَّحَايَا هَلْ سَمِعْتُمْ بِقَتْلِ إِنْسٍ يُجَزُّ مِنْ قَفَاهُ غَيْرَ الْحُسَيْنِ بَرَايَا ؟ بَاتَ طُعُمَ السُّيُوْفِ فِيْ الْفَلوَاتِ هُمْ أُلُوْفٌ حَاطُوْا بِهِ مِنْ جَدَايَا أَثْخَنَتْهُ الْجِرَاحُ مِنْ ضَرَبَاتٍ طَعَنُوْهُ بِالرُّمْحِ بَيْنَ الثَّنَايَا طَعَنَاتُ الْأَوْبَاشِ فِيْ صَدْرِهِ قَدْ شَقَّقَتْ قَلْبَهُ بِكُلِّ الزَّوَايَا ظَلَّ يَحْمِيْ حِمَاهُ مِنْ كُلِّ صَوْبٍ جَالِسًا تَعْتَرِيْهِ أَيْدِي الْجَنَايَا نَاءَ نَوْءً وَكَبَّ ضَرْبًا وَعَطْشًا لَا يُطِيْقُ الْوُقُوْفَ نَزْفًا تَعَايَا حَرَّضَ الْقَوْمَ اِبْنُ سَعْدٍ عَلَيْهِ ذَبَحَ السِّبْطَ شَمْرُ اِبْنُ بَغَايَا وَهْوَ مِنْ سَادَةِ الْأَنَامِ وَلَكِنْ دَاسَتِ الْخَيْلُ جِسْمَهُ وَالْمَطَايَا طَرَحُـوْهُ عَلَى الْـعَـرَاءِ ثَـلَاثًـا ثُـمَّ سَـاقُـوْا عِـيَـالَـهُ كَسَبَايَـا قَـطَّـعُـوْهُ إِرْبًـا وَإِرْبًـا عِـنَـادًا سَلَبُوْهُ سَلْبًا تَنَاسَوْا وَصَايَا كَيْفَ أَنْسَى الطُّفُوْفَ وَالْغَاضِرِيَّهْ لَا وَرَبِّ السَّمَاءِ ذَا مِنْ سَجَايَا لَا كَيَوْمِ الْحُسَيْنِ يَوْمَ الْمُصَابِ لَا كَزُرْءِ الْحُسَيْنِ زُرْءَ الْبَرَايَا لَا كَشَهْرِ الْحُسَيْنِ بَيْنَ الشُّهُوْرِ لَا كَمَوْتِ الْحُسَيْنِ بَيْنَ الْمَنَايَا يَا شَهِيْدَ الطُّفْوْفِ مِنِّيْ إِلَيْكَ نَفَحَاتٌ وَأَلْفُ أَلْفِ تَحَايَا صَلِّيَنْ سَلِّمَنْ عَلَى السِّبْطِ رَبِّيْ عَدَدَ الرَّمْلِ وَالْحَصَى وَالنَّقَايَا وَعَلَى آلهِ وَمَنْ بَذَلُوْا أَرْ وَاحُهُمُ فِيْ جِهَارهِمْ وَالْخَفَايَا ✍️خادم آل محمد العبد الفاني الكنوي ٣ / المحرّم الحرام / ١٤٤٥هـ

LABARAN KARBALA DA ASHURA (61H) . "Isowar Imam Hussaini Karbala😭" Bayan doguwar tafiya mai dogon zango data shafe kwanaki 24 (Daga Makka zuwa) , Imam Hussain (a.s.) ya iso filin Karbala da tafiyar kilomita 1403 har da garin Makka da ya baro zuwa Karbala. Imam Husaini ya iso Karbala a ranar 2 ga watan Almuharram shekara ta 61 ɗaya hijra , yayi tafiyar kwanaki 14 a yankin Hijaz (Saudiyya) da kwanaki 9 a lardin Iraki , sai kuma saurin tafiyar kilomita 63.91 da sukan iya kaiwa a kowanne wuni . Bayan Imam Hussain (a.s.) ya isa Karbala sai aka ga dokinsa ya tsaya kuma ya cije a wurin , sai Imam Hussain ya tambaya ya sunan wannan wuri da muke ? aka ce masa : Alghadiriyya , sai ya ƙara tambaya yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa : ana ce masa Nainawa , sai Imam ya kara tambaya ko yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa : ana ce masa gaɓar Furatu, sai Imam Hussain ya kara cewa ko yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa ana ce masa Karbala , sai kawai aka ga Imam Hussain ya ja numfashi ya fashe da kuka mai tsanani sai yace : Ya Ubangiji ina neman tsari a gunka daga baƙin ciki da bala'i, sannan yace musu : Ku tsaya anan kar ku ƙara gaba daga nan inda muke , domin wallahi anan ne za'a sheƙar da jinanenmu, wallahi anan za'a keta alfarmar masu alfarmarmu , wallahi anan ne za'a kashe mazajenmu , wallahi anan ne za'a kashe mazajenmu , wallahi nan za'a ziyarci ƙaburburanmu , wallahi a wannan turɓayar kakana yayi min alƙawari kuma alkawarinsa baya tashi . Jagoran tawagar Imam Hussain (a.s) yayi shela ga ƴan tawagar kan su yi masauki na ƙarshe a wannan wuri . Zamu cigaba .... السلام على المقتول صبرا 😭 يا حسين ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

"Kar ku zarge mu a watan Al-muharram idan kuka ganmu ba yanda kuka saba ganinmu ba , domin giyar soyayya ba yanda bata yi da
"Kar ku zarge mu a watan Al-muharram idan kuka ganmu ba yanda kuka saba ganinmu ba , domin giyar soyayya ba yanda bata yi da mahaukacin masoyi" ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

عَزَاءُ الْغَرِيْبِ.pdf5.19 KB

Repost from N/a
عَزَاءُ الْغَرِيْبِ.pdf5.19 KB

"عَزَاءُ الْغَرِيْبِ بِحَدِيْثِ الرَّيَّانِ بْنِ شَبِيْبٍ " بَدَاْتُ اقْتِبَاسِيْ بِاسْمِ مُبْدِعِ خَلْقِنَا وََأََحْمَدُهُ حَمْدًا يَفُوْقُ ذُرَى الثَّنَا أُصَلِّي عَلَى خَيْرِ الْبَرَايَا وَآلِهِ أُوْلِي الطُّهْرِ وَالْإِحْسَانِ سَادَاتِ أَمْرِنَا رَوَى فِي الْأَمَاليِّ الصَّدُوْقُ بِمَجْلِسٍ حَوَى غُرَّةَ الشَّهْرِ الْحَرَامِ كَيَوْمِنَا بِإِسْنَادِهِ أَعْلَاهُ اِبْنُ شَبِيْبِ عَنْ رِضَا الْخَلْقِ فِي الْبَلْوَى عَلَيْهِ سَلَامُنَا دَخَلْتُ عَلَى الْمَوْلَى الرِّضَا ذَاتَ غُرَّةِ الْـ ـمُحَرّمِ شَهْرِ الْكَرْبِ فِيْمَا رَوَى لَنَا فَقَالَ لَهُ اِبْنُ النَّبِيِّ : أَصَائِمٌ ؟ أَيَا بْنَ شَبِيْبٍ أَوَّلُ الشَّهْرِ يَوْمُنَا أَجَابَ بِلَا يَا سَيِّدِيْ لَسْتُ صَائِمًا فَأَخْبَرَهُ مَغْزَى السُّؤَالِ إِمَامُنَا دَعَا زَكَرِيَّا وَاسْتَجَابَ إِلَهُنَا لَه مَا دَعَا فِيْ مِثْلِ ذَا الْيَوْمِ عِنْدَنَا دَعَا : رَبِّ هَبْ لِيْ وَارِثًا يَا سَمِيْعَ مَنْ دَعَاهُ بِحُسْنِ الْقَلْبِ يُعْطِيْهِ مَأْمَنَا فَبَشَّرَهُ الْبَارِيْ بِيَحْيَى مُبَارَكًا وَأَصْلَحَ مَا فِيْ زَوْجِهِ قَوْلُ رَبِّنَا فَمَنْ صَامَ هَذَا الْيَوْمَ يَلْقَى إِجَابَةً بِحُسْنِ قَبُوْلِ اللهِ فَضْلٌ بِلَا عَنَا أَيَا ابْنَ شَبِيْبٍ إِنَّ هَذَا مُحَرَّمٌ وَكَانَتْ رِجَالُ الْجَاهِلِيَّةِ قَبْلَنَا تُحَرِّمُ فِيْهِ الظُّلْمَ وَالْقَتْلَ حُرْمَةً وَمَا عَرَفَتْ هَذِي الْعِصَابَةُ حَقَّنَا فَلَمْ يَعْرِفُوْا لِلشَّهْرِ أَيَّ كَرَامَةٍ وَلَا لِلنَّبِيِّ الْمُصْطَفَى حُرْمَةَ السَّنَا لَقَدْ قَتَلُوْا ذُرِّيَّةَ الطُّهْرِ فِيْهِ مَا رَعَوْا حُرْمَةَ الْإِيْصَاءِ يَا بْنَ شَبِيْبِنَا قَدِ انْتَهَكُوْا حِرْمَ النَّبِيِّ بِكَرْبِلَا فَلَا غَفَرَ اللهُ الذُّنُوْبَ لِمَنْ جَنَى أَيَا ابْنَ شَبِيْبِ الْخَيْرِ إِنْ كُنْتَ بَاكِيًا لِشَيْءٍ فَأَوْلَى بِالْبُكَاءِ حُسَيْنُنَا لَقَدْ ذَبَحُوْهُ ذَبْحَ كَبْشِ الضَّحِيَّةِ وَعِشْرِيْنَ إِلَّا اثْنَيْنِ مِنْ نَسْلِ جَدِّنََا تَوَفَّوْا عَطَاشَى مَا لَهُمْ مِنْ مُشَابِهٍ بِكُلِّ بِلَادِ اللهِ جِسْمًا وَمَعْدِنَا سَمَوَاتُ سَبْعٍ قَدْ بَكَتْهُ وَأَرْضُهَا وَأَرْبَعُ آلَافِ الْمَلائِكِ جَاءَنَا أَتَوْا نُصْرَةً لِلسِّبْطِ فِيْ أَرْضِ كَرْبَلَا سِوَى أَنْ رَأَوْهُ بِالتُّرَابِ مُكَفَّنَا فَهُمْ عِنْدَ قَبْرِ السِّبْطِ شُعْثٌ بَوَاكِيًا وَغُبْرًا إِلَى يَوْمِ الظُّهُوْرِ وَثَأْرِنَا فَيَغْدُوْنَ أَنْصَارًا لَهُ وَشِعَارُهُمْ أَلَا يَا لَثَارَاتِ الحُسَيْنِ قَتِيْلِنَا لَقَدْ حَدَّثَ الْمَاضِيْ أَبِيْ عَنْ جُدُوْدِهِ بِأَنَّ السَّمَا قَدْ أَمْطَرَتْ دَمَ كَرْبِنَا كَذَاكَ تُرَابًا أَحْمَرًا يَوْمَ قَتْلِهِ فَيَا ابْنَ شَبِيْبٍ اِبْكِ مَا دُمْتَ حِبَّنَا فَلَوْ سَالَ مِنْكَ الدَّمْعُ حُزْنًا لِقَتْلِهِ فَذَنْبُكَ مَغْفُوْرٌ بِفَضْلِ إِلَهِنَا صَغِيْرًا كَبِيْرًا أَوْ قَلِيْلاً وَضِدَّهُ يُكَفِّرُهُ الرَّحْمَنُ عَنْكَ لِأَجْلِنَا أَيَا ابْنَ شَبِيْبٍ إِنْ أَرَدْتَ لِقَاءَهُ بِلَا سَيِّئَاتٍ زُرْ حُسَيْنًا فَتُحْصَنَا وَإِنْ سَرَّكَ الْإِسْكَانُ فِي الْغُرَفِ الَّتِيْ بَنَاهَا إِلَهُ الْعَرْشِ لِلْآلِ مَسْكَنَا مَعَ الْمُصْطَفَى فَالْعَنْ طُغَاةً تَعَمَّدُوْا قِتَالَ حُسَيْنٍ تَلْقَ فِي الْخُلْدِ مَأْمَنَا وَإِنْ سَرَّكَ الْأَجْرُ الْعَظِيْمُ كَمَنْ قَضَى فِدَاءً لَهُ قُلْ حِيْنَ تَذْكُرُ جَدَّنَا أَلَا لَيْتَنِيْ مَعْهُمْ بِأَرْضِ بَلَائِهِمْ لِكَيْمَا أَرَى فَوْزًا عَظِيْمًا مَعَ الْهَنَا أَيَا ابْنَ شَبِيْبٍ إِنْ يَسُرُّكَ كَوْنُنَا مَعًا فِيْ رَفِيْعِ الشَّأْنِ حَيْثُ بَقَاءُنَا فَأَحْزَنْ لِحُزْنِ الْآلِ وَافْرَحْ لِبَهْجِهِمْ وَوَالِ بَنِي الزَّهْراءِ وَاتْرُكْ خِلَافَنَا فَلَوْ أَنَّ عَبْدًا عَلَّقَ الْقَلْبَ وَالْوَلَا بِصَخْرٍ لَوَالَى الصَّخْرَ فِيْ يَوْمِ بَعْثِنَا فَهَذَا عَزَاءُ الْحَقِّ مِنْ سَيِّدِي الرِّضَا تُؤَيِّدُهُ الْأَخْبَارِ فِيْ جُلِّ كُتْبِنَا أَيَا صَاحِ فَالْزَمْ مَا رَوَتْهُ ثِقَاتُنَا تَفُزْ يَوْمَ يَرْجُو النَّاسُ مَنْجًى عَنِ الْعَنَا إِذَا زُرْتَ مَوْلَانَا الْحُسَيْنَ بِكَرْبَلَا فَلَا تَنْسَنِيْ فِي السُّؤْلِ بِالْخَيْرِ عُمَّنَا وَبَلِّغْ سَلَامِيْ إِنْ مَسَكْتَ ضَرِيْحَهُ وَكُنْ ذُخْرَ ذَا الْفَانِيِّ عِنْدَ إِمَامِنَا تُعَرْقِلُنِي الْآثَامُ وَالنَّفْسُ تَلْتَوِي وَأَرْجُو خَلَاصَ الْحَالِ مِنْهُ كَذَا الْمُنَى صَلَاةٌ وَتَسْلِيْمٌ عَلَيْهِ وَصَحْبِهِ مَتَى مَا أَتَى شَهْرُ الْحَرَامِ وَحُزْنِنَا ✍️خادم العترة الطاهرة ️ العبد الفاني الكنوي ١ / المحرم الحرام / ١٤٤٨م

موسم الأحزان هلّ المحرّم موسم الأحزان شهر البكا والكرب والأشجان شهر العزاء لعترة المختار شهر المآتم عند ذي الإيمان شهر الحسين
موسم الأحزان هلّ المحرّم موسم الأحزان شهر البكا والكرب والأشجان شهر العزاء لعترة المختار شهر المآتم عند ذي الإيمان شهر الحسين وآله الأبرار وصحابه الأبطال والشجعان شهر بعاشره على الرّمضاء ضحّى بهم ظلمًا بنو السّفيان شهر الّذي أبكى النّبيّ الهادي من قبل غُرّته من الأحزان جلّت مصيبته بقتل السّبط في الطّفّ شهر تورّم الأجفان فالتنشروا لون السّواد حَزانى والترفعوا الرّيات في الأوطان وتجنّبوا الأفراح فيه تأسّيا بالآل أهل الخير والإحسان واسعوا لنشر رسالة الأحرار من هدي يوم الطفّ بالإتقان وتذاكروا يوم الحسين عليه صلوات ربّي دائمَ الأزمان ✍️نزيل النجف الاشرف العبد الفاني الكنوي ١/ محرم الحرام/ ١٤٤٤هـ

TSAKANIN MU DAKU WANE NE ƘIRƘIRAR YAHUDAWA ??? (ƘALU BALE GAREKU) Daga cikin abubuwan da maƙiya Shi'a suke yiwa Ƴan Shi'a sharri da ƙage dashi , shine danganta Shi'anci da yahudanci , wai asalin Shi'a wani Bayahude da ake kira Abdullahi ɗan Saba'i ne ya ƙirƙirota , abun dariya da takaici !!! Tare da cewa har manyan Malamansu sun ƙaryata wannan maganasuka tabbatar da bata da asali , suka tabbatar da ba komai bace face yarfe da kuce dan a ɓata Shi'a da Shi'anci , Bugu da ƙari akan haka ga wani ƙalu bale ga duk wani mai tuhumar Asalin Aƙidar Shi'a da Yahudanci : In har kun kasance masu gaskiya cikin abunda kuke faɗa , ga littattafan Shi'a nan sun cika Duniya tun daga ƙarni na farko har zuwa yau , in kun isa ku kawo mana ruwaya ko da guda ɗaya ce da aka ce wannan Abdullahi ɗan Saba'i ne ya rawaito ta (Ba an tawaito akansa ba ) , ko ku kawo mana wata Aƙida guda ɗaya daga cikin Aƙidun Shi'a da aka ruwaito cewa daga Abdullahi ɗan Saba'i take , ko ku kawo mana wani hukuncin Fiqhun Shi'a guɗa daya tak da aka ce ɗan Saba'i ne ya rawaito shi ko daga gareshi yake . Don Allah da Annabi mun ƙalu balance ku kuyi hakan Ya ku tarin ...... BUGU DA ƘARI Amma ku kuma babu wani littafin Tafsiri naku da za'a buɗe face an samu riwayar Addinin ku daga Ka'abul Ahbari , Wanda kowa yasan tsohon ƙasurgumin malamin Yahudawa ne wanda ya musulunta a Zamanin Mulkin Umar Bin Khaɗɗab, daga nan ya zama Babban Maruwaicin Hadisi da kuke ji da shi a Addinin ku , abune tabbatacce Ka'abu ya ƙware wajen rawaito ruwayoyin tastuniyoyi na Isra'iliyyat , kuma yana da Tafsiri a Addinin ku saɓanin mu , sam Abdullahi bin Saba'i bai da wani tasiri a wurinmu , sai dai ruwayoyi da suke la'antar shi in ma akwaishi ɗin yana samuwa kenan fa ! Gini akan yadda kuke riyawa Mu da ku waye ƙasurgumin Bayahude yayiwa Tasiri a Addinin sa ? Waye yake cewa Bayahude : Radiyallahu anhu a litattafan Tafsirin sa in ba ku ba ? Waye yake la'antar Bayahude a littattafansa in bamu ba ? Su waye suka ce Bayahude ne Malamin Sahabbai a fannin Tafsirin Alkur'ani in ba ku ba ? Ba Ka'abul Ahbari ba , akwai manyan manyan malaman Yahudawa da suka shahara suka yiwa Musulunci kuste kuma suka wayi gari sune manyan turakunku na Addini , Kamar su Abdullahi ɗan Salami da Wahbu ɗan Maniyyata da sauransu .... Kai manyan waɗanda kuke ji dasu a hadisi malamanku sun tabbatar da daga wajen Yahudawan suke rawaito Hadisai kuma an ingantasu kuna Addini da su . Mhm !!! Wai mai gidan gilashi ne yake cewa ayi wasan jifa da dutse !!! ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

JA'AFARIYYA BA MAZHABAR FIƘHU BACE KAWAI Imam Ja'afar As-sadiƙ (A.S) ba mazhabar fiƙhu kawai yake da ita ba - a daura da irin
JA'AFARIYYA BA MAZHABAR FIƘHU BACE KAWAI Imam Ja'afar As-sadiƙ (A.S) ba mazhabar fiƙhu kawai yake da ita ba - a daura da irin Malikiyya ko Shafi'iyya - shi limami ne na addinin Annabi (Saww) na asali , watau koyarwarsa ta tattaro komai tun daga aƙida , fiƙhu tazkiyya da abinda yafi gaban nan idan akwai , wannan gamammen tsarin na Imam Ja'afar Al-sadiƙ (A.S) ake kira Shi'a Imamiyya ko Rifidanci , Ja'afariyya ba mazhabar fiƙhu bace kawai ta shanye mazhaba ta lasheta. ✍️ Khãdimul AshrãfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

WAƘI'AR HARRA (JUYIN JUYA HALIN MUTANEN MADINA GA GWAMNATIN YAZIDU ƊAN MU'AWIYAH L) . Yaƙi ne da ya gudana a ranar 27 Ko 28 ga watan Zul-Hijja shekara ta 63 bayan hijira , tsakanin mutanen garin Madina da suka yi tawaye ƙarkashin jagorancin Abdullahi bin Hanzala da sojojin Sham karkashin umarnin Yazid bin Muawiyah bin Abi Sufyan, karkashin jagorancin Muslim bin Uƙbah Al-Marri . A wannan lokacin ne aka kashe dayawa daga cikin mutanen Madina birnin Manzon Allah (sawa) , wadanda suka hada da sahabbai 80 da Mahaddatan Alƙur'ani 700, kusan mata dubu aka yiwa ciki ba ta hanyar aure ba , aka tsananta wa garin tare da halartar komai nashi tsawon kwanaki uku , aka wawushe dukiyoyin mutane, aka keta alfarmar masallacin Annabi bisa umarnin Yazidu L .Imam Sajjad (a.s.) ya kasance a tsakiya game da yunkurin da mutanen Madina suka yi (a wannan lokacin baya tare da kowanne ɓangarori biyun) kuma ya bawa mutane da dama mafaka ciki har da iyalan Marwan binil Hakam. An ce Sojoji sun kashe sama da mutane 4000 ko 11700 ko 10700, daga cikinsu mutum 700 sun haddace Alkur’ani da Sahabban Manzon Allah 80 wasu daga cikinsu sun halarci yaƙin Badar ne . A lokacin aka kashe Abdullahi bin Hanzala da ‘ya’yansa . Bayan kwana uku ana tafka barna da munanan ayyuka a cikin garin Madina , sai Muslim bin Uqbah Al-Marri ya tara sauran mazauna garin Madina , ya bukaci su yi mubaya'a ga Yazidu ɗan Mu'awiyah a kan cewa sun zama bayinsa. Wato ganima ce ga Yazid bn Muawiyah , kuma waɗanda ba su karɓi wannan mubaya’a ba suka fille kawukansu . Wanda suka rage basu shiga wannan mubaya'ar ba kuma suka tsira mutum biyu ne kawai sune : Ali bin Abdullah bin Al-Abbas ( Saboda sulhun daya daga cikin danginsa a cikin rundunar Yazidu ya shiga wannan mubaya'a) Sai kuma Imam Ali Zainul Abidin Assajjad (a.s.) . Wannan waki'ar ta faru biyo bayan kashe Imam Hussain da kuma yadda miyagun ayyukan Yazidu ɗan Mu'awiyah suka kara bayyana ga mutane , har sukayi tawaye ga Gwamantinsa . Haka nan wannan hari da rundunar Yazidu suka kai Madina yana ɗaya daga cikin miyagun ayyuka Uku da Yazidu L yayi a shekara ukun da ya yi a Mulki, shekara ta farko ya kashe Imam Hussain (a.s.) shekara ta biyu aka kaiwa garin Makka hari sannan a shekara ta uku aka kaiwa Madina Hari . ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 28/Zul-hajji/1443H - 28/7/2022

cewa "Kulluhum Kuffarun wa Fusuuƙun " suna bibiyar tarihi da abinda ya tabbata na rayuwar Sahabbai bisa ma'aunai na Shari'a, su ƙaunace su don Allah da gaskiya ko su ƙyamaci aikinsu don Allah da gaskiya . Batun gaskiya da gaskiya ƴan Shi'a basu da wata maslaha ta musamman cikin so ko ƙin Sahabbai . Abun takaici shine yadda maƙiya ƴan Shi'a suka cakuɗa waɗannan mas'alolin da gangan don su ɓata ƴan Shi'a . Ba komai yasa ba za su yarda da Aƙidar ƴan Shi'a game da Sahabbai ba sai dan hakan zai lazimta rushewar Aƙidar su da Addinin su baki ɗaya game , wanda wannan Aƙidar tasu itace ainihin ƙin Sahabbai da zaluntar su , ko Sahabban ba za su yarda da wannan Aƙidar ta "Kullhum Uduulun" bari ma sun ƙaryata ga duk wanda ya bibiyi tarihin rayuwar su , don haka ne ma muka ce ƴan Shi'a ne masoya Sahabbai na gaskiya . A dunƙule dai abinda yake Hujjar cirar Shari'a da Addini daga gareshi a wurin ƴan Shi'a Alkur'ani ne da Sunnah , Ma'ana Sunnar Annabi da Ai'mmatu Ahlil baiti (a.s.) , wanɗanda sune Khalifofi kuma Jagorori bayan Manzon Allah (saww) , su kaɗai ne Hujja banda wanin su . Allah ka ƙara tsira, aminci , albarka da yarda ga zaɓaɓɓun Sahabban Manzon Allah (saww) . Wassalamu alaikum warahmatullahi wabaraka tuhu 👏 ✍️ Khadimul AshrãfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 26/Jumadhal Ula/1444H - 21/12/2022

ƳAN SHI'A NE MASOYA SAHABBAI NA GASKIYA Wanda yace : Duk Sahabban Annabi ba mutanen kirki bane shine mutumin banza kuma ya halaka ya taɓe , kuma wannan ba ita bace Aƙida da Matsayar Shi'a game da Sahabban Annabi (saww) . Wanda yace : Sahabban Annabi (saww) baki ɗayan su Adalai ne na gari ne ya saki layi , domin hakan ya saɓawa Waƙi'i da Nassin Alkur'ani da Hadisai da Sirar Sahabban , babu shakka wannan ma ba matsayar ƴan Shi'a bace game da Sahabban Manzon Allah (saww) , domin Sahabbai kashi-kashi ne kuma hawa hawa ne , akwai Uduulun akwai kuma akasin haka . Babu wanda ya isa ya musa haka sai Jahili ko kuma mutum kangararre munkiri . TO MECE CE MATSAYAR ƳAN SHI'A GAME DA SAHABBAI ??? A ko da yaushe maƙiya Shi'a da Shi'awa sukan ƙoƙarin ɓata su da nuna su a matsayin wasu maƙiya Sahabbai ko wasu mutane da basa ƙaunar duk Sahabban Annabi (saww) , wanda wannan tsantsan rashin Adalci ne ga ƴan Shi'a, domin ba ita bace Aƙidar su game da Sahabbai , ƴan Shi'a basa yiwa Sahabbai kuɗin goro su zage su ko su kafirta su ko su aibatasu kamar yanda aka ruɗi dayawan jahilai da wawaye da hakan , wasu an musu gadar zare suka faɗa , wasu kuma suna yine da gangan da ganganci , suka ɗauki zagin Sahabbai a matsayin wani makami da zasu yaƙi Shi'a dashi a wajen jahilan mutane da basu san Shi'a ba . Ƴan Shi'a suna ƙudurce cewa Sahabban Manzon Allah (saww) sun kasu kamar haka ; 1 . Daga Sahabbai akwai Adilai, Muminai , Waliyyai , Salhai da suka kai wani matsayi a wajen Allah da ba masanin haƙiƙanin sa sai Allah da Manzonsa . Tabbas Waɗannan sun rabauta duniya da lahira , kuma zama da Manzon Allah ya amfane su cikin taikonsa da yin imani na haƙiƙa da shi , Radiyallahu Anhum Wa Radhu Anhum . Duk sanda kaji an yabi Sahabbai ko an jinjina musu a cikin Alkur'ani da Sunna to da wannan kashi ake .Ƴan Shi'a suna ƙaunar waɗannan Sahabbai, suna neman alabarkarsu dare da rana kuma Adilai ne ko shakka babu 2. Akwai kuma akasin kashi na farko , Waɗanda zama da Annabi (saww) bai amfana musu komai ba , saboda rashin Imaninsu da shi Imani na haƙiƙa da taimakon sa da riƙe alƙawari a bayan sa , bari ma sun cutar da shi cutarwar da ba'a yiwa wani abun halitta kamarta ba a cikin halitta . Duk inda kaji suka ko allawadai da sashin wasu Sahabbai a cikin Alkur'ani mai girma to dasu ake , irin su ne aka rawaito Annabi (saww) yace : A cikin Sahabbai na akwai munafukai goma sha biyu na za su shiga Aljanna ba , irin su ne suka dinga shirya kashe Manzon Allah (saww) lokaci bayan lokaci har a ƙarshen rayuwar sa , irinsu ne suka assasa cutar da iyalansa a bayansa har aka kai ga halin da ake ciki a yau , irin su ne irin su ..... Tarihi ya sajjala ayyukan su da halayen su . Ahmadu ɗan Hambali ya rawaito a cikin Musnad , Manzon Allah (saww) ya ce : A cikin Sahabbai na akwai wanda bazai ƙara gani na ba har Abada . ma'ana dai daga ƙabarinsa sai wutar Jahannama. A ruwayoyin Bukhari da Muslim kuwa , Akwai wadanda sai anzo dasu Annabi (saww) ya gansu a ranar Alkiyama sai kuma a korasu Wuta , har ya dinga ya Ubangiji Sahabbaina ne Sahabbaina ne , Sai ace ai sun sauya a bayanka. 3 . Akwai kuma Waɗanda Allah da Manzonsa ne kawai suka san halinsu a Duniya da lahira , suna cikin kashin farko ne ko na biyu ? Tarihi bai hakaito wani abu akansu a rarrabe ba ballantana ayi naƙadin rayuwarsu , koma sam ba'a san sunansu da halayensu ba . Domin gabaƙi ɗaya Sahabban da aka yi Tarjamarsu a littattafan Tarajimu basu ne Jumlar Sahabban Manzon Allah (saww) . Shi yasa akwai abun mamaki tattare da masu yiwa Sahabbai Kuɗin goro da Adala da Imani na gaskiya , ta yanda suke yin hukunci akan abinda basu san shi ba basu san halinsa ba , wato dai suna yin hukunci akan Majhuli . Uwa uba ma yadda suke sabawa hankali , Ayoyin Alkur'ani, Hadisai , Waƙi'i da Sirar Sahabban Kansu a cikin hakan . A taƙaice dai ƴan Shi'a suna rarrabe hukunci da matsayar su dangane da Sahabban Manzon Allah (saww) , matsayarsu matsayar Alkur'ani da Sunnah ce game da Sahabbai , basu gaza ba a cikin haƙƙin su kuma basu wuce gona da iri ba kamar yanda wasu suka yi , Basu yadda da ƙa'idar "Kullhum Uduulun ba" Kuma ba sa

Ghadir sirrin haɗin kai الملتقى العلمائي برعاية مركز الجنوب الثقافي الإسلامي

RANAR DA MANZON ALLAH (SAWW) YA FITO YIN MUBAHALA DA KIRISTOCIN NAJRAN TANA NUFIN : 1 . Duk Duniya Manzon Allah (saww) bashi da tamkar waɗanda ya fito dasu wato Imam Ali , Sayyida Faɗima da ƴaƴanta Hasanain (a.s) , domin da yana da kamar su bayansu da ya fito da su a wannan rana . 2 . Wannan rana tana nufin babu waɗanda Annabi (saww) yake ƙauna kamar su inda da akwai shi da anga ya kirawo shi , domin babu ma'anar ya zama akwai wanda yafi su ko yake sama dasu a matsayi gunsa amma ya barshi a gida , saboda zuwa da abinda mutum bai da kamarsa ke nuna yana kan gaskiya akan abinda ya fito ayi muguwar addu'a akansa , ma'ana dai da ace akwai wanda suka fi su Imam Ali da Sayyida Zahra (a.s) a wurin Annabi (saww) kuma yaƙi fito da su da hakan ya nuna ba da gaske yake ba. 3 . Zuwan da Manzon Allah (saww) yayi da ƴaƴan ɗakinsa ya nuna gaskiyar Annabcinsa wanda hakan yasa Kiristocin Najran duka janye ƙudirun su daga ƙarshe suka nemi sulhu da Annabi (saww) domin da ace bai da hujja akan gaskiyar Addinin da yake kai da bai zai zo da su Imam Ali (a.s) ba sai dai aga yazo da wasu daga Sahabbansa ko Matansa da sauran Musulmi ko wasu bare can . 4 . Abinda ya faru a wannan rana ya nuna Imam Ali (a.s) ya kai ƙololuwar matsayi da falala da girma kuma babu wani mutum da ya kai shi daraja bayan Manzon Allah (saww) domin Nassin Alƙur'ani cikin ayar Mubahala ya tabbatar da shi Nafsun Manzon Allah (saww) ne ; فَمَنْ حَاجَّكَ فِيهِ مِن بَعْدِ مَا جَاءَكَ مِنَ الْعِلْمِ فَقُلْ تَعَالَوْا نَدْعُ أَبْنَاءَنَا وَأَبْنَاءَكُمْ وَنِسَاءَنَا وَنِسَاءَكُمْ وَأَنفُسَنَا وَأَنفُسَكُمْ ثُمَّ نَبْتَهِلْ فَنَجْعَل لَّعْنَتَ اللهِ عَلَى الْكَاذِبِينَ (آل عمران/٦١). Imam Ali (a.s) shi Annabi (saww) ya fito dashi a matsayin kansa da ransa , kenan idan ba Annabi (saww) babu wanda zai zama tamkar Annabi (saww) a faɗin Duniya tamkar Imam Ali (a.s) . 5 . Shi yasa Mubahala tana cikin dalilan da suke nuna Khalifancin Imam Ali (a.s) da Imamancin sa bayan Annabi (saww) , domin Annabi shine Imami kuma Khalifan Allah a sanda yake nan idan kuma babu shi babu wanda ya cancanci wannan matsayin sai wanda ya zama Nafsunsa (Ransa) wato Imam Ali (a.s) da zuriyarsa . 6 . Wannan Mubahala tana daga dalilan da suke tabbatar da kasancewar Imam Hasan da Husain (a.s) a matsayin ƴaƴan Annabi (saww) ne na haƙiƙa ba ƴaƴan kara ba , domin Allah cewa yayi ; Ya Rasulallahi kace mu kira ƴaƴanmu kuma ku kira ƴaƴanku نَدْعُ أَبْنَاءَنَا وَأَبْنَاءَكُمْ , shi yasa har wala yau Malaman da suka tafi akan ɗan mace ɗa ne na haƙiƙa a wajen kakansa na wajen uwa suke kafa hujja da Mubahalar Annabi (saww) ta kam wannan ayar kamar yanda za muyi nuni a bayanin mas'alar shariftar ɗan mace nan gaba In sha Allah. A taƙaice dai ranar Mubahala da wannan ayar suna nuni da wanni matsayi na musamman ga Ahlul Baiti (a.s) babu wani da yayi tarayya dasu cikinsa a kaf wannan al'uma kuma rana ce daga ranaku mafiya girma a tarihin Musulunci , domin a cikinta ne aka yanke tambabar duk wani mai tambaba akan gaskiyar Annabcin Annabi Muhammad (saww) kuma ƙarya ta bayyana kowa ya santa . Tarihi ya nuna fitowa domin wannan Mubahala ya wakana ne a rana mai kamar yau 24 ga watan Zulhijjah ɗin shekara ta goma bayan hijira a garin Madina mai alfarma , ma'ana a ƙarshe-ƙarshen rayuwar Annabi (saww). ✍️Khadimu A'atabi Ãli Muhammad Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 24 / Zulhijjah / 1445H - 1/ 7 / 2024 Miladiyya.

Wannan idan an kau da kai daga rikita-rikitar da take cikin wasu zikirai da tawassulan ɗarika kenan ! 5 . Sannan Shi'a suna da zikirai da manhaji na ibada da duk abinda mutum yake bukata a ɓangaren suluki da gyaran ruhi fiye da kowa ba alfahari ba ! To yaushe mutum ya gama da Mafatihul Jinan da sauran kundaye manya na gyaran zuciya da rai har yake tunanin rakito wani ko haɗawa da wasu daban !? Shin ba zai shiga cikin babin rinjiyar da abinda aka rinjaya tare da cikar abinda yafi rinjaye ba ? Matukar mutum yayi imani da cikar Ahlul Baiti (A.S) da girmama falalar duk abinda ya tabbata daga garesu a addini me yasa ba zai wadatu da wannan ba ? Shin hakan ba ya lazimta tufka da warware? Kamar fa mutum ne ana raba zinare , daimon, biliyoyin daloli da kyautuka ne kece raini a gidansu sai a ganshi a gidan maƙwabtansu yana barar a taimaka masa shi mabuƙaci ne ba shi da yanda zai yi ! ✍️ Khãdimul AshrãfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 23 / Zhul Hijja / 1447H - 9 / 6 / 2026 Miladiyya.

SHIN IYA ZIKIRAI DA ADDU'OI NE A CIKIN ƊARIƘAR SUFAYE ? 1 . Tabbas idan mutum yana sauraren masu kira zuwa ga ɗariƙa ko masu da'awar yiwuwar haɗata da Shi'anci za kaji suna cewa : Ai ita ɗarika ba komai bace face karanta zikirai da addu'oi (Istigfari , hailala da salati) , to amma abin tambaya su kaɗai ne ma'anar yin ɗariƙa a haƙiƙa ko akwai wani abu bayan su ? Domin idan iya waɗannan ne hatta Bawahabiye ɗan dariƙa ne saboda yana da wasu zikirai da addu'oi na shi na musamman , kuma yana yin salatin Ibrahimiyya. Kamar ɗan Shi'a ne idan kaji yana ce maka Shi'anci shi ne bin Imamu Ali (A.S) da soyayyar Āhlul Baiti (A.S) wannan ba ya nuni da cewa iya wannan ne Shi'anci tayu yana faɗa maka rukuni ne ko tushe. 2 . To yana da kyau mu fahimci shi salon da'awa (kira) a kowacce al'uma da aƙida yana da maƙamai da yanda ake yinsa , kuma abu ne da yake sananne hatta a wajen malaman fannin magana da usulul fiƙhi cewa : Shi mai da'awa akwai sanda yake kasancewa a muƙamin ihmali (Kau da kai) a kan wasu abubuwa da yake ƙudircewa a sanda yake kiran mutane a ciki da matakin shar'antawa , ba komai yake faɗa ba saboda ba wannan bane manufarsa , yana maƙamin assasawa ne da shar'anta asalin tafarkinsa , don haka zai dunƙule magana ne , kuma ko a magana hakan na faruwa , za mu ga sanda Alƙur'ani yake bayyana mana batun halascin cin abinda dabbar farauta - misali - ta kamo ba zai yi magana a kan shi hukuncin wurin da dabbar ta cafka ba saboda ba wannan bane muƙamin bayanin hakan. To haka shima in kaga mai magana ko kira zuwa ga dariƙa ko yana ce maka hanyar mu itace Istigfari, hailala da salati, hakan ba ya nuna iya shikkenan ba wani abu da yake raka wannan domin shi kan shi zikiran suna da sharaɗai na musamman da kaifiyya keɓantacciya amma in banda haka Bawahabiye ma ɗan dariƙa ne da wata ma'anar. Haka ɗan Shi'a idan kaji yana cewa Shi'anci shi ne walaya Imam Ali (A.S) , hakan ba ya nuna babu wasu aƙidu ko hukunce-hukunce ko suluki na aiki a Shi'anci . 3 . Don haka dariƙa kowacce iri ce hanya ce daga cikin hanyoyin sufanci da sufi ko mai ƙoƙarin zama sufi da arifi yake bi , shi kuma sufancin gaba ɗaya ba iya zikirai bane , akwai wasu aƙidu (abinda da ake ƙudircewa a zuciya) ayyuka ,zikirai da addu'oi da kuma wasu abubuwan da ake azamar lazimtarsu a aiki da tarbiyya kamar sharaɗai da ladubai kuma duk suna da alaƙa da ƙudiri da tunani. Abinda yake faruwa yanzu na dambarwa a kan Imam Mahdi (A.J.T.F) ya isa ya tabbatar maka ƴan dariƙa sun ginu a kan aƙidu da nazariyyoyi , bugu da ƙari idan kana karanta litattafan aƙidu za kaga ana kawo ra'ayoyin sufaye da ƴan ɗariƙa a kan wasu abubuwa , kuma suna da gingima-gingiman littattafai masu yawa da suka shafi nazariyyoyinsu a kan kowanne ɓangare na addini , kamar yanda suna da ra'ayoyi a kan abinda ya shafi nazariyyar ma'arifa ta tsarin halitta da rayuwa kamar wahdatul wujudi. Na'am , tayu ace su ba aƙida bane mai zaman kanta idan aka kalli babin aƙidun tushe da ake da rabe-rabe , amma kuma haka ba ya nufin ba su da aƙidun reshe , domin aƙidu kala biyu ne akwai asali akwai tushe , ko manya da ƙanana. 4 . Sannan idan an ɗauka ɗariƙa iya zikirai da addu'oi ne , to ita kebantacciyar kaifiyya da sharaɗan yin wannan wuridai da zikiran da lazimtar yinsu da idan mutum bai yi ba sai ya rama ko abu kaza da kaza na fiƙhun ɗariƙa ..... Abu ne da an shiga babin fiƙhu da shari'a da ake neman tabbatar da hakan da isnadi ko dalilai keɓantattu daga Alƙur'ani da Sunnah , wanda babu wannan dalilan na musamman face Shehu wane yace ko Shehu wane ya sadu da Annabi (Saww) bashi yace a dinga yi da wannan salo , ko an yiwa Shehu wane kashafi ko yayi mafarki , kuma hakan ba a lura da shi a tafarkin ƴan Shari'a, bari ma shubhar shar'anta abinda babu shi a addini tana iya shigowa kuma haramun ne da laifi mai girma. Na'am , ba laifi bane mutum ya ɗau wani zikiri ko addu'a da bata saɓawa Shari'a ba ya karanta amma kuma ba da ma'anar ya maida shi alƙawarin wani Shehi da tafarki ba , hakan yana buƙatar dalili ta fuskar Shari'a.

Wannan idan an kau da kai daga rikita-rikitar da take cikin wasu zikirai da tawassulan ɗarika kenan ! 5 . Sannan Shi'a suna da zikirai da manhaji na ibada da duk abinda mutum yake bukata a ɓangaren suluki da gyaran ruhi fiye da kowa ba alfahari ba ! To yaushe mutum ya gama da Mafatihul Jinan da sauran kundaye manya na gyaran zuciya da rai har yake tunanin rakito wani ko haɗawa da wasu daban !? Shin ba zai shiga cikin babin rinjiyar da abinda aka rinjaya tare da cikar abinda yafi rinjaye ba ? Matukar mutum yayi imani da cikar Ahlul Baiti (A.S) da girmama falalar duk abinda ya tabbata daga garesu a addini me yasa ba zai wadatu da wannan ba ? Shin hakan ba ya lazimta tufka da warware? Kamar fa mutum ne ana raba zinare , daimon, biliyoyin daloli da kyautuka ne kece raini a gidansu sai a ganshi a gidan maƙwabtansu yana barar a taimaka masa shi mabuƙaci ne ba shi da yanda zai yi ! ✍️ Khãdimul AshrãfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 23 / Zhul Hijja / 1447H - 9 / 6 / 2026 Miladiyya.

SHIN IYA ZIKIRAI DA ADDU'OI NE A CIKIN ƊARIƘAR SUFAYE ? 1 . Tabbas idan mutum yana sauraren masu kira zuwa ga ɗariƙa ko masu da'awar yiwuwar haɗata da Shi'anci za kaji suna cewa : Ai ita ɗarika ba komai bace face karanta zikirai da addu'oi (Istigfari , hailala da salati) , to amma abin tambaya su kaɗai ne ma'anar yin ɗariƙa a haƙiƙa ko akwai wani abu bayan su ? Domin idan iya waɗannan ne hatta Bawahabiye ɗan dariƙa ne saboda yana da wasu zikirai da addu'oi na shi na musamman , kuma yana yin salatin Ibrahimiyya. Kamar ɗan Shi'a ne idan kaji yana ce maka Shi'anci shi ne bin Imamu Ali (A.S) da soyayyar Āhlul Baiti (A.S) wannan ba ya nuni da cewa iya wannan ne Shi'anci tayu yana faɗa maka rukuni ne ko tushe. 2 . To yana da kyau mu fahimci shi salon da'awa (kira) a kowacce al'uma da aƙida yana da maƙamai da yanda ake yinsa , kuma abu ne da yake sananne hatta a wajen malaman fannin magana da usulul fiƙhi cewa : Shi mai da'awa akwai sanda yake kasancewa a muƙamin ihmali (Kau da kai) a kan wasu abubuwa da yake ƙudircewa a sanda yake kiran mutane a ciki da matakin shar'antawa , ba komai yake faɗa ba saboda ba wannan bane manufarsa , yana maƙamin assasawa ne da shar'anta asalin tafarkinsa , don haka zai dunƙule magana ne , kuma ko a magana hakan na faruwa , za mu ga sanda Alƙur'ani yake bayyana mana batun halascin cin abinda dabbar farauta - misali - ta kamo ba zai yi magana a kan shi hukuncin wurin da dabbar ta cafka ba saboda ba wannan bane muƙamin bayanin hakan. To haka shima in kaga mai magana ko kira zuwa ga dariƙa ko yana ce maka hanyar mu itace Istigfari, hailala da salati, hakan ba ya nuna iya shikkenan ba wani abu da yake raka wannan domin shi kan shi zikiran suna da sharaɗai na musamman da kaifiyya keɓantacciya amma in banda haka Bawahabiye ma ɗan dariƙa ne da wata ma'anar. Haka ɗan Shi'a idan kaji yana cewa Shi'anci shi ne walaya Imam Ali (A.S) , hakan ba ya nuna babu wasu aƙidu ko hukunce-hukunce ko suluki na aiki a Shi'anci . 3 . Don haka dariƙa kowacce iri ce hanya ce daga cikin hanyoyin sufanci da sufi ko mai ƙoƙarin zama sufi da arifi yake bi , shi kuma sufancin gaba ɗaya ba iya zikirai bane , akwai wasu aƙidu (abinda da ake ƙudircewa a zuciya) ayyuka ,zikirai da addu'oi da kuma wasu abubuwan da ake azamar lazimtarsu a aiki da tarbiyya kamar sharaɗai da ladubai kuma duk suna da alaƙa da ƙudiri da tunani. Abinda yake faruwa yanzu na dambarwa a kan Imam Mahdi (A.J.T.F) ya isa ya tabbatar maka ƴan dariƙa sun ginu a kan aƙidu da nazariyyoyi , bugu da ƙari idan kana karanta litattafan aƙidu za kaga ana kawo ra'ayoyin sufaye da ƴan ɗariƙa a kan wasu abubuwa , kuma suna da gingima-gingiman littattafai masu yawa da suka shafi nazariyyoyinsu a kan kowanne ɓangare na addini , kamar yanda suna da ra'ayoyi a kan abinda ya shafi nazariyyar ma'arifa ta tsarin halitta da rayuwa kamar wahdatul wujudi. Na'am , tayu ace su ba aƙida bane mai zaman kanta idan aka kalli babin aƙidun tushe da ake da rabe-rabe , amma kuma haka ba ya nufin ba su da aƙidun reshe , domin aƙidu kala biyu ne akwai asali akwai tushe , ko manya da ƙanana. 4 . Sannan idan an ɗauka ɗariƙa iya zikirai da addu'oi ne , to ita kebantacciyar kaifiyya da sharaɗan yin wannan wuridai da zikiran da lazimtar yinsu da idan mutum bai yi ba sai ya rama ko abu kaza da kaza na fiƙhun ɗariƙa ..... Abu ne da an shiga babin fiƙhu da shari'a da ake neman tabbatar da hakan da isnadi ko dalilai keɓantattu daga Alƙur'ani da Sunnah , wanda babu wannan dalilan na musamman face Shehu wane yace ko Shehu wane ya sadu da Annabi (Saww) bashi yace a dinga yi da wannan salo , ko an yiwa Shehu wane kashafi ko yayi mafarki , kuma hakan ba a lura da shi a tafarkin ƴan Shari'a, bari ma shubhar shar'anta abinda babu shi a addini tana iya shigowa kuma haramun ne da laifi mai girma. Na'am , ba laifi bane mutum ya ɗau wani zikiri ko addu'a da bata saɓawa Shari'a ba ya karanta amma kuma ba da ma'anar ya maida shi alƙawarin wani Shehi da tafarki ba , hakan yana buƙatar dalili ta fuskar Shari'a.

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗 - Estadísticas y analítica del canal de Telegram @tafarkintsiratv