es
Feedback
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

Ir al canal en Telegram

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

Mostrar más
2 404
Suscriptores
-124 horas
-17 días
+10030 días

Carga de datos en curso...

Nube de Etiquetas
Sin datos
¿Algún problema? Por favor, actualice la página o contacte a nuestro gerente de soporte.
Menciones Entrantes y Salientes
---
---
---
---
---
---
Atraer Suscriptores
septiembre '26
septiembre '26
+3
en 0 canales
agosto '26
+141
en 0 canales
Get PRO
julio '26
+43
en 0 canales
Get PRO
junio '26
+61
en 0 canales
Get PRO
mayo '26
+38
en 0 canales
Get PRO
abril '26
+16
en 0 canales
Get PRO
marzo '26
+18
en 0 canales
Get PRO
febrero '26
+36
en 0 canales
Get PRO
enero '26
+15
en 0 canales
Get PRO
diciembre '25
+40
en 0 canales
Get PRO
noviembre '25
+44
en 0 canales
Get PRO
octubre '25
+29
en 0 canales
Get PRO
septiembre '25
+33
en 0 canales
Get PRO
agosto '25
+24
en 0 canales
Get PRO
julio '25
+60
en 0 canales
Get PRO
junio '25
+33
en 0 canales
Get PRO
mayo '25
+66
en 0 canales
Get PRO
abril '25
+43
en 0 canales
Get PRO
marzo '25
+60
en 0 canales
Get PRO
febrero '25
+110
en 0 canales
Get PRO
enero '25
+40
en 0 canales
Get PRO
diciembre '24
+68
en 0 canales
Get PRO
noviembre '24
+172
en 0 canales
Get PRO
octubre '24
+185
en 0 canales
Get PRO
septiembre '24
+136
en 0 canales
Get PRO
agosto '24
+184
en 0 canales
Get PRO
julio '24
+72
en 0 canales
Get PRO
junio '24
+49
en 0 canales
Get PRO
mayo '24
+54
en 0 canales
Get PRO
abril '24
+52
en 0 canales
Get PRO
marzo '24
+92
en 0 canales
Get PRO
febrero '24
+68
en 0 canales
Get PRO
enero '24
+59
en 0 canales
Get PRO
diciembre '23
+51
en 0 canales
Get PRO
noviembre '23
+44
en 0 canales
Get PRO
octubre '23
+55
en 0 canales
Get PRO
septiembre '23
+54
en 0 canales
Get PRO
agosto '23
+23
en 0 canales
Get PRO
julio '23
+59
en 0 canales
Get PRO
junio '23
+62
en 0 canales
Get PRO
mayo '23
+28
en 0 canales
Get PRO
abril '23
+33
en 0 canales
Get PRO
marzo '23
+58
en 0 canales
Get PRO
febrero '23
+49
en 0 canales
Get PRO
enero '23
+42
en 0 canales
Get PRO
diciembre '22
+39
en 0 canales
Get PRO
noviembre '22
+20
en 0 canales
Get PRO
octubre '22
+24
en 0 canales
Get PRO
septiembre '22
+7
en 0 canales
Get PRO
agosto '22
+16
en 0 canales
Get PRO
julio '22
+14
en 0 canales
Get PRO
junio '22
+37
en 0 canales
Get PRO
mayo '22
+52
en 0 canales
Get PRO
abril '22
+527
en 0 canales
Fecha
Crecimiento de Suscriptores
Menciones
Canales
06 septiembre0
05 septiembre0
04 septiembre0
03 septiembre+1
02 septiembre+1
01 septiembre+1
Publicaciones del Canal
To ina kuma ga wanda yafi kowa daraja da girma Manzon Allah (sawa) , wanda zuwansa ne ya haskaka duniya da zuƙata , ya tseratar da halitta daga halakar duniya da lahira , in ba'a yi Maulidin godiya a ranar da yazo ba me kuwa za'a yi ???? Zan cigaba Insha Allahu Ta'ala....... https://t.me/tafarkintsiratv ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 21/Rabi'ul Auwal/1444H - 18/10/2022

2
A hankalce da wurin masu hankali abune mummuna kuma aibune wani yayi maka wata ni'ima amma kaƙi gode masa , ko ka ƙi nuna farinci da hakan . Shi yasa in masu Maulidi suka zargi ɗan ƙungiya ko suka tuhumi son Annabinsa kar ya zargi kowa ya zargi kansa , saboda shine ya saɓawa zaunanniyar ƙa'idar hankali da take wajabta masa yin Mauludin, ita ko zaunanniyar dokar hankali da masu hankali ba masu saɓa mata sai masu rangwamen hankali da tunani , ko wanda yake da shubha ko taurin kai da kangarewa . MA'ANAR GODIYA Godiya shine yin (i'itirafi) yarda da ni'imar wanda yayi ni'ima tare da girmamashi . Kuma baya wadatuwa da yarda da cewa ai wane yayi min ni'ima, a'a muhallin godiya wuri uku ne , akwai Zuciya wanda anan ake yarda da ita ni'imar , sannan harshe domin yin hamdala da bayyana yarda da ni'imar , sai kuma gaɓobi da suke taimakawa zuciyar da harshen wajen bayyana godiyar da tabbatar da ita , wannan itace cikakkiyar godiya . wasu kuma suka ce ; Rukunan godiya bisa ni'ima guda biyar ne , Risinawa da girmamawar mai godiya ga abun godewar , nuna masa ƙauna da soyayya, da yarda da cewa tabbas ya yi ni'ima , sannan kuma kar ya aikata abinda abun godewar nasa bayaso . Wallahi ko makiyin masu Maulidi yasan waɗannan abubuwan ake yi a wurin Maulidi , ana aikata waɗannan rukunai na godiya ne ga Allah Ta'ala, bisa ni'imar da yayi ta samuwar farin jakada Annabi Muhammad (sawa) . Haka nan dole ya zama mutum ya nuna godiyar abisa ni'ima gwargwadon ni'imar da akayi masa , ko da mutum ne ya yi maka wata hidima ko kyauta dole godiyarka ta zama tayi daidai da abinda ya maka , shi yasa aka rawaito daga Manzon Allah (sawa ) cewa ; إن الله جعل قلوب عباده على حب من أحسن إليها وبغض من أساء إليها Ma'ana : Allah ya sanya zuƙatan bayinsa abisa son wanda ya kyautata musu , da ƙin wanda ya munana musu . A wata ruwayar kuma da mai ɗakinsa A'isha bintu Abi Bakr ta tambayeshi , game da yanda yake ƙara zage damtse da matsawa kansa wajen yin ibada , duk da cewa an gafarta masa abinda ya gabata da wanda ya jinkirta , sai Manzon Allah (saww) yace mata ; ya ke A'isha shin bazan kasance bawa mai yawan godiya ba (أفلا أكون عبداً شكوراً) ? A wata ruwayar kuma Imam Ali (a.s) yana cewa ; (الإنسان عبد الإحسان) shi mutum bawan kyautatawa ne , wannan magana ce mai fadi da take buƙatar sharhi . Dukkan waɗannan hadisai suna ƙarfafa wannan ƙai'dar ta hankali da muka ambata . Shin muma ba zamu kasance bayi masu yawan godiya , bisa ni'imar da Allah yayi mana ta bamu Manzon Allah (saww) ? KOMAWA FARKO ..... Ta wata fuskar za mu iya cewa : a asali ma Maulidin Annabi (saww) ya wadatu da ace wai yana buƙatar sai an kawo wasu dalilai akan halascin yinsa , domin a wujdaani da lamiri na kowanne mutum zai ji cewa Maulidi baya buƙatar hakan . Yanzu da za'a ce kuna zaune a wani gari a dokar daji , kuna cikin ƙangin rayuwa , talauci , yunwa , wahala , ƙishirwa , annoba , rashin lafiya , duhun jahilci da sauransu ....Kwatsam sai aka ce wani mutum mai daraja yazo rana guda ya kuɓutar daku daga wannan yanayi , ya samar muku da ƴantacciyar rayuwa , ya raya garinku ya zama wani babban birni , ya maidaku mutane mafiya izza da iko a duniya bayan ƙaskanci , a take za kuji zuciya da lamirinku suna motsaku ga nuna duk wani nau'i na farin ciki da godiya , kuma a wannan lokacin ba za ma ku tsaya tunani ko tambayar wai menene dalili ko hujjar da za ta sa kuka yi murna da godiya ba ! Me yasa saboda asalin ɗabi'arku da fiɗirarku anyitane a hakan , don haka (Automatically) za ku yi farin ciki da godiya ta ko wacce hanya ba tare da kun tsaya sauraren dalili ko hujja ba , kamar yanda in kuna jin ƙishirwa ko yunwa bakwa buƙatar dalilin da zai sa ku nemi abinci ko ruwa , to haka shima Maulidi ba ka buƙatar hakan a fiɗirance . Ita kanta ranar da mutumin nan yazo ya kuɓutar daku daga ƙangin da kuke ciki dole ta kasance rana ta musamman gareku , in har da kuna ganin ƙima da darajar wannan mutumi mai daraja da ya ceceku .
51
3
HUJJOJI DA DALILAN YIN MAULIDI (01)...... Yana daga cikin abun mamakan zamani ace wai akwai wani mai amsa sunan Musulmi da yake inkarin asalin halascin Maulidin Manzon Allah (sawa) ! Ace har akwai wani mai amsa sunan Musulmi da yake ganin Maulidi a matsayin wani mummunan abu , Bidi'a, saɓawa Shari'a, har takai ga yin ƙazafi da ƙage ga masu yin Maulidin Annabi (sawa) , wai suna iskanci (Wal'izabillah) ..... A tare da haka za kaji suna cewa a basu hujjojin Maulidi , ai ba'a isa a kawo Aya ko Hadisi da suke tabbatar da halasci ko tabbatar da maulidi a matsayin Ibada . Malamai sukance rashin sanin abu ko ganinsa ba shi ke tabbatar da babu shi ba , dan baƙo yaje gari bai ga gidan sarki ba hakan baya nuna babu sarki a garin , za tayu a ƙofar gidan Sarkin ya kwana amma rashin sani yasashi jahiltar hakan , haka suma masu ja da al'amarin Maulidi, ko musa dalilin yinsa rashi sani yakan sa su yi inkari , duk da wani lokacin akwai nau'i na ƙeƙashewar zuciya da son zuciya da taurin kai . Tabbas anyi rubuce-rubuce da raddoji da munazarori akan Maulidi tun shekaru aru-aru, kuma ba'a gushe ba ana basu gamsasshiyar amsa akan wannan mas'alar, to amma abunka da munkiri ! Kuma komai akai da aura sai yaci kara, basu gushe ba suna suna haushin a basu dalili ko hujjar Maulidi! Wannan rubutu zai maida hankali wajen rairayo wasu daga cikin muhimman dalilai da hujjojin yin Maulidi, shiryarwa ga waɗanda ya zama akwai sauran hasken fahimtar gaskiya a tare dasu daga waɗannan mutane , a lokaci kuma amsa ga wasu dayawa da suka nemi in ɗan yi rubutu game da wannan maudu'i ko a taƙaice ne , sai dai ayi haƙuri da ɗan tsawaitawa kaɗan . Zamu kasa dalilai da hujjojin kashi uku ne , kashi na farko dalilai ne na hankali duk da su basa aiki da hankali basu ma sanshi ba , kashi na biyu da na uku kuma daga Alkur'ani da Hadisai ne . KASHI NA FARKO Daga cikin dalilai da hujjojin hankali da suke tabbatar da asalin Maulidi , wanda duk mutum mai lafiyayyen hankali in ya tsaya tsam yayi tunani , zai fahimci cewa Maulidi bama iya halasta yayi bane , a'a , wajibi a hankalice muyi murnar samuwar Annabi (saww) , ƙarƙashin zaunanniyar Ƙa'idar nan da ake mata take da (وجوب شكر المنعم ) ma'ana; Wajabcin godewa wanda yayi maka wata ni'ima. Babu shakka hankali yana yin hukunci da lalurar yin godiya ga duk wani da ya yi maka wata ni'ima . A hankalce duk wanda ya baka wata kyauta komi ƙankantarta ko tsadarta , musamman ace yayi maka kyautar ba zata ko ta ƙure maneji a sanda kake tsananin buƙata , to ya zama wajibi ka gode masa bisa wannan kyauta ko ni'imar da yayi maka . Tom , ina kuma ga ace an maka kyauta da ni'ima da abinda yafi komai tsada da daraja a duniya da lahira , wato Manzon Allah (saww) , shin har akwai wata kyauta ko ni'ima da za'a baka a matsayinka na Musulmi da ta kai Manzon Allah (saww) ? Yanzu da za'a baka dala tiriliyan dubu da duk wata ni'ima ta zahiri da rayuwar yau da gobe, kana buƙatar ace kayi godiya ga wanda ya baka Waɗannan abubuwa ? Yau in akwai wani abu da kake matukar buƙatarsa a rayuwa in akace ga wani da yayi maka silar samunsa kana buƙatar ace sai kayi farin ciki da godiya bisa samunsa ? To shima haka Maudlin Manzon Allah (sawa) wani nau'i ne na Godiya ga Allah Ta'ala, bisa babbar ni'ima da kyautar da yayi mana , ni'ima da kyautar da babu kamarta ta samuwar rahama ga talikai baki ɗaya . A tare da haka har kana jin cewa taron yin godiya ga Allah bisa wannan ni'imar bidi'a ne ? Ko bai da asali ? Ko iskanci ne ? Bayan ga hankalinka yana faɗa maka ka nuna duk wani nau'i na farin ciki gwargwadon iyawakarka , wajen yin godiya ga Allah abisa wannan ni'imar , amma ka saɓawa hankalinka . in ma ba za kayi taka godiyar ta hanyar yin taron Maulidi ba , ai bai kamata ace kuma ka zama mai yiwa wani inkari ba , dan shi yayi tashi godiyar ta hanyar Mauludi .
41
4
MAULUDI TSAKANIN MASU YAƘARSA DA SUNAN KARE ADDINI DA MASU AMFANI DA SUNANSHI WAJEN ƁARNA DA KAUCE HANYA !!? 1 . Kuskure ne babba dan kana faɗa da Mauludi ko baka da ra'ayin sa ka dinga ɗakko bidiyoyi da hotunan wasu marasa ɗa'a da tarbiyya da suke amfani da zagayen Mauludi wajen ɓarna da raye-rayen banza da kaɗe-kaɗe na wuce gona da iri da sunan Mauludi da son Annabi (saww) , tabbas hakan da suke yi ba tarbiyyar Mauludi bace kuma karantarwar Musulunci ba ce, kamar yanda yada abinda suke yi yaɗa ɓarna da alfasha ne a ban ƙasa , ƙiyyarka da Mauludi ba shi ke baka dama ka dinga bibiyar wasu abubuwan banza da wawaye ke yi a wajen zagayen Mauludi ba . 2 . Masu yaɗa ɓarnar masu ɓarna da sunan Mauludi me yasa basa yaɗa alkhairai da abubuwan da ake yi a wajen Mauludi na daga karatun Alƙur'ani , tarihin Manzon Allah (saww) , wa'azozi da sauran abubuwa masu kyau da daɗi ?! Allah Ta'ala yana cewa : Kada gaba da ƙiyayyar wasu mutane tasa ku ƙi yi musu adalci .... ولا يجرمنّكم شنآن قوم على ألّا تعدلوا 3 . Ayyukan wauta da rashin dai-dai da wasu suke yi da sunan Mauludi ba ya taɓa zama dalili na rashin halascin yin Mauludi kamar yanda maƙiya Mauludi suke ƙoƙarin nunawa da yada ɓarnar da suke yi , domin zagayen Mauludi ba shi bane kawai Mauludi don haka dalilin su keɓantacce ne , Ko da zagayen Mauludi ko babu shi za a iya yin Mauludi domin ko a iya cikin gida mutum zai iya yin Mauludi shi da iyalan sa . Don haka kuskure da ɓarna da wasu jahilai suke yi da sunan Mauludi ba shi da maraba da barna da shakiyancin da wasu suke yi da sunan sallar tahajjudi da daddare , wata ƙila ma ɓarnar da ake yi da sunan Tahajjudi ba a yinta da sunan Mauludi , in har ɓarnar da ake yi da sunan zagayen Mauludi dalili ne haramta Mauludi to ɓarnar da ake da sunan Tahajjudi ma dalili ne na haramcin yin jami'in Tahajjudi da daddare , wanda babu wani da ya fahimci Shari'a da zai faɗi haka da sunan fatawa , don mutum ya zira hannu a hannun na kusa da shi yayi sata yayin jam'in sallah hakan baya nuna haramcin sallar jam'i a Masallaci , haka satar takalmi a masallaci bata zama dalilin haramcin zuwa Masallaci da sallah . 4 . Masu yaɗa irin waɗannan munanan abubuwan don su nuna haramcin Mauludi ya kamata su nemo wani Malamin Mauludi da yayi fatawa da halascin yin hakan ko ya nuna hakan shine Mauludi a sannan ne suke da bakin magana , Duk da hakan ma ba zai zama dalilin haramcin Mauludi ba . 5 . Tabbas dayawa suna fakewa da sunan zagayen Mauludi suna abubuwan da ba su kamata ba bisa sani ko rashin sani , wanda wannan nauyi ne akan Malamai da Jagororin wannan zagaye da masu kula da shi har masu fitar wajen tashi tsaye domin sa ido da kula akan balagurbi da kuma masu aikata abubuwan da suka saɓawa koyarwar Manzon Allah (saww) da sunan Mauludi ko soyayyar Shugaba (saww) , Allah ya aiko Annabi (saww) don ya shiryar da bayi ya gyara dabi'u da halayen su kuma da wannan ne zai yi alfahari da al'umar sa ba da wani abu ba . Allah ya rabamu da wuce gona da iri a cikin soyayya ko ƙiyayya. ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
71
5
YAUSHE AKA FARA BIKIN MAULIDI KUMA SUWAYE SUKA FARESHI ??? Abinda ya shahara a wurin malabarta tarihi cewa farkon wanda ya fara shirya bikin maulidi shine sarkin Irbil "Al-Muzaffar" wanda ya rasu shekara ta 630 bayan hijra , sannan sarakunan daular Faɗimiyyah ta Misra suka ƙayata shi dama wasu daga sarakuna da manyan mutane inda daga nan ne al'amarin maulidi ya yaɗu a tsakanin Musulmi suka karɓe shi hannu bibbiyu. Sai dai abinda nafi rinjayarwa bayan tahƙiƙi da bincike cewa ƴan Shi'a Imamiyya Ithna Ashariyya - Ayyadallahu Burhãnahum - sune farkon wanda suka fara raya al'amarin maulidi kuma suka yi shi , yana daga abinda yake tabbatar da hakan abinda Shehunmu Muhammad bin Muhammad bin Al-nu'uman wanda aka fi sani da Sheikh Al-Mufid ko Ibnul Mu'allim (413H) ya ambata a cikin littafinsa (Masãrush Shi'a shafi na 29) - shekara 136 kafin haihuwar Sarkin Irbil Muzaffar inda Shehun malamin yake cewa : "A ranar 17 ga watan (Rabi'ul Awwal) haihuwar shugabanmu jakadan Allah ta kasance yayin ketowar alfijir a shekarar Giwa , rana ce mai daraja da girman albarka kuma tuntuni nagartattu daga zuriyar Muhammadu basu gushe ba suna girmamata suna sanar da girmanta da kiyaye alfarmarta kuma suna azumtarta , an ruwaito daga limaman shiriya cewa : Wanda ya azumci ranar 17 ga watan Rabi'ul Awwal ranar haihuwar Annabi (saww) Allah zai rubuta masa ladan azumin shekara , kuma a wannan ranar an so yin sadaka , ziyarar wurare masu alfarma , aikata ayyukan alkhairai da farantawa ahlinsa". Haka nan a muƙaddimar littafin nan dai Sheikh Al-Mufid (R) yana cewa : Mutanen kirki daga wannan tawagar (Shi'a) - Allah ya karesu - a tsawon lokuta suna kulawa da waɗannan tarihohi saboda yin ibadu a lokutan tunawa da su , da yin ayyukan neman kusanci da yin abinda ya wajaba ayi na abinda aka ambata da tsaida iyakokin addini a lokacin farin ciki (kamar Mauludi) da baƙin ciki (kamar Ashura) . Don haka wannan magana ta Shehunmu Al-Mufid (R) ta muna yanda Shi'a da jagororinsu (a.s) suke raya al'amarin Mauludi dama juyayi tun ƙarnin farko na Muslunci shekaru ɗaruruwa kafin Sarki Muzaffar da daular ƴan Shi'a Fãɗimiyyah dake Misra su fara nasu . Na'am , za mu iya haɗa ra'ayoyin biyu muce ; Shi'a Imamiyya sune suka fara yin Maulidi da wani salo na musamman na su sannan shima Sarkin Irbil da Faɗimiyyawa suka zo suka yi na su da wani salo daban sai ya zama babu karo in an danganta fara Maulidi ga Shi'a ko da Sarkin Irbil . Irin hakan ne kamar yanda ya shahara a ƙasarmu Najeriya cewa ana yin maulidin Annabi (saww) tun zamanin Shehu ɗan Fodiyo dama kafin nan amma kuma za ka samu mutane da yawa suna cewa Shehu Tijjani Usman Z/bare-bari shine ya fara yin maulidi to anan ma babu tufka da warwara cikin maganganun biyu , domin Maulidin da ake yi a zamanonin baya kafin Shehu Tijjani Usman sun bambanta da irin salon maulidin da shi yazo da shi bayan dawowarsa daga ƙasar Sinigal a ziyararsa Shehu Ibrahim Nyass inda yaga yanda suke yin nasu a can sannan yayi shi a yankinmu har ya yaɗu ya zama shi aka fi sani da Mauludin Annabi (saww) , a kowanne hali dai falalar yin maulidi kowanne iri ne tana komawa ga Shi'a Imamiyyah da jagororinsu domin ance falala tana ga na farkon da ya fara abu "الفضل للمتقدّم". Sannan ayyana tarihin fara maulidi ba shi da wani muhimmaci sosai bayan tabbatuwar mustahabbancin yinsa a Shari'a, kai hatta ayyana tarihin ranar da aka haifi Annabi (saww) ba shi da tasiri wajen hana yin taron Maulidi in mun kau da kai ga mas'alar neman albarka da kuma wasu ayyukan lada da aka ruwaito ana so ayi a ranar . Wallãhul Musta'ãn. ✍️ Khaɗimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 2 / Rajabul Asab / 1446 - 3 / 1 / 2025 Miladiyya.
108
6
YAUSHE AKA HAIFI ANNABI (SAWW) ??? Duk ɓangarorin Musulmi da Malaman tarihi sun haɗu akan an haifi Annabi (saww) a shekarar Giwa ba tare da saɓani ba , sai dai anyi saɓani ne akan wane wata ko wace rana aka haifi Annabi (saww) , cikin taƙaita zance da mas'alar saɓanin shine : 1 . Mafi yawan Malaman Ahlussunnah Wal jama'a sun tafi akan cewa an haifi Annabi (saww) ranar Litinin 12 ga watan Rabi'ul Auwal a shekarar Giwa , duk da akwai wasu da suka saɓa hakan a cikin su da kuma ruwayoyin da suka ce , a ranar 8 ga watan ne aka haife shi , wasu suka ce 9 ne , wasu suka ce 10 ne , wasu suka ce 22 ne , wasu suka a ƙarshen watan ne , wasu ma suka ce a watan Ramadan ko Safar ko Rabi'ul Thani aka haifi Annabi (saww) , amma 12 ga watan Rabi'ul Auwal shine zance mafi shahara a wajen su , duk da a maƙamin tabbatar da haka akwai magana . 2 . Zance mafi shahara koma ace kusan wanda duk Malaman Shi'a suka tafi akan shi ( magabata , ƴan baya da na yanzu ) , shine an haifi Annabi (saww) ranar Juma'a 17 ga watan Rabi'ul a lokacin ketowar Alfijir, wannan shine abinda Shehun mu Almufid , Sheik Assaduƙ , Ibnu Ɗawus , Al-allamatul Majlisi da wasun su (Rahimahullah) suka ambata , a cikin "Bihar" ma Al-allamatul Majlisi yana cewa babu wanda ya saɓawa haka sai zance shazi . Na'am, a cikin Littafin Alkafi mai girma Shehun mu Muhammad bin Ya'aƙub Alkulaini (Rahimahullah) ya ambaci cewa a ranar 12 ga watan Rabi'ul Auwal ne aka haifi Annabi (saww) . Amma ba laifi shima abu ne mai kyau yin murna da farin ciki a wannan ranar dama sauran ranaku, kamar yanda ake raya duk watan wasu ma suke tarbar sa da raka shi da murna da farin ciki , tabbas Manzon Allah (saww) ya cancanci fiye da haka , Annabi (saww) ba abun iyakancewa bane da dare ko wuni ko shekara . Sayyid Ibnu Ɗawus yana cewa : Ya kamata girmama ranar haihuwar Annabi (saww) - 17 ga watan Rabi'ul Auwal - ta zama daidai da irin girmamawar da ake wa Annabi mai girma (saww). Lallai wannan magana ce mai girma da dake buƙatar tadabburi akan ta sosai . ME YASA SHI'A SUKA CE RANAR 17 GA WATA AKA HAIFI ANNABI (SAWW)? Abune sananne kuma tabbatacce a hankali da shari'a in ana so a san tarihin mutum musamman lokacin haihuwarsa ana komawa iyayen sa ko makusantan sa da jini da zumunci , ko waɗanda suka san shi , domin ko ba komai su suka fi kowa sanin sa da kusanci dashi , hakan ne yasa Shi'a suka dogara da zantukan makusantan Annabi (saww) da zuriyar sa , wato Ahlul Baiti (a.s) , sunyi bayanin cewa a ranar 17 ga Rabi'ul Auwal aka haifi Annabi (saww) , kuma dama a wajen su Annabi (saww) yace a karɓi Addini a bayan sa . Don haka wannan dalilin kaɗai ya isa ya rinjayar da ra'ayin Shi'a game da tarihin haihuwar Annabi (saww) . اللهم صلّ على من شرفت الصلاة بالصلاة عليه وعلى وآله الأطهار الأخيار . ✍️ hãdimul AshrãfAl-Abdul Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
121
7
ABINDA JAGORORIN GWAGWARMAYAR DUNIYA SUKA FAƊA A KAN AYATULLAHI SAYYID ALI SISTANI DA ƳAN SHI'AR IRAƘI FITA TA BAKWAI (07) Wannan jawabin yana ɗauke da wasu muhimman kalmomin jagororin gwagwarmayar wannan ƙarni a haƙƙin Ayatullahi Sayyid Ali Sistaniy (H) da kuma jinjinarsu ga ƴan Shi'ar Iraƙi , wanda haka yake rushe shubhar masu sukar Ayatullahi Sistani da sunan gwagwarmaya ko suke nuna bambanci tsakanin Shi'ancin Iraƙi da Iran. Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 15/ Rabi'ul Awwal / 1448H - 29 / 8 / 2026 M
175
8
Audio from العبد الفاني الكنوي
155
9
SHIN AYATULLAHI SISTANI NE YA SHIGO DA AMERIKAWA IRAƘI HAR YA BASU MAFAKA DA IKON ZAMA ??? FITA TA SHIDA (06) *Wannan jawabin yana ɗauke da amsoshi , fatawoyi da bayanan Sayyid Ali Sistaniy (H) a kan sha'anin Iraƙi tun bayan faɗuwar Gwamnatin Saddam L zuwa yau, duk cikin warware shubhohin masu sukarsa da zaginsa a zauren Nurul Haq* Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 👇👇👇👇👇👇 https://t.me/tafarkintsiratv 13/ Rabi'ul Awwal / 1448H - 25 / 8 / 2026 M
214
10
Audio from العبد الفاني الكنوي
199
11
*Amshoshin Sayyid Ali Sistaniy (H) daga ofishinsa a kan Amerika da siyasar iraƙi tun bayan faɗuwar Saddam (L) zuwa yau* *WARWARE SHUBHOHIN UWAR ƳAN NURUL HAƘƘI DA ƳAN KORENTA* *FITA TA BIYAR (05)* *Wannan jawabin yana ɗauke da amsoshi , fatawoyi da bayanan Sayyid Sistaniy a kan sha'anin Iraƙi tun bayan faduwar Gwamnatin Saddam zuwa yau* Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 11/ Rabi'ul Awwal / 1447H - 25 / 8 / 2026 M
301
12
Audio from العبد الفاني الكنوي
249
13
Daga cikin matan Manzon Allah (saww) Sayyida Khadija tafi kowacce samun matsayi mai girma da daraja a wurinsa, wasu ruwayoyin tarihi sun tabbatar da cewa ; Ya kasance a tsawon rayuwarsa yana ambatonta da alkhairi , yana mai tabbatar da matsayinta a cikin zuciyarsa maɗaukakiya , yana yabonta sannan baya ganin akwai wacce zata samu matsayinta a wajensa , ba ita ba har ƙawaye da makusantanta ya cigaba da kyautata musu a bayan rayuwarta saboda albarkacinta . Sayyida Khadijah ta kasance tare da Manzon Allah (saww) hannu da hannu , a cikin dukkan yanayin da ya shiga a takura da ƙuntatawa a farkon fara da'awar musulunci, ta bashi gudummawa da kariya da duk abinda ta mallaka , misalai da ƙissoshi sun yawaita akan haka . Ta kasance mai kyawawan da ɗabi'un girma da ɗaukaka , ma'abociyar sifofin kamala da cika (Radiyallahu anha) . ✍️Khadimul Itrah Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 10/Rabi'ul Auwal/1444H - 7/10/2022 https://t.me/tafarkintsiratv
292
14
AUREN MANZON ALLAH DA NANA KHADIJA (A.S.) 🌹 A ranar 10 ga watan Rabi'ul Awwal ɗin shekara ta 15 kafin aiko Annabi (28 kafin hijira) , aka ɗaura auren Manzon Allah Muhammad bin Abdullah (saww) , da Sayyida Khaidijatul Kubra bint Khuwailid (Radiyallahu anha) . Ruwayoyin Malaman Tarihi sunyi saɓani akan takameman shekarunsu -Musamman Sayyida Khadija- lokacin da aka yi auren . Auren Manzon Allah mai girma da Sayyida Khadija bint Khuweilid (a.s) mataki ne mai albarka, kuma lamari ne mai matuƙar muhimmanci a tarihin Musulunci; Ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar Annabi (s) kafin da kuma bayan aiko shi . Wannan aure - banda kasancewarsa aure mai albarka, wanda ya samar da zuriya mai albarka , ta yanda ya zama duk zuriyar Annabi daga tsatsonta suka fita - Aure ne da ya kasance cikin maslahar sakon Musulunci, domin karfafa shi da kareshi, Sayyida Khadija (S) ta kasance mai taimako da dafawa Manzon Allah (saww) , a cikin yanayi mafi tsanani da tsauri , kuma ta sadaukar duk Dukiyarta wajen ganin saƙon Musulunci ya cimma gaci,, kuma hakan ne ya tabbata , shi yasa aka rawaito daga Annabi (saww) ; Musulunci bai kafu ba sai da Dukiyar Khaidijatul Kubra da Takobin Ali bin Abi Ɗalib (a.s) . Wannan aure mai Albarka ya kasance samfurin kyawawan ɗabi'u , musamman ma gaskiyar zance da riƙon amana da kyawawan ɗabi'un da suka zama sune jigon yin wannan aure , domin kuwa ɗaya daga cikin riwayoyin auren kuma mafi shahara na cewa ; Sayyida Khadija bint Khuwailid ta kasance mace mai daraja da tarin dukiya , wacce takan yi haya ko sufurtar matane domin yin mu'amala ta kasuwanci daga dukiyarta , a lokacin da labarin Manzon Allah (saww) ya isketa , game da gaskiyarsa , amanarsa da karamcinsa, sai ta aika masa akan tana so ya tafi Sham (Siriya) domin yayi mata kasuwanci da Dukiyarta , za ta haɗashi tare da wani yaronta mai suna Maisarah. Bayan Manzon Allah (saww) ya yarda da hakan , sai ya tafi da Dukiyarta zuwa Sham , anan wani mai ibadar Addinin Kiristanci ya ganshi , sunansa "Nasɗur" sai ya shaidawa Maisarah (Yaron Nana Khadija ) cewa ; Wannan da kuke tare shine Annabin wannan al’umma . Daga nan Manzon Allah (saww) ya siyar da abinda ya tafi dashi kuma ya siyo abinda ake buƙata , sannan ya dawo garin Makkah ga Nana Khadija , ga Dukiyarta ga kuma riba mai tarin yawa , sannan Maisarah ya bata labarin abinda ya faru tsakaninsu da wannan mai ibadar da suka haɗu dashi . Daga nan ne Sayyida Khadijah ta aikawa Manzon Allah (saww) cewa ; Tana son ta aureshi , saboda alaƙar zumuntarta dashi , da darajarsa , amanarsa kyawawan halayensa , gaskiyarsa da ɗaukakar sha'aninsa . Sai Manzon Allah (saww) ya yarda da aurenta akan Uƙiya Goma sha biyu , watau Dirhami Arba'in . Tabbas akwai izna da abun lura a cikin wannan kyakkyawar ƙissa ta auren Manzon Allah (s) , duk da akwai wata riwayar bayan wannan , sai dai wannan ita tafi shahara a wajen Malaman Tarihi . Batun cewa Sayyida Khadija ta taɓa yin aure kafin ta auri Manzon Allah (saww) , mas'alace da aka yi saɓani da jidali akanta tsakanin malaman ɓangarorin Musulunci , Domin kuwa mafi yawan Malaman Ahlussunna Wal jama'a sun tafi akan cewa Sayyida Khadijah tayi aure sau biyu kafin ta auri Annabi (saww) , har ma ta haifi ƴaƴa a lokacin da tayi zaman waɗancan auratayya . A ɓangare guda kuwa Muhaƙƙiƙan Malaman tarihi na Shi'a sun tafi akan rashin ingancin wannan magana da matsaya ta Ahlussunna Wal jama'a , tare da kafa dalilai da hujjoji masu ƙarfi da inganci a cikin littafan Su Ahlussunna Wal jama'a ɗin , bugu da ƙari da yin amfani da wasu ƙarinoni (Alamu) da suke kore abinda wasu malaman Ahlussunna suka tafi akansa . Ruwayoyin tarihi sun haɗu a kan cewa ; Matar Manzon Allah (saww) ta farko da ya fara aura itace Sayyida Khadija bint Khuwailid, kuma bai auri kowa ba a rayuwarta har sai bayan wafatinta . Uwa uba itace mace ta farko da ta fara yin Imani dashi da kuma shiga Addinin Musulunci.
193
15
WARWARE SHUBHOHIN UWAR ƳAN NURUL HAƘƘI DA ƳAN KORENTA *Fita ta (04) Yaƙin Najaf da matsayar Sayyid Ali Sistaniy (H) / matsayar Sayyid Ali Sistaniy a kan siyasar Iraƙi da abinda suke faruwa. Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
262
16
Audio from العبد الفاني الكنوي
226
17
INNA LILLAHI WA INNA ILAHI RAJIUUN....😭 A ranar 8 ga watan Rabi'ul Auwal shekara ta 260 bayan hijira , Imam Hassan Al-askari yayi shahada a garin Samarra na kasar Iraqi , bayan ya fuskanci ƙuntatawa da takura daga Gwamantin Azzalumai (Abbasiyyawa) , wanda a karshe suka yi sular shahadarsa a matsayinsa na Mahaifin Limami na goma sha biyu a jerin limaman shiriya , yayi shahada yana da shekara 28 a duniya . Bayan Imam yayi shahada ɗansa Imam Muhammad Mahdi (a.t.f) yayi masa Sallah da jana'iza, wanda daga nan ne Imamancin Imam Mahdi (a.s.) ya fara , lokacin yana ɗan shekara kusan 5 a rayuwarsa , hakan yasa ya zama Imami mafi ƙarancin shekaru yayin fara Imamancinsa . Kuma wannan ba komai bane daga cikin iko da hikima ta Allah Ta'ala , domin Allah ya sanya Annabi Isa ya zama Annabi tun yana zanin goyo, yayi magana sannan ya fadawa mutanen Mahaifiyarsa (Maryam) cewa shi Annabi ne kuma bawan Allah ; قَالَ إِنِّى عَبْدُ ٱللَّهِ ءَاتَنِىَ ٱلْكِتَٰبَ وَجَعَلَنِى نَبِيًّا Haka Allah ya bawa Annabi Yahaya Annabta a lokacin da yake yarinta; يَا يَحْيَىٰ خُذِ الْكِتَابَ بِقُوَّةٍ ۖ وَآتَيْنَاهُ الْحُكْمَ صَبِيًّا .... Dan haka ba mai inkari da musanta hakan sai munkiri marashin rabo . أعظم الله اجورنا وأجوركم بذكرى هذا المصاب الجلل 😭وجعنا الله وإياكم من أنصار المهدي المستشهدين بين يديه بحق محمد وال محمد. ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
294
18
KIFI NA GANINKA MAI JAR KOMA !!! *Tabbas kun zagi malamanmu , kunci zarafinsu da yi musu sharri da ƙage* *Fita ta biyu 03* Tare da ɗan uwa 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 7 /Rabi'ul Auwal / 1448H 21/ 8 / 2026 https://t.me/tafarkintsiratv
259
19
Audio from العبد الفاني الكنوي
245
20
DAGA SAYYID ALI SISTANI (H) ZUWA GA ƳAN ZAUREN NURUL HAQ MASU TUHUMARSHI DA HALASTA LUWAƊI !!! *Fita ta biyu 02* Tare da ɗan uwa 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 6 /Rabi'ul Auwal / 1448H 20/ 8 / 2026 https://t.me/tafarkintsiratv
362