cookie

Utilizamos cookies para mejorar tu experiencia de navegación. Al hacer clic en "Aceptar todo", aceptas el uso de cookies.

avatar

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

Mostrar más
Nigeria3 999El idioma no está especificadoReligión y espiritualidad61 473
Publicaciones publicitarias
1 248
Suscriptores
+224 horas
+167 días
+4530 días

Carga de datos en curso...

Tasa de crecimiento de suscriptores

Carga de datos en curso...

GAME DA ZANGA-ZANGA..... FAHIMTATA !!! Babu shakka mahukuntan Najeriya babu yaran da suke ji kamar yaren bore da naƙi bisa mawuyacin halin da suka jefa al'umar da suke mulka cikinsa , sam baza su taɓa fahimtar yaren nasiha ko wa'azi ba domin zukatan su sun ƙeƙashe kuma kunnuwansu sun toshe ga barin jin gaskiya sannan idanuwan su sun makance ballantana suga dai-dai, babu abinda suke fahimta da gani face hawa kujerar naƙi da ban yarda ba , daga ciki akwai yin zanga-zangar rashin amincewa dasu da yanda suke tafi da al'amura ko da ba da sunan Addini ba . Amma inda gizon ke saƙa , ita zanga-zanga tana buƙatar wasu sharuɗa yayin yinta da za su sanya tayi tasiri ko sauya yanayi wanda matuƙar sharuɗan nan basu samu ba to zanga-zangar nan bata haifar da ɗa mai ido ko samun abun nema , bari ma takan rikiɗe ta zama yaƙi ko tashin hankalin da zai babbake kowa . Daga cikin waɗannan muhimman sharuɗan ; Dole ya zama akwai tsayayyen jagoranci a harkar zanga-zanga ba wai kara zube za a yita ba kowa ya fito yayi abinda yaga dama , jagoranci ne kawai zai iya samar da sharaɗi na biyu watau tsari mai karfi cikin lamarin , bayan haka kuma ya zama akwai bayyanannen hadafin yinta wanda ko da an nemi zama za su gabatar dashi ko ya zama shine taken da za su ɗaga don asan me suke yi a gida da waje , sai kuma batun haƙuri da juriya duk rintsi duk wuya ba gudu ba ja da baya , amma in ya zama da anzo an harba bindiga sama ko barkonon tsohuwa da za a gudu to ba batun zanga-zanga , domin ba a samun ƴanci da jin daɗi ko cikin sauƙi , hasali ma dole sai wasu sun bada ransu wasu suke rayuwa , ita kanta Duniyar a haka take tafiya a tsarin halittar ta sai anyi girgizar ƙasa wasu ke rayuwa a doron ta . Wallahi matukar babu waɗannan sharuɗan to zanga-zanga aikin banza ce bata da wani amfani sai ma ƙara dagula al'amari. Domin rashin tsayayyen jagorancin mutane da suka san me suke yi da kuma tsari a cikinta yakan saka a samu wasu da ake kira ɓangare na uku (الطرف الثالث) wanda kai tsaye suke yiwa zan-zanga kutse wajen cimma muradansu ko ja iyayen gidan su wanda mun ga wannan da idanuwan mu a wasu ƙasashe ba wai labari aka bamu ba . Gwamnati ce da kanta za ta samar da wasu su muku kutse ko wasu ƴan siyasa ko masu kuɗi ko ƙasashen waje da za su zuba maƙudan kuɗaɗe wajen ganin sun lalata komai , ita Gwamnati ta tuhumeku dama ba son abun take yi ba kuma tayi amfani da haka wajen murƙusheku , ƴan siyasa su biya buƙatunsu na adawa daku , ƙasashen waje su samu damar shigowa ƙasarku don yi muku mamaya ko ci da gumimku cikin sauƙi , Malaman da suka haramta kuma suji daɗi suce ai dama mun faɗa muku sai su kara biyan buƙatar su . Don haka indai baku shirya yin zanga-zanga mai jagoranci da tsari da dakewa ba to wallahi karma ku soma don aikin banzan da zai cutar da ku za ku yi , ko yan Shi'a da kuke cewa sune suka san hannun su har suke baku sha'awa don suna da jagoranci da tsari ne idan suka fito Muzahharar suma ba kara zube suke ba , amma ko su ɗin ku tambaye su kuji yanda ake ƙoƙafin musu kutse wani lokacin ko kuma Gwamnati tayi musu sharri sau dayawa . Allah ya kawowa kasar mu mafita gaggawa da zaman lafiya . ✍️Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 6 / Al-Muharram / 1445H - 13 / 7 / 2024 Miladiyya.
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

Duk dan kar suyi baƙin cikin kisan gillar da aka yiwa zuriyar Annabi (saww) kuma saɓawa yan Shi'a suka kirkiri ƙarya tafi dubu don a bawa ranar Ashura wata ma'ana ta daban , suka ce a ranar Ashura Allah ya tseratar da Annabi Musa (a.s) , ana so ayi cika ciki , ana so a farantawa maraya, ana so ayi Azumim nafila ana so , ana so ..... A lokaci guda kuma sai suce baya halasta tuna abunda ya faru Shekarau sama da dubu , to me yasa suke bikin murnar tseratar da Annabi Musa (a.s) tunda shima ya riga wuce sama da shekaru Dubu Uku ??? Dama nace in mutum yayi ƙarya ɗaya sai yayi dubu kafin ya kare ta . ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

ƘWARYA TABI ƘWARYA .... Yazidu ɗan Mu'awiyah L ya ɗora daga inda iyayensa da kakkaninsa suka tsaya ne , ya huce fushinsu akan iyalan gidan Manzon Allah (s), sannan ya cika musu burinsu da suka daɗe suna fatan samu . Tun sanda Manzon Allah (s) yazo da hasken shiriya da adalci , ya kauda karagar kafirci da shirka da su Abu Sufyan ke jagorantarta , sai fa suka ƙulkaceshi ! sukayi ta neman dama ko sababin da zasu ga bayan Manzon Allah (s) . Har Annabi yayi hijira kuma yazo ya buɗe Makka , sannan suka shiga Musulunci ba dan suna so ba , sai dan ba yanda za suyi an cisu da yaƙi da gaskiya da tayi hakinta. Haka na an karɓi Musuluncinsu ba dan sun yi Imani da gaske ba sai dan a tausashi zuciyarsu . Shi yasa ba wai shiga Musulunci sukayi kamar yanda kowa yayi ba , an dai ce musu kuje yanzu kun zama sakakku (إذهبوا فانتم الطلقاء) , bayan an yi musu kara akace duk wanda ya shiga gidan Abu Sufyan ya tsira .... Duk da haka ba su gushe ba suna yiwa Addini bita da ƙulli da kitimurmura da munafurci har a garin Madina . Sun sha ƙoƙarin ganin sun kashe Annabi basu yi nasara ba , daga ƙarshe suka koma yakar wanda zai gaji Annabi (s) , domin dukkan tunaninsu ya za'a yi Annabi ya kauce ya basu wuri su koma yanda suke a zamanin jahiliyya. Bayan Annabi yayi shahada, suka cigaba da kambama wannan gaba da ƙiyayya kan iyakan gidansa da masoyansa na gaskiya , suka fara far musu tare da zaluntarsu da cutar da masoyansa daya bayan ɗaya . Har ta kai ga sun fara dafa madafan iko , sai suka fara kashe iyalansa da ƙoƙarin huce fushinsu da Annabi akan ƴaƴan Ɗakinsa . Suna kashesu da su da mabiyansu har duniya ta ƙara yi musu ƙunci da tamani . Bayan Mu'awiyah ya kauce sai ɗansa Yazidu L ya ɗora daga inda uabansa ya tsaya , sannan ya fito da irin maitar iyayensa da kakkaninsa a fili sosai , fiye da mahaifin nasa ma ta wata fuskar , domin da kansa ya faɗa a cikin shahararriyar wakar nan da take nuna kafirci da zundikancinsa yana mai cewa : ليت أشياخي ببدر شهدوا جزع الخزرج من وقع الأسل حين حكت بقباء بركها واستحر القتل في عبد الأشل قد قتلنا الضعف من أشرافهم وعدلنا ميل بدر فاعتدل لعبت هاشم بالملك فلا خبر جاء ولا وحي نزل Yana nuna farin ciki da murna da irin mummunan aikin da ya aikata a Karbala , har yana fatan imama ace iyayensa da kakanninsa da Annabi ya kashe masa a Badar , za su dawo suga yadda ya ɗau musu fansa akan zuriyar Annabi (s) , da sunyi alfahari dashi har suyi guɗa da shewa . Uwa uba yadda ya ƙaryata Annabta ya siffantata da mulki , yana mai cewa ; babu wani wahayin da yazo daga Allah (swt) , wasa ne da rainin wayo Banu Hashim suka yi da mulki da sunan Annabta . Subhanallah ! Wannan kaɗai ya isa ya nuna kafircin matsiyacin mutumi , da kuma yadda ya huce fushin iyayensa akan iyalan Annabi (s) , sannan ya sanyaya zuciyarsu da cika musu manufarsu ta ran gini . A tare da haka ake samun wasu masu da'awar Musulunci da soyayyar Ƙarya ga Annabi (s) , suna bawa wannan shaiɗani kariya dashi da waɗanda suka kawo shi , dama wanɗanda suka yi musu sharar fage har suka zo sukayi abinda sukayi . Allah ka dawwamar da tsinuwa da azabarka , kan dukkan wanda ke da hannu wajen cutar da iyalan Manzon Allah (s) da zaluntarsu , kowaye ! Na jiya da yau da gobe , da wanda yaji abinda akayi musu ya yarda ko yayi murna da hakan . السلام عليك يا أبا عبدالله الحسين 😭 وعلى الأرواح التي حلت بفنائك ، عليكم مني سلام الله أبدا ما بقيت وبقي الليل والنهار ، ولا جعله الله آخر العهد مني لزيارتكم ، السلام عليكم ورحمة الله تعالى وبركاته ومغفرته . ✍️Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

WANE NE IMAM HUSAIN (A.S) ??? 1 . Imam Husain (a.s) jagora ne da ya kai ƙololuwa wajen azama da tabbatuwa akan hadafinsa , bai taɓa sunkuya zalunci da kama karya ba . 2 . Imam Husain (a.s) ramzi ne na sadaukantaka da dakewa yayi fito na fito da zalunci bai yi ƙasa a gwiwa ba wajen taimakon gaskiya da dukkan ƙarfinsa . 3 . Imam Husain (a.s) jagora ne na ruhi da ya tattare duk wata hikima da hangen nesa , kuma ya kira al'uma zuwa ga aikin alheri fa tsayar da adalci. 4 . Imam Husain (a.s) ɗaya ne daga cikin Ahlul Baiti (a.s) da babu takardu a halitta bayan Manzon Allah (saww) . 5 . Imam Husain jagora ne mai tsananin son alkhairi da kawo gyara ga al'uma , a ko da yaushe burinsa shine tabbatar da adalci da daidaito cikin al'uma . 6 .Imam Hussain (a.s) abun koyi ne wajen haƙuri da juriya wajen fuskantar wahalhalu da musibu da dukkannin imani tare da sallamawa Allah . 7 . Imam Husain (a.s) shugaba ne da yayi imani da ya yarda da kansa kuma yasan cewa babu makawa wata rana gaskiya za tayi nasara akan ƙarya a ƙarshen al'amari da izinin Allah . ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

LABARAN KARBALA DA ASHURA (61H) . "Isowar Imam Hussaini Karbala😭" Bayan doguwar tafiya mai dogon zango data shafe kwanaki 24 (Daga Makka zuwa Lardin Iraqi) , Imam Hussain (a.s.) ya iso filin Karbala da tafiyar kilomita 1403 har da garin Makka da ya baro zuwa Karbala. Imam Husaini ya iso Karbala a ranar 2 ga watan Almuharram shekara ta 61 ɗaya hijra , yayi tafiyar kwanaki 14 a yankin Hijaz (Saudiyya) da kwanaki 9 a lardin Iraki , sai kuma saurin tafiyar kilomita 63.91 da sukan iya kaiwa a kowanne wuni . Bayan Imam Hussain (a.s.) ya isa Karbala sai aka ga dokinsa ya tsaya kuma ya cije a wurin , sai Imam Hussain ya tambaya ya sunan wannan wuri da muke ? aka ce masa : Alghadiriyya , sai ya ƙara tambaya yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa : ana ce masa Nainawa , sai Imam ya kara tambaya ko yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa : ana ce masa gaɓar Furatu, sai Imam Hussain ya kara cewa ko yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa ana ce masa Karbala , sai kawai aka ga Imam Hussain ya ja numfashi ya fashe da kuka mai tsanani sai yace : Ya Ubangiji ina neman tsari a gunka daga baƙin ciki da bala'i, sannan yace musu : Ku tsaya anan kar ku ƙara gaba daga nan inda muke , domin wallahi anan ne za'a sheƙar da jinanenmu, wallahi anan za'a keta alfarmar masu alfarmarmu , wallahi anan ne za'a kashe mazajenmu , wallahi anan ne za'a kashe mazajenmu , wallahi nan za'a ziyarci ƙaburburanmu , wallahi a wannan turɓayar kakana yayi min alƙawari kuma alkawarinsa baya tashi . Jagoran tawagar Imam Hussain (a.s) yayi shela ga ƴan tawagar kan su yi masauki na ƙarshe a wannan wuri . Zamu cigaba .... السلام على المقتول صبرا 😭 يا حسين ✍️Khadimu A'atabi Ali Muhammad Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

KARANTA HAR ZUWA ƘARSHE...... Yazo a cikin wani Hadisi da Rayyan ɗan Shabib ya ruwaito daga Imam Ridha (a.s) yake cewa dashi ; Ya kai ɗan Shabib , haƙiƙa watan Almuharram wata ne da mutanen zamanin Jahiliyya suke haramta zalunci da yaƙi a cikinsa saboda alfarmarsa , amma wannan al'uma basu san alfarmar Watansu da Annabinsu ba , a cikin wannan watan ne suka kashe masa zuriyarsa sannan suka ribace matansa kuma suka wawashe masa abubuwa masu daraja , to kada Allah yayi musu gafara akan hakan har abada . Ya kai ɗan Shabib , in har ka kasance mai yin kuka ga wani abu to kayiwa Imam Husain ɗan Ali ɗan Abi Ɗalib (a.s) kuka , domin an yankashi kamar yanda ake yanka rago kuma aka kashe a tare dashi mutum sha takwas daga iyalan gidansa da basu da kwatankwaci a ban ƙasa , sammai da ƙassai bakwai sun yi kuka saboda kasheshi, kuma wasu daga Mala'iku su dubu huɗu sun sakko saboda su taimakeshi amma bai yi musu izini ba , wanda har yanzu suna nan a inda ƙabarinsa yake cikin yanayi na ƙura-ƙura da yanƙwanannen gashi har Alƙa'imu (a.s) ya bayyana sai su zama daga cikin mataimakansa kuma takensu shine "Ya Latharatul Hussain" . Ya kai ɗan Shabib, lallai mahaifina ya zantar dani daga kakansa cewa ; Yayin da aka kashe kakanna Husaini (a.s) sama tayi kukan jini da jar turɓaya . Ya kai ɗan Shabib, in har kayiwa Imam Hussain (a.s) har hawayenka suka zuba a bisa kuncinka Allah zai gafarta maka duk wani zunubin da ka yishi babba ne ko ƙarami . Ya kai ɗan Shabib , in har zai faranta maka ka sadu da Allah ba wani zunubi akanka to ka ziyarci Husaini (a.s). Ya kai ɗan Shabib , in har zai faranta maka ka samu masauki a ɗakuna ababan ginawa a cikin Aljanna tare da Annabi (saww) to ka la'anci makasan Hussain . Ya kai ɗan Shabib , in har zai faranta maka ya zama kana da lada irin n waɗanda aka kashe tare da Imam Husaini ɗan abi Ɗalib (a.s) ka faɗa a duk sanda ka ambaceshi : "Inama na kasance tare dasu dana rabauta rabo mai girma " Ya kai ɗan Shabib, in har zai faranta maka ka kasance tare damu a darajojinmu maɗaukaka a cikin Aljannatai to kayi baƙin ciki da baƙin cikinmu kuma kayi farin ciki da farin cikinmu , kuma na horeka da yin riƙo da wilayarmu , da ace mutum zai so wani dutse da Allah ya tasheshi tare dashi a ranar Alƙiyama . (Duba littafin Uyunul Alkhbar Ridha (a.s) na Shehunmu Assaduuq (Rahimahullah) , Juzu'i na 2 shafi na 268 ) . السلام عليك يا أبا عبد الله الحسين ✍️ Khadimu A'atabi Ali MuhammadAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv Al-muharramul Haram /1444H - 22 / 7/2023 Miladiy .
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

3 . Haka nan kamar yanda baya halasta mutum ya auri matar kakan sa wajen uba haka baya halasta ya auri matar kakansa na wajen uba bisa faɗin Allah : وَ لٰا تَنْكِحُوا مٰا نَكَحَ آبٰاؤُكُمْ مِنَ النِّسٰاءِ.... Wanda ba dan kasancewarsa ɗa na haƙiƙa ga kakan nasa na wajen uwa da ya halasta ya auri matarsa . 3 . Rantsuwar Imam Ja'afar Assadiƙ (a.s) da Allah da cewa su ƴaƴan Annabi (saww) ne na haƙiƙa ba wai makusantan sa ba tare da cewa ta ɓangaren Sayyida Fatima (a.s) suke komawa gareshi , kamar yanda yazo a hadisi yana mai cewa : إي والله إنا لولده وما نحن بذوي قرابته ثلاث مرات قالها ..... 4 . Haka nan Manzon Allah (saww) ya kasance yana kiran Imam Hasanaiyn da ƴaƴansa kai tsaye (...ابني هذا), don haka suma zuriyarsa ne kuma ƴaƴan sa . 5 . Haka nan a cikin ayar mubahala da Annabi (saww) ya fito da Imam Hasan da Husain (a.s) a matsayin ƴaƴan sa ; أبناءنا وأبناءكم .... Bisa umarnin Allah Ta'ala . ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 27 / Thul Hijjah / 1445H - 4 / 7 / 2024 Miladiyya.
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

MATSAYIN WANDA MAHAIFIYAR SA CE SHARIFIYA BA MAHAIFIN SA BA ??? (GYARA FAHIMTA 03) Sai kuma batun matsayin wanda mahaifiyar sa ta kasance sharifiya ba mahaifinsa ba wanda a wasu ƙasashen gabas ake kira da "Mirza" ميرزا" wacce asalinta kalma ce ta Turkanci ko Farisanci kuma kalma biyu ce "Mir da Zadah duk da dai yakanzo a matsayin sunan yanka , ma'anarsa kuwa itace "Ɗan Sarki" ko yarima , to yaya matsayin sa yake ? To babu shakka wanda mahaifiyarsa ta kasance sharifiya to shima yana daga zuriyar Manzon Allah (saww) tamkar wanda mahaifinsa ya kasance sharifi babu banbanci ta wannan fuskar , dukkansu zuriyar Annabi (saww) ne . Na'am , Malamai sunyi saɓani akan matsayin ɗan ƴa mace a wajen kakansa na wajen uwa shin ɗa ne na haƙiƙa ko ɗa ne majazi (na kara) , mafi yawansu suka ce ɗa ne na kara ba na haƙiƙa ba , wasunsu kuma sukace shima ɗa ne na haƙiƙa ba na kara ba a wajen kakan sa na wajen uwa , kuma kowanne ɓangare sun dogara da dalilai masu yawa wanda nan ba mahallin tattauna su bane . Sakamakon wannan saɓanin nasu yana bayyana ne a irin wannan mas'alar da muke magana yanzu ta shariftaka da muke dama mas'alar yin waƙafi idan mutum yace yayi waƙafin wata kadara tasa ga ƴaƴansa shin ƴaƴan mace za su shiga ko ba za su shiga ba ? haka a babin gado da Khumusi da Zakka. To waɗanda suka ce ɗan mace ɗa ne na haƙiƙa a wajen kakansa na wajen uwa ba na kara ba a babin sharifta sukan bashi hukuncin wanda babansa sharifi ne , don haka sukace shima zai ci Khumusi kuma bazai ci sadakar wajibi ba kamar dai Sharifi , daga waɗanda suka shahara akan wannan ra'ayin akwai Sayyid Almurtdha ɗan uwa ga Sharifur Radhiy (Mai littafin Nahjul Balagha) da Shehunmu Yusuful Bahraniy da wasun su , su kuma waɗanda suka ce ɗan mace ɗa ne na kara ga kakansa suka ce ba za a bashi hukuncin wanda ya gaji sharifta ta ɓangaren uba ba , don haka su a wajensu zai ci sadakar wajibi kamar Zakka amma kuma baya halasta yaci Khumusi , amma dai duka dai zai shiga cikin zuriyar Manzon Allah (saww) kamar ɗan Namiji sai dai hukuncin Shari'a ya banbantasu a babin khumusi da Zakka. Ayatullahi Sayyid Ali Khamene'i (H) ya bada irin wannan amsar a tambayar da aka masa cikin Risalar Ajubatul Istifta'at , yace ; Wanda iyayensu mata ne sharifai ba mahaifa maza ba suma zuriyar Annabi (saww) sai dai kawai su ba za su ɗauki hukuncin Shari'a na Fiqhu ba , yana nufin basa cikin wanda sadakar wajibi ta haramta garesu da waɗanda Khumusi ya halasta garesu , saɓanin irin su Sayyid Murtadha (R) da suka ce har Khumusin ma za su ci saboda suma ƴaƴa ne na haƙiƙa. Wannan mas'alar ce aka sha tambayar Ai'immatu Ahlil Baiti (a.s) akan me yasa ake kiran su da ƴaƴan Manzon Allah (saww) bayan su ƴaƴan Sayyida Faɗima ne nasabar su ga Imam Ali (a.s) take komawa , kuma sun kawo dalilai da hujjoji daga Alƙur'ani da Sunnah da suke tabbatar dasu ƴaƴan Annabi (saww) ne na haƙiƙa ba wai kawai makusantan sa ba shi yasa yake ce musu ƴaƴan Annabi (saww) , daga cikin dalilan : 1 . Allah ya danganta Annabi Isa ɗan Maryam (a.s) ga Annabi Nuhu ko Ibrahim (a.s) a wasu ayoyi da yake jero nasabar Annabawan sa a tare da cewa Annabi Isa (a.s) ɗan mace ne bama shi da mahaifi shi sam , wanda hakan yana nuna cewa ɗa ne na haƙiƙa ba wai na kara ba , Allah yana cewa : وَوَهَبْنَا لَهُ إِسْحَاقَ وَيَعْقُوبَ ۚ كُلًّا هَدَيْنَا ۚ وَنُوحًا هَدَيْنَا مِن قَبْلُ ۖ وَمِن ذُرِّيَّتِهِ دَاوُودَ وَسُلَيْمَانَ وَأَيُّوبَ وَيُوسُفَ وَمُوسَىٰ وَهَارُونَ ۚ وَكَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ.. وَزَكَرِيَّا وَيَحْيَىٰ وَعِيسَىٰ وَإِلْيَاسَ ۖ كُلٌّ مِّنَ الصَّالِحِينَ [ الأنعام: ٨٤ و٨٥]. 2 . Rashin yiwuwar auren Annabi (saww) da ɗaya daga cikin zuriyar Sayyida Fatima (a.s) kamar yanda yake haramun mutum ya auri ƴarsa ko ɗaya daga cikin zuriyar ƴarsa , wannan ma yana nuna cewa su ƴaƴansa ne na haƙiƙa ba na kara ba , kamar yanda Allah yake cewa : حُرِّمَتْ عَلَيْكُمْ أُمَّهَاتُكُمْ وَبَنَاتُكُمْ..... Wanda haramcin auren ƴa ya game hatta zuriyarta , hakan na nuna ƴaƴanta ne na haƙiƙa .
Mostrar todo...
SHARIFTA DA HANYOYIN TABBATAR DA ITA (GYARA FAHIMTA 02) Abinda ake nufi da Sharifi ko Sayyid ; Shine wanda nasabar sa take komawa ga kakan Manzon Allah (saww) Hashim ɗan Abdul Manafi ko Abdul Muɗɗalibi bisa ra'ayin wasu Malaman , sawa'un nasabarsa tana komawa ga Sayyida Fatima da Imam Ali (a.s) zuwa ga Annabi (saww) har kakansa Hashim bin Abdul Muɗɗalibi ko tana komawa ta baffan Manzon Allah (saww) Abbas ko ƴan uwan Imam Ali (a.s) Ɗalib da Aƙil da Ja'afar zuwa ga Hashim bin Abdul Muɗɗalibi , shine ake cewa sharifi ko Sayyid . Ma'ana ba sharaɗi bane nasabar sharifi ta koma ga Annabi (saww) ko Sayyida Fatima da Imam Ali (a.s) kai tsaye , matuƙar dai tana komawa ga Hashim bin Abdul Muɗɗalibi ta wanɗancen gidajen to shi sharifi ne , duk da dai waɗanda suke komawa ga gidan Annabi (saww) na musamman ne domin komai na Annabi da iyalansa tsarkaka na daban ne . Dangane da hanyoyin tabbatar da sharifta kuwa sune : 1 . Samun ilmi ko nutsuwa akan nasabar ta madogarar hankali kamar kiyayeta ko rubutata tiryan-tiryan har zuwa ga danganenta na ƙarshe kamar yanda yafi shahara a wasu ƙasashen Larabawa da yankunan da ake da sharifai dayawa , sukan rubuta nasabar kakannin su su zanata kamar bishiya (Tashjir) da rassanta a kowanne gida suna masu taskaceta . 2 . Yaɗuwar sanin wannan nasabar ta mutum a garin su ko a garin da yake zaune , ta yanda gidan su zai shahara da sharifta a garin nasu tun iyaye da kakanni ba tare da wani yankewa ba . Waɗannan sune hanyoyin da Malamai suka ambata na tabbatar da sharifta kuma ilmi da hankali suke hukunta tabbatarta da su , amma batun mutum yace yayi mafarki yace an bashi sharifta ko yaga alamunta ko wani yace masa ya bashi sharifta saboda shi sharifi ne duk ba abun dogaro da hujja bane a hankalce da illamance , kuma hakan kuskure ne kuma mafarar kaucewa hanya madaidaiciya ne . To duk wanda ya zama sharifi (Sayyid) to yana da hukunce-hukuncensa na Shari'a da Malaman fiƙhu suka ambata dogaro da dalilai na Shari'a ; Haramun ne gareshi yaci sadaka ta wajibi kamar Zakka da zakkar fidda kai daga wanda ba sharifi ɗan uwansa ba , sannan yana daga cikin wanda ya halasta suci Khumusi a kason sharifai. A rubutu na gaba za muyi bayanin matsayin wanda mahaifiyarsa take sharifiyya da hukuncinsa , Insha Allah. ✍️ Khadimul Ashraf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 26 / Thul Hijjah / 1445H - 3 / 7 / 2024 Miladiyya.
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

RANAR DA MANZON ALLAH (SAWW) YA FITO YIN MUBAHALA DA KIRISTOCIN NAJRAN TANA NUFIN : 1 . Duk Duniya Manzon Allah (saww) bashi da tamkar waɗanda ya fito dasu wato Imam Ali , Sayyida Faɗima da ƴaƴanta Hasanain (a.s) , domin da yana da kamar su bayansu da ya fito da su a wannan rana . 2 . Wannan rana tana nufin babu waɗanda Annabi (saww) yake ƙauna kamar su inda da akwai shi da anga ya kirawo shi , domin babu ma'anar ya zama akwai wanda yafi su ko yake sama dasu a matsayi gunsa amma ya barshi a gida , saboda zuwa da abinda mutum bai da kamarsa ke nuna yana kan gaskiya akan abinda ya fito ayi muguwar addu'a akansa , ma'ana dai da ace akwai wanda suka fi su Imam Ali da Sayyida Zahra (a.s) a wurin Annabi (saww) kuma yaƙi fito da su da hakan ya nuna ba da gaske yake ba. 3 . Zuwan da Manzon Allah (saww) yayi da ƴaƴan ɗakinsa ya nuna gaskiyar Annabcinsa wanda hakan yasa Kiristocin Najran duka janye ƙudirun su daga ƙarshe suka nemi sulhu da Annabi (saww) domin da ace bai da hujja akan gaskiyar Addinin da yake kai da bai zai zo da su Imam Ali (a.s) ba sai dai aga yazo da wasu daga Sahabbansa ko Matansa da sauran Musulmi ko wasu bare can . 4 . Abinda ya faru a wannan rana ya nuna Imam Ali (a.s) ya kai ƙololuwar matsayi da falala da girma kuma babu wani mutum da ya kai shi daraja bayan Manzon Allah (saww) domin Nassin Alƙur'ani cikin ayar Mubahala ya tabbatar da shi Nafsun Manzon Allah (saww) ne ; فَمَنْ حَاجَّكَ فِيهِ مِن بَعْدِ مَا جَاءَكَ مِنَ الْعِلْمِ فَقُلْ تَعَالَوْا نَدْعُ أَبْنَاءَنَا وَأَبْنَاءَكُمْ وَنِسَاءَنَا وَنِسَاءَكُمْ وَأَنفُسَنَا وَأَنفُسَكُمْ ثُمَّ نَبْتَهِلْ فَنَجْعَل لَّعْنَتَ اللهِ عَلَى الْكَاذِبِينَ (آل عمران/٦١). Imam Ali (a.s) shi Annabi (saww) ya fito dashi a matsayin kansa da ransa , kenan idan ba Annabi (saww) babu wanda zai zama tamkar Annabi (saww) a faɗin Duniya tamkar Imam Ali (a.s) . 5 . Shi yasa Mubahala tana cikin dalilan da suke nuna Khalifancin Imam Ali (a.s) da Imamancin sa bayan Annabi (saww) , domin Annabi shine Imami kuma Khalifan Allah a sanda yake nan idan kuma babu shi babu wanda ya cancanci wannan matsayin sai wanda ya zama Nafsunsa (Ransa) wato Imam Ali (a.s) da zuriyarsa . 6 . Wannan Mubahala tana daga dalilan da suke tabbatar da kasancewar Imam Hasan da Husain (a.s) a matsayin ƴaƴan Annabi (saww) ne na haƙiƙa ba ƴaƴan kara ba , domin Allah cewa yayi ; Ya Rasulallahi kace mu kira ƴaƴanmu kuma ku kira ƴaƴanku نَدْعُ أَبْنَاءَنَا وَأَبْنَاءَكُمْ , shi yasa har wala yau Malaman da suka tafi akan ɗan mace ɗa ne na haƙiƙa a wajen kakansa na wajen uwa suke kafa hujja da Mubahalar Annabi (saww) ta kam wannan ayar kamar yanda za muyi nuni a bayanin mas'alar shariftar ɗan mace nan gaba In sha Allah. A taƙaice dai ranar Mubahala da wannan ayar suna nuni da wanni matsayi na musamman ga Ahlul Baiti (a.s) babu wani da yayi tarayya dasu cikinsa a kaf wannan al'uma kuma rana ce daga ranaku mafiya girma a tarihin Musulunci , domin a cikinta ne aka yanke tambabar duk wani mai tambaba akan gaskiyar Annabcin Annabi Muhammad (saww) kuma ƙarya ta bayyana kowa ya santa . Tarihi ya nuna fitowa domin wannan Mubahala ya wakana ne a rana mai kamar yau 24 ga watan Zulhijjah ɗin shekara ta goma bayan hijira a garin Madina mai alfarma , ma'ana a ƙarshe-ƙarshen rayuwar Annabi (saww). ✍️Khadimu A'atabi Ãli Muhammad Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 24 / Zulhijjah / 1445H - 1/ 7 / 2024 Miladiyya.
Mostrar todo...
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

Elige un Plan Diferente

Tu plan actual sólo permite el análisis de 5 canales. Para obtener más, elige otro plan.