TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗
Ir al canal en Telegram
2 293
Suscriptores
+224 horas
Sin datos7 días
+130 días
Carga de datos en curso...
Canales Similares
Nube de Etiquetas
Sin datos
¿Algún problema? Por favor, actualice la página o contacte a nuestro gerente de soporte.
Menciones Entrantes y Salientes
---
---
---
---
---
---
Atraer Suscriptores
julio '26
julio '26
+37
en 0 canales
junio '26
+61
en 0 canales
Get PRO
mayo '26
+38
en 0 canales
Get PRO
abril '26
+16
en 0 canales
Get PRO
marzo '26
+18
en 0 canales
Get PRO
febrero '26
+36
en 0 canales
Get PRO
enero '26
+15
en 0 canales
Get PRO
diciembre '25
+40
en 0 canales
Get PRO
noviembre '25
+44
en 0 canales
Get PRO
octubre '25
+29
en 0 canales
Get PRO
septiembre '25
+33
en 0 canales
Get PRO
agosto '25
+24
en 0 canales
Get PRO
julio '25
+60
en 0 canales
Get PRO
junio '25
+33
en 0 canales
Get PRO
mayo '25
+66
en 0 canales
Get PRO
abril '25
+43
en 0 canales
Get PRO
marzo '25
+60
en 0 canales
Get PRO
febrero '25
+110
en 0 canales
Get PRO
enero '25
+40
en 0 canales
Get PRO
diciembre '24
+68
en 0 canales
Get PRO
noviembre '24
+172
en 0 canales
Get PRO
octubre '24
+185
en 0 canales
Get PRO
septiembre '24
+136
en 0 canales
Get PRO
agosto '24
+184
en 0 canales
Get PRO
julio '24
+72
en 0 canales
Get PRO
junio '24
+49
en 0 canales
Get PRO
mayo '24
+54
en 0 canales
Get PRO
abril '24
+52
en 0 canales
Get PRO
marzo '24
+92
en 0 canales
Get PRO
febrero '24
+68
en 0 canales
Get PRO
enero '24
+59
en 0 canales
Get PRO
diciembre '23
+51
en 0 canales
Get PRO
noviembre '23
+44
en 0 canales
Get PRO
octubre '23
+55
en 0 canales
Get PRO
septiembre '23
+54
en 0 canales
Get PRO
agosto '23
+23
en 0 canales
Get PRO
julio '23
+59
en 0 canales
Get PRO
junio '23
+62
en 0 canales
Get PRO
mayo '23
+28
en 0 canales
Get PRO
abril '23
+33
en 0 canales
Get PRO
marzo '23
+58
en 0 canales
Get PRO
febrero '23
+49
en 0 canales
Get PRO
enero '23
+42
en 0 canales
Get PRO
diciembre '22
+39
en 0 canales
Get PRO
noviembre '22
+20
en 0 canales
Get PRO
octubre '22
+24
en 0 canales
Get PRO
septiembre '22
+7
en 0 canales
Get PRO
agosto '22
+16
en 0 canales
Get PRO
julio '22
+14
en 0 canales
Get PRO
junio '22
+37
en 0 canales
Get PRO
mayo '22
+52
en 0 canales
Get PRO
abril '22
+527
en 0 canales
| Fecha | Crecimiento de Suscriptores | Menciones | Canales | |
| 30 julio | +2 | |||
| 29 julio | +4 | |||
| 28 julio | +1 | |||
| 27 julio | +2 | |||
| 26 julio | 0 | |||
| 25 julio | +1 | |||
| 24 julio | +3 | |||
| 23 julio | +2 | |||
| 22 julio | +1 | |||
| 21 julio | +1 | |||
| 20 julio | +1 | |||
| 19 julio | +5 | |||
| 18 julio | +2 | |||
| 17 julio | +1 | |||
| 16 julio | +1 | |||
| 15 julio | 0 | |||
| 14 julio | 0 | |||
| 13 julio | +1 | |||
| 12 julio | 0 | |||
| 11 julio | +3 | |||
| 10 julio | +1 | |||
| 09 julio | +1 | |||
| 08 julio | 0 | |||
| 07 julio | +1 | |||
| 06 julio | 0 | |||
| 05 julio | +1 | |||
| 04 julio | +1 | |||
| 03 julio | 0 | |||
| 02 julio | +1 | |||
| 01 julio | 0 |
Publicaciones del Canal
MUSIBUN AHLUL BAITI (A.S.) DA WATAN SAFAR
Tayu wani yace ; Ai kuma a watan Safar akwai munasabobin juyayi da alhini na abinda ya sami Ahlul baiti (a.s) , shin hakan bai da alaƙa da rashin albarka da wancen camfi na mutane keyi ga watan ba ???
Shima dai zamu masa ; Eh , kuma a'a . Lallai wata ne na alhini da juyayi ga abinda ya samu Ahlul Baiti na musiba kamar Almuharram, domin a cikin sa ne ake Arba'in , Imam Hassan yayi shahada, da Imam Ridha da Manzon Allah (sawa) , dama wasu abubuwa na alhini , ana so ayi juyayi da makoki , amma kuma hakan baya nuna cewa watan bai da albarka ko alkhairi bare a camfa shi .
In da za'a Camfa shi saboda wannan dalilin to watan Almuharram ne yafi cancanta da hakan , domin shi watan Safar akwai abubuwan farin ciki da suka faru cikinsa , kamar haihuwar Imam Musal Kazim , da auren Annabi da Nana Khadijah (a.s) da sauransu , saɓanin watan Almuharram da shi babu wani abun farin ciki da murna da ya faru a cikinsa .
RUFEWA
A takaice dai , batun cewa watan Safar bashi da albarka ko watane na saukar bala'i ga mutane , da Camfa shi , da yin wasu abubuwa na maguzanci a ciki , abuna bai da asali , bai da alaƙa da Addini , kuma baya halatta yinsu da yaɗasu da imani dasu , ya zama wajibi ga mumini ya ƙaurace musu yayi watsi dasu .
MAFITA
Mutum ya dogara ga Allah , ya yawaita neman tsari a cikin kowanne wata ba iya Safar ba , ta hanyar yin Addu'oi Ma'asurai da sadaka da karatun Aljur'ani.
Kuma ya zama wajibi mu sani Ahlul Baiti (a.s) sun yi hani da yin imani da yarda da waɗannan abubuwan , har a wasu ruwayoyin sun kwadaitar da yin aiki da sakankancewa a Larabar ƙarshe ta wata (Safar) , duk dan su yaƙi waccen al'ada ta jahiliyya da mutane ke Camfa rana ko watan Safar, ba rana ko watan Safar ba har awanni sun hana a zage su ko a la'ance su .
Ba dan tsoron tsawaitawa ba , da mun kawo Nassi na ruwayoyi da maganganun Malamai akan wannan mas'alar, mun wadatu da iya abinda muka rairayo daga waɗannan riwayoyi da maganganun Malamai saboda takaitawa , In sha Allah.
Wasallamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu 👏
✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv
Asabar , 6/Safar /1443H - 3/Satumba/2022 Miladiyya.
| 2 | DA GASKE NE WATAN SAFAR WATAN BALA'I NE , BASHI DA ALKHAIRI DA ALBARKA ???
Kamar yanda yake a al'adar mutane a ƙasar Hausa , dama larabawa da wasu al'ummatan Musulmi sukan camfa watan Safar , suce ; Wata ne da na saukar da bala'ai da musibu kan mutane ,bashi da albarka , wata ne nahisi, a cikinsa akwai larabgana . Wasu al'ummatan ma basa yin abubuwa na rayuwarsu da yawa a cikinsa , kamar aure ko tarewa a sabon gida , ko ziyaratar mara lafiya da sauransu .
Ya zama ba abinda suke yi a wannan watan face , shiga firgici da tashin hankali , da aikata wasu al'adu na camfi da maguzanci da basu da asali da sunan neman kariya da mafita daga sharrin wannan shu'umin wata (Na Safar , kamar yadda suke faɗa) . Abun tambaya anan shine , shin da gaske duk waɗannan abubuwan da ake faɗa ko tsammani ? A matsayin mu na Musulmi (Mabiya Ahlul Baiti) mene ne matsayar su da Addininmu game da hakan ?
AMSA :
Tabbataciyya magana mai inganci , duk waɗannan maganganu da abubuwan da mutane suke yi a watan Safar , basu da wani asali a Addini, Camfi ne da shu'umanci da maguzanci irin na mutanen jahiliyya , kamar yanda yake a wajen kowacce al'umma , suna da abubuwa na camfi da suke camfawa , kamar larabawa tun zamanin jahiliyya sukan camfa wasu dabbobi, tsuntsaye, ranaku , lokuta kamar watan Safar misali , shi yasa har yaƙi suna farashi ne a cikinsa Safar, haka muma Hausawa muna da wannan abubuwan dayawa , wanda gado ne na maguzanci .
Dukkanin su basu da asali , sun saɓawa karantarwar Addini da Ahlul Baiti (a.s.) , riwayoyi da yawa sunzo da suke hani da camfa wasu ranaku ko lokuta ,Annabi (saww) yana cewa : Duk wanda yake camfi da sihiri da bokanci baya tare dashi . Kamar yanda babu wani dalili tabbatacce da yake nuna cewa an ware wani wata daga cikin watanni goma sha biyu (12) da ake da su a matsayin watan bala'i da bashi da albarka da alkhairi. Hasali ma shi wannan watan na Safar ana masa lakabi da Safar ɗin alkhairi (صفر الخير)ko Safar ɗin Nasara (صفر المظفر) , kamar yanda galibi malamai suke rubutawa a rubuce-rubucen su .
RIWAYOYI DA DALILAI
Haka nan , ruwayoyin da wasu ke kawowa game da Camfa watan safar da rashin alkhairin sa basu da wani asali da inganci , riwayoyi ne ƙirƙirarru , Umayyawa da aka cusasu cikin litattafan Addini , ko ake dangantawa Annabi da Ahlinsa (a.s) , wanda haramun ne ga mutum danganta musu hakan domin bai tabbata ba . Haka duk dalilan da wasu suke ƙoƙarin jingina dasu wajen Camfa watan Safar , kamar ayoyi basu da inganci a wajen Ahlin ilmi da tahƙiƙi .
MAI LITTAFIN MAFATIHUL JINAN DA WATAN SAFAR
Tayu wani yace ; Ai a cikin littafin Mafatihul Jinan Sheik Abbasul Ƙummi ya yi magana akan cewa , watan Safar wata ne Nahisi har ya kawo addu'ar tsari , a farkon A'amal na watan Safar , ya zamuyi da wannan?
Sai ince : Eh hakane, ba haka bane . Abinda nake nufi hakane shine , tabbas Almuhaddisul ƙummi ya kawo magana cewa , watan Safar Nahisi ne , amma abinda yace shine : Ka sani wannan wata na Safar wata ne da ya sanu da Nahisanci (Rashin alkhairi da bala'i) , sai ya kawo addu'a . Amma abinda nake nufi da ba haka bane shine ;
Sheik Abbas ba yana tabbatar da cewa wannan camfe-camfen na mutane hakane suna da inganci ! A'a , yana faɗar abinda ya shahara ya sanu a wajen mutane ne , kuma dama ba komai bane da ya shahara yake daidai ko tabbatacce (رب مشهور لا أصل له) , shi yasa ya kawo wannan addu'ar ta (يا شديد القوى) , ya kuma ce mutum yayi sadaka da isti'azah , saboda akwai mutanen da ko da sun san cewa abu camfi ne , ransu baya nustuwa saboda sabo da al'ada da kuma yadda abun ya zame musu jiki , shi yasa ake basu addu'a suyi , amma ba wai don abun haka ne , kuma dama ita addu'ar neman tsari da sadaka ai ana yin su a kowanne wata dan neman tsari da mafita , ba wai sai a iya watan Safar ba .
Sannan kuma dama ba ana kore cewa bala'i ko wani abu mara daɗi bazai iya faruwa ba a watan Safar , sai dai cewa babu wani dalili bai kuma tabbata ba , ware wannan watan ko wata rana a cikin sa , a camfasu da bala'i ko rashin alkhairi, don haka babu wani ishkali a cikin addu'a da maganar Sheikh Abbasul Ƙummi (Rahimahullah) . | 61 |
| 3 | YANDA AKE ISTIKHARA DA AL-ƘUR'ANI MAI GIRMA A SAUƘAƘE
🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv | 75 |
| 4 | Dama Manzon Allah (saww) ya faɗa a cikin wani hadisi ingantacce cewa :
" Ya Ali , nayi yaƙi abisa saukar Alkur'ani, kai kuma za kayi yaƙi a bisa tawalinsa a bayana "
Tabbas hakan ta faru a bayan Annabi (s) , domin duk wanda suka yaƙi Imam Ali sun yaƙeshi ne suna masu zaluntarsa da kare ɓarna , shi yasa babu banbanci tsakanin wadanda suka yaki Imam Ali da waɗanda suka yaki Manzon Allah (s) , sai dai cewa su kafirai da mushrikai sun yaki Annabi akan saukar Alkur'ani, su kuma wadanda suka yaƙi Imam Ali (a.s.) sun yaƙeshi akan Tawaili da kare Musulunci na gaskiya .
Ya kuma zo a hadisi Manzon Allah (s) yana cewa : Ali yana tare da gaskiya haka gaskiya tana tare da Ali .
Basa rabuwa duk inda kaga gaskiya zaka ga Ali , akasin haka shima daidai ne , kai ! Gaskiya ce take bin bayan Imam Ali a baya shi kuma yana gabanta , kamar yanda yake a sashin wasu hadisai .
السلام عليك يا أمير المؤمنين وإمام الموحدين وقائد الغر المحجلين إلى جنات النعيم.
Wasallamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu 👏
✍️Khadimul AshrãfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey
Talata , 10 /Safar/1443H dai-dai da 7/9/2022 , Miladi . | 70 |
| 5 | DAREN "AL-HARIR" A YAƘIN SIFFIN / ƘWAMIN ƘARSHE DA JARUMTAR IMAM ALI (A.S)
A rana mai kamar yau , daren 11 ga watan Safar ɗin shekara ta 37 bayan hijira , shine daren gumurzu da fafatawa ta ƙarshe a yaƙin Siffin , wanda aka ɗau tsawon lokaci ana yi tsakanin rundunar Imam Ali (a s.) , Da kuma rundunar Sarkin Sham Mu'awiyah L , Kuma shi ake kira daren Alharir , watau daren hayaniya da sautin gumurzun mayaƙa a wata ma'anar da aka bashi , an fara fafatawa tun magriba har safiya ana gwabzawa . Kamar yanda muka faɗa a baya cewa yakin Siffin ya ɗau lokaci ana yinsa sai a daren ne akayi fatawar ƙarshe , biyo bayan abinda ya faru na yaudara , ga cikakken bayani :
Daren Al-Harir yana daga dararen da tarihi ya rubuta jarumtar mam Ali (a.s) da ruwan Zinare , domin a daren ne aka dinga neman Imam Ali (a.s) ana rasashi , har aka dinga zaton ko an kasheshi , Imam Hassan yana cewa ; Ni dai nasan yana nan ba'a kasheshi ba , sai can daga baya aga Imam Ali (a s) yana Sallah a tsakiyar rundunonin biyu ko kuma yana zubar da mazajea ƙasa . A daren ne takobin Imam Ali (Zul faƙar) ya dinga lauyewa Imam na miƙar dashi da gwiwarsa mai albarka , Tunda Imam Ali ya zari takobinsa (ran maza ya ɓaci ) ya kutsa fagen daga , sai daya kashe mayaƙa dari biyar da ashirin da biyar ko ɗari biyar (500) shi kadai a wannan dare .
Ba'a taɓa jin wani kwamandan wasu mutane da ya kashe wannan adadin da hannunsa a irin wannan ɗan lokaci sai Imam Ali (a.s.) . Idan takobinsa ya lanƙwashe sai aji yace ; Ina neman afwar Allah da daku , Manzon Allah naji yana cewa ; Ba matashi sai Ali kuma babu takobi sai Zul faƙar .
Yaƙi yayi yaƙi ! Da Mu'awiyah ɗan Abi Sufyan yaga haka , sai ya kira Amru binil Aas yace masa : wannan dare ne da zai kaimu ga ƙarshenmu , sai Amru binil Aas yace dashi : Mazajenka basu yi daidai da mazajensa ba , kuma kaima ba kwatankwacinsa bane , shi yana yaƙarka akan wani abinda kai ba'a kansa kake yaƙarsa ba , Ali yana son ƙarewa (Fana'i) kai kuma kana son wanzuwa (baka'i) , Sannan mutanen Iraki suna jin tsoronka in kayi nasara kan abinda zaka yi musu (Zalunci) , su kuma mutanen Sham basa tsoron abinda Ali zai musu in ya kamasu (Adalci) .
Dake Amru binil Aas mutun ne da ya shahara wajen hatsabibanci da iya shirya tuggu da shaiɗana , sai yacewa Mu'awiyya L ; Ka bijirar musu da abinda in suka karɓeshi zai kawo musu rabuwar kai da saɓani , haka in suka ƙi karɓarshi kansu zai sa suyi saɓani , shine ka kirasu zuwa ga Alkur'ani kace shine zai zama mai hukunci a tsakaninka dasu , da shine za ka biya buƙatarka akansu , Sai Mu'awiyah L yace masa lallai kayi gaskiya .
Daga nan Mu'awiyah yayi umarni da a ɗaga Alkur’ani a saman mashi, don haka a ranar Juma’ar 10b ga watan Safar ɗin shekara ta 37 bayan hijira , mutane basu wayi gari ba sai da Alkur’ani fiye da dari biyar ba a kan masunsu, suna shela da cewa :
Ya ku mutanen Iraki Littafin Allah ne tsakaninmu da ku, menene laifin mata da yara? Don haka sai aka yi wa mutanen Iraki wayo aka yaudari tunaninsu , sai aka shigar da saɓani a tsakaninsu, suka rabu biyu tsakanin masu ganin a cigaba da yakin nan , wasu kuma suna ganin “Ba ya halatta a gare mu mu yaki mutanen da suke kiranmu zuwa ga littafin Allah (Alkur'ani) , Sai wadannan ɗin suka yi galaba a kan lamarin saɓanin , daga na sai yaƙin ya kare duk da kasantuwar Amirul Muminin (a.s) da sahabbansa na hakika suna nan , amma Mu'awiyah yayi nasarar raba kan rundunar da jefa saɓani a tsakaninsu . Daga bisani akayi al'amarin "Attahkim" ɗin yaudara , Sarkin Sham ya cimma burinsa na ɓallewa da zama shugaba mai zaman kansa ko ta ƙaƙa .
Ta ɓangaren waɗanda suke ganin a dakatar da yaƙi kuwa , sune suka zama Khawarijawa a ƙarshen al'amari , duk da wasunsu a lokacin sun tuba bayan tattaunawa da kai ruwa rana da akayi dasu , waɗanda basu tuba ba sai ɓatan basira ya kaisu ga kafirta Imam Ali (a.s.) da mabiyansa, suka ɓalle daga rundunarsa suka je suka kafa barikinsu a Nahra wan suna aikin ta'addanci da ɓarna a bayan ƙasa , wanda shine sababin yin yakin Nahrawan (yaƙi na uku da Imam Ali yayi ) bayan Jamal da Siffin sai Nahrawan . | 69 |
| 6 | ƘALU BALE ZUWA GA FARFESA SANI R/LEMO
Fita ta farko (01)
🎙️Al-Abdul Faneey Al-kanaweey | 81 |
| 7 | SHAHADAR AMMAR BIN YASIR DA KHUZAIMATU BIN THABIT DA HASHIMUL MIRƘAL (R.T.A) A YAƘIN SIFFIN TARE DA IMAM ALI (A.S.)
Sunyi Shahada a rana mai kamar yau , 9 ga watan Safar shekara ta 37 bayan hijira , lokacin da suke yaki a cikin rundunar Imam Ali (a.s.) a yaƙin Siffin da aka yi da rundunar Azzalumai ta mutanen Sham .
-Ammar bn Yasir ya kasance ɗaya daga cikin manyan Sahabban Manzon Allah (s) masu daraja , wanda Annabi yayi masa bushara da cewa rundunar Azzalumai ce za ta kasheshi , kuma hakan ta faru bayan shekaru masu yawa da komawar Annabi ga Ubangijinsa , inda Ammar Bn Yasir yayi shahada a hannun rundunar Azzaluman Sham (Rundunar Mu'awiyah ɗan Abi Sufyan ) . Shahadar Ammar Bin Yasir tana daga cikin Mu'ujizozin da Annabi ya bada labarinsu , kuma tana tabbatar da kasancewar rundunar Sarkin Sham Mu'awiyah , a matsayin Azzaluman ƴan Ta'adda.
- Khuzaimatu bin Thabit Al-ansari , wanda ake ma laƙabi da Zush shadataini (ma'abocin sheda biyu ) , shima yana daga cikin manyan Sahabbai managarta , da suka Sallamawa Annabi da iyalan gidansa , kuma suka tsaya tsayin daka a bayan Annabi (s) wajen kare iyalansa , tun daga Saƙifa har ranar da yayi shahada a tare da Imam Ali (a.s.) lokacin yaƙin Siffin a rana mai kamar yau .Kuma ya kasance mawaƙi da ya yawaita yabon Imam Ali da bayanin matsayinsa da falalarsa .
- Shima Hashim bn Utbatu bn Abi Waƙkas , wanda aka fi sani da Almirƙal yana daga cikin Sahabban da suka bawa Musulunci gudummawa tun ran gini , kuma ya kasance cikin rundunar Imam Ali (a.s) a yaƙin Siffin , a lokacin da Alharis Bn Munzir ya lallaɓo ya sokeshi a cikinsa .
✍️Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv | 93 |
| 8 | masoyansu.
Amma muna jefa kule ga duk masu ra'ayin biyu da su kawo inda Sayyid Khumaini ko Sayyid Khamene'i (R) suka ce ku dena yarda ana ce muku Shi'a don kar kai ya rarrabu ! Amma dai mun san sun hana amfani da sunan Shi'a wajen kawo rarrabuwar kai da rikici.
Idan ban manta ba a jawabin Sayyid shugaban Kudu (Allah ya jiƙan shi) na ranar Ƙudus ɗin shekarar 2013 , yana bugar ƙirji da karsashi yana faɗawa duniya : Mu ne rundunar ...tawagar Musuluncin Shi'a Imamiyya Ithna Ashariyya ... Mu ne Shi'ar Ali ɗan Abi Ɗalib a duniya .
ونحن حزب ...الحزب الإسلامي الشيعي الإمامي الإثني عشر .... نحن شيعة علي بن أبي طالب في العالم .
Kuma ban jin akwai wanda zai ce bai fahimci gw@gwarmaya ko fikra ingantacciya ba sai ɗan son zuciya .
7 . Don haka zance na gaskiya da adalci bisa dai-daito kar a kore sunan Musulmi ko a kore na Shi'a domin duka suna da asali mai kyau , bari dai a tashi a yaƙi amfani da su wajen kawo rikici ko rabuwar kai shi ne mafita.
Domin ba sunan Shi'anci ba ita kanta kalmar Musulmi ɗin ana iya amfani da ita a kawo rarrabuwar kai , kenan itama kalmar Musulmin sai mu dena kiran kanmu da ita ?
8 . Kuma duk yanda ka kai ga dena kiran kanka Shi'a matuƙar ka yarda da aƙidar to ba za kaga kuɓuta ba , tunda dai za a dinga ganinka da ayyuka da taken su , bari ma dai za a tuhumeka da mai taƙiyya ne ko mai raina wayo .
Don haka muna tare da hana amfani da sunan Shi'a wajen kawo rarrabuwar kai da rikici , amma bama tare dena amfani da sunan Shi'a da da'awar neman haɗin kai ko cimma manufa , kuma hakan ba ya nuna bama tare da haɗin kai ko kusanto da juna .
Wannan ra'ayina ne kuma kowa yana da ikon faɗin albarkacin bakinsa .
Ni nake da alhakin rubutuna mai karatu kuma shi ne zai ɗauki alhakin duk fahimtar da yayi min .
✍️Masoyin Al-shaikhul Mufid Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv
9 / Safarul Khair / 1448H - 24 / 7 / 2026 miladiyya. | 82 |
| 9 | BA HANA AMFANI DA SUNAN SHI'A BANE MAFITA HANA AMFANI DA SUNAN SHI'A WAJEN RARRABA KAN MUSULMI SHI NE DAI-DAI !!!
1 . Tabbas Allah Ta'ala ya siffanta Annabi Ibrahim da sauran Annabawa (A.S) da musulmi , amma hakan ba ya nuna cewa su ba muminai ba ne , ko su ba mukhlasai ba ne , ko su ba hanifai bane .... Kamar yanda a wata ayar ya kira Annabi Ibrahim da Shi'a, domin - bisa zance na tahƙiƙi a wurin malamai - sifa ba ta da mafhumi kamar laƙabi take mafhumi su ba hujja bane.
Shi yasa Allahn da ya siffanta su da Musulmi shi ne kuma a wasu ayoyin ya siffanta su da Mukhlasai, a wasu ayoyin kuma hanifai , a wasu ayoyin kuma da Muminai da sauran siffofi masu girma ..saboda yawaitar suna ko sifa yana nuna daraja da ɗaukakar ma'abocinsu.
2 . Kamar yanda siffanta Musulmi da wannan sifa ko laƙabi ba ya nuna haramci ko rashin kyautatuwar siffanta su da wani suna bayan wannan ko kuma yana kore ya zama suna da wani laƙabi ko suna na daban , ƙa'ida ce zaunanniya ta hankali cewa "Tabbatar da wani abu ba ya kore waninsa" إثبات الشيء لا ينفي غيره kowanne abu da mahallinsa.
3 . Ko da an ɗauka kalmar Musulmi sunan yanka ne ga duk wanda yayi kalmar shahada biyu , hakan ba ya hana ya zama sunaye da laƙubba da matakai mabanbanta , domin shi Musulunci ba komai bane face maudhu'i na hukunce-hukunce kamar haramta jinin mutum da dukiyarsa da halascin aurensa da sauran su .
4 . Bugu da ƙari dalilai masu tarin yawa - bayan Alƙur'ani - sun tabbatar da wani suna ko laƙabi ga wasu Musulmi saboda daraja ko hususiyarsu , kamar Muminai , ƴan Shi'a ,Rofidhawa ... Kuma shi sunan ƴan Shi'a halsataccen suna ne garesu daga Annabi (Saww) da iyalan gidansa tsarkaka , bari ma ya tabbata a hadisai masu tarin yawa suna kiran mabiyansu da ƴan Shi'a , suna masu cewa ƴan Shi'ar mu kaza da kaza , ƴan Shi'ar mu su ne masu kaza , kuma ba wai kawai siffantasu suke da haka ba a muƙamin magana sun ayyana musu waɗannan sunaye ne kai tsaye.
Domin kuwa ya zo a hadisai masu tarin yawa lokacin da wasu maƙiya Shi'a suka matsa da tsokanar ƴan Shi'a ko kiran ƴan Shi'a da sunansu na Rafidha , sun kawowa Imam Muhammadul Baƙir (AS) koke wata rana sai yace : Nima Rafhidi ne kuma ina daga cikin su , a wani hadisi an bayyana musu tun zamanin Annabi Musa (A.S) ake kiran waɗanda suka kangarewa ɓarna da wannan suna , a wani hadisi na Allah ne ya kira su da wannan sunan.
5 . Don haka idan muka ce za mu dena kiran kanmu da sunan da Allah da Manzon Allah (SAWW) da limaman shiriya suka raɗa mana - saboda kauda saɓani ko haɗin kai - to ai ba iya suna ba gaba ɗaya aƙidar za mu dena yi ; saboda ba sunan bane matsalar abinda aka sawa sunan ne matsala kenan , shi suna take ne mai bada labari , don ka ce a dena kiran ka Shi'a amma ka ci-gaba da Aƙida , ibada da mu'amala irin na Shi'a bata sauya zani ba , ba cinya ba kafar baya kenan.
Dole ka dena zaman Ashura ; don shima take ne na Shi'a a duniya , dole ka dena magana irin ta Shi'a ko saka.kaya irin na Shi'a ko malaman Shi'a , dole ka dena komai ka koma kamar zamanin da aka saukar da aya ta farko ga Annabi (SAWW) kafin a fara saukar da hukunce-hukunce.
Kainko ka koma hakan saɓani ba zai kau ba domin sunnar Allah ce a cikin halitta , ba za su gushe ba suna masu saɓani ... na'am hakan ba zai hana ayi ƙoƙarin haɗin kai da kusanto da juna , amma haɗin kai ba ya nufin kowa ya shafe "Huwiyyarsa" gaba ɗaya.
6 . Wannan ya nuna mana shi sunan Shi'a a kankin kansa ba shi bane matsala idan ana so a yi da'awa ga mutane , amfani da sunan Shi'ar wajen kawo rarrabuwa shi ne illah kuma shi ya kamata a kira a hana su , kuma wannan itace fikirar malaman Shi'a kaf ɗinsu (Musamman Sayyidunal Khumaini da Sayyid Khamene'i Allah ya ƙara musu yarda) bayanan su da littattafan su cike suke da hakan.
Tabbas duk wanda ya koma maganganun waɗannan jagororin fikrar Musulunci zai ga suna bayani a kan haɗarin fakewa da sunan Shi'a ko aƙidar Shi'a wajen kawo rarrabar Musulmi , amma ba za ka samu suna cewa ku dena kiran kanmu Shi'a , abu ne da ba zai taɓa yiwuwa ba su faɗi hakan , duk da wasu maƙiyansu suna tuhumarsu da hakan saboda suma basu fahimce su ba kamar wasu | 83 |
| 10 | Imam Hassan (a.s) ya rayu tsawon shekaru 47 , tare da Imamancin Shekaru goma , tun bayan Shahadar mahaifinsa Imam Ali (a.s.) a shakara ta Arba'in (40) bayan hijira , shi kuma Imam Hassan ya rasu a ranar bakwai ga watan Safar shekara ta Hamsin bayan Hijira , A wata ruwayar kuma ; 28 ga watan Safar ne ranar shahadar Imam Hassan (a.s.) .
السلام عليك أيها المظلوم الشهيد ورحمة الله وبركاته ومغفرته
✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv
7 / Safar/ 1444H - 24/8/2023 Miladiyya | 91 |
| 11 | SHAHADAR IMAM HASSAN AL-MUJTABA (A.S.)
A ranar bakwai ga watan Safar , shekara ta 50 bayan Hijira , babban jikan Manzon Allah (saww) , limami na biyu daga jerin Limaman shiriya, Karimu Ahlil baiti , Imam Hassan ɗan Imam Ali da Sayyida Fatima (a.s) yayi shahada a garin Madina .
Tun bayan yarjejeniyar da akayi tsakanin Imam Hassan (a.s) da Mu'awiyah ɗan Abi Sufyan (L), Mu'awiya ya cigaba da warware waɗannan sharuddan da aka gindaya masa , har ta kai ga yazo ya amshi caffa ga ɗansa Yazidu , a matsayin yarima mai jiran gado , wanda hakan ya saɓawa yarjejeniyar da akayi dashi. Daga cikin Sharuɗɗan shine zai ci gaba da gudanar da harkar Gwamanti , idan ya mutu to al'amari zai dawo wajen masu shi ko Imam Hassan ko Imam Hussain (a.s.) , amma bai iya cika wannan alƙawari ba . Abul Faraj ya rawaito cewa :
Tun sanda aka gama sulhu tsakanin Imam Hassan (a.s) da Mu'awiyah (L), sai Mu'awiyah ya tara wasu mutanensa yace musu ; Sulhun da muka yi da Hassan na takeshi a ƙarƙashin ƙafata , kuma Ni ai ba don Sallah ko Azumi Ko Zakka da Hajji nake wannan rigimar ba , mulkin nan na kakannina nakeso , kuma gashi ya dawo hannuna .
Ta ɓangaren Imam Hassan (a.s ) ya shagaltu da ibada da shiryar da mutane da karantar dasu Addini na haƙika , sai ya zama Gwamanti tana hannun Mu'awiya , mutanen Allah da zuciyoyinsu suna tare da Imam Hassan (a.s) , hakan ya cigaba da ƙuntatawa Mu'awiyah (L) sosai , daga nan ya shiga kokarin ganin ya kawar da Imam Hassan (a s.) baki ɗaya don mulki ya cigaba a zuriyarsa yadda ya tsara ba tare da cikas gareshi ba .
Yayi ta sawa ana bawa Imam Hassan (a.s) guba yana sha , amma Allah yana tseratar da Imam Hassan (a.s.) daga sharrinsa , sai a ƙarshe da ajalin Imam Hassan (a.s) yayi , Mu'awiya ya biya matar Imam Hassan (a.s) don ta shayar dashi guba ƴar Rum, tare da yi mata alƙawuran da bai cika mata ba , kamar aura mata Yazidu da samun ɗinbin dukiya mai yawa . Haka ko tayi masa abinda yake so , ta shayar da Imam Hassan (a.s) wannan guba da Mu'awiya (L) ya bata , lokacin da Imam Hassan (a.s) yake ƙoƙarin bude baki yayin da yayi Azumi .
Daga nan ne wannan gubar ƴar Rum ta kwantar da Imam Hassan (a.s) na ƴan wasu kwanaki , tana yawo cikin jininsa da jijiyarsa da namansa , har ta kai ga ta fara farfasa masa ƴaƴan hanjinsa ! Imam Hassan (a.s) ya dinga aman jininsa da hantarsa saboda ƙarfin wannan gubar da tasirinta, daga ƙarshe yayi wasiyyoyi ga ɗan uwansa Imam Hussain (a.s) , sannan ya koma ga Ubangijinsa a matsayin shahidi abun zalunta .Allahu Akbar !!!
An rawaito cewa ; Lokacin da Imam Hussain (a s.) ya ɗauki gawar Imam Hassan mai tsarki, da nufin binneta a maƙabartar Baki'u kamar yanda Imam Hassan (a.s) yayi masa wasiyya , cewa ya fara kaishi wurin Annabi kakansa suyi bankwana , sannan ya tafi dashi can ya binne shi a kusa da kakarsa Sayyida Fatima Bintu Asad. Sai Marwan Binil Hakam (L) ya ɗebo yaransa Umayyawa suka tare Imam Hussain (a.s) a hanya , suna tsammanin zai binneshi kusa da Annabi (saww) ne , suna cewa ai muma ba'a bari mun binne Usman bn Affan a kusa da Annabi ba don haka kuma baku isa ba .
Da labari ya isa ga matar Manzon Allah (saww) , Aisha bintu Abi Bakr, sai ta hayo kan Alfadara kamar yanda ta hau raƙumi a yaƙin Jamal , tazo tana cewa ; Nima bazan yardaa ku binne min wanda banaso ba a ɗaƙina ba sam , wuri ya yamuste da rikici da hayaniya , har ta kai ga an fara harbin gawar Imam Hassan (a.s) da kibiya ! Sai Imam Hussain (a.s) ya aiwatar da wasiyyar ɗan uwansa Imam Hassan (a.s) , ta kar ya bari a sheƙar da jini a lokacin jana'izarsa , take suka juya aka tafi can Maƙabartar Baƙiy , aka binne Imam Hassan kusa da kakarsa Sayyida Fadima Bintu Asad (Mahaifiyar Imam Ali ) tsira da Amincin Allah su ƙara dawwama a gare su baki ɗaya .
Kafin Imam Hasan (a.s) ya cika , a ko da yaushe Imam Husain (a.s.) yana shiga wajensa , har suyi ta kuka da jimamin halin da suka shiga tun bayan rashin kakansu Annabi da Mahaifansu , Imam Hasan (a.s) ya kasance yana cewa ; Wannan ne abinda kakanmu Manzon Allah (a.s) yace zai samemu , lallai ya gaskata a cikin zancensa . | 95 |
| 12 | "Duk al'umar da suka zaɓi shiru da ɗaukar ƙasƙanci tabbas za su zama bayin azzalumai"
✍️Al-Abdul Faneey Al-kanaweey | 127 |
| 13 | ISOWAR IYALAN GIDAN MAZON ALLAH (SAWW) CIKIN GARIN SHAM !!!
A ranar 1 ga watan Safar ɗin shekara ta 61H , sojojin Umayyawa suka shigo da ayarin zuriyar Manzon Allah cikin garin Sham ta ƙofar "Bab al-Sa’at (Bab Touma) inda kan Imam Husain (a.s) yake sahun gaba a tsire a kan dogon mashi da sauran kawukan da aka yanke a Karbala , dama jerin gwanon mata da yara na daga zuriyar Annabi (saww) , sun shiga gaban Imam Ali Zainul Abidin (a.s) a lokacin da aka ɗaure hannunsa da sarƙoki .
Daga ɓangaren mutanen garin Sham kuwa , sun caɓa ado sun fito tarbarsu da kiɗe-kiɗe da raye-raye da murna da farin ciki , fiye da yadda suke yi ranar Idi , masu jifa nayi , masu zagi nayi , masu ihu da shewa nayi ta ko ina .
السلام على جبل الصبر زينب 😭
✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv | 185 |
| 14 | SHAHADAR BABBAN SAHABIN ANNABI HUZAIFATU IBNUL YAMAN (R.T.A)
A ranar 28 ga watan Muharram , shekara ta 36 bayan hijirar Annabi (s) , babban sahabin nan Huzaifatul yamani yayi wafati.
GA TAƘAITACCEN TARIHINSA :
Shine Abu Abdillah , Huzaifah bin Hisal (Husayl) bin Jabir bin Amr bin Rabi'ah.
Mahaifinsa kuwa shine Husail bin Jabir , shahararren sahabi .
Mahaifiyarsa itace : Al-Rubab bint Ka'ab bin Adi bin Abdul Ashal, daga Ƙabilar Aus , mutuniyar Madina .
Ƴa'yansa: Su ne Sa'ad bin Huzaifa bin Al-Yaman, wasu suka ce Saeed ne sunansa , Sai Safwan bin Huzaifa bin Al-Yaman , Da Husail bin Huzaifa bin Al-Yaman.
Da Abu Ubaidah bn Hudhaifa bn Al-Yaman, wanda shine Bilal .
An ruwaito cewa an kashe Sa'ad ko Sa’eed da ɗan uwansa Safwan ‘ya’yan Huzaifa bin Al-Yaman tare da Imam Ali (a.s) a Siffin, kuma sun yi mubaya’a ga Imam Ali (a.s). bisa wasiyyar mahaifinsu.
Huzaifa yana daga cikin fitattun manyan sahabban manzon Allah (saw) masu daraja , shine ma'abocin sirrin Annabi , kuma mafi sanin mutane akan lamarin munafukai , domin shi Annabi yake sanarwa da sunayen munafukai . Ya halarci yaƙin Uhudu da sauran yakoƙin da suka biyo baya , kuma yana daga cikin wadanda suka yi tsayin daka a kan imaninsu , suka tabbata a bayan wafatin Manzon Allah (saww) .
Ya kasance tare da Imam Ali (a.s.) kasancewa ta gaskiya , kuma yana daga cikin tsirarun mutanen da suka halarci jana'izar Sayyida Fatimatuz Zahra (a.s) , ya kuma tsaya akan gawarsa Mai tsarki yayi mata sallah .
Ya yi Gwamnan garin Mada'in a zamanin Umar da Usman, kuma ya yi rashin lafiya a farkon halifancin Amirul Muminina Imam Ali (a.s), dauk da wannan bai iya yin shiru ba , ya kasance yana faɗar falaloli da darajojin Imam Ali , har ya hau mimbari yana halin rashin lafiyarsa , ya yabi Imam Ali , yayi masa kirari , sannan yace : Wallahi Ali yana kan gaskiya a ƙarshe da farko . Ya kuma ce : Ali ne mafi alherin mutane bayan Annabinku. Ya karɓarwa Imam Ali bai'a , kuma shima da kansa ya yi masa mubaya'a, ya kuma yi wasiyya ga 'ya'yansa, yana mai jaddada cewa kada su yi kasa a gwiwa wajen bin Imam Ali (a.s.) ko bayan ransa .
Huzaifa yana da tarin matsayi da daraja da falala a cikin wannan al'umma , ya isheshi matsayi da daraja kasancewarsa cikin keɓantattun Imam Ali (a.s.) , sannan mataimakinsa tun a farkon al'amari ta yadda dashi akayi jana'izar Sayyida Fadima (a.s.) . An karɓo daga Manzon Allah (saww) ya ce: “Huzaifa ɗan Yaman yana daga cikin zaɓaɓɓun Allah Arrahamanu . Sannan Annabi ya haɗashi ƴan uwantaka da Ammar bn Yasir a Madina .
Bayan wafatinsa an binne shi a garin Mada'in dake ƙasar Iraƙi , a yanzu haka ƙabarinsa yana kusa da ƙabarin Sahabin nan Salmanul Farisi , dama Abdullahi bin Jabirul Ansari da Aliyuɗdahir .
A shekarar 1933 aka dakko Huzaifa aka dawo dashi wannan wurin da yake a yanzu , aka sake binne shi saboda matsalar ambaliyar ruwan Dijla, a lokacin anga gawarsu lafiya kalau tana haske da sheƙi kamar ranar aka binne su , duk an share sama da shekaru dubu da yi musu binnewar farko , anyi gagarumin taro a kasar Iraki ranar da aka kawo su kusa da Salmanul Muhammadi , kuma manyan karamomi sun bayyana ga mutane . Sannan har yanzu suna wurin ana ci gaba da ziyararsu a unguwar da katangar Kisra take .
✍️ Khadimu ã'atabi ãli Muhammad Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv
28/ Almuharramul Haraam - 27/8/2022 | 167 |
| 15 | Ba a Karbala gwagwarmayar ta fara ba kuma ba ta ƙare da kashe Imam Husaini ba !!!
https://t.me/tafarkintsiratv | 122 |
| 16 | SHAHADAR IMAM ALIYU ZAINUL ABIDIN (ALAIHIS SALÃM)
Ya zo a hadisi cewa Imam Ali Zainul Abidin (a.s) ya yi kukan shakara 25 ko 40 saboda kisan gillar da aka yiwa mahaifinsa Imam Husaini ( Alaihis salãm) da danginsa a Karbala.
Wata rana wani daga cikin barorinsa ya gan shi ya jiƙe fuskarsa da gamunsa mai albarka da hawaye sai yace masa : Ya shugabana shin lokaci bai yi bane da baƙin cikinka zai yanke haka nan kukanka ya ƙaranta ? Sai Imam Sajjad yace da shi : Kayi hattara! Lallai Ya'aƙubu ɗan Ishaƙ ɗan Ibrahim ya kasance Annabi ɗan Annabi kuma yana da ƴaƴa goma sha biyu , sai Allah ya fakar da guda ɗayansu , amma sai da kansa yayi furfura saboda baƙin ciki , haka nan bayansa ya ranƙwafa saboda damuwa da ƙunci kuma ganinsa ya tafi saboda kuka alhalin ɗan nasa yana raye a gidan Duniya , Ni kuma naga babana da ɗan uwana tare da mutum sha bakwai daga dangina an musu kisan gilla ta yaya baƙin cikinna zai yanke kuma na dena kuka ?!
An ruwaito tun bayan waƙi'ar Karbala ba a taɓa ajiye abinci da ruwa gabansa ba face sai ya jiƙa shi da hawaye saboda abinda aka yiwa mahaifinsa da danginsa a saharar Karbala .
A wani hadisin Imam Ja'afar Assadiƙ (A.S) yana cewa : Al-bakka'ūn (Masu yawan kuka a duniya) biyar ne , Adamu , Ya'aƙubu , Yusufu , Faɗimatu bintu Muhammad da Aliyu bin Husaini (a.s) .
Tabbas Imam Ali Zainul Abidin (a.s) ya tsaya tsayin daga wajen raya al'amarin Ashura da Karbala da kuma sanar da Musulmi har tashin alkiyama mazlumiyyar su (Ahlul Baiti) ta hanyar amfani da salo daban-daban da kuma matakai mabanbanta duk da yanayin da ya sami kansa mai wahala , bugu da ƙari ya sadaukar da rayuwarsa wajen isar da saƙon Musulunci na haƙiƙa da sanar da duniya matsayinsu hatta a cikin salo na addu'a da munajati , kuma yakan sayi bayi ya ƴanta su sannan ya sanya su bazama sassan duniya domin karantarwa bayan ya raine su , in ko ana maganar gudun duniya , sanin Allah , jarumta , kyauta , ibada , sadaka , da duk wani halin girma da tadojin kirki shi maƙura ne .
Imam Sajjad (a.s) ya yi shahada a garin Madina mai girma a ranar 25 ga watan Al-Muharram ɗin shakara ta 95 bayan hijira , watau shakara 35 da waƙi'ar Karbala .
✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv | 177 |
| 17 | "سليل الكرام"
غاب نجمٌ وصفوةٌ في الأنامِ
خمنئيُّ العلى سليلُ الكرامِ
ليس يسلي الفؤادَ عن حرّ حزني
غيرَ يوم الظّهورِ والانتقامِ
يا لها من فجيئةٍ كدتُ أسقى
من لظى شجوها كؤوسُ الحِمامِ
كيف غطّى التّرابُ وجهَك يا من
شرّف الأرضَ بالصّلا والصّيامِ
كيف يخبو نور النّضال وقد كا
ن منارًا لنا مدى الأعوامِ
آيةَ الله كنتَ في الففهِ والفكـ
ـر وصونِ البلادِ دون انخرامِ
يا ملاذَ الضّعيفِ شرقًا وغربًا
من بكتْ فقدَه عيونُ الغمامِ
كلّ شبرٍ بكاكَ في الأرض شجوًا
من زُبى قدسِنا لدار السّلامِ
أيّ شوقٍ يجتاحني وحنينٍ
لشهيدٍ أذلّ جيشَ الطّغامِ
قد ملأتَ الفؤادَ حبّا وفخرًا
راسخًا في الحشا كشدّ العظامِ
كنتَ في المكرماتِ رمزًا عزيزًا
وصراطًا للحقّ يومَ الصّدامِ
فقدكم ثلمةٌ عديمةُ سدّ
غرق الكونُ بعدها في الظّلامِ
من لنا سيّدي فتي الحربُ عادتْ
كيف نقضي على حبالِ الخصامِ !
أيّها القائدُ العظيمُ سلامٌ
من قلوبٍ تذوبُ قبل الكلامِ
قد رثتكَ الأحرارُ من كلّ أرضٍ
يا زعيمَ النّضال بينَ الأنامِ
موضعُ العهد في القلوبِ حصينٌ
ثابت لا يزولُ حتّى الختامِ
ليس من شأننِا التراجعُ حتّى
لو رُمينا بجمرةٍ وسهامِ
نحن ماضون مثلما كنتَ تبغي
ومصرّون في شديد اعتزامِ
في سبيلِ الهدى ندوسُ المنايا
ونصونُ الطّريقَ من كلّ رامِ
في أمانِ الإلهِ يا بن عليٍّ
وابن ياسين بلسمَ الأسقامِ
ذا وداعي والدّمعُ يجري بدَفقٍ
ولهيبِ الأسى وهجرِ المنامِ
ذا وداعي بصرخةٍ وعويلِ
في قريضِ الرّثا ودمعِ القلامِ
نمْ قريرَ العينينِ فالنّهجُ باقٍ
في قلوبِ الرّجال والأعلامِ
وعليك السّلام ثمّ التّحايا
يا رئيسَ النّضالِ نجلَ الكرامِ
✍️خادم العترة الطّاهرة
️ العبد الفاني
الكنوي
٢٤ / المحرم الحرام / ١٤٤٨هـ | 148 |
| 18 | ƘARYA FURE TAKE BATA ƳAƳA
Wai ƴan Shi'a suna yin murna da kashe Imam Ali in ji wani mabiyin addinin Wahhabiyawa!
🎙️ https://t.me/tafarkintsiratv | 147 |
| 19 | TUNAWA DA HARIN SAMARRA
A ranar 23 ga watan Al-muharram shekara ta 1427 bayan hijira , dai-dai da (22 ga watan Fabrairu , 2006 AD). Ƴan ta'addan Wahhabiyawa masu kafirta mutane suka kai harin bama-bamai a garin Samarra dake ƙasar Iraki , inda suka rusa ƙubbar zinare dake ƙabarin Imam Aliyul Hadi da Imam Hasan Al-askari da Sayyida Narjis da Sayyida Hakima suke kwance , tare da abubuwan tarihi masu muhimmanci da daraja , suka yi mummunar ɓarna da aikin ta'addanci .
Garin Samarra , gari ne mai cike da abubuwan tarihi , a nan kurkukun da aka saka Imam Aliyul Hadi da Imam Askari (A.S) take , wanda duk mai imani in yaga wannan kurkuku sai ya zuba hawaye , da gidansu Imam Mahdi (a.j.)anan garin yake shima . Kuma dama nan ne babban birnin Daular Abbasiyyawa L da cibiyarsu , anan suka ci karensu ba babbaka na tsawon shekaru bayan sun baro birnin Bagadaza .
Alhamdulillahi , duk waɗanda suka yi ta shirya wannan shegantakar garin ya gagare su zama kuma ga ƴan Shi'a ba ci gaba da zuwa ziyara .
✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
https://t.me/tafarkintsiratv | 142 |
| 20 | SHAHIDI NA FARKO BAYAN WAƘI'AR KARBALA
(ABDULLAHI BIN AFIF AL-AZDI)
- Me ka sani game dashi ???
Abdullahi bin Afif Al-Azdi Al-Ghamidi (Allah ya kara masa yarda) , yana daga cikin manyan sahabban Amirul Muminin Ali bin Abi Ɗalib (a.s.), ya rasa idonsa na hagu a yakin Jamal dana dama a yakin Siffin yana cikin rundunar Imam Ali , bayan da ya rasa idanuwansa biyu sai ya shagaltu da bautar Allah tsantsa , kuma ya kasance daga cikin manyan bayin Allah masu zuhudu a garin Kufa .
Ya kasance a cikin masallacin Kufa majlisin da Ibnu Ziyad (Allah Ya la'ance shi) ya shirya , lokacin da aka kawo Imam Sajjad da Sayyiida Zainab da sauran zuriyar Annabi (s) kufa , a matsayin ribattatun yaƙi da fursunonin Yazidu L , bayan an kashe Imam Hussain da kwana biyu .
Sai Gwmanan Kufa Ibnu Ziyad (L) yace : Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya bayyanar da gaskiya da mutanenta, ya taimaki Amirul Muminin (ma'ana Yazidu ) da mabiyansa, kuma ya kashe makaryaci dan makaryaci (yana nufin Amirul Muminin Imam Ali da Imam Hussein ) , wai sune maƙaryata !
Jin haka ke da wuya sai Abdullahi bin Afif ya tashi a tsakiyar mutane ya cewa Ibnu Ziyad :
Ya kai ɗan Marjana yi mana shiru , Kai da mahaifinka da wanda ya jiɓintaka da mahaifinsa ne maƙaryata , ya kai makiyin Allah, ka kashe ‘ya’yan Annabawa (zuriyar Annabi ) kuma kana faɗin waɗannan kalmomi a kan mimbarin muminai? (Kana magana irin ta mutanen kirki bayan aikin da kayi) .
A lokacin ne sojojin Ibnu Ziyad sukayi kansa za su kamashi , sai ƙabilarsa suka hana su ta hanyar rufeshi da tada hayaniya a masallacin , ko da suka fitar da shi daga Masallacin , da ya isa gidansa sai sojojin Ibnu Ziyad suka kewaye gidansa suka karya ƙofa suka far masa. Duk da kasancewarsa makaho amma yayi yaƙi irin na mazaje , yana da wata ƴa mace mai suna "Safiyya" wacce ta dinga taya shi faɗa a cikin gidan , tana ce masa : Baba gasu nan ta damanka, Baba gasu nan ta bayanka, ko kuma daga gabanka, shi kuma yana kai sara duk ta inda tace masa ya kai sara ko duka , tana tayashi ita da wani ɗansa Namiji guda ɗaya ga shekarunsa sun ja , ya tsufa sosai .
Daga baya suka kara yawa har suka kashe ɗiyarsa Safiyya da dansa Namijin , sannan suka kama Abdullahi bin Afif suka kai shi fadar Ibnu Ziyad . Ko da ya isa fadar , sai Ibnu Ziyad yace masa : Godiya ta tabbata ga Ubangijin daya wulakantaka , sai Abdullahi bin Afif ya mayar masa da martani cikin waƙa yana cewa :
يا عدو الله ، وبماذا أخزاني الله ؟
والله لو فرج لي عن بصري
ضاق عليك موردي ومصدري
وكنت منـكم قـد شفيـت غلتي
إن لم يكن ذا اليـوم قومي تخفـر
أم كيف لي والأصبحي قـد أتى
فـي جيشـه إلى لقا الـغضنفـر
لـو بارزونـي واحـداً فواحـداً
أفنيتـم بمـوردي ومصـدري
يا ويحكم والسيف أبـدا مشرفـاً
لا ينبغـي إلا مقـر الحنجـر
ويح ابن مرجان الدعي وقد أتى
ويزيد إذ يؤتى بهم في المحشر
والحكـم فـيه للإله وخصمهـم
خير البرية أحمد مـع حيـدر
Ya cigaba da ce masa : Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai , na kasance ina roƙon Allah Ubangijina Ya ba ni shahada tun kafin mahaifiyarka ta haifeka ........ Bayan na makance sai na fidda rai daga samun shahada, amma yanzu Alhamdulillahi Allah ya azurtani da ita , ya nunan ya daɗe da amsar addu'ata .
Sai Ibnu Ziyad (Allah Ya tsine masa) yace : Kuje ku sare min kansa ! Sai kuwa aka je aka sare wuyansa kuma aka gicciye shi .😭
Ya yi shahada ne a ranar 12 ga watan Muharram, wata ruwayar kuma ance a ranar 13 ga Muharram ne , shekara ta 61 bayan hijira .
Amincin Allah ya tabbata a gare shi ranar da aka haife shi, da ranar da ya yi shahada, da ranar da za a tashe shi rayuwa kuma ƴantacce.
✍️ Khâdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
12/ Almuharramul Haraam - 11 /8/2022 . | 153 |
