en
Feedback
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY๐ŸŽฅ๐Ÿ“š๐Ÿ“—

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY๐ŸŽฅ๐Ÿ“š๐Ÿ“—

Open in Telegram

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

Show more
2 292
Subscribers
+124 hours
+77 days
+3730 days
Posts Archive
ME YASA KUKE DAMUWA DA ABINDA YA FARU A KARBALA BAYAN YA RIGA YA WUCE ALLAH NE ZAI YI HISABI ?!! https://t.me/tafarkintsiratv

Karbala ba labari bane na wani tarihi da ya ruga ya shuษ—e , gamammiyar makaranta ce mai cike da iznar da duk ษ—an Adam yake bu
Karbala ba labari bane na wani tarihi da ya ruga ya shuษ—e , gamammiyar makaranta ce mai cike da iznar da duk ษ—an Adam yake bukatar komawa gareta har ranar tashin ฦ™iyama. Tabbas Karbala fitila ce mai haskaka rayuwa. โœ๏ธ Khรฃdimul Ashrรฃf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

LABARAN KARBALA DA ASHURA (61H) . -Isowar Umar bin Sa'ad Karbala A ranar 3 ga watan Almuharram shekara ta 61 bayan hijira , Umar ษ—an Sa'ad ษ—an Abi Waฦ™kas ya iso filin karbala da rundunarsa mutu dubu huษ—u wani ฦ™aulin dubu Talatin , bisa umarnin Gwamnan Kufa Ubaidullahi ibnu Ziyad cewa in ya kashe Imam Hussaini (a.s) zai bashi Mulkin garin (Raiy) . - Shirye-shiryen Rundunonin Banu Umayyah A safiyar yau ne sansanin Annakhilah ya zama sansanin sojojin Umayyawa don yaฦ™ar Imam Hussain (a.s), an bada umarnin kaddamar da rundunoni kamar haka : 1. Naษ—a Shammar bin Zhul-Jaushan al-Kilabi ya jagoranci bataliyar mayaฦ™a 4,000 sannan ya nufi Karbala nan take. 2 . Bawa al-Husayn bin Namir al-Hamsi jagorancin bataliyar mayaฦ™a 4,000 tare da garzayawa Karbala nan take. 3. Sanya Kaโ€™b bin Dalha ya jagoranci bataliyar mayaฦ™a 3,000 sannan ya nufi Karbala nan take. 4. Naษ—a Mudayir Al-Mazini ya jagoranci bataliyar mayaka 3,000 sannan ya nufi Karbala nan take. 5. Naษ—a Nasr bin Harsha ya jagoranci bataliyar mayaฦ™a 3000 sannan ya nufi Karbala nan take. 6. Naษ—a Yazid bn Rikab jagorancin bataliyar mayaka 2000 da garzayawa zuwa Karbala nan take. 7. Sanya Shabath bin Rabiโ€™i ya jagoranci bataliyar mayaฦ™a 2000 sannan ya nufi Karbala nan take. 8. Naษ—a Hajjar bin Abjar ya jagoranci bataliyar mayaka dubu daya da gaggawar zuwa Karbala. 9. An umarci Al-Jaafi ya zauna tare da wata rundunar tsaro da ta ฦ™unshi mayaka dubu a kewayen gadar kogin Sarat (arewacin Kufa) , don hana kabilar Azd da Hamdan kaiwa Imam Hussain (a.s) ษ—auki a Karbala. 10- Suwaid Al-Munqari zai ci gaba da kula da harkokin tsaro a Kufa. Dukkanin rukunin sojojin suna ฦ™arkashin kwamandan Sojoji Umar Ibn Sa'ad Ibn Abi Waqqasn L ne. Wasu daga fitattun bataliyoyi masu dauke da makamai da suka taka rawa wajen kashe Imam Hussain (a.s.) , kuma sun yi raunuka da dama a jikin Abul Fadl Al-Abbas (a.s.) lokacin da ya kutsa su . 1. Jar Bataliyar Dailam Ta ฦ™unshi mayaka dubu 4, kuma Shammar ne ke jagorantarsu, waษ—anda suka fito daga garin Rayy suka zauna a Kufa, sun kasance maฦ™iya Ahlul Baiti (a.s) kuma sune rabin mutanen Kufa. Masu kula da al'amarin tsaron cikin gida a gwamnatin Ibn Ziyad, kuma sun taka rawa wajen kashe Muslim bn Aฦ™il (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) , sannan sun riฦ™e manyan muฦ™amai na gudanarwa a garin Kufa . Sun kasance masu sa ido a kusa da kufa , domin katse duk wani ษ—auki da za'a iya kawowa Imam (a.s) a kwanakin farko , daga bisani kuma suka shiga Karbala suka yi yaki har aka kashe Imam Husaini (a.s). 2. Busasshiyar Bataliya , Sham : Ita ce bataliyar Al-Hosayn bn Numair al-Homsi L , mutum ne da jamiโ€™an leฦ™en asirin (Rum) suka horar da shi ta hanyar (Sargon) mutumin Rum, wanda shi ne wakilin gwamnatin Rum a Gwamantin Muโ€™awiya L . Malaman tarihi sun haษ—u akan cewa ; Sargon ne ya bawa Yazidu shawarar kashe Imam (a.s.) koma ya masa umarnin hakan , wannan busasshiyar bataliya wata bataliya ce ta musamman wacce Gwamnatin Rum ta horar. Dukkansu sun haษ—u don su kashe jikan Manzon Allah (saww) da baida mataimaka , ba sojoji ba mayaฦ™a face mutanen da basu wuce 80 ba . ุงู„ุณู„ุงู… ุนู„ู‰ ุงู„ู…ู‚ุชูˆู„ ุตุจุฑุง ๐Ÿ˜ญ โœ๏ธ Khรฃdimul Ashrรฃf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 3/Almuharram/1444H - 21/7/2023 Miladiyya. https://t.me/tafarkintsiratv

"ุดูŽู‡ู’ุฑู ุงู„ุดู‘ูุฌููˆู’ู†ู" ู‡ูŽู„ู‘ูŽ ุดูŽู‡ู’ุฑู ุงู„ุดู‘ูุฌู’ูˆู’ู†ู ููŽูˆู’ู‚ูŽ ุงู„ู’ุจูŽุฑูŽุงูŠูŽุง ุฌูŽุฏู‘ูŽุฏูŽ ุงู„ู’ุญูุฒู’ู†ูŽ ูˆูŽุงู„ู’ุจููƒูŽุง ูˆูŽุงู„ู’ุจูŽู„ูŽุงูŠูŽุง ูŠูŽุง ู‡ูู„ูŽุงู„ูŽ ุงู„ู’ุญูŽุฑูŽุงู…ู ุญูŽุฑู‘ูŽู…ู’ุชูŽ ู‚ูŽู„ู’ุจููŠู’ ุทููŠู’ุจูŽ ุนูŽูŠู’ุดู ูˆูŽุฑูŽุบู’ุฏูู‡ู ุจูุงู„ุฑู‘ูŽุฒูŽุงูŠูŽุง ูŠูŽุง ู‡ูู„ูŽุงู„ูŽ ุงู„ู’ุญูŽุฑูŽุงู…ู ุฃูŽูˆู’ุฌูŽุนู’ุชูŽ ู‚ูŽู„ู’ุจููŠู’ ูˆูŽุณูŽุฑูŽู‰ ุงู„ู’ูˆูŽุฌู’ุนู ูููŠ ุงู„ุฏู‘ูู…ูŽุง ูˆูŽุงู„ู’ุฎู’ู„ูŽุงูŠูŽุง ูƒูŽูŠู’ููŽ ู„ูŽุง ุจูŽุนู’ุฏูŽ ุฐูŽุจู’ุญู ู†ููˆู’ุฑู ููุคูŽุงุฏููŠู’ ูููŠู’ูƒูŽ ุฐูŽุจู’ุญู‹ุง ูƒูŽุงู„ู’ูƒุจู’ุดู ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ุงู„ุถู‘ูŽุญูŽุงูŠูŽุง ู‡ูŽู„ู’ ุณูŽู…ูุนู’ุชูู…ู’ ุจูู‚ูŽุชู’ู„ู ุฅูู†ู’ุณู ูŠูุฌูŽุฒู‘ู ู…ูู†ู’ ู‚ูŽููŽุงู‡ู ุบูŽูŠู’ุฑูŽ ุงู„ู’ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ุจูŽุฑูŽุงูŠูŽุง ุŸ ุจูŽุงุชูŽ ุทูุนูู…ูŽ ุงู„ุณู‘ููŠููˆู’ูู ูููŠู’ ุงู„ู’ููŽู„ูˆูŽุงุชู ู‡ูู…ู’ ุฃูู„ููˆู’ููŒ ุญูŽุงุทููˆู’ุง ุจูู‡ู ู…ูู†ู’ ุฌูŽุฏูŽุงูŠูŽุง ุฃูŽุซู’ุฎูŽู†ูŽุชู’ู‡ู ุงู„ู’ุฌูุฑูŽุงุญู ู…ูู†ู’ ุถูŽุฑูŽุจูŽุงุชู ุทูŽุนูŽู†ููˆู’ู‡ู ุจูุงู„ุฑู‘ูู…ู’ุญู ุจูŽูŠู’ู†ูŽ ุงู„ุซู‘ูŽู†ูŽุงูŠูŽุง ุทูŽุนูŽู†ูŽุงุชู ุงู„ู’ุฃูŽูˆู’ุจูŽุงุดู ูููŠู’ ุตูŽุฏู’ุฑูู‡ู ู‚ูŽุฏู’ ุดูŽู‚ู‘ูŽู‚ูŽุชู’ ู‚ูŽู„ู’ุจูŽู‡ู ุจููƒูู„ู‘ู ุงู„ุฒู‘ูŽูˆูŽุงูŠูŽุง ุธูŽู„ู‘ูŽ ูŠูŽุญู’ู…ููŠู’ ุญูู…ูŽุงู‡ู ู…ูู†ู’ ูƒูู„ู‘ู ุตูŽูˆู’ุจู ุฌูŽุงู„ูุณู‹ุง ุชูŽุนู’ุชูŽุฑููŠู’ู‡ู ุฃูŽูŠู’ุฏููŠ ุงู„ู’ุฌูŽู†ูŽุงูŠูŽุง ู†ูŽุงุกูŽ ู†ูŽูˆู’ุกู‹ ูˆูŽูƒูŽุจู‘ูŽ ุถูŽุฑู’ุจู‹ุง ูˆูŽุนูŽุทู’ุดู‹ุง ู„ูŽุง ูŠูุทููŠู’ู‚ู ุงู„ู’ูˆูู‚ููˆู’ููŽ ู†ูŽุฒู’ูู‹ุง ุชูŽุนูŽุงูŠูŽุง ุญูŽุฑู‘ูŽุถูŽ ุงู„ู’ู‚ูŽูˆู’ู…ูŽ ุงูุจู’ู†ู ุณูŽุนู’ุฏู ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ู ุฐูŽุจูŽุญูŽ ุงู„ุณู‘ูุจู’ุทูŽ ุดูŽู…ู’ุฑู ุงูุจู’ู†ู ุจูŽุบูŽุงูŠูŽุง ูˆูŽู‡ู’ูˆูŽ ู…ูู†ู’ ุณูŽุงุฏูŽุฉู ุงู„ู’ุฃูŽู†ูŽุงู…ู ูˆูŽู„ูŽูƒูู†ู’ ุฏูŽุงุณูŽุชู ุงู„ู’ุฎูŽูŠู’ู„ู ุฌูุณู’ู…ูŽู‡ู ูˆูŽุงู„ู’ู…ูŽุทูŽุงูŠูŽุง ุทูŽุฑูŽุญูู€ูˆู’ู‡ู ุนูŽู„ูŽู‰ ุงู„ู’ู€ุนูŽู€ุฑูŽุงุกู ุซูŽู€ู„ูŽุงุซู‹ู€ุง ุซูู€ู…ู‘ูŽ ุณูŽู€ุงู‚ูู€ูˆู’ุง ุนูู€ูŠูŽู€ุงู„ูŽู€ู‡ู ูƒูŽุณูŽุจูŽุงูŠูŽู€ุง ู‚ูŽู€ุทู‘ูŽู€ุนูู€ูˆู’ู‡ู ุฅูุฑู’ุจู‹ู€ุง ูˆูŽุฅูุฑู’ุจู‹ู€ุง ุนูู€ู†ูŽู€ุงุฏู‹ุง ุณูŽู„ูŽุจููˆู’ู‡ู ุณูŽู„ู’ุจู‹ุง ุชูŽู†ูŽุงุณูŽูˆู’ุง ูˆูŽุตูŽุงูŠูŽุง ูƒูŽูŠู’ููŽ ุฃูŽู†ู’ุณูŽู‰ ุงู„ุทู‘ููููˆู’ููŽ ูˆูŽุงู„ู’ุบูŽุงุถูุฑููŠู‘ูŽู‡ู’ ู„ูŽุง ูˆูŽุฑูŽุจู‘ู ุงู„ุณู‘ูŽู…ูŽุงุกู ุฐูŽุง ู…ูู†ู’ ุณูŽุฌูŽุงูŠูŽุง ู„ูŽุง ูƒูŽูŠูŽูˆู’ู…ู ุงู„ู’ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ุงู„ู’ู…ูุตูŽุงุจู ู„ูŽุง ูƒูŽุฒูุฑู’ุกู ุงู„ู’ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ุฒูุฑู’ุกูŽ ุงู„ู’ุจูŽุฑูŽุงูŠูŽุง ู„ูŽุง ูƒูŽุดูŽู‡ู’ุฑู ุงู„ู’ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ุจูŽูŠู’ู†ูŽ ุงู„ุดู‘ูู‡ููˆู’ุฑู ู„ูŽุง ูƒูŽู…ูŽูˆู’ุชู ุงู„ู’ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ุจูŽูŠู’ู†ูŽ ุงู„ู’ู…ูŽู†ูŽุงูŠูŽุง ูŠูŽุง ุดูŽู‡ููŠู’ุฏูŽ ุงู„ุทู‘ููู’ูˆู’ูู ู…ูู†ู‘ููŠู’ ุฅูู„ูŽูŠู’ูƒูŽ ู†ูŽููŽุญูŽุงุชูŒ ูˆูŽุฃูŽู„ู’ูู ุฃูŽู„ู’ูู ุชูŽุญูŽุงูŠูŽุง ุตูŽู„ู‘ููŠูŽู†ู’ ุณูŽู„ู‘ูู…ูŽู†ู’ ุนูŽู„ูŽู‰ ุงู„ุณู‘ูุจู’ุทู ุฑูŽุจู‘ููŠู’ ุนูŽุฏูŽุฏูŽ ุงู„ุฑู‘ูŽู…ู’ู„ู ูˆูŽุงู„ู’ุญูŽุตูŽู‰ ูˆูŽุงู„ู†ู‘ูŽู‚ูŽุงูŠูŽุง ูˆูŽุนูŽู„ูŽู‰ ุขู„ู‡ู ูˆูŽู…ูŽู†ู’ ุจูŽุฐูŽู„ููˆู’ุง ุฃูŽุฑู’ ูˆูŽุงุญูู‡ูู…ู ูููŠู’ ุฌูู‡ูŽุงุฑู‡ูู…ู’ ูˆูŽุงู„ู’ุฎูŽููŽุงูŠูŽุง โœ๏ธุฎุงุฏู… ุขู„ ู…ุญู…ุฏ ุงู„ุนุจุฏ ุงู„ูุงู†ูŠ ุงู„ูƒู†ูˆูŠ ูฃ / ุงู„ู…ุญุฑู‘ู… ุงู„ุญุฑุงู… / ูกูคูคูฅู‡ู€

LABARAN KARBALA DA ASHURA (61H) . "Isowar Imam Hussaini Karbala๐Ÿ˜ญ" Bayan doguwar tafiya mai dogon zango data shafe kwanaki 24 (Daga Makka zuwa) , Imam Hussain (a.s.) ya iso filin Karbala da tafiyar kilomita 1403 har da garin Makka da ya baro zuwa Karbala. Imam Husaini ya iso Karbala a ranar 2 ga watan Almuharram shekara ta 61 ษ—aya hijra , yayi tafiyar kwanaki 14 a yankin Hijaz (Saudiyya) da kwanaki 9 a lardin Iraki , sai kuma saurin tafiyar kilomita 63.91 da sukan iya kaiwa a kowanne wuni . Bayan Imam Hussain (a.s.) ya isa Karbala sai aka ga dokinsa ya tsaya kuma ya cije a wurin , sai Imam Hussain ya tambaya ya sunan wannan wuri da muke ? aka ce masa : Alghadiriyya , sai ya ฦ™ara tambaya yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa : ana ce masa Nainawa , sai Imam ya kara tambaya ko yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa : ana ce masa gaษ“ar Furatu, sai Imam Hussain ya kara cewa ko yana da wani suna bayan wannan? Sai akace masa ana ce masa Karbala , sai kawai aka ga Imam Hussain ya ja numfashi ya fashe da kuka mai tsanani sai yace : Ya Ubangiji ina neman tsari a gunka daga baฦ™in ciki da bala'i, sannan yace musu : Ku tsaya anan kar ku ฦ™ara gaba daga nan inda muke , domin wallahi anan ne za'a sheฦ™ar da jinanenmu, wallahi anan za'a keta alfarmar masu alfarmarmu , wallahi anan ne za'a kashe mazajenmu , wallahi anan ne za'a kashe mazajenmu , wallahi nan za'a ziyarci ฦ™aburburanmu , wallahi a wannan turษ“ayar kakana yayi min alฦ™awari kuma alkawarinsa baya tashi . Jagoran tawagar Imam Hussain (a.s) yayi shela ga ฦดan tawagar kan su yi masauki na ฦ™arshe a wannan wuri . Zamu cigaba .... ุงู„ุณู„ุงู… ุนู„ู‰ ุงู„ู…ู‚ุชูˆู„ ุตุจุฑุง ๐Ÿ˜ญ ูŠุง ุญุณูŠู† โœ๏ธ Khรฃdimul Ashrรฃf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

"Kar ku zarge mu a watan Al-muharram idan kuka ganmu ba yanda kuka saba ganinmu ba , domin giyar soyayya ba yanda bata yi da
"Kar ku zarge mu a watan Al-muharram idan kuka ganmu ba yanda kuka saba ganinmu ba , domin giyar soyayya ba yanda bata yi da mahaukacin masoyi" โœ๏ธ Khรฃdimul Ashrรฃf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

ุนูŽุฒูŽุงุกู ุงู„ู’ุบูŽุฑููŠู’ุจู.pdf5.19 KB

Repost from N/a
ุนูŽุฒูŽุงุกู ุงู„ู’ุบูŽุฑููŠู’ุจู.pdf5.19 KB

"ุนูŽุฒูŽุงุกู ุงู„ู’ุบูŽุฑููŠู’ุจู ุจูุญูŽุฏููŠู’ุซู ุงู„ุฑู‘ูŽูŠู‘ูŽุงู†ู ุจู’ู†ู ุดูŽุจููŠู’ุจู " ุจูŽุฏูŽุงู’ุชู ุงู‚ู’ุชูุจูŽุงุณููŠู’ ุจูุงุณู’ู…ู ู…ูุจู’ุฏูุนู ุฎูŽู„ู’ู‚ูู†ูŽุง ูˆูŽูŽุฃูŽูŽุญู’ู…ูŽุฏูู‡ู ุญูŽู…ู’ุฏู‹ุง ูŠูŽูููˆู’ู‚ู ุฐูุฑูŽู‰ ุงู„ุซู‘ูŽู†ูŽุง ุฃูุตูŽู„ู‘ููŠ ุนูŽู„ูŽู‰ ุฎูŽูŠู’ุฑู ุงู„ู’ุจูŽุฑูŽุงูŠูŽุง ูˆูŽุขู„ูู‡ู ุฃููˆู’ู„ููŠ ุงู„ุทู‘ูู‡ู’ุฑู ูˆูŽุงู„ู’ุฅูุญู’ุณูŽุงู†ู ุณูŽุงุฏูŽุงุชู ุฃูŽู…ู’ุฑูู†ูŽุง ุฑูŽูˆูŽู‰ ูููŠ ุงู„ู’ุฃูŽู…ูŽุงู„ูŠู‘ู ุงู„ุตู‘ูŽุฏููˆู’ู‚ู ุจูู…ูŽุฌู’ู„ูุณู ุญูŽูˆูŽู‰ ุบูุฑู‘ูŽุฉูŽ ุงู„ุดู‘ูŽู‡ู’ุฑู ุงู„ู’ุญูŽุฑูŽุงู…ู ูƒูŽูŠูŽูˆู’ู…ูู†ูŽุง ุจูุฅูุณู’ู†ูŽุงุฏูู‡ู ุฃูŽุนู’ู„ูŽุงู‡ู ุงูุจู’ู†ู ุดูŽุจููŠู’ุจู ุนูŽู†ู’ ุฑูุถูŽุง ุงู„ู’ุฎูŽู„ู’ู‚ู ูููŠ ุงู„ู’ุจูŽู„ู’ูˆูŽู‰ ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ู ุณูŽู„ูŽุงู…ูู†ูŽุง ุฏูŽุฎูŽู„ู’ุชู ุนูŽู„ูŽู‰ ุงู„ู’ู…ูŽูˆู’ู„ูŽู‰ ุงู„ุฑู‘ูุถูŽุง ุฐูŽุงุชูŽ ุบูุฑู‘ูŽุฉู ุงู„ู’ู€ ู€ู…ูุญูŽุฑู‘ู…ู ุดูŽู‡ู’ุฑู ุงู„ู’ูƒูŽุฑู’ุจู ูููŠู’ู…ูŽุง ุฑูŽูˆูŽู‰ ู„ูŽู†ูŽุง ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ู„ูŽู‡ู ุงูุจู’ู†ู ุงู„ู†ู‘ูŽุจููŠู‘ู : ุฃูŽุตูŽุงุฆูู…ูŒ ุŸ ุฃูŽูŠูŽุง ุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจู ุฃูŽูˆู‘ูŽู„ู ุงู„ุดู‘ูŽู‡ู’ุฑู ูŠูŽูˆู’ู…ูู†ูŽุง ุฃูŽุฌูŽุงุจูŽ ุจูู„ูŽุง ูŠูŽุง ุณูŽูŠู‘ูุฏููŠู’ ู„ูŽุณู’ุชู ุตูŽุงุฆูู…ู‹ุง ููŽุฃูŽุฎู’ุจูŽุฑูŽู‡ู ู…ูŽุบู’ุฒูŽู‰ ุงู„ุณู‘ูุคูŽุงู„ู ุฅูู…ูŽุงู…ูู†ูŽุง ุฏูŽุนูŽุง ุฒูŽูƒูŽุฑููŠู‘ูŽุง ูˆูŽุงุณู’ุชูŽุฌูŽุงุจูŽ ุฅูู„ูŽู‡ูู†ูŽุง ู„ูŽู‡ ู…ูŽุง ุฏูŽุนูŽุง ูููŠู’ ู…ูุซู’ู„ู ุฐูŽุง ุงู„ู’ูŠูŽูˆู’ู…ู ุนูู†ู’ุฏูŽู†ูŽุง ุฏูŽุนูŽุง : ุฑูŽุจู‘ู ู‡ูŽุจู’ ู„ููŠู’ ูˆูŽุงุฑูุซู‹ุง ูŠูŽุง ุณูŽู…ููŠู’ุนูŽ ู…ูŽู†ู’ ุฏูŽุนูŽุงู‡ู ุจูุญูุณู’ู†ู ุงู„ู’ู‚ูŽู„ู’ุจู ูŠูุนู’ุทููŠู’ู‡ู ู…ูŽุฃู’ู…ูŽู†ูŽุง ููŽุจูŽุดู‘ูŽุฑูŽู‡ู ุงู„ู’ุจูŽุงุฑููŠู’ ุจููŠูŽุญู’ูŠูŽู‰ ู…ูุจูŽุงุฑูŽูƒู‹ุง ูˆูŽุฃูŽุตู’ู„ูŽุญูŽ ู…ูŽุง ูููŠู’ ุฒูŽูˆู’ุฌูู‡ู ู‚ูŽูˆู’ู„ู ุฑูŽุจู‘ูู†ูŽุง ููŽู…ูŽู†ู’ ุตูŽุงู…ูŽ ู‡ูŽุฐูŽุง ุงู„ู’ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ูŠูŽู„ู’ู‚ูŽู‰ ุฅูุฌูŽุงุจูŽุฉู‹ ุจูุญูุณู’ู†ู ู‚ูŽุจููˆู’ู„ู ุงู„ู„ู‡ู ููŽุถู’ู„ูŒ ุจูู„ูŽุง ุนูŽู†ูŽุง ุฃูŽูŠูŽุง ุงุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจู ุฅูู†ู‘ูŽ ู‡ูŽุฐูŽุง ู…ูุญูŽุฑู‘ูŽู…ูŒ ูˆูŽูƒูŽุงู†ูŽุชู’ ุฑูุฌูŽุงู„ู ุงู„ู’ุฌูŽุงู‡ูู„ููŠู‘ูŽุฉู ู‚ูŽุจู’ู„ูŽู†ูŽุง ุชูุญูŽุฑู‘ูู…ู ูููŠู’ู‡ู ุงู„ุธู‘ูู„ู’ู…ูŽ ูˆูŽุงู„ู’ู‚ูŽุชู’ู„ูŽ ุญูุฑู’ู…ูŽุฉู‹ ูˆูŽู…ูŽุง ุนูŽุฑูŽููŽุชู’ ู‡ูŽุฐููŠ ุงู„ู’ุนูุตูŽุงุจูŽุฉู ุญูŽู‚ู‘ูŽู†ูŽุง ููŽู„ูŽู…ู’ ูŠูŽุนู’ุฑููููˆู’ุง ู„ูู„ุดู‘ูŽู‡ู’ุฑู ุฃูŽูŠู‘ูŽ ูƒูŽุฑูŽุงู…ูŽุฉู ูˆูŽู„ูŽุง ู„ูู„ู†ู‘ูŽุจููŠู‘ู ุงู„ู’ู…ูุตู’ุทูŽููŽู‰ ุญูุฑู’ู…ูŽุฉูŽ ุงู„ุณู‘ูŽู†ูŽุง ู„ูŽู‚ูŽุฏู’ ู‚ูŽุชูŽู„ููˆู’ุง ุฐูุฑู‘ููŠู‘ูŽุฉูŽ ุงู„ุทู‘ูู‡ู’ุฑู ูููŠู’ู‡ู ู…ูŽุง ุฑูŽุนูŽูˆู’ุง ุญูุฑู’ู…ูŽุฉูŽ ุงู„ู’ุฅููŠู’ุตูŽุงุกู ูŠูŽุง ุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจูู†ูŽุง ู‚ูŽุฏู ุงู†ู’ุชูŽู‡ูŽูƒููˆู’ุง ุญูุฑู’ู…ูŽ ุงู„ู†ู‘ูŽุจููŠู‘ู ุจููƒูŽุฑู’ุจูู„ูŽุง ููŽู„ูŽุง ุบูŽููŽุฑูŽ ุงู„ู„ู‡ู ุงู„ุฐู‘ูู†ููˆู’ุจูŽ ู„ูู…ูŽู†ู’ ุฌูŽู†ูŽู‰ ุฃูŽูŠูŽุง ุงุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจู ุงู„ู’ุฎูŽูŠู’ุฑู ุฅูู†ู’ ูƒูู†ู’ุชูŽ ุจูŽุงูƒููŠู‹ุง ู„ูุดูŽูŠู’ุกู ููŽุฃูŽูˆู’ู„ูŽู‰ ุจูุงู„ู’ุจููƒูŽุงุกู ุญูุณูŽูŠู’ู†ูู†ูŽุง ู„ูŽู‚ูŽุฏู’ ุฐูŽุจูŽุญููˆู’ู‡ู ุฐูŽุจู’ุญูŽ ูƒูŽุจู’ุดู ุงู„ุถู‘ูŽุญููŠู‘ูŽุฉู ูˆูŽุนูุดู’ุฑููŠู’ู†ูŽ ุฅูู„ู‘ูŽุง ุงุซู’ู†ูŽูŠู’ู†ู ู…ูู†ู’ ู†ูŽุณู’ู„ู ุฌูŽุฏู‘ูู†ูŽูŽุง ุชูŽูˆูŽูู‘ูŽูˆู’ุง ุนูŽุทูŽุงุดูŽู‰ ู…ูŽุง ู„ูŽู‡ูู…ู’ ู…ูู†ู’ ู…ูุดูŽุงุจูู‡ู ุจููƒูู„ู‘ู ุจูู„ูŽุงุฏู ุงู„ู„ู‡ู ุฌูุณู’ู…ู‹ุง ูˆูŽู…ูŽุนู’ุฏูู†ูŽุง ุณูŽู…ูŽูˆูŽุงุชู ุณูŽุจู’ุนู ู‚ูŽุฏู’ ุจูŽูƒูŽุชู’ู‡ู ูˆูŽุฃูŽุฑู’ุถูู‡ูŽุง ูˆูŽุฃูŽุฑู’ุจูŽุนู ุขู„ูŽุงูู ุงู„ู’ู…ูŽู„ุงุฆููƒู ุฌูŽุงุกูŽู†ูŽุง ุฃูŽุชูŽูˆู’ุง ู†ูุตู’ุฑูŽุฉู‹ ู„ูู„ุณู‘ูุจู’ุทู ูููŠู’ ุฃูŽุฑู’ุถู ูƒูŽุฑู’ุจูŽู„ูŽุง ุณููˆูŽู‰ ุฃูŽู†ู’ ุฑูŽุฃูŽูˆู’ู‡ู ุจูุงู„ุชู‘ูุฑูŽุงุจู ู…ููƒูŽูู‘ูŽู†ูŽุง ููŽู‡ูู…ู’ ุนูู†ู’ุฏูŽ ู‚ูŽุจู’ุฑู ุงู„ุณู‘ูุจู’ุทู ุดูุนู’ุซูŒ ุจูŽูˆูŽุงูƒููŠู‹ุง ูˆูŽุบูุจู’ุฑู‹ุง ุฅูู„ูŽู‰ ูŠูŽูˆู’ู…ู ุงู„ุธู‘ูู‡ููˆู’ุฑู ูˆูŽุซูŽุฃู’ุฑูู†ูŽุง ููŽูŠูŽุบู’ุฏููˆู’ู†ูŽ ุฃูŽู†ู’ุตูŽุงุฑู‹ุง ู„ูŽู‡ู ูˆูŽุดูุนูŽุงุฑูู‡ูู…ู’ ุฃูŽู„ูŽุง ูŠูŽุง ู„ูŽุซูŽุงุฑูŽุงุชู ุงู„ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ู‚ูŽุชููŠู’ู„ูู†ูŽุง ู„ูŽู‚ูŽุฏู’ ุญูŽุฏู‘ูŽุซูŽ ุงู„ู’ู…ูŽุงุถููŠู’ ุฃูŽุจููŠู’ ุนูŽู†ู’ ุฌูุฏููˆู’ุฏูู‡ู ุจูุฃูŽู†ู‘ูŽ ุงู„ุณู‘ูŽู…ูŽุง ู‚ูŽุฏู’ ุฃูŽู…ู’ุทูŽุฑูŽุชู’ ุฏูŽู…ูŽ ูƒูŽุฑู’ุจูู†ูŽุง ูƒูŽุฐูŽุงูƒูŽ ุชูุฑูŽุงุจู‹ุง ุฃูŽุญู’ู…ูŽุฑู‹ุง ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ู‚ูŽุชู’ู„ูู‡ู ููŽูŠูŽุง ุงุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจู ุงูุจู’ูƒู ู…ูŽุง ุฏูู…ู’ุชูŽ ุญูุจู‘ูŽู†ูŽุง ููŽู„ูŽูˆู’ ุณูŽุงู„ูŽ ู…ูู†ู’ูƒูŽ ุงู„ุฏู‘ูŽู…ู’ุนู ุญูุฒู’ู†ู‹ุง ู„ูู‚ูŽุชู’ู„ูู‡ู ููŽุฐูŽู†ู’ุจููƒูŽ ู…ูŽุบู’ูููˆู’ุฑูŒ ุจูููŽุถู’ู„ู ุฅูู„ูŽู‡ูู†ูŽุง ุตูŽุบููŠู’ุฑู‹ุง ูƒูŽุจููŠู’ุฑู‹ุง ุฃูŽูˆู’ ู‚ูŽู„ููŠู’ู„ุงู‹ ูˆูŽุถูุฏู‘ูŽู‡ู ูŠููƒูŽูู‘ูุฑูู‡ู ุงู„ุฑู‘ูŽุญู’ู…ูŽู†ู ุนูŽู†ู’ูƒูŽ ู„ูุฃูŽุฌู’ู„ูู†ูŽุง ุฃูŽูŠูŽุง ุงุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจู ุฅูู†ู’ ุฃูŽุฑูŽุฏู’ุชูŽ ู„ูู‚ูŽุงุกูŽู‡ู ุจูู„ูŽุง ุณูŽูŠู‘ูุฆูŽุงุชู ุฒูุฑู’ ุญูุณูŽูŠู’ู†ู‹ุง ููŽุชูุญู’ุตูŽู†ูŽุง ูˆูŽุฅูู†ู’ ุณูŽุฑู‘ูŽูƒูŽ ุงู„ู’ุฅูุณู’ูƒูŽุงู†ู ูููŠ ุงู„ู’ุบูุฑูŽูู ุงู„ู‘ูŽุชููŠู’ ุจูŽู†ูŽุงู‡ูŽุง ุฅูู„ูŽู‡ู ุงู„ู’ุนูŽุฑู’ุดู ู„ูู„ู’ุขู„ู ู…ูŽุณู’ูƒูŽู†ูŽุง ู…ูŽุนูŽ ุงู„ู’ู…ูุตู’ุทูŽููŽู‰ ููŽุงู„ู’ุนูŽู†ู’ ุทูุบูŽุงุฉู‹ ุชูŽุนูŽู…ู‘ูŽุฏููˆู’ุง ู‚ูุชูŽุงู„ูŽ ุญูุณูŽูŠู’ู†ู ุชูŽู„ู’ู‚ูŽ ูููŠ ุงู„ู’ุฎูู„ู’ุฏู ู…ูŽุฃู’ู…ูŽู†ูŽุง ูˆูŽุฅูู†ู’ ุณูŽุฑู‘ูŽูƒูŽ ุงู„ู’ุฃูŽุฌู’ุฑู ุงู„ู’ุนูŽุธููŠู’ู…ู ูƒูŽู…ูŽู†ู’ ู‚ูŽุถูŽู‰ ููุฏูŽุงุกู‹ ู„ูŽู‡ู ู‚ูู„ู’ ุญููŠู’ู†ูŽ ุชูŽุฐู’ูƒูุฑู ุฌูŽุฏู‘ูŽู†ูŽุง ุฃูŽู„ูŽุง ู„ูŽูŠู’ุชูŽู†ููŠู’ ู…ูŽุนู’ู‡ูู…ู’ ุจูุฃูŽุฑู’ุถู ุจูŽู„ูŽุงุฆูู‡ูู…ู’ ู„ููƒูŽูŠู’ู…ูŽุง ุฃูŽุฑูŽู‰ ููŽูˆู’ุฒู‹ุง ุนูŽุธููŠู’ู…ู‹ุง ู…ูŽุนูŽ ุงู„ู’ู‡ูŽู†ูŽุง ุฃูŽูŠูŽุง ุงุจู’ู†ูŽ ุดูŽุจููŠู’ุจู ุฅูู†ู’ ูŠูŽุณูุฑู‘ููƒูŽ ูƒูŽูˆู’ู†ูู†ูŽุง ู…ูŽุนู‹ุง ูููŠู’ ุฑูŽูููŠู’ุนู ุงู„ุดู‘ูŽุฃู’ู†ู ุญูŽูŠู’ุซู ุจูŽู‚ูŽุงุกูู†ูŽุง ููŽุฃูŽุญู’ุฒูŽู†ู’ ู„ูุญูุฒู’ู†ู ุงู„ู’ุขู„ู ูˆูŽุงูู’ุฑูŽุญู’ ู„ูุจูŽู‡ู’ุฌูู‡ูู…ู’ ูˆูŽูˆูŽุงู„ู ุจูŽู†ููŠ ุงู„ุฒู‘ูŽู‡ู’ุฑุงุกู ูˆูŽุงุชู’ุฑููƒู’ ุฎูู„ูŽุงููŽู†ูŽุง ููŽู„ูŽูˆู’ ุฃูŽู†ู‘ูŽ ุนูŽุจู’ุฏู‹ุง ุนูŽู„ู‘ูŽู‚ูŽ ุงู„ู’ู‚ูŽู„ู’ุจูŽ ูˆูŽุงู„ู’ูˆูŽู„ูŽุง ุจูุตูŽุฎู’ุฑู ู„ูŽูˆูŽุงู„ูŽู‰ ุงู„ุตู‘ูŽุฎู’ุฑูŽ ูููŠู’ ูŠูŽูˆู’ู…ู ุจูŽุนู’ุซูู†ูŽุง ููŽู‡ูŽุฐูŽุง ุนูŽุฒูŽุงุกู ุงู„ู’ุญูŽู‚ู‘ู ู…ูู†ู’ ุณูŽูŠู‘ูุฏููŠ ุงู„ุฑู‘ูุถูŽุง ุชูุคูŽูŠู‘ูุฏูู‡ู ุงู„ู’ุฃูŽุฎู’ุจูŽุงุฑู ูููŠู’ ุฌูู„ู‘ู ูƒูุชู’ุจูู†ูŽุง ุฃูŽูŠูŽุง ุตูŽุงุญู ููŽุงู„ู’ุฒูŽู…ู’ ู…ูŽุง ุฑูŽูˆูŽุชู’ู‡ู ุซูู‚ูŽุงุชูู†ูŽุง ุชูŽููุฒู’ ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ูŠูŽุฑู’ุฌููˆ ุงู„ู†ู‘ูŽุงุณู ู…ูŽู†ู’ุฌู‹ู‰ ุนูŽู†ู ุงู„ู’ุนูŽู†ูŽุง ุฅูุฐูŽุง ุฒูุฑู’ุชูŽ ู…ูŽูˆู’ู„ูŽุงู†ูŽุง ุงู„ู’ุญูุณูŽูŠู’ู†ูŽ ุจููƒูŽุฑู’ุจูŽู„ูŽุง ููŽู„ูŽุง ุชูŽู†ู’ุณูŽู†ููŠู’ ูููŠ ุงู„ุณู‘ูุคู’ู„ู ุจูุงู„ู’ุฎูŽูŠู’ุฑู ุนูู…ู‘ูŽู†ูŽุง ูˆูŽุจูŽู„ู‘ูุบู’ ุณูŽู„ูŽุงู…ููŠู’ ุฅูู†ู’ ู…ูŽุณูŽูƒู’ุชูŽ ุถูŽุฑููŠู’ุญูŽู‡ู ูˆูŽูƒูู†ู’ ุฐูุฎู’ุฑูŽ ุฐูŽุง ุงู„ู’ููŽุงู†ููŠู‘ู ุนูู†ู’ุฏูŽ ุฅูู…ูŽุงู…ูู†ูŽุง ุชูุนูŽุฑู’ู‚ูู„ูู†ููŠ ุงู„ู’ุขุซูŽุงู…ู ูˆูŽุงู„ู†ู‘ูŽูู’ุณู ุชูŽู„ู’ุชูŽูˆููŠ ูˆูŽุฃูŽุฑู’ุฌููˆ ุฎูŽู„ูŽุงุตูŽ ุงู„ู’ุญูŽุงู„ู ู…ูู†ู’ู‡ู ูƒูŽุฐูŽุง ุงู„ู’ู…ูู†ูŽู‰ ุตูŽู„ูŽุงุฉูŒ ูˆูŽุชูŽุณู’ู„ููŠู’ู…ูŒ ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ู ูˆูŽุตูŽุญู’ุจูู‡ู ู…ูŽุชูŽู‰ ู…ูŽุง ุฃูŽุชูŽู‰ ุดูŽู‡ู’ุฑู ุงู„ู’ุญูŽุฑูŽุงู…ู ูˆูŽุญูุฒู’ู†ูู†ูŽุง โœ๏ธุฎุงุฏู… ุงู„ุนุชุฑุฉ ุงู„ุทุงู‡ุฑุฉ ๏ธ ุงู„ุนุจุฏ ุงู„ูุงู†ูŠ ุงู„ูƒู†ูˆูŠ ูก / ุงู„ู…ุญุฑู… ุงู„ุญุฑุงู… / ูกูคูคูจู…

ู…ูˆุณู… ุงู„ุฃุญุฒุงู† ู‡ู„ู‘ ุงู„ู…ุญุฑู‘ู… ู…ูˆุณู… ุงู„ุฃุญุฒุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ุจูƒุง ูˆุงู„ูƒุฑุจ ูˆุงู„ุฃุดุฌุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ุนุฒุงุก ู„ุนุชุฑุฉ ุงู„ู…ุฎุชุงุฑ ุดู‡ุฑ ุงู„ู…ุขุชู… ุนู†ุฏ ุฐูŠ ุงู„ุฅูŠู…ุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ุญุณูŠู†
ู…ูˆุณู… ุงู„ุฃุญุฒุงู† ู‡ู„ู‘ ุงู„ู…ุญุฑู‘ู… ู…ูˆุณู… ุงู„ุฃุญุฒุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ุจูƒุง ูˆุงู„ูƒุฑุจ ูˆุงู„ุฃุดุฌุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ุนุฒุงุก ู„ุนุชุฑุฉ ุงู„ู…ุฎุชุงุฑ ุดู‡ุฑ ุงู„ู…ุขุชู… ุนู†ุฏ ุฐูŠ ุงู„ุฅูŠู…ุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ุญุณูŠู† ูˆุขู„ู‡ ุงู„ุฃุจุฑุงุฑ ูˆุตุญุงุจู‡ ุงู„ุฃุจุทุงู„ ูˆุงู„ุดุฌุนุงู† ุดู‡ุฑ ุจุนุงุดุฑู‡ ุนู„ู‰ ุงู„ุฑู‘ู…ุถุงุก ุถุญู‘ู‰ ุจู‡ู… ุธู„ู…ู‹ุง ุจู†ูˆ ุงู„ุณู‘ููŠุงู† ุดู‡ุฑ ุงู„ู‘ุฐูŠ ุฃุจูƒู‰ ุงู„ู†ู‘ุจูŠู‘ ุงู„ู‡ุงุฏูŠ ู…ู† ู‚ุจู„ ุบูุฑู‘ุชู‡ ู…ู† ุงู„ุฃุญุฒุงู† ุฌู„ู‘ุช ู…ุตูŠุจุชู‡ ุจู‚ุชู„ ุงู„ุณู‘ุจุท ููŠ ุงู„ุทู‘ูู‘ ุดู‡ุฑ ุชูˆุฑู‘ู… ุงู„ุฃุฌูุงู† ูุงู„ุชู†ุดุฑูˆุง ู„ูˆู† ุงู„ุณู‘ูˆุงุฏ ุญูŽุฒุงู†ู‰ ูˆุงู„ุชุฑูุนูˆุง ุงู„ุฑู‘ูŠุงุช ููŠ ุงู„ุฃูˆุทุงู† ูˆุชุฌู†ู‘ุจูˆุง ุงู„ุฃูุฑุงุญ ููŠู‡ ุชุฃุณู‘ูŠุง ุจุงู„ุขู„ ุฃู‡ู„ ุงู„ุฎูŠุฑ ูˆุงู„ุฅุญุณุงู† ูˆุงุณุนูˆุง ู„ู†ุดุฑ ุฑุณุงู„ุฉ ุงู„ุฃุญุฑุงุฑ ู…ู† ู‡ุฏูŠ ูŠูˆู… ุงู„ุทูู‘ ุจุงู„ุฅุชู‚ุงู† ูˆุชุฐุงูƒุฑูˆุง ูŠูˆู… ุงู„ุญุณูŠู† ุนู„ูŠู‡ ุตู„ูˆุงุช ุฑุจู‘ูŠ ุฏุงุฆู…ูŽ ุงู„ุฃุฒู…ุงู† โœ๏ธู†ุฒูŠู„ ุงู„ู†ุฌู ุงู„ุงุดุฑู ุงู„ุนุจุฏ ุงู„ูุงู†ูŠ ุงู„ูƒู†ูˆูŠ ูก/ ู…ุญุฑู… ุงู„ุญุฑุงู…/ ูกูคูคูคู‡ู€

TSAKANIN MU DAKU WANE NE ฦ˜IRฦ˜IRAR YAHUDAWA ??? (ฦ˜ALU BALE GAREKU) Daga cikin abubuwan da maฦ™iya Shi'a suke yiwa ฦณan Shi'a sharri da ฦ™age dashi , shine danganta Shi'anci da yahudanci , wai asalin Shi'a wani Bayahude da ake kira Abdullahi ษ—an Saba'i ne ya ฦ™irฦ™irota , abun dariya da takaici !!! Tare da cewa har manyan Malamansu sun ฦ™aryata wannan maganasuka tabbatar da bata da asali , suka tabbatar da ba komai bace face yarfe da kuce dan a ษ“ata Shi'a da Shi'anci , Bugu da ฦ™ari akan haka ga wani ฦ™alu bale ga duk wani mai tuhumar Asalin Aฦ™idar Shi'a da Yahudanci : In har kun kasance masu gaskiya cikin abunda kuke faษ—a , ga littattafan Shi'a nan sun cika Duniya tun daga ฦ™arni na farko har zuwa yau , in kun isa ku kawo mana ruwaya ko da guda ษ—aya ce da aka ce wannan Abdullahi ษ—an Saba'i ne ya rawaito ta (Ba an tawaito akansa ba ) , ko ku kawo mana wata Aฦ™ida guda ษ—aya daga cikin Aฦ™idun Shi'a da aka ruwaito cewa daga Abdullahi ษ—an Saba'i take , ko ku kawo mana wani hukuncin Fiqhun Shi'a guษ—a daya tak da aka ce ษ—an Saba'i ne ya rawaito shi ko daga gareshi yake . Don Allah da Annabi mun ฦ™alu balance ku kuyi hakan Ya ku tarin ...... BUGU DA ฦ˜ARI Amma ku kuma babu wani littafin Tafsiri naku da za'a buษ—e face an samu riwayar Addinin ku daga Ka'abul Ahbari , Wanda kowa yasan tsohon ฦ™asurgumin malamin Yahudawa ne wanda ya musulunta a Zamanin Mulkin Umar Bin Khaษ—ษ—ab, daga nan ya zama Babban Maruwaicin Hadisi da kuke ji da shi a Addinin ku , abune tabbatacce Ka'abu ya ฦ™ware wajen rawaito ruwayoyin tastuniyoyi na Isra'iliyyat , kuma yana da Tafsiri a Addinin ku saษ“anin mu , sam Abdullahi bin Saba'i bai da wani tasiri a wurinmu , sai dai ruwayoyi da suke la'antar shi in ma akwaishi ษ—in yana samuwa kenan fa ! Gini akan yadda kuke riyawa Mu da ku waye ฦ™asurgumin Bayahude yayiwa Tasiri a Addinin sa ? Waye yake cewa Bayahude : Radiyallahu anhu a litattafan Tafsirin sa in ba ku ba ? Waye yake la'antar Bayahude a littattafansa in bamu ba ? Su waye suka ce Bayahude ne Malamin Sahabbai a fannin Tafsirin Alkur'ani in ba ku ba ? Ba Ka'abul Ahbari ba , akwai manyan manyan malaman Yahudawa da suka shahara suka yiwa Musulunci kuste kuma suka wayi gari sune manyan turakunku na Addini , Kamar su Abdullahi ษ—an Salami da Wahbu ษ—an Maniyyata da sauransu .... Kai manyan waษ—anda kuke ji dasu a hadisi malamanku sun tabbatar da daga wajen Yahudawan suke rawaito Hadisai kuma an ingantasu kuna Addini da su . Mhm !!! Wai mai gidan gilashi ne yake cewa ayi wasan jifa da dutse !!! โœ๏ธ Khรฃdimul Ashrรฃf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

JA'AFARIYYA BA MAZHABAR FIฦ˜HU BACE KAWAI Imam Ja'afar As-sadiฦ™ (A.S) ba mazhabar fiฦ™hu kawai yake da ita ba - a daura da irin
JA'AFARIYYA BA MAZHABAR FIฦ˜HU BACE KAWAI Imam Ja'afar As-sadiฦ™ (A.S) ba mazhabar fiฦ™hu kawai yake da ita ba - a daura da irin Malikiyya ko Shafi'iyya - shi limami ne na addinin Annabi (Saww) na asali , watau koyarwarsa ta tattaro komai tun daga aฦ™ida , fiฦ™hu tazkiyya da abinda yafi gaban nan idan akwai , wannan gamammen tsarin na Imam Ja'afar Al-sadiฦ™ (A.S) ake kira Shi'a Imamiyya ko Rifidanci , Ja'afariyya ba mazhabar fiฦ™hu bace kawai ta shanye mazhaba ta lasheta. โœ๏ธ Khรฃdimul AshrรฃfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

WAฦ˜I'AR HARRA (JUYIN JUYA HALIN MUTANEN MADINA GA GWAMNATIN YAZIDU ฦŠAN MU'AWIYAH L) . Yaฦ™i ne da ya gudana a ranar 27 Ko 28 ga watan Zul-Hijja shekara ta 63 bayan hijira , tsakanin mutanen garin Madina da suka yi tawaye ฦ™arkashin jagorancin Abdullahi bin Hanzala da sojojin Sham karkashin umarnin Yazid bin Muawiyah bin Abi Sufyan, karkashin jagorancin Muslim bin Uฦ™bah Al-Marri . A wannan lokacin ne aka kashe dayawa daga cikin mutanen Madina birnin Manzon Allah (sawa) , wadanda suka hada da sahabbai 80 da Mahaddatan Alฦ™ur'ani 700, kusan mata dubu aka yiwa ciki ba ta hanyar aure ba , aka tsananta wa garin tare da halartar komai nashi tsawon kwanaki uku , aka wawushe dukiyoyin mutane, aka keta alfarmar masallacin Annabi bisa umarnin Yazidu L .Imam Sajjad (a.s.) ya kasance a tsakiya game da yunkurin da mutanen Madina suka yi (a wannan lokacin baya tare da kowanne ษ“angarori biyun) kuma ya bawa mutane da dama mafaka ciki har da iyalan Marwan binil Hakam. An ce Sojoji sun kashe sama da mutane 4000 ko 11700 ko 10700, daga cikinsu mutum 700 sun haddace Alkurโ€™ani da Sahabban Manzon Allah 80 wasu daga cikinsu sun halarci yaฦ™in Badar ne . A lokacin aka kashe Abdullahi bin Hanzala da โ€˜yaโ€™yansa . Bayan kwana uku ana tafka barna da munanan ayyuka a cikin garin Madina , sai Muslim bin Uqbah Al-Marri ya tara sauran mazauna garin Madina , ya bukaci su yi mubaya'a ga Yazidu ษ—an Mu'awiyah a kan cewa sun zama bayinsa. Wato ganima ce ga Yazid bn Muawiyah , kuma waษ—anda ba su karษ“i wannan mubayaโ€™a ba suka fille kawukansu . Wanda suka rage basu shiga wannan mubaya'ar ba kuma suka tsira mutum biyu ne kawai sune : Ali bin Abdullah bin Al-Abbas ( Saboda sulhun daya daga cikin danginsa a cikin rundunar Yazidu ya shiga wannan mubaya'a) Sai kuma Imam Ali Zainul Abidin Assajjad (a.s.) . Wannan waki'ar ta faru biyo bayan kashe Imam Hussain da kuma yadda miyagun ayyukan Yazidu ษ—an Mu'awiyah suka kara bayyana ga mutane , har sukayi tawaye ga Gwamantinsa . Haka nan wannan hari da rundunar Yazidu suka kai Madina yana ษ—aya daga cikin miyagun ayyuka Uku da Yazidu L yayi a shekara ukun da ya yi a Mulki, shekara ta farko ya kashe Imam Hussain (a.s.) shekara ta biyu aka kaiwa garin Makka hari sannan a shekara ta uku aka kaiwa Madina Hari . โœ๏ธ Khรฃdimul Ashrรฃf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 28/Zul-hajji/1443H - 28/7/2022

cewa "Kulluhum Kuffarun wa Fusuuฦ™un " suna bibiyar tarihi da abinda ya tabbata na rayuwar Sahabbai bisa ma'aunai na Shari'a, su ฦ™aunace su don Allah da gaskiya ko su ฦ™yamaci aikinsu don Allah da gaskiya . Batun gaskiya da gaskiya ฦดan Shi'a basu da wata maslaha ta musamman cikin so ko ฦ™in Sahabbai . Abun takaici shine yadda maฦ™iya ฦดan Shi'a suka cakuษ—a waษ—annan mas'alolin da gangan don su ษ“ata ฦดan Shi'a . Ba komai yasa ba za su yarda da Aฦ™idar ฦดan Shi'a game da Sahabbai ba sai dan hakan zai lazimta rushewar Aฦ™idar su da Addinin su baki ษ—aya game , wanda wannan Aฦ™idar tasu itace ainihin ฦ™in Sahabbai da zaluntar su , ko Sahabban ba za su yarda da wannan Aฦ™idar ta "Kullhum Uduulun" bari ma sun ฦ™aryata ga duk wanda ya bibiyi tarihin rayuwar su , don haka ne ma muka ce ฦดan Shi'a ne masoya Sahabbai na gaskiya . A dunฦ™ule dai abinda yake Hujjar cirar Shari'a da Addini daga gareshi a wurin ฦดan Shi'a Alkur'ani ne da Sunnah , Ma'ana Sunnar Annabi da Ai'mmatu Ahlil baiti (a.s.) , wanษ—anda sune Khalifofi kuma Jagorori bayan Manzon Allah (saww) , su kaษ—ai ne Hujja banda wanin su . Allah ka ฦ™ara tsira, aminci , albarka da yarda ga zaษ“aษ“ษ“un Sahabban Manzon Allah (saww) . Wassalamu alaikum warahmatullahi wabaraka tuhu ๐Ÿ‘ โœ๏ธ Khadimul AshrรฃfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 26/Jumadhal Ula/1444H - 21/12/2022

ฦณAN SHI'A NE MASOYA SAHABBAI NA GASKIYA Wanda yace : Duk Sahabban Annabi ba mutanen kirki bane shine mutumin banza kuma ya halaka ya taษ“e , kuma wannan ba ita bace Aฦ™ida da Matsayar Shi'a game da Sahabban Annabi (saww) . Wanda yace : Sahabban Annabi (saww) baki ษ—ayan su Adalai ne na gari ne ya saki layi , domin hakan ya saษ“awa Waฦ™i'i da Nassin Alkur'ani da Hadisai da Sirar Sahabban , babu shakka wannan ma ba matsayar ฦดan Shi'a bace game da Sahabban Manzon Allah (saww) , domin Sahabbai kashi-kashi ne kuma hawa hawa ne , akwai Uduulun akwai kuma akasin haka . Babu wanda ya isa ya musa haka sai Jahili ko kuma mutum kangararre munkiri . TO MECE CE MATSAYAR ฦณAN SHI'A GAME DA SAHABBAI ??? A ko da yaushe maฦ™iya Shi'a da Shi'awa sukan ฦ™oฦ™arin ษ“ata su da nuna su a matsayin wasu maฦ™iya Sahabbai ko wasu mutane da basa ฦ™aunar duk Sahabban Annabi (saww) , wanda wannan tsantsan rashin Adalci ne ga ฦดan Shi'a, domin ba ita bace Aฦ™idar su game da Sahabbai , ฦดan Shi'a basa yiwa Sahabbai kuษ—in goro su zage su ko su kafirta su ko su aibatasu kamar yanda aka ruษ—i dayawan jahilai da wawaye da hakan , wasu an musu gadar zare suka faษ—a , wasu kuma suna yine da gangan da ganganci , suka ษ—auki zagin Sahabbai a matsayin wani makami da zasu yaฦ™i Shi'a dashi a wajen jahilan mutane da basu san Shi'a ba . ฦณan Shi'a suna ฦ™udurce cewa Sahabban Manzon Allah (saww) sun kasu kamar haka ; 1 . Daga Sahabbai akwai Adilai, Muminai , Waliyyai , Salhai da suka kai wani matsayi a wajen Allah da ba masanin haฦ™iฦ™anin sa sai Allah da Manzonsa . Tabbas Waษ—annan sun rabauta duniya da lahira , kuma zama da Manzon Allah ya amfane su cikin taikonsa da yin imani na haฦ™iฦ™a da shi , Radiyallahu Anhum Wa Radhu Anhum . Duk sanda kaji an yabi Sahabbai ko an jinjina musu a cikin Alkur'ani da Sunna to da wannan kashi ake .ฦณan Shi'a suna ฦ™aunar waษ—annan Sahabbai, suna neman alabarkarsu dare da rana kuma Adilai ne ko shakka babu 2. Akwai kuma akasin kashi na farko , Waษ—anda zama da Annabi (saww) bai amfana musu komai ba , saboda rashin Imaninsu da shi Imani na haฦ™iฦ™a da taimakon sa da riฦ™e alฦ™awari a bayan sa , bari ma sun cutar da shi cutarwar da ba'a yiwa wani abun halitta kamarta ba a cikin halitta . Duk inda kaji suka ko allawadai da sashin wasu Sahabbai a cikin Alkur'ani mai girma to dasu ake , irin su ne aka rawaito Annabi (saww) yace : A cikin Sahabbai na akwai munafukai goma sha biyu na za su shiga Aljanna ba , irin su ne suka dinga shirya kashe Manzon Allah (saww) lokaci bayan lokaci har a ฦ™arshen rayuwar sa , irinsu ne suka assasa cutar da iyalansa a bayansa har aka kai ga halin da ake ciki a yau , irin su ne irin su ..... Tarihi ya sajjala ayyukan su da halayen su . Ahmadu ษ—an Hambali ya rawaito a cikin Musnad , Manzon Allah (saww) ya ce : A cikin Sahabbai na akwai wanda bazai ฦ™ara gani na ba har Abada . ma'ana dai daga ฦ™abarinsa sai wutar Jahannama. A ruwayoyin Bukhari da Muslim kuwa , Akwai wadanda sai anzo dasu Annabi (saww) ya gansu a ranar Alkiyama sai kuma a korasu Wuta , har ya dinga ya Ubangiji Sahabbaina ne Sahabbaina ne , Sai ace ai sun sauya a bayanka. 3 . Akwai kuma Waษ—anda Allah da Manzonsa ne kawai suka san halinsu a Duniya da lahira , suna cikin kashin farko ne ko na biyu ? Tarihi bai hakaito wani abu akansu a rarrabe ba ballantana ayi naฦ™adin rayuwarsu , koma sam ba'a san sunansu da halayensu ba . Domin gabaฦ™i ษ—aya Sahabban da aka yi Tarjamarsu a littattafan Tarajimu basu ne Jumlar Sahabban Manzon Allah (saww) . Shi yasa akwai abun mamaki tattare da masu yiwa Sahabbai Kuษ—in goro da Adala da Imani na gaskiya , ta yanda suke yin hukunci akan abinda basu san shi ba basu san halinsa ba , wato dai suna yin hukunci akan Majhuli . Uwa uba ma yadda suke sabawa hankali , Ayoyin Alkur'ani, Hadisai , Waฦ™i'i da Sirar Sahabban Kansu a cikin hakan . A taฦ™aice dai ฦดan Shi'a suna rarrabe hukunci da matsayar su dangane da Sahabban Manzon Allah (saww) , matsayarsu matsayar Alkur'ani da Sunnah ce game da Sahabbai , basu gaza ba a cikin haฦ™ฦ™in su kuma basu wuce gona da iri ba kamar yanda wasu suka yi , Basu yadda da ฦ™a'idar "Kullhum Uduulun ba" Kuma ba sa

Ghadir sirrin haษ—in kai ุงู„ู…ู„ุชู‚ู‰ ุงู„ุนู„ู…ุงุฆูŠ ุจุฑุนุงูŠุฉ ู…ุฑูƒุฒ ุงู„ุฌู†ูˆุจ ุงู„ุซู‚ุงููŠ ุงู„ุฅุณู„ุงู…ูŠ

RANAR DA MANZON ALLAH (SAWW) YA FITO YIN MUBAHALA DA KIRISTOCIN NAJRAN TANA NUFIN : 1 . Duk Duniya Manzon Allah (saww) bashi da tamkar waษ—anda ya fito dasu wato Imam Ali , Sayyida Faษ—ima da ฦดaฦดanta Hasanain (a.s) , domin da yana da kamar su bayansu da ya fito da su a wannan rana . 2 . Wannan rana tana nufin babu waษ—anda Annabi (saww) yake ฦ™auna kamar su inda da akwai shi da anga ya kirawo shi , domin babu ma'anar ya zama akwai wanda yafi su ko yake sama dasu a matsayi gunsa amma ya barshi a gida , saboda zuwa da abinda mutum bai da kamarsa ke nuna yana kan gaskiya akan abinda ya fito ayi muguwar addu'a akansa , ma'ana dai da ace akwai wanda suka fi su Imam Ali da Sayyida Zahra (a.s) a wurin Annabi (saww) kuma yaฦ™i fito da su da hakan ya nuna ba da gaske yake ba. 3 . Zuwan da Manzon Allah (saww) yayi da ฦดaฦดan ษ—akinsa ya nuna gaskiyar Annabcinsa wanda hakan yasa Kiristocin Najran duka janye ฦ™udirun su daga ฦ™arshe suka nemi sulhu da Annabi (saww) domin da ace bai da hujja akan gaskiyar Addinin da yake kai da bai zai zo da su Imam Ali (a.s) ba sai dai aga yazo da wasu daga Sahabbansa ko Matansa da sauran Musulmi ko wasu bare can . 4 . Abinda ya faru a wannan rana ya nuna Imam Ali (a.s) ya kai ฦ™ololuwar matsayi da falala da girma kuma babu wani mutum da ya kai shi daraja bayan Manzon Allah (saww) domin Nassin Alฦ™ur'ani cikin ayar Mubahala ya tabbatar da shi Nafsun Manzon Allah (saww) ne ; ููŽู…ูŽู†ู’ ุญูŽุงุฌู‘ูŽูƒูŽ ูููŠู‡ู ู…ูู† ุจูŽุนู’ุฏู ู…ูŽุง ุฌูŽุงุกูŽูƒูŽ ู…ูู†ูŽ ุงู„ู’ุนูู„ู’ู…ู ููŽู‚ูู„ู’ ุชูŽุนูŽุงู„ูŽูˆู’ุง ู†ูŽุฏู’ุนู ุฃูŽุจู’ู†ูŽุงุกูŽู†ูŽุง ูˆูŽุฃูŽุจู’ู†ูŽุงุกูŽูƒูู…ู’ ูˆูŽู†ูุณูŽุงุกูŽู†ูŽุง ูˆูŽู†ูุณูŽุงุกูŽูƒูู…ู’ ูˆูŽุฃูŽู†ููุณูŽู†ูŽุง ูˆูŽุฃูŽู†ููุณูŽูƒูู…ู’ ุซูู…ู‘ูŽ ู†ูŽุจู’ุชูŽู‡ูู„ู’ ููŽู†ูŽุฌู’ุนูŽู„ ู„ู‘ูŽุนู’ู†ูŽุชูŽ ุงู„ู„ู‡ู ุนูŽู„ูŽู‰ ุงู„ู’ูƒูŽุงุฐูุจููŠู†ูŽ (ุขู„ ุนู…ุฑุงู†/ูฆูก). Imam Ali (a.s) shi Annabi (saww) ya fito dashi a matsayin kansa da ransa , kenan idan ba Annabi (saww) babu wanda zai zama tamkar Annabi (saww) a faษ—in Duniya tamkar Imam Ali (a.s) . 5 . Shi yasa Mubahala tana cikin dalilan da suke nuna Khalifancin Imam Ali (a.s) da Imamancin sa bayan Annabi (saww) , domin Annabi shine Imami kuma Khalifan Allah a sanda yake nan idan kuma babu shi babu wanda ya cancanci wannan matsayin sai wanda ya zama Nafsunsa (Ransa) wato Imam Ali (a.s) da zuriyarsa . 6 . Wannan Mubahala tana daga dalilan da suke tabbatar da kasancewar Imam Hasan da Husain (a.s) a matsayin ฦดaฦดan Annabi (saww) ne na haฦ™iฦ™a ba ฦดaฦดan kara ba , domin Allah cewa yayi ; Ya Rasulallahi kace mu kira ฦดaฦดanmu kuma ku kira ฦดaฦดanku ู†ูŽุฏู’ุนู ุฃูŽุจู’ู†ูŽุงุกูŽู†ูŽุง ูˆูŽุฃูŽุจู’ู†ูŽุงุกูŽูƒูู…ู’ , shi yasa har wala yau Malaman da suka tafi akan ษ—an mace ษ—a ne na haฦ™iฦ™a a wajen kakansa na wajen uwa suke kafa hujja da Mubahalar Annabi (saww) ta kam wannan ayar kamar yanda za muyi nuni a bayanin mas'alar shariftar ษ—an mace nan gaba In sha Allah. A taฦ™aice dai ranar Mubahala da wannan ayar suna nuni da wanni matsayi na musamman ga Ahlul Baiti (a.s) babu wani da yayi tarayya dasu cikinsa a kaf wannan al'uma kuma rana ce daga ranaku mafiya girma a tarihin Musulunci , domin a cikinta ne aka yanke tambabar duk wani mai tambaba akan gaskiyar Annabcin Annabi Muhammad (saww) kuma ฦ™arya ta bayyana kowa ya santa . Tarihi ya nuna fitowa domin wannan Mubahala ya wakana ne a rana mai kamar yau 24 ga watan Zulhijjah ษ—in shekara ta goma bayan hijira a garin Madina mai alfarma , ma'ana a ฦ™arshe-ฦ™arshen rayuwar Annabi (saww). โœ๏ธKhadimu A'atabi รƒli Muhammad Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 24 / Zulhijjah / 1445H - 1/ 7 / 2024 Miladiyya.

Wannan idan an kau da kai daga rikita-rikitar da take cikin wasu zikirai da tawassulan ษ—arika kenan ! 5 . Sannan Shi'a suna da zikirai da manhaji na ibada da duk abinda mutum yake bukata a ษ“angaren suluki da gyaran ruhi fiye da kowa ba alfahari ba ! To yaushe mutum ya gama da Mafatihul Jinan da sauran kundaye manya na gyaran zuciya da rai har yake tunanin rakito wani ko haษ—awa da wasu daban !? Shin ba zai shiga cikin babin rinjiyar da abinda aka rinjaya tare da cikar abinda yafi rinjaye ba ? Matukar mutum yayi imani da cikar Ahlul Baiti (A.S) da girmama falalar duk abinda ya tabbata daga garesu a addini me yasa ba zai wadatu da wannan ba ? Shin hakan ba ya lazimta tufka da warware? Kamar fa mutum ne ana raba zinare , daimon, biliyoyin daloli da kyautuka ne kece raini a gidansu sai a ganshi a gidan maฦ™wabtansu yana barar a taimaka masa shi mabuฦ™aci ne ba shi da yanda zai yi ! โœ๏ธ Khรฃdimul AshrรฃfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 23 / Zhul Hijja / 1447H - 9 / 6 / 2026 Miladiyya.

SHIN IYA ZIKIRAI DA ADDU'OI NE A CIKIN ฦŠARIฦ˜AR SUFAYE ? 1 . Tabbas idan mutum yana sauraren masu kira zuwa ga ษ—ariฦ™a ko masu da'awar yiwuwar haษ—ata da Shi'anci za kaji suna cewa : Ai ita ษ—arika ba komai bace face karanta zikirai da addu'oi (Istigfari , hailala da salati) , to amma abin tambaya su kaษ—ai ne ma'anar yin ษ—ariฦ™a a haฦ™iฦ™a ko akwai wani abu bayan su ? Domin idan iya waษ—annan ne hatta Bawahabiye ษ—an dariฦ™a ne saboda yana da wasu zikirai da addu'oi na shi na musamman , kuma yana yin salatin Ibrahimiyya. Kamar ษ—an Shi'a ne idan kaji yana ce maka Shi'anci shi ne bin Imamu Ali (A.S) da soyayyar ฤ€hlul Baiti (A.S) wannan ba ya nuni da cewa iya wannan ne Shi'anci tayu yana faษ—a maka rukuni ne ko tushe. 2 . To yana da kyau mu fahimci shi salon da'awa (kira) a kowacce al'uma da aฦ™ida yana da maฦ™amai da yanda ake yinsa , kuma abu ne da yake sananne hatta a wajen malaman fannin magana da usulul fiฦ™hi cewa : Shi mai da'awa akwai sanda yake kasancewa a muฦ™amin ihmali (Kau da kai) a kan wasu abubuwa da yake ฦ™udircewa a sanda yake kiran mutane a ciki da matakin shar'antawa , ba komai yake faษ—a ba saboda ba wannan bane manufarsa , yana maฦ™amin assasawa ne da shar'anta asalin tafarkinsa , don haka zai dunฦ™ule magana ne , kuma ko a magana hakan na faruwa , za mu ga sanda Alฦ™ur'ani yake bayyana mana batun halascin cin abinda dabbar farauta - misali - ta kamo ba zai yi magana a kan shi hukuncin wurin da dabbar ta cafka ba saboda ba wannan bane muฦ™amin bayanin hakan. To haka shima in kaga mai magana ko kira zuwa ga dariฦ™a ko yana ce maka hanyar mu itace Istigfari, hailala da salati, hakan ba ya nuna iya shikkenan ba wani abu da yake raka wannan domin shi kan shi zikiran suna da sharaษ—ai na musamman da kaifiyya keษ“antacciya amma in banda haka Bawahabiye ma ษ—an dariฦ™a ne da wata ma'anar. Haka ษ—an Shi'a idan kaji yana cewa Shi'anci shi ne walaya Imam Ali (A.S) , hakan ba ya nuna babu wasu aฦ™idu ko hukunce-hukunce ko suluki na aiki a Shi'anci . 3 . Don haka dariฦ™a kowacce iri ce hanya ce daga cikin hanyoyin sufanci da sufi ko mai ฦ™oฦ™arin zama sufi da arifi yake bi , shi kuma sufancin gaba ษ—aya ba iya zikirai bane , akwai wasu aฦ™idu (abinda da ake ฦ™udircewa a zuciya) ayyuka ,zikirai da addu'oi da kuma wasu abubuwan da ake azamar lazimtarsu a aiki da tarbiyya kamar sharaษ—ai da ladubai kuma duk suna da alaฦ™a da ฦ™udiri da tunani. Abinda yake faruwa yanzu na dambarwa a kan Imam Mahdi (A.J.T.F) ya isa ya tabbatar maka ฦดan dariฦ™a sun ginu a kan aฦ™idu da nazariyyoyi , bugu da ฦ™ari idan kana karanta litattafan aฦ™idu za kaga ana kawo ra'ayoyin sufaye da ฦดan ษ—ariฦ™a a kan wasu abubuwa , kuma suna da gingima-gingiman littattafai masu yawa da suka shafi nazariyyoyinsu a kan kowanne ษ“angare na addini , kamar yanda suna da ra'ayoyi a kan abinda ya shafi nazariyyar ma'arifa ta tsarin halitta da rayuwa kamar wahdatul wujudi. Na'am , tayu ace su ba aฦ™ida bane mai zaman kanta idan aka kalli babin aฦ™idun tushe da ake da rabe-rabe , amma kuma haka ba ya nufin ba su da aฦ™idun reshe , domin aฦ™idu kala biyu ne akwai asali akwai tushe , ko manya da ฦ™anana. 4 . Sannan idan an ษ—auka ษ—ariฦ™a iya zikirai da addu'oi ne , to ita kebantacciyar kaifiyya da sharaษ—an yin wannan wuridai da zikiran da lazimtar yinsu da idan mutum bai yi ba sai ya rama ko abu kaza da kaza na fiฦ™hun ษ—ariฦ™a ..... Abu ne da an shiga babin fiฦ™hu da shari'a da ake neman tabbatar da hakan da isnadi ko dalilai keษ“antattu daga Alฦ™ur'ani da Sunnah , wanda babu wannan dalilan na musamman face Shehu wane yace ko Shehu wane ya sadu da Annabi (Saww) bashi yace a dinga yi da wannan salo , ko an yiwa Shehu wane kashafi ko yayi mafarki , kuma hakan ba a lura da shi a tafarkin ฦดan Shari'a, bari ma shubhar shar'anta abinda babu shi a addini tana iya shigowa kuma haramun ne da laifi mai girma. Na'am , ba laifi bane mutum ya ษ—au wani zikiri ko addu'a da bata saษ“awa Shari'a ba ya karanta amma kuma ba da ma'anar ya maida shi alฦ™awarin wani Shehi da tafarki ba , hakan yana buฦ™atar dalili ta fuskar Shari'a.

Wannan idan an kau da kai daga rikita-rikitar da take cikin wasu zikirai da tawassulan ษ—arika kenan ! 5 . Sannan Shi'a suna da zikirai da manhaji na ibada da duk abinda mutum yake bukata a ษ“angaren suluki da gyaran ruhi fiye da kowa ba alfahari ba ! To yaushe mutum ya gama da Mafatihul Jinan da sauran kundaye manya na gyaran zuciya da rai har yake tunanin rakito wani ko haษ—awa da wasu daban !? Shin ba zai shiga cikin babin rinjiyar da abinda aka rinjaya tare da cikar abinda yafi rinjaye ba ? Matukar mutum yayi imani da cikar Ahlul Baiti (A.S) da girmama falalar duk abinda ya tabbata daga garesu a addini me yasa ba zai wadatu da wannan ba ? Shin hakan ba ya lazimta tufka da warware? Kamar fa mutum ne ana raba zinare , daimon, biliyoyin daloli da kyautuka ne kece raini a gidansu sai a ganshi a gidan maฦ™wabtansu yana barar a taimaka masa shi mabuฦ™aci ne ba shi da yanda zai yi ! โœ๏ธ Khรฃdimul AshrรฃfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 23 / Zhul Hijja / 1447H - 9 / 6 / 2026 Miladiyya.