fa
Feedback
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

رفتن به کانال در Telegram

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

نمایش بیشتر
2 393
مشترکین
+124 ساعت
-67 روز
+3230 روز
آرشیو پست ها
KU SAKE SHI BAN SHIGAR DA ƘARA A KANSA BA ! Ayatullahi Sayyid Ali Sistaniy (H) ya buƙaci babbar kotun bincike ta Bagadaza dake Rasafa da ta saki matashin nan da ya fito kafafen sadarwa ya zazzage shi ya ci zarafinsa a yayin da yake ƙona hotonsa . A cikin takardar da ofishin Sayyid Ali Sistanin ya aikewa kotun yayi roƙon a saki wannan matashi mai suna Mustafa Sãmi Musa kuma ya ƙara da cewa shi bai shigar da ƙara a kansa ba sam , don haka a taimaka a sake shi ba tare da jan al'amarin da nisa ba . Ba wannan bane karo na farko da Ayatullahi Sistani yake aikewa da takardar neman afwa kan waɗanda suka zagin shi ko suke cin zarafinsa , duk da cewa a Iraƙi doka ne kuma akwai hukunci oan duk wanda aka kama da cin zarafin maraji'an addini da irin wannan salo na tunzuri. Dama afuwa da saka mummuna da kyakkyawa shi ne halin Imam Ali (A.S) da mabiyansa na gaskiya . Hoton dake ƙasa yana nuna wasikar da ofishin Sayyid Ali Sistanin suka aike zuwa ga kotu ne don a saki matashin. ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

HUKUNCIN YIN ADDU'A DA HAUSA A CIKIN SALLAH Mas'alar yin addu'a da wani yare da ba larabci ba - musamman a yayin alƙunuti - mas'ala ce ta saɓani a tsakanin malaman fiƙhu da malamanmu masu girma , wasu sun halasta wasu kuma akasin haka . Dayake akwai akwai ƙa'ida zaunanniya a Musulunci da kusan kowa ya yarda da ita cewa "Tauƙifi shi ne asali a ibada" ma'ana : Ba a sauya ko a ƙara ko a rage ko a jirkita wani abu da yazo a shari'a na ibada idan ba da izinin Shari'a , yanda aka ce mutum yayi abu haka zai yi kwabo da kwabo , sai dai idan batun lalura ya shigo ko aka yi rangwame a wannan abun. To tunda sallah ibada ce ya zamana adadin raka'ointa ko zikirai da addu'ointa ko karatu suka zama tabbatatattun da ba a sauya su sai idan wani dalili na musamman ya zo daga Shari'a yace yayi rangwame . Kuma da zamana babu wani dalili ɓaro-ɓaro da yazo daga mai Shari'a da yace ayi addu'a da wani yare da ba Larabci ba a sallah kuma babu wani dalili ɓaro-ɓaro da ya hana yasa wasu malamai suka yi riƙo da wannan asalin na ibada , watau tauƙifi , suka ce hatta kuskure na nahwu ko ginin kalma ba a yi. Wasu kuma suka kalli wasu dalilai da ka'idojin fiƙhu suka ga zai yu a yi addu'a , musamman a abinda Shari'a bata iyakance tace dole da iya wannan salo za a yi shi kamar alƙunuti ko da kuwa an ruwaito wasu addu'oi na musamman da ake so ayi su. KOMAWA FARKO 1 . Mafi yawan malaman Shi'a Imamiyya sun tafi a kan ihtiyaɗi - ba fatawa kai tsaye ba - na nisantar yin addu'a da wani yaren da ba larabci ba , kai hatta kuskure na karin kalma ko nahwu suka ce a nisanta duk da sun ce idan mutum yayi ba ya ɓata masa sallah . 2 . Wasu malaman kuma suka ce ya halasta yin addu'a musamman yayin alƙunuti da duk wani yare ba sai larabci ba , don haka gini a kan ra'ayin su za a iya yi da Hausa ko turanci ko yarbanci ko fillanci da sauran su . A . Daga cikin malaman da suka halasta hakan , akwai marigayi Shahid Ayatullahi Sayyid Ali Khamene'i (Rahimahullah) inda yake cewa : "Ya halasta yin addu'a da istigfari (neman gafarar Allah) da neman biyan buƙatu da farisanci dama ko wane irin yare". يجوز الدعاء والاستغفار وطلب الحاجات بالفارسية أو أي لغة أخرى. (Risalatus salati was saum/mas'ala ta 310) B . Haka nan Ayatullahi Sayyid Muhammad Taƙiy Al-Mudarrisi (H) yana cewa : Ya halasta (addu'a da Yaren da ba Larabci ba a sallah) amma abinda yake mustahabbi nisantarsa. يجوز ، ولكن الأحوط تركه. (Ahkamu af'aãlus Salah /138) C . Shima Ayatullahi Muhammad Sa'idul Hakim (Rahimahullah) : Ya halasta yin alƙunuti da wani Yaren da ba Larabci ba ko da Larabcin da ba miƙaƙƙe ba matuƙar dai bai sauya ma'ana ba kuma yana wadatarwa. (Minhajus salihin) يجوز القنوت بغير العربي و بالعربي المطحون إذا لم يكن مغيرًا للمعنى، وتؤدي به وظيفة القنوت. (Minhajus salihin /242) To amma fa kusan dukkansu suna kan cewa keɓantattun addu'oi ko zikirai ko karatun da ake yi a sallah (Kamar karatun fatiha ko sura ko tasbihan sujjada da ruku'u) ba a yin su idan ba da larabci ba , saboda wancan asalin da muka faɗa na tauƙifi. Kamar yanda mas'alar ɓacin sallah da yin magana (zance irin na ɗan adam) tana nan bata sauya ba a wajen kowa. Don haka , wannan mas'ala ce ta saɓani wasu sun halasta yin addu'a da wani larabci , wasu kuma suna ganin abinda yafi taka tsantsan nisantar hakan ko da kuwa ba ya ɓata sallah , har da larabci karyayye a nahwu ko ginin kalma basa ganin ingancin yi . Sannan Sayyid Ali Khamene'i (R) ya halasta yin addu'a da a alƙunuti da yaren da ba Larabci ba kamar Hausa ko waninsa. Wallãhuk musta'an....🤲 ✍️ Khâdimul AshrãfAl-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 3 / Rabi'ul Thani / 1448H - 15 / 9 / 2026 Miladiyya

SULHUN IMAM HASSAN (A.S.) DA MU'AWIYAH (L) A ranar 26 ga watan Rabi'ul Auwal a shekara ta 41 bayan hijira, Imam Hasanul Mujtaba (a.s) yayi sulhu da Mu'awiyah bin Abi Sufyan (L) . Imam Hassan (a.s.) ya sharɗantawa Mu'awiyah sharaɗai masu yawa daga ciki : 1. Mu'awiyah da Jama'arsa za su dena zagin Mahaifinsa Imam Ali (a.s.) akan mimbarorinsu na huɗuba da Akunutin Sallah , kuma kar su yarda su ambaci Imam Ali (a.s) sai da alkhairi. 2 . Kuma Mu'awiyya ya dena cutar da ƴan Shi'ar Imam Ali (a.s.) a duk inda suke , a sirrance ko a ɓoye . 3. Zai yi aiki da Littafin Allah da sunnar Manzon Allah (sawa) . 4. Kyautatawa Banu Hashim da ƴaƴan waɗanda aka kashe tare da Imam Ali (a.s.) a yaƙin Siffin da Jamal , cikin baye-bayen haƙƙoƙi . 5. Mu'awiyah bai da haƙƙin sanya wani a bayansa , a bayansa al'amari zai koma ga Imam Hassan (a.s.) in kuma babu Imam Hassan (a.s) , zai koma ga ɗan uwansa Imam Hussain (a.s.) . 6. Dole Mu'awiyah ya samar da aminci da zaman lafiya a lardin Musulunci, kuma a bawa duk wani mai haƙƙi haƙƙinsa ba tare da an zalunceshi ba . Bayan haka ne Mu'awiyah L ya yarda da waɗannan sharaɗai da yarjejeniya kuma aka zartar . Sai dai bayan ya koma wajen mutanensa - Kamar yanda Malaman tarihin Ahlussunna Wal jama'a suka rawaito - ya musa hakan , kuma yace duk wani sharaɗin da Hassan ya sa min na takeshi a ƙasan ƙafata , ban yaƙeku dan kuyi Sallah ko Azumi ko Hajji ba , nayi abinda nayi saboda samun karagar mulki kuma na sameta . Abul Hasanul Asfahani ya rawaito a cikin littafin (مقاتل الطالبيين) shafi na 45 : عن أبي إسحاق قال : سمعت معاوية بالنخيلة يقول : ألا إن كل شئ أعطيته الحسن بن علي تحت قدمي هاتين لا أفي به ، قال أبو إسحاق : وكان والله غداراً. Duk da hakan Mu'awiyah bai haƙura ba , daya ga Mulki a hannunsa amma kuma zuƙatan mutane Muminai suna tare da Imam Hassan (a.s.) , sai ya cigaba da shirya makirci da kitimurmura , ya dinga sawa ana shayar da Imam Hassan (a.s.) guba , har daga ƙarshe Imam yayi shahada da gubar Rum ɗin da suka shayar dashi , wacce ya biya matar Imam Hassan (a.s) ta shayar dashi . TAMBIHI A . Sulhun da Imam Hassan (a.s) yayi da Mu'awiyah baya nufin Imam Hassan (a.s) ya bawa Mu'awiyah Imamanci ko Khalifancin Ubangiji , abinda Imam Hassan (a.s.) ya bawa Mu'awiyah shine ragamar Gwamanti da shugabancin zahiri , amma ba Imamancinsa na haƙiƙa da Allah ya zaɓeshi dashi tun fil azal ba , Manzon Allah (saww) yana cewa ; Imam Hassan da Imam Hussain Imamai ne guda biyu sun tashi ko sun zauna (A kowanne hali ) . Don haka Imamancin Imam Hassan haƙƙi ne da ba'a iya sarayar dashi a kowanne hali , kamar yadda ba'a raba wuta da zafi haka bazai yu a rabashi da Imam Hassan ba a kowanne hali , don haka al'amarim ba kamar yadda wasu suke ɗauka bane sam . B . Sulhun da akayi da Imam Hassan (a.s.) baya nufin ƙaskanci ko rashin nasarar Imam Hassan (a.s.) ko taɓewar al'amarisa , bari dai wannan shi ya ƙara fito da matsayi, buwaya, nasara da wane ne Imam Hassan (a.s.) . C . Manufa da tafarkin dukkan Ai'mmatu Ahlil baiti (a.s) guda ɗayace babu banbanci , sai dai kaifiyya da yanayin cimma wannan manufa kan banbanta a zahiri , amma babu tufka da warwara ko saɓani a cikin dukkan wata matsaya da suka ɗauka a rayuwarsu , bari dai maslaha da hikima ce take hukunta matsayar da matakin kowanne ya ɗauka . Shi yasa za'a ga Imam Ali (a.s) a farkon al'amari bai yi yaƙi ba , daga ƙarshe kuma yayi yaƙoƙi uku , Imam Hassan (a.s.) kuma yayi sulhu saboda dalilai masu yawa , daga ciki akwai banbancin shaksiyyar Mu'awiyah L data banbanta da ta Yazidu, shi yasa Imam Hussain (a.s) bai motsa ba a lokacin rayuwar Mu'awiya har sai bayan shekara goma , haka nan sauran Ai'mmatu Ahlil baiti (a.s) kowa da irin yanayin da ya rayu , sannan kuma akwai Taklifinsa da salonsa , amma duk hadafin guda ɗaya ne , shi ko Imam Mahdi (a.j.t.f) ya shiga Ghaiba har guda biyu , ya kuma damka amanarmu a hannun Adalan jagorori tare da cikakkiyar kulawa mai ɗorewa daga luɗfin Allah Ta'ala. ✍️ Khâdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 28/Rabi'ul Auwal/1444H - 25/10/2022

Ba komai bane yin bukukuwam maulidi face ɗaukaka ambaton Manzon Allah (saww) , da kambama muƙaminsa , cikin kirari da yabo da ambaton sirarsa mai tsarki da akeyi . 6 . Ciki akwai faɗin Allah Ta'ala : فَالَّذِينَ آمَنُوا بِهِ وَعَزَّرُوهُ وَنَصَرُوهُ .. الاعراف:157) Wannan aya tana magana akan yin imani da Annabi (saww) da girmamashi da taimakonsa, cikin taimakon saƙon da yazo dashi daga Allah Ta'ala, shin menene maulidi in ba ƙara ɗamfara zuƙata da ambaton Manzon Allah (saww) ba , da girmamashi , da taimakonsa cikin taimakon saƙon da yazo dashi ??? 7 . Ciki akwai faɗin Allah Ta'ala: رَبَّنَا أَنزِل عَلَينَا مَآئِدَةً مِّنَ السَّمَاء تَكُونُ لَنَا عِيداً لأَوَّلِنَا وَآخِرِنَا وَآيَةً مِّنكَ وَارزُقنَا وَأَنتَ خَيرُ الرَّازِقِينَ (المائدة:114) . Wannan Ayar tana magana akan yadda aka saukarwa da mutanen Annabi Isa (saww) da kaɓakin abinci daga sama , bayan sun roƙi Allah kuma aka yi musu hakan , har ranar saukar ta zama ido gsresu saboda murna ..... Indai har saukar da kaɓakin abinci daga sama zai zama ranar Idi da murna , Ina ga ranar da shugaban farko da karshe ya sauka ! Ranar da Allah ya haskaka duniya da hasken shiriya da falala , ita tafi cancanta da zama idi mafi girma a tarihin dan adam , fiye da ranar da aka saukar da abinci daga sama . 8 . Daga dai jerin waɗannan ayoyi akwai faɗin Allah Ta'ala: وَالضُّحَى . وَاللَّيلِ إِذَا سَجَى (الضحى:1-2) Mallam Al-halabi ya hakaitar cewa ; A cikin waɗannan ayoyin guda biyu ,Allah yayi rantsuwa da daren da aka haifi Annabi (saww) ne , a wani ƙaulin kuma ance ; Ana nufin daren Isra'i . Amma kuma babu karo In ance duka biyun ake nufi za su haɗu . Don haka indai Allah Ta'ala zai yi rantsuwa da daren da aka haifi Annabi (saww) , to hakan yana nuna cewa wannan dare akwai wani sirri da falala cikinsa , kuma ya cancanci a rayashi da ambato da tuna wanda aka haifa a cikinsa . Akwai ayoyin Alkur'ani dayawa da malamai suka ambata a wannan babin , amma zamu wadatu da wannan gwargwado , sai kuma mu tsallaka bangaren hadisai da aka kafa hujja dasu a wannan babin . Zan cigaba Insha Allah....... ✍️Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 25/Rabi'ul Auwal/1444H - 22/10/2022

HUJJOJI DA DALILAN MAULIDI (02) A kashi na farko bayani ya gabata cewa wannan rubutu zai maida hankali ne wajen rairayo dalilai da hujjojin yin Maulidi da asalin a Shari'ar Musulunci , cikin abinda malaman Musulunci suka ambata a rubuce-rubucensu , Inda muka fara bayani akan hujjar yin maulidi bisa dalili na hankali da kuma fiɗira da lamirin ɗan Adam, wanda a yau Insha Allah za mu tsallaka kan dalilai na Ayoyi da kuma Hadisai ne kai tsaye . 1. Daga cikin ayoyin Alkur'ani mai girma da za mu iya rikarsu a matsayin hujja da dalilin yin maulidi, akwai faɗin Allah Ta'ala : ( ذَلِكَ وَمَن يُعَظِّم شَعَائِرَ اللهِ فَإِنَّهَا مِن تَقوَى القُلُوبِ ) (سورة الحج:32) Ma'ana : Cananka (haka lamarin yake) , duk wanda yake giramama alamomin Allah to Lallai hakan na daga taƙawar zuƙata . Ma'anar alamomin Allah shine duk wasu alamomi da abubuwan Addini da suke nuni zuwa ga Allah , to girmama waɗannan abubuwan yana daga cikin Taƙawar zuƙata , musamman abinda ya shafi aikin Hajji da ake magana Misali, mafi yawancin ayyukan da ake yi na aikin Hajji ba komai bane face maimaicin wasu abubuwa da suka taɓa faruwa a tarihi , a lokacin Annabi Ibrahim (a.s.) , ake tunawa dasu da kuma sake rayasu da girmamasu. Su kuma alamomin Ubangijin nan da wannan aya take magana ma'ana ce wacce take da faɗi , za ta haɗo har da Manzon Allah (saww) shima alama ce daga alamomi Ubangiji da duk wani abu da ya shafeshi , don haka girmama Manzon Allah (saww) wajibi ne , kuma yin Maulidi da sauran munasabobin raya ambaton Annabi (sawa) zai shiga cikin alamomin Allah (شعائر الله )da wannan aya ke magana , ma'ana dai raya munasanar haihuwar Annabi (saww) don girmama Annabi da ɗaukaka ambatonsa, yana daga girmama Annabin , haka kuma girmama Annabi (saww) wajibi ne kuma yana daga cikin girmama alamomin Allah Ta'ala, girmama alamomin Allah kuma yana daga cikin girmama Allah , kenan Maulidi ba komai bane face raya alamomin Ubangiji da grimamasu da mafhumin wannan aya mai albarka . 2 . Daga ciki akwai faɗin Allah Ta'ala: ( ذَكِّرهُم بِأَيَّامِ اللهِ )) (ابراهيم:5) Ma'ana : Ya Rasulallahi , ka tunatar dasu kwanakin Allah (swt) . Abun nufi da kwanakin Allah a wannan aya mai albarka shine ; kwanakin nan da gaskiya tayi galaba akan ƙarya kuma gaskiya ta bayyana , haka nan raya munasabar tunawa da haihuwar Manzon Allah (saww) , itama akwai tunatar da ranakun Allah Ta'ala ce, ko ba komai in an zauna a wajen Maudli ana karanta tarihi da sirar Manzon Allah (saww) , tun kafin aikoshi da bayan aikoshi da yadda aka sha fama har addini ya tabbata , a taƙaice da Mauludin Annabi (sawa) shima (أيام الله ) ne . 3 . Daga cikin jerin waɗannan ayoyi akwai faɗin Allah : ( قُل بِفَضلِ اللهِ وَبِرَحمَتِهِ فَبِذَلِكَ فَليَفرَحُوا ......) (يونس:58) . Ma'ana: Ka faɗa musu(Ya Rasulallahi) suyi farin ciki da falalar Allah da rahamarsa ..... Haihuwar Manzon Allah (saww) tana ɗaya daga cikin falala da rahamar Allah mafi girma da bayyana , domin kuwa Allah ya aiko Annabi kaco kam dan ya zama rahama ga talikai da Nassin Ayar Alkur'ani , kenan yin biki da taron Mauludi domin farin cikin zuwan babbar rahamar Allah , abune mai asali kuma abunso a Addinin Musulunci . Wannan aya tana daga cikin hujjoji mafiya ƙarfi da bayyana cikin tabbatar da mashru'iyyar Maulidi . 4 . Yana daga haka faɗin Allah Ta'ala : قُل لاَّ أَسأَلُكُم عَلَيهِ أَجراً إِلاَّ المَوَدَّةَ فِي القُربَى.....) (الشورى:23) Ma'ana : Ka faɗa musu (Ya Rasulallahi) bana tambayarku wani lada akan abinda nazo muku dashi , face ku nuna ƙauna ga makusantana . A taƙaice wannan aya tana bayanin wajabcin don makusantan Annabi daka shi Annabin (saww) , don haka yin Maulidan Annabi da makusantansa , da ambaton tarihin rayuwarsu yana daga so da ƙauna garesu da Alkur'ani yayi umarni da ita . Ba ta yadda za'a yi ace mutum ya shirya wani taron murna da farin cikin wani abu daya sami masoyinsa kuma ace ba ƙauna tasa yayi hakan ba . 5 . Haka nan faɗin Allah Ta'ala: ( وَرَفَعنَا لَكَ ذِكرَكَ )) (الشرح: 4) Ma'ana : Kuma muka ɗaukaka maka ambatonka (Ya Rasulallahi) .

SAI ME IDAN ƊAN MALAM YAƘI HALIN MALAM KO ALBASA BATA YI HALIN RUWA BA ?! Babu inda aka ce idan mutum yana malami dole ɗansa ya zama malami ko ya zama mutumin kirki , kamar yanda ba dole bane don mutum yana Musulmi dole ɗansa ya zama musulmi ta ƙarfi da yaji. Abinda yake wajibi shi ne malami yayi duk yanda zai yi wajen shimfiɗawa ɗansa shimfiɗar da zai taka ta zama mutumin kirki ko ya gaje shi ta hanyar ba shi ingantacciyar tarbiyya , haka musulmi - malami da ba wanda ba malami ba - ya yiwa ahli da zuriyarsa tarbiyyar musulunci tare da tsayuwa tsayin daka wajen tseratar da su da shi kansa daga halaka ko wuta . يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا قُوا أَنْفُسَكُمْ وَأَهْلِيكُمْ نَارًا وَقُودُهَا النَّاسُ وَالْحِجَارَة... Amma faruwar hakan da zaman sa dole ya faru a aikace ba ya kan mutum kuma ba a hannunsa yake ba , kamar wanda yayi shuka ne , abinda yake wajibi yabi dokokin yin shuka da abinda zai sa a samu kyakkyawan amfani da yabanya , amma faruwar kyakkyawan amfani ta dole ba a hannunsa yake ba . أَفَرَأَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ. أَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُ أَمْ نَحْنُ الزَّارِعُونَ Saboda akwai babin jarrabawa da sauransu a Musulunci , shi kan shi dawwamar uba ko malami a kan shiriya da kyakkyawar makomarsa ba a hannunsa take ba. Abinda yake zama aibu ko matsala lalacewar ɗa da sakacin mahaifi ko makusantansa. Amma al'umarmu ta ginu a kan wani tunani na dole ɗan malami ya zama malami ko ta wace hanya , shi yasa ake cinsu da buguzum a ko da yaushe. Kuma mene ne abun murna don ɗan wani ya zama Kirista ko ma mulhidi ? Hatta ƴaƴan wasu Annabawa da makusantansu sun kasance a kan saɓanin da'awar su kuma suna yaƙar ma tafarkin su . Sannan ko da malami ya haifi ƴaƴa 100 kuma duk suka gaje shi suka zama malamai hakan ba ya nuni da ba za a iya jarrabarsa a kan su ba yana raye ko bayan ya koma ga Allah ; ko ba za su iya sauka daga kan layi ba har su mutu , zai yu suyi ta rikici da saɓani har su zama fitina a cikin al'uma da gara ace ba su zama malaman ba . Kuma tara ƴaƴa ba aibu bane matuƙar mutum zai yi musu tarbiyya kuma yana da ikon yin hakan a duniyance da zamannace. Yanzu mafi yawan ƙasashen turawa da larabawa basa haifar fiye da ƴaƴa biyu zuwa uku , amma tare da hakan za kaga taɓarɓarewar tarbiyyar yara a yankainsu ya fi yanda yake a yankinmusau dayawa. Don haka ba tara yara ko rashin tara su bane matsalar , ma'aunin tara su ko rashin tara su ne . Muna roƙon Allah ya bamu kyakkyawan ƙarshe da dacewa . ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 25 / Rabi'ul Awwal / 1448H - 8 / 9 / 2026M

To ina kuma ga wanda yafi kowa daraja da girma Manzon Allah (sawa) , wanda zuwansa ne ya haskaka duniya da zuƙata , ya tseratar da halitta daga halakar duniya da lahira , in ba'a yi Maulidin godiya a ranar da yazo ba me kuwa za'a yi ???? Zan cigaba Insha Allahu Ta'ala....... https://t.me/tafarkintsiratv ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 21/Rabi'ul Auwal/1444H - 18/10/2022

A hankalce da wurin masu hankali abune mummuna kuma aibune wani yayi maka wata ni'ima amma kaƙi gode masa , ko ka ƙi nuna farinci da hakan . Shi yasa in masu Maulidi suka zargi ɗan ƙungiya ko suka tuhumi son Annabinsa kar ya zargi kowa ya zargi kansa , saboda shine ya saɓawa zaunanniyar ƙa'idar hankali da take wajabta masa yin Mauludin, ita ko zaunanniyar dokar hankali da masu hankali ba masu saɓa mata sai masu rangwamen hankali da tunani , ko wanda yake da shubha ko taurin kai da kangarewa . MA'ANAR GODIYA Godiya shine yin (i'itirafi) yarda da ni'imar wanda yayi ni'ima tare da girmamashi . Kuma baya wadatuwa da yarda da cewa ai wane yayi min ni'ima, a'a muhallin godiya wuri uku ne , akwai Zuciya wanda anan ake yarda da ita ni'imar , sannan harshe domin yin hamdala da bayyana yarda da ni'imar , sai kuma gaɓobi da suke taimakawa zuciyar da harshen wajen bayyana godiyar da tabbatar da ita , wannan itace cikakkiyar godiya . wasu kuma suka ce ; Rukunan godiya bisa ni'ima guda biyar ne , Risinawa da girmamawar mai godiya ga abun godewar , nuna masa ƙauna da soyayya, da yarda da cewa tabbas ya yi ni'ima , sannan kuma kar ya aikata abinda abun godewar nasa bayaso . Wallahi ko makiyin masu Maulidi yasan waɗannan abubuwan ake yi a wurin Maulidi , ana aikata waɗannan rukunai na godiya ne ga Allah Ta'ala, bisa ni'imar da yayi ta samuwar farin jakada Annabi Muhammad (sawa) . Haka nan dole ya zama mutum ya nuna godiyar abisa ni'ima gwargwadon ni'imar da akayi masa , ko da mutum ne ya yi maka wata hidima ko kyauta dole godiyarka ta zama tayi daidai da abinda ya maka , shi yasa aka rawaito daga Manzon Allah (sawa ) cewa ; إن الله جعل قلوب عباده على حب من أحسن إليها وبغض من أساء إليها Ma'ana : Allah ya sanya zuƙatan bayinsa abisa son wanda ya kyautata musu , da ƙin wanda ya munana musu . A wata ruwayar kuma da mai ɗakinsa A'isha bintu Abi Bakr ta tambayeshi , game da yanda yake ƙara zage damtse da matsawa kansa wajen yin ibada , duk da cewa an gafarta masa abinda ya gabata da wanda ya jinkirta , sai Manzon Allah (saww) yace mata ; ya ke A'isha shin bazan kasance bawa mai yawan godiya ba (أفلا أكون عبداً شكوراً) ? A wata ruwayar kuma Imam Ali (a.s) yana cewa ; (الإنسان عبد الإحسان) shi mutum bawan kyautatawa ne , wannan magana ce mai fadi da take buƙatar sharhi . Dukkan waɗannan hadisai suna ƙarfafa wannan ƙai'dar ta hankali da muka ambata . Shin muma ba zamu kasance bayi masu yawan godiya , bisa ni'imar da Allah yayi mana ta bamu Manzon Allah (saww) ? KOMAWA FARKO ..... Ta wata fuskar za mu iya cewa : a asali ma Maulidin Annabi (saww) ya wadatu da ace wai yana buƙatar sai an kawo wasu dalilai akan halascin yinsa , domin a wujdaani da lamiri na kowanne mutum zai ji cewa Maulidi baya buƙatar hakan . Yanzu da za'a ce kuna zaune a wani gari a dokar daji , kuna cikin ƙangin rayuwa , talauci , yunwa , wahala , ƙishirwa , annoba , rashin lafiya , duhun jahilci da sauransu ....Kwatsam sai aka ce wani mutum mai daraja yazo rana guda ya kuɓutar daku daga wannan yanayi , ya samar muku da ƴantacciyar rayuwa , ya raya garinku ya zama wani babban birni , ya maidaku mutane mafiya izza da iko a duniya bayan ƙaskanci , a take za kuji zuciya da lamirinku suna motsaku ga nuna duk wani nau'i na farin ciki da godiya , kuma a wannan lokacin ba za ma ku tsaya tunani ko tambayar wai menene dalili ko hujjar da za ta sa kuka yi murna da godiya ba ! Me yasa saboda asalin ɗabi'arku da fiɗirarku anyitane a hakan , don haka (Automatically) za ku yi farin ciki da godiya ta ko wacce hanya ba tare da kun tsaya sauraren dalili ko hujja ba , kamar yanda in kuna jin ƙishirwa ko yunwa bakwa buƙatar dalilin da zai sa ku nemi abinci ko ruwa , to haka shima Maulidi ba ka buƙatar hakan a fiɗirance . Ita kanta ranar da mutumin nan yazo ya kuɓutar daku daga ƙangin da kuke ciki dole ta kasance rana ta musamman gareku , in har da kuna ganin ƙima da darajar wannan mutumi mai daraja da ya ceceku .

HUJJOJI DA DALILAN YIN MAULIDI (01)...... Yana daga cikin abun mamakan zamani ace wai akwai wani mai amsa sunan Musulmi da yake inkarin asalin halascin Maulidin Manzon Allah (sawa) ! Ace har akwai wani mai amsa sunan Musulmi da yake ganin Maulidi a matsayin wani mummunan abu , Bidi'a, saɓawa Shari'a, har takai ga yin ƙazafi da ƙage ga masu yin Maulidin Annabi (sawa) , wai suna iskanci (Wal'izabillah) ..... A tare da haka za kaji suna cewa a basu hujjojin Maulidi , ai ba'a isa a kawo Aya ko Hadisi da suke tabbatar da halasci ko tabbatar da maulidi a matsayin Ibada . Malamai sukance rashin sanin abu ko ganinsa ba shi ke tabbatar da babu shi ba , dan baƙo yaje gari bai ga gidan sarki ba hakan baya nuna babu sarki a garin , za tayu a ƙofar gidan Sarkin ya kwana amma rashin sani yasashi jahiltar hakan , haka suma masu ja da al'amarin Maulidi, ko musa dalilin yinsa rashi sani yakan sa su yi inkari , duk da wani lokacin akwai nau'i na ƙeƙashewar zuciya da son zuciya da taurin kai . Tabbas anyi rubuce-rubuce da raddoji da munazarori akan Maulidi tun shekaru aru-aru, kuma ba'a gushe ba ana basu gamsasshiyar amsa akan wannan mas'alar, to amma abunka da munkiri ! Kuma komai akai da aura sai yaci kara, basu gushe ba suna suna haushin a basu dalili ko hujjar Maulidi! Wannan rubutu zai maida hankali wajen rairayo wasu daga cikin muhimman dalilai da hujjojin yin Maulidi, shiryarwa ga waɗanda ya zama akwai sauran hasken fahimtar gaskiya a tare dasu daga waɗannan mutane , a lokaci kuma amsa ga wasu dayawa da suka nemi in ɗan yi rubutu game da wannan maudu'i ko a taƙaice ne , sai dai ayi haƙuri da ɗan tsawaitawa kaɗan . Zamu kasa dalilai da hujjojin kashi uku ne , kashi na farko dalilai ne na hankali duk da su basa aiki da hankali basu ma sanshi ba , kashi na biyu da na uku kuma daga Alkur'ani da Hadisai ne . KASHI NA FARKO Daga cikin dalilai da hujjojin hankali da suke tabbatar da asalin Maulidi , wanda duk mutum mai lafiyayyen hankali in ya tsaya tsam yayi tunani , zai fahimci cewa Maulidi bama iya halasta yayi bane , a'a , wajibi a hankalice muyi murnar samuwar Annabi (saww) , ƙarƙashin zaunanniyar Ƙa'idar nan da ake mata take da (وجوب شكر المنعم ) ma'ana; Wajabcin godewa wanda yayi maka wata ni'ima. Babu shakka hankali yana yin hukunci da lalurar yin godiya ga duk wani da ya yi maka wata ni'ima . A hankalce duk wanda ya baka wata kyauta komi ƙankantarta ko tsadarta , musamman ace yayi maka kyautar ba zata ko ta ƙure maneji a sanda kake tsananin buƙata , to ya zama wajibi ka gode masa bisa wannan kyauta ko ni'imar da yayi maka . Tom , ina kuma ga ace an maka kyauta da ni'ima da abinda yafi komai tsada da daraja a duniya da lahira , wato Manzon Allah (saww) , shin har akwai wata kyauta ko ni'ima da za'a baka a matsayinka na Musulmi da ta kai Manzon Allah (saww) ? Yanzu da za'a baka dala tiriliyan dubu da duk wata ni'ima ta zahiri da rayuwar yau da gobe, kana buƙatar ace kayi godiya ga wanda ya baka Waɗannan abubuwa ? Yau in akwai wani abu da kake matukar buƙatarsa a rayuwa in akace ga wani da yayi maka silar samunsa kana buƙatar ace sai kayi farin ciki da godiya bisa samunsa ? To shima haka Maudlin Manzon Allah (sawa) wani nau'i ne na Godiya ga Allah Ta'ala, bisa babbar ni'ima da kyautar da yayi mana , ni'ima da kyautar da babu kamarta ta samuwar rahama ga talikai baki ɗaya . A tare da haka har kana jin cewa taron yin godiya ga Allah bisa wannan ni'imar bidi'a ne ? Ko bai da asali ? Ko iskanci ne ? Bayan ga hankalinka yana faɗa maka ka nuna duk wani nau'i na farin ciki gwargwadon iyawakarka , wajen yin godiya ga Allah abisa wannan ni'imar , amma ka saɓawa hankalinka . in ma ba za kayi taka godiyar ta hanyar yin taron Maulidi ba , ai bai kamata ace kuma ka zama mai yiwa wani inkari ba , dan shi yayi tashi godiyar ta hanyar Mauludi .

MAULUDI TSAKANIN MASU YAƘARSA DA SUNAN KARE ADDINI DA MASU AMFANI DA SUNANSHI WAJEN ƁARNA DA KAUCE HANYA !!? 1 . Kuskure ne babba dan kana faɗa da Mauludi ko baka da ra'ayin sa ka dinga ɗakko bidiyoyi da hotunan wasu marasa ɗa'a da tarbiyya da suke amfani da zagayen Mauludi wajen ɓarna da raye-rayen banza da kaɗe-kaɗe na wuce gona da iri da sunan Mauludi da son Annabi (saww) , tabbas hakan da suke yi ba tarbiyyar Mauludi bace kuma karantarwar Musulunci ba ce, kamar yanda yada abinda suke yi yaɗa ɓarna da alfasha ne a ban ƙasa , ƙiyyarka da Mauludi ba shi ke baka dama ka dinga bibiyar wasu abubuwan banza da wawaye ke yi a wajen zagayen Mauludi ba . 2 . Masu yaɗa ɓarnar masu ɓarna da sunan Mauludi me yasa basa yaɗa alkhairai da abubuwan da ake yi a wajen Mauludi na daga karatun Alƙur'ani , tarihin Manzon Allah (saww) , wa'azozi da sauran abubuwa masu kyau da daɗi ?! Allah Ta'ala yana cewa : Kada gaba da ƙiyayyar wasu mutane tasa ku ƙi yi musu adalci .... ولا يجرمنّكم شنآن قوم على ألّا تعدلوا 3 . Ayyukan wauta da rashin dai-dai da wasu suke yi da sunan Mauludi ba ya taɓa zama dalili na rashin halascin yin Mauludi kamar yanda maƙiya Mauludi suke ƙoƙarin nunawa da yada ɓarnar da suke yi , domin zagayen Mauludi ba shi bane kawai Mauludi don haka dalilin su keɓantacce ne , Ko da zagayen Mauludi ko babu shi za a iya yin Mauludi domin ko a iya cikin gida mutum zai iya yin Mauludi shi da iyalan sa . Don haka kuskure da ɓarna da wasu jahilai suke yi da sunan Mauludi ba shi da maraba da barna da shakiyancin da wasu suke yi da sunan sallar tahajjudi da daddare , wata ƙila ma ɓarnar da ake yi da sunan Tahajjudi ba a yinta da sunan Mauludi , in har ɓarnar da ake yi da sunan zagayen Mauludi dalili ne haramta Mauludi to ɓarnar da ake da sunan Tahajjudi ma dalili ne na haramcin yin jami'in Tahajjudi da daddare , wanda babu wani da ya fahimci Shari'a da zai faɗi haka da sunan fatawa , don mutum ya zira hannu a hannun na kusa da shi yayi sata yayin jam'in sallah hakan baya nuna haramcin sallar jam'i a Masallaci , haka satar takalmi a masallaci bata zama dalilin haramcin zuwa Masallaci da sallah . 4 . Masu yaɗa irin waɗannan munanan abubuwan don su nuna haramcin Mauludi ya kamata su nemo wani Malamin Mauludi da yayi fatawa da halascin yin hakan ko ya nuna hakan shine Mauludi a sannan ne suke da bakin magana , Duk da hakan ma ba zai zama dalilin haramcin Mauludi ba . 5 . Tabbas dayawa suna fakewa da sunan zagayen Mauludi suna abubuwan da ba su kamata ba bisa sani ko rashin sani , wanda wannan nauyi ne akan Malamai da Jagororin wannan zagaye da masu kula da shi har masu fitar wajen tashi tsaye domin sa ido da kula akan balagurbi da kuma masu aikata abubuwan da suka saɓawa koyarwar Manzon Allah (saww) da sunan Mauludi ko soyayyar Shugaba (saww) , Allah ya aiko Annabi (saww) don ya shiryar da bayi ya gyara dabi'u da halayen su kuma da wannan ne zai yi alfahari da al'umar sa ba da wani abu ba . Allah ya rabamu da wuce gona da iri a cikin soyayya ko ƙiyayya. ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

YAUSHE AKA FARA BIKIN MAULIDI KUMA SUWAYE SUKA FARESHI ??? Abinda ya shahara a wurin malabarta tarihi cewa farkon wanda ya fara shirya bikin maulidi shine sarkin Irbil "Al-Muzaffar" wanda ya rasu shekara ta 630 bayan hijra , sannan sarakunan daular Faɗimiyyah ta Misra suka ƙayata shi dama wasu daga sarakuna da manyan mutane inda daga nan ne al'amarin maulidi ya yaɗu a tsakanin Musulmi suka karɓe shi hannu bibbiyu. Sai dai abinda nafi rinjayarwa bayan tahƙiƙi da bincike cewa ƴan Shi'a Imamiyya Ithna Ashariyya - Ayyadallahu Burhãnahum - sune farkon wanda suka fara raya al'amarin maulidi kuma suka yi shi , yana daga abinda yake tabbatar da hakan abinda Shehunmu Muhammad bin Muhammad bin Al-nu'uman wanda aka fi sani da Sheikh Al-Mufid ko Ibnul Mu'allim (413H) ya ambata a cikin littafinsa (Masãrush Shi'a shafi na 29) - shekara 136 kafin haihuwar Sarkin Irbil Muzaffar inda Shehun malamin yake cewa : "A ranar 17 ga watan (Rabi'ul Awwal) haihuwar shugabanmu jakadan Allah ta kasance yayin ketowar alfijir a shekarar Giwa , rana ce mai daraja da girman albarka kuma tuntuni nagartattu daga zuriyar Muhammadu basu gushe ba suna girmamata suna sanar da girmanta da kiyaye alfarmarta kuma suna azumtarta , an ruwaito daga limaman shiriya cewa : Wanda ya azumci ranar 17 ga watan Rabi'ul Awwal ranar haihuwar Annabi (saww) Allah zai rubuta masa ladan azumin shekara , kuma a wannan ranar an so yin sadaka , ziyarar wurare masu alfarma , aikata ayyukan alkhairai da farantawa ahlinsa". Haka nan a muƙaddimar littafin nan dai Sheikh Al-Mufid (R) yana cewa : Mutanen kirki daga wannan tawagar (Shi'a) - Allah ya karesu - a tsawon lokuta suna kulawa da waɗannan tarihohi saboda yin ibadu a lokutan tunawa da su , da yin ayyukan neman kusanci da yin abinda ya wajaba ayi na abinda aka ambata da tsaida iyakokin addini a lokacin farin ciki (kamar Mauludi) da baƙin ciki (kamar Ashura) . Don haka wannan magana ta Shehunmu Al-Mufid (R) ta muna yanda Shi'a da jagororinsu (a.s) suke raya al'amarin Mauludi dama juyayi tun ƙarnin farko na Muslunci shekaru ɗaruruwa kafin Sarki Muzaffar da daular ƴan Shi'a Fãɗimiyyah dake Misra su fara nasu . Na'am , za mu iya haɗa ra'ayoyin biyu muce ; Shi'a Imamiyya sune suka fara yin Maulidi da wani salo na musamman na su sannan shima Sarkin Irbil da Faɗimiyyawa suka zo suka yi na su da wani salo daban sai ya zama babu karo in an danganta fara Maulidi ga Shi'a ko da Sarkin Irbil . Irin hakan ne kamar yanda ya shahara a ƙasarmu Najeriya cewa ana yin maulidin Annabi (saww) tun zamanin Shehu ɗan Fodiyo dama kafin nan amma kuma za ka samu mutane da yawa suna cewa Shehu Tijjani Usman Z/bare-bari shine ya fara yin maulidi to anan ma babu tufka da warwara cikin maganganun biyu , domin Maulidin da ake yi a zamanonin baya kafin Shehu Tijjani Usman sun bambanta da irin salon maulidin da shi yazo da shi bayan dawowarsa daga ƙasar Sinigal a ziyararsa Shehu Ibrahim Nyass inda yaga yanda suke yin nasu a can sannan yayi shi a yankinmu har ya yaɗu ya zama shi aka fi sani da Mauludin Annabi (saww) , a kowanne hali dai falalar yin maulidi kowanne iri ne tana komawa ga Shi'a Imamiyyah da jagororinsu domin ance falala tana ga na farkon da ya fara abu "الفضل للمتقدّم". Sannan ayyana tarihin fara maulidi ba shi da wani muhimmaci sosai bayan tabbatuwar mustahabbancin yinsa a Shari'a, kai hatta ayyana tarihin ranar da aka haifi Annabi (saww) ba shi da tasiri wajen hana yin taron Maulidi in mun kau da kai ga mas'alar neman albarka da kuma wasu ayyukan lada da aka ruwaito ana so ayi a ranar . Wallãhul Musta'ãn. ✍️ Khaɗimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 2 / Rajabul Asab / 1446 - 3 / 1 / 2025 Miladiyya.

YAUSHE AKA HAIFI ANNABI (SAWW) ??? Duk ɓangarorin Musulmi da Malaman tarihi sun haɗu akan an haifi Annabi (saww) a shekarar Giwa ba tare da saɓani ba , sai dai anyi saɓani ne akan wane wata ko wace rana aka haifi Annabi (saww) , cikin taƙaita zance da mas'alar saɓanin shine : 1 . Mafi yawan Malaman Ahlussunnah Wal jama'a sun tafi akan cewa an haifi Annabi (saww) ranar Litinin 12 ga watan Rabi'ul Auwal a shekarar Giwa , duk da akwai wasu da suka saɓa hakan a cikin su da kuma ruwayoyin da suka ce , a ranar 8 ga watan ne aka haife shi , wasu suka ce 9 ne , wasu suka ce 10 ne , wasu suka ce 22 ne , wasu suka a ƙarshen watan ne , wasu ma suka ce a watan Ramadan ko Safar ko Rabi'ul Thani aka haifi Annabi (saww) , amma 12 ga watan Rabi'ul Auwal shine zance mafi shahara a wajen su , duk da a maƙamin tabbatar da haka akwai magana . 2 . Zance mafi shahara koma ace kusan wanda duk Malaman Shi'a suka tafi akan shi ( magabata , ƴan baya da na yanzu ) , shine an haifi Annabi (saww) ranar Juma'a 17 ga watan Rabi'ul a lokacin ketowar Alfijir, wannan shine abinda Shehun mu Almufid , Sheik Assaduƙ , Ibnu Ɗawus , Al-allamatul Majlisi da wasun su (Rahimahullah) suka ambata , a cikin "Bihar" ma Al-allamatul Majlisi yana cewa babu wanda ya saɓawa haka sai zance shazi . Na'am, a cikin Littafin Alkafi mai girma Shehun mu Muhammad bin Ya'aƙub Alkulaini (Rahimahullah) ya ambaci cewa a ranar 12 ga watan Rabi'ul Auwal ne aka haifi Annabi (saww) . Amma ba laifi shima abu ne mai kyau yin murna da farin ciki a wannan ranar dama sauran ranaku, kamar yanda ake raya duk watan wasu ma suke tarbar sa da raka shi da murna da farin ciki , tabbas Manzon Allah (saww) ya cancanci fiye da haka , Annabi (saww) ba abun iyakancewa bane da dare ko wuni ko shekara . Sayyid Ibnu Ɗawus yana cewa : Ya kamata girmama ranar haihuwar Annabi (saww) - 17 ga watan Rabi'ul Auwal - ta zama daidai da irin girmamawar da ake wa Annabi mai girma (saww). Lallai wannan magana ce mai girma da dake buƙatar tadabburi akan ta sosai . ME YASA SHI'A SUKA CE RANAR 17 GA WATA AKA HAIFI ANNABI (SAWW)? Abune sananne kuma tabbatacce a hankali da shari'a in ana so a san tarihin mutum musamman lokacin haihuwarsa ana komawa iyayen sa ko makusantan sa da jini da zumunci , ko waɗanda suka san shi , domin ko ba komai su suka fi kowa sanin sa da kusanci dashi , hakan ne yasa Shi'a suka dogara da zantukan makusantan Annabi (saww) da zuriyar sa , wato Ahlul Baiti (a.s) , sunyi bayanin cewa a ranar 17 ga Rabi'ul Auwal aka haifi Annabi (saww) , kuma dama a wajen su Annabi (saww) yace a karɓi Addini a bayan sa . Don haka wannan dalilin kaɗai ya isa ya rinjayar da ra'ayin Shi'a game da tarihin haihuwar Annabi (saww) . اللهم صلّ على من شرفت الصلاة بالصلاة عليه وعلى وآله الأطهار الأخيار . ✍️ hãdimul AshrãfAl-Abdul Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

ABINDA JAGORORIN GWAGWARMAYAR DUNIYA SUKA FAƊA A KAN AYATULLAHI SAYYID ALI SISTANI DA ƳAN SHI'AR IRAƘI FITA TA BAKWAI (07) Wannan jawabin yana ɗauke da wasu muhimman kalmomin jagororin gwagwarmayar wannan ƙarni a haƙƙin Ayatullahi Sayyid Ali Sistaniy (H) da kuma jinjinarsu ga ƴan Shi'ar Iraƙi , wanda haka yake rushe shubhar masu sukar Ayatullahi Sistani da sunan gwagwarmaya ko suke nuna bambanci tsakanin Shi'ancin Iraƙi da Iran. Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 15/ Rabi'ul Awwal / 1448H - 29 / 8 / 2026 M

Audio from العبد الفاني الكنوي

SHIN AYATULLAHI SISTANI NE YA SHIGO DA AMERIKAWA IRAƘI HAR YA BASU MAFAKA DA IKON ZAMA ??? FITA TA SHIDA (06) *Wannan jawabin yana ɗauke da amsoshi , fatawoyi da bayanan Sayyid Ali Sistaniy (H) a kan sha'anin Iraƙi tun bayan faɗuwar Gwamnatin Saddam L zuwa yau, duk cikin warware shubhohin masu sukarsa da zaginsa a zauren Nurul Haq* Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 👇👇👇👇👇👇 https://t.me/tafarkintsiratv 13/ Rabi'ul Awwal / 1448H - 25 / 8 / 2026 M

Audio from العبد الفاني الكنوي

*Amshoshin Sayyid Ali Sistaniy (H) daga ofishinsa a kan Amerika da siyasar iraƙi tun bayan faɗuwar Saddam (L) zuwa yau* *WARWARE SHUBHOHIN UWAR ƳAN NURUL HAƘƘI DA ƳAN KORENTA* *FITA TA BIYAR (05)* *Wannan jawabin yana ɗauke da amsoshi , fatawoyi da bayanan Sayyid Sistaniy a kan sha'anin Iraƙi tun bayan faduwar Gwamnatin Saddam zuwa yau* Tare da 🎙️ Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 11/ Rabi'ul Awwal / 1447H - 25 / 8 / 2026 M

Audio from العبد الفاني الكنوي

Daga cikin matan Manzon Allah (saww) Sayyida Khadija tafi kowacce samun matsayi mai girma da daraja a wurinsa, wasu ruwayoyin tarihi sun tabbatar da cewa ; Ya kasance a tsawon rayuwarsa yana ambatonta da alkhairi , yana mai tabbatar da matsayinta a cikin zuciyarsa maɗaukakiya , yana yabonta sannan baya ganin akwai wacce zata samu matsayinta a wajensa , ba ita ba har ƙawaye da makusantanta ya cigaba da kyautata musu a bayan rayuwarta saboda albarkacinta . Sayyida Khadijah ta kasance tare da Manzon Allah (saww) hannu da hannu , a cikin dukkan yanayin da ya shiga a takura da ƙuntatawa a farkon fara da'awar musulunci, ta bashi gudummawa da kariya da duk abinda ta mallaka , misalai da ƙissoshi sun yawaita akan haka . Ta kasance mai kyawawan da ɗabi'un girma da ɗaukaka , ma'abociyar sifofin kamala da cika (Radiyallahu anha) . ✍️Khadimul Itrah Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 10/Rabi'ul Auwal/1444H - 7/10/2022 https://t.me/tafarkintsiratv