📚🖍Darul Fikr Na Mahdi Sanda 📚🖍
Ir al canal en Telegram
وَأَعِدُّوا لَهُم مَّا اسْتَطَعْتُم مِّن قُوَّةٍ.......! #Fikira_Ruhi_Jiki. #Kai_Da_Jama'a.
Mostrar más802
Suscriptores
+124 horas
-17 días
-630 días
Carga de datos en curso...
Canales Similares
Sin datos
¿Algún problema? Por favor, actualice la página o contacte a nuestro gerente de soporte.
Nube de Etiquetas
Sin datos
¿Algún problema? Por favor, actualice la página o contacte a nuestro gerente de soporte.
Menciones Entrantes y Salientes
---
---
---
---
---
---
Atraer Suscriptores
septiembre '26
septiembre '26
+1
en 0 canales
agosto '26
+10
en 0 canales
Get PRO
julio '26
+4
en 0 canales
Get PRO
junio '26
+6
en 0 canales
Get PRO
mayo '26
+4
en 0 canales
Get PRO
abril '26
+4
en 0 canales
Get PRO
marzo '26
+23
en 0 canales
Get PRO
febrero '26
+4
en 0 canales
Get PRO
enero '26
+12
en 0 canales
Get PRO
diciembre '25
+33
en 1 canales
Get PRO
noviembre '25
+20
en 0 canales
Get PRO
octubre '25
+113
en 0 canales
Get PRO
septiembre '25
+9
en 0 canales
Get PRO
agosto '25
+7
en 0 canales
Get PRO
julio '25
+7
en 0 canales
Get PRO
junio '25
+20
en 0 canales
Get PRO
mayo '25
+15
en 0 canales
Get PRO
abril '25
+18
en 0 canales
Get PRO
marzo '25
+5
en 0 canales
Get PRO
febrero '25
+18
en 0 canales
Get PRO
enero '25
+5
en 0 canales
Get PRO
diciembre '24
+15
en 0 canales
Get PRO
noviembre '24
+23
en 0 canales
Get PRO
octubre '24
+17
en 0 canales
Get PRO
septiembre '24
+125
en 0 canales
Get PRO
agosto '24
+120
en 0 canales
Get PRO
julio '24
+21
en 0 canales
Get PRO
junio '24
+17
en 0 canales
Get PRO
mayo '24
+26
en 0 canales
Get PRO
abril '24
+27
en 0 canales
Get PRO
marzo '24
+9
en 0 canales
Get PRO
febrero '24
+7
en 0 canales
Get PRO
enero '24
+26
en 0 canales
Get PRO
diciembre '23
+8
en 0 canales
Get PRO
noviembre '23
+4
en 0 canales
Get PRO
octubre '23
+5
en 0 canales
Get PRO
septiembre '230
en 0 canales
Get PRO
agosto '23
+4
en 0 canales
Get PRO
julio '23
+3
en 0 canales
Get PRO
junio '23
+5
en 0 canales
Get PRO
mayo '23
+4
en 0 canales
Get PRO
abril '23
+1
en 0 canales
Get PRO
marzo '23
+10
en 0 canales
Get PRO
febrero '23
+7
en 0 canales
Get PRO
enero '23
+25
en 0 canales
Get PRO
diciembre '22
+17
en 0 canales
Get PRO
noviembre '22
+274
en 0 canales
| Fecha | Crecimiento de Suscriptores | Menciones | Canales | |
| 03 septiembre | +1 | |||
| 02 septiembre | 0 | |||
| 01 septiembre | 0 |
Publicaciones del Canal
Da alama ra’ayin Imam shi ne cewa, duk da cewa Musulunci yana da wani nau’i na musamman na mulki, da shirye-shirye da kuma ka’ida ta musamman idan aka kwatanta da wasu shakalolin gwamnati, ana iya ɗaukar wannan ka’ida ta musamman a matsayin ka’ida “marar sharadi” (la bisharɗiyya) idan aka kwatanta da wasu nau’o’in gwamnati. A wannan yanayin kuma, ana girmama ra’ayin al’umma kuma yana da tasiri da girmamawa kuma yana zama tilas.
Idan muka yi zurfin nazari a kan waɗannan bayanai biyu na ƙarshe da aka nakalto daga Imam Khumaini, za mu samu tabbaci ga wannan fassarar. Domin ya bar ƙayyade shakalin Jamhuriyar Musulunci ga al’umma, tare da tabbatar da muhimman abubuwa biyu: dogaro da Musulunci da kuma kula da ra’ayin al’umma tare.
A bayyane yake cewa waɗannan abubuwa guda biyu dukansu suna daga cikin muhimman shakalolin tsarin gwamnati. Duk da haka, tsare-tsaren gwamnati masu dogaro da al’umma da kuma masu dogaro da wata akida suna ƙunshe da wasu abubuwa masu yawa fiye da haka, inda al’umma take wakiltar ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa.
Saboda haka, amsar tambayar da aka gabatar a farkon wannan bincike ita ce: A mahangar Imam Khumaini, Musulunci yana da kuma ba shi da shakalin gwamnati a lokaci guda.
Ma’anar wannan ita ce: Musulunci yana da wasu ƙa’idoji da iyakoki na musamman game da gwamnati, kuma waɗannan ƙa’idoji a zahiri suna da ikon ƙayyade wani nau’i na musamman na gwamnati. Amma dangane da nau’o’in da wannan nau’in gwamnati, wato Gwamnatin Musulunci, ya ƙunsa, Imam ya bar wannan al’amari ga buƙatun lokaci da wuri, da kuma yadda mutane suke karɓa ko juya baya.
Dangane da wannan muhimmin batu, Imam ya yi magana a kan wasu bambance-bambancen da suke tsakanin Gwamnatin Musulunci da wasu siffofin tsarin mulki da ake da su. A wasu lokuta kuma bai ba shakalin gwamnati muhimmanci sosai ba, yayin da a lokaci guda yake nuni da wasu shakalin na Gwamnatin Musulunci waɗanda ake ɗauka cewa “ana karɓarsu a duk inda aka same su a cikin wani tsarin gwamnati.”
Yana da kyau a yi nuni a nan cewa ra’ayin Imam gaba ɗaya ya yi daidai da abin da Allamah Muhammad Husain aɗ-Ɗabaɗaba’i ya kawo a cikin risalarsa mai suna “Al-Walayah waz-Za'amah fil-Islam”, inda yake cewa:
“A cikin Shari’ar Musulunci ba a samu wani hukunci da ya bayyana (wani takamaiman tsarin gwamnati) ba. Kuma gaskiyar magana ita ce, bai kamata hakan ya kasance ba, domin Shari’a ta ƙunshi ginshiƙai da dokoki tabbatattu na addini ne kawai, yayin da shakali/siffar gwamnati take fuskantar sauyi da canji, wanda shi ne halin kowace al’umma, gwargwadon ci gaban wayewar kai. Saboda haka, abin da kawai za a iya cewa game da wannan al’amari shi ne, dole ne a ƙayyade shakali/siffar Gwamnatin Musulunci tare da yin la’akari da abubuwa uku tabbatattu a cikin Shari’ar Musulunci.”
Bayan haka, marigayi Allamah ya yi nuni da abubuwa uku da aka ambata, waɗanda za mu tattauna daga baya. Ya kuma bayyana a cikin risalarsa cewa, duk da sassaucin da Musulunci ya nuna wajen ƙayyade siffa da nau’in gwamnati, hakan ba yana nufin ya yi watsi da ƙa’idojin da suka tabbata a cikin Gwamnatin Musulunci ba, waɗanda a mahangar Allamah, guda uku ne. Saboda haka, muna ganin Musulunci yana ƙin wasu shakalolin gwamnati waɗanda ba su ƙunshi waɗannan abubuwa ba.
A wata ma’anar, abin da ya bambanta shakalin Gwamnatin Musulunci shi ne ba ta amincewa da kowane irin shakalin gwamnati ba, ko yaya aka same shi ko, duk da faɗin mahangarta da yalwar da’irar da take da.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
| 2 | Duk da haka, Imam Khumaini ya musanta sau da yawa wannan da’awar cewa Musulunci yana da wani takamaiman tsari na mulki. Lokacin da wakilin jaridar “The Guardian” ta Biritaniya ya tambaye shi cewa: “To, ya kai Ayatullah, kuna son ku kifar da tsarin sarautar da ake da shi, ku maye gurbinsa da tsarin jamhuriya. Wane irin tsarin jamhuriya kuke shirin kafawa? Shin zai yi kama da tsarin Amurka ne ko na Faransa?” Sai Imam ya amsa da cewa:
“Muna son kafa Jamhuriyar Musulunci, wadda ita ce gwamnati da ta dogara ga ra’ayoyin al’umma. Amma shakalin ƙarshe na wannan gwamnati, al’umma da kanta za ta ayyana ta bisa ga yanayi da buƙatun da ake ciki a yanzu a cikin al’ummarmu.”
A cikin amsar da ya bayar ga tambayar wakilin mujallar “Al-Mustaqbal” cewa: “Shin kuna son kafa gwamnatin Musulunci mai kama da gwamnatin da take a zamanin Imam Ali (A.S.)?” Imam ya ce:
“Gwamnatin Jamhuriyar Musulunci da muke burin kafawa tana yin koyi da tafarkin Annabi Mai Girma (S.) da Imam Ali (A.S.), kuma ta dogara ga ra’ayoyin al’umma. Za a ƙayyade shakalin gwamnati ne ta hanyar komawa ga ra’ayin al’umma.”
Idan muka ajiye waɗannan bayanai biyu a gefe, za mu ga cewa hanyar da Imam Khumaini ya bi wajen gudanar da ƙuri’ar jin ra’ayin jama’a kan shakalin gwamnati bayan nasarar Juyin Juya Halin Musulunci, tana nuni a sarari cewa takamaiman shakalin gwamnati — kamar Jamhuriyar Musulunci — bai samo asali kai tsaye daga Musulunci ba. Domin babu ma’anar gudanar da ƙuri’ar jama’a kan wani hukunci da ake cewa wajibi ne a tsarin da aka riga aka ayyana cewa zai yi aiki bisa Musulunci.
Idan muka amince da shakku cewa, saboda cikakken tsammanin Imam da kuma tabbataccen hasashensa cewa al’umma za ta kada ƙuri’a don goyon bayan Jamhuriyar Musulunci, wannan ƙuri’a ba komai ba ce face wani mataki na dogaro sosai da al’umma, da kuma wani matakin dabara da aka ɗauka a matsayin martani ga yanayin da ake ciki a ƙasashen duniya; to, idan muka amince da wannan, kalaman Imam cewa:
“Shakalin ƙarshe na wannan gwamnati an bar shi ga al’umma da kanta domin ta yanke hukunci a kansa bisa ga yanayi da buƙatun da ake ciki a yanzu a cikin al’ummarmu.”
suna nuna a sarari cewa bai goyi bayan ra’ayin cewa akwai shakali guda ɗaya tak na gwamnati a Musulunci wanda dole ne a bi a kowane zamani da kowane lokaci ba. Saboda haka, muna ganin cewa bai bar batun ƙayyade nau’in gwamnati ga ra’ayin al’umma kawai ba, har ma ya danganta shi da yanayi da buƙatun kowane mataki na lokaci.
Saboda abin da aka ambata, kuma tun da tambayar farko, wato: “Shin Musulunci yana da takamaiman shakali, ka’ida ko tsarin gwamnati?” tana da amsoshi biyu waɗanda a zahiri suke kama da masu karo da juna, babu makawa mu koma ga batun da muka yi nuni da shi a baya.
Da alama dai musantawa da tabbatarwar Imam ba su faru a wuri guda ba, kuma ba su shafi abu guda ba. Haɗa batun tabbatar da cewa Musulunci yana da wata ka’ida ta musamman game da gwamnati, tare da musanta cewa yana da ita, abu ne mai yiwuwa. Mun riga mun ambata cewa ana iya kallon wasu shakalolin gwamnati a matsayin shakali na musamman na gwamnati daga wata mahangar; daga wata mahangar kuma, ana iya ɗaukar su a matsayin ɗaya daga cikin shakalolii, ta hanyar kwatanta su da wasu abubuwa daban-daban.
Ana iya kallon su a matsayin wani nau’i mai faɗi wanda ya ƙunshi shakaloli daban-daban. Misali, duk da cewa dimokuraɗiyya tana wakiltar wani takamaiman shakali na gwamnati idan aka kwatanta da aristocracy, kuma Plato ya yi imani cewa aristocracy ita ce mafi kyawun nau’in gwamnati, yana kuma ƙin dimokuraɗiyya; duk da haka, wannan takamaiman shakalin gwamnati ba haka yake ba idan aka kwatanta da faɗin nau’o’in dimokuraɗiyya: dimokuraɗiyyar jari-hujja, dimokuraɗiyyar gurguzu, dimokuraɗiyya mai ’yanci, da dimokuraɗiyya mai ’yanci da adalci.
Haka nan lamarin yake game da tsarin mulki a Musulunci. | 19 |
| 3 | WACE GWAMNATI CE TAFI? Al'ummomi da Neman Mulki Mafi Kyawu.
KASHI NA SHIDA (8).
Shakalin Gwamnatin Musulumci.
Domin Amsa wannan tambayar cewa: Shin Musulunci ya gabatar da wani takamaiman shakalin gwamnati ko kuwa bai gabatar ba?.
Zamu dogara d Ra’ayin Imam Khumaini (Q.d) gun bayyana wannan. A tafiyar rayuwarsa ta tunani da siyasa, Imam Khumaini bai yi magana a kan batun Shakalin Gwamnatin Musulunci ba sai a wasu lokuta na musamman. Idan aka yi la’akari da yanayi na lokaci da wuri, wadanda a zahiri za'a iya kallon sun ci karo da juna, Shi kansa ya yi nuni da waɗannan matsayoyan a jere a cikin littafinsa mai suna “Kashful-Asrar”, yayin da yake mayar da martani ga shubuhohin da suke bayyana Shi’a da malaman addini a matsayin masu haifar da hargitsi da masu adawa da gwamnati.
Bayan haka, musamman a shekarun farko na gwagwarmayar da aka kira “lokacin ihuwa”, ya tsayu zuwa wani haddi don watsi da irin tsarin gwamnatin da ake da shi a lokacin, tare da bayyana wasu daga cikin shakalin Gwamnatin Musulunci. Daga baya kuma ya fara tattauna batun Walayatul-Faqih a cikin “Kitabul-Baie’”. A lokacin da ya biyo baya, ya ƙara yin bayani dalla-dalla game da shakalin Gwamnatin Musulunci, tare da kwatanta ta da sauran tsare-tsaren gwamnati masu kama da ita, yayin da yake amsa tambayoyin ’yan jarida na ƙasashen waje kafin da kuma bayan wasu watanni daga nasarar Juyin Juya Halin Musulunci, har a ƙarshe aka amince da tsarin gwamnatin da aka gabatar a cikin Kundin Tsarin Mulkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Tabbas, ana iya fahimtar sigar ƙarshe ta ka’idarsa ta hanyar kalaman da ya yi bayan nasarar Juyin Juya Halin Musulunci, da kuma ra’ayoyinsa a cikin shekarar ƙarshe ko shekaru biyu na ƙarshe na rayuwarsa.
Dangane da tambayar da aka gabatar a farkon wannan bincike kuwa, Imam Khumaini ya ba da amsarta ta hanyoyi daban-daban kuma masu bambancin matsayi. A wasu daga cikinsu ya tabbatar da cewa Musulunci yana da shakali da ka’idar gwamnati, yayin da a wasu amsoshin kuma ya musanta hakan.
Da farko za mu fara da waɗannan kalamai da suke tabbatar da samuwar wata ka’ida ta musamman game da Gwamnatin Musulunci:
“Musulunci yana da nasa tsarin zamantakewa, tattalin arziki da al’adu na musamman, kuma yana da dokoki da ƙa’idoji masu yawa waɗanda suka shafi dukkan fannoni da al’amuran rayuwar mutum da al’umma, kuma ba ya amincewa da wani abu daban da su a matsayin abin da zai tabbatar da farin cikin al’umma.”
Yana da kyau a yi nuni a nan cewa Imam Khumaini ya faɗi wannan magana ne a matsayin amsa ga tambayar da wakilin jaridar “The Times” ta London ya yi masa. Kamar yadda yake a fili, Imam bai yi magana game da nau’in tsarin na musamman ba, kuma bai yi nuni da shakalin wannan tsarin ba. Bayanin da ya yi kawai yana da alaƙa da yalwar dokokin Musulunci a fagen ibada da siyasa.
Ma’anar wannan ita ce, hakika Musulunci ya yi magana game da dokokin zamantakewa da na siyasa a lokaci guda, amma wannan ba lallai ne ya nuna cewa Musulunci yana da wani takamaiman shakalin gwamnati ba. Ko yaya dai, abin da zai iya kawar da ruɗanin da ke tattare da nau’in tsarin addini na musamman da aka ambata a wannan magana shi ne amsar da Imam ya bayar ga wata tambaya daga wannan wakilin jarida ɗin. Ya tambaye shi a sarari cewa: Wane irin gwamnati kuke son kafawa a Iran? Sai Imam ya amsa da cewa:
“Mun gabatar da tsarin Jamhuriyar Musulunci, kuma al’umma ta amince da shi tare da kada ƙuri’a a kansa ta hanyar zanga-zangar da suka gudanar. Gwamnati ce da ta dogara ga ra’ayin al’umma da kuma ƙa’idoji da ma’aunan Musulunci.”
Sai dai wannan magana da Imam ya yi ba ta wadatar da buƙata kamar wadda ta gabata ba. Na farko, saboda shakalin gwamnatin da ya ambata a amsar ba ita ce, a zahiri, takamaiman shakalin da ake nufi da Gwamnatin Musulunci ba. Na biyu kuma, saboda ya takaita ne kawai da ambaton shakaloli guda biyu waɗanda Gwamnatin Musulunci ta dogara da su, wato “dogaro da ra’ayin al’umma” da kuma “tsayuwa a kan ƙa’idoji da ma’aunan Musulunci.” | 13 |
| 4 | Sin texto... | 10 |
| 5 | Da alama ra’ayin Imam shi ne cewa, duk da cewa Musulunci yana da wani nau’i na musamman na mulki, da shirye-shirye da kuma ka’ida ta musamman idan aka kwatanta da wasu shakalolin gwamnati, ana iya ɗaukar wannan ka’ida ta musamman a matsayin ka’ida “marar sharadi” (la bisharɗiyya) idan aka kwatanta da wasu nau’o’in gwamnati. A wannan yanayin kuma, ana girmama ra’ayin al’umma kuma yana da tasiri da girmamawa kuma yana zama tilas.
Idan muka yi zurfin nazari a kan waɗannan bayanai biyu na ƙarshe da aka nakalto daga Imam Khumaini, za mu samu tabbaci ga wannan fassarar. Domin ya bar ƙayyade shakalin Jamhuriyar Musulunci ga al’umma, tare da tabbatar da muhimman abubuwa biyu: dogaro da Musulunci da kuma kula da ra’ayin al’umma tare.
A bayyane yake cewa waɗannan abubuwa guda biyu dukansu suna daga cikin muhimman shakalolin tsarin gwamnati. Duk da haka, tsare-tsaren gwamnati masu dogaro da al’umma da kuma masu dogaro da wata akida suna ƙunshe da wasu abubuwa masu yawa fiye da haka, inda al’umma take wakiltar ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa.
Saboda haka, amsar tambayar da aka gabatar a farkon wannan bincike ita ce: A mahangar Imam Khumaini, Musulunci yana da kuma ba shi da shakalin gwamnati a lokaci guda.
Ma’anar wannan ita ce: Musulunci yana da wasu ƙa’idoji da iyakoki na musamman game da gwamnati, kuma waɗannan ƙa’idoji a zahiri suna da ikon ƙayyade wani nau’i na musamman na gwamnati. Amma dangane da nau’o’in da wannan nau’in gwamnati, wato Gwamnatin Musulunci, ya ƙunsa, Imam ya bar wannan al’amari ga buƙatun lokaci da wuri, da kuma yadda mutane suke karɓa ko juya baya.
Dangane da wannan muhimmin batu, Imam ya yi magana a kan wasu bambance-bambancen da suke tsakanin Gwamnatin Musulunci da wasu siffofin tsarin mulki da ake da su. A wasu lokuta kuma bai ba shakalin gwamnati muhimmanci sosai ba, yayin da a lokaci guda yake nuni da wasu shakalin na Gwamnatin Musulunci waɗanda ake ɗauka cewa “ana karɓarsu a duk inda aka same su a cikin wani tsarin gwamnati.”
Yana da kyau a yi nuni a nan cewa ra’ayin Imam gaba ɗaya ya yi daidai da abin da Allamah Muhammad Husain aɗ-Ɗabaɗaba’i ya kawo a cikin risalarsa mai suna “Al-Walayah waz-Za'amah fil-Islam”, inda yake cewa:
“A cikin Shari’ar Musulunci ba a samu wani hukunci da ya bayyana (wani takamaiman tsarin gwamnati) ba. Kuma gaskiyar magana ita ce, bai kamata hakan ya kasance ba, domin Shari’a ta ƙunshi ginshiƙai da dokoki tabbatattu na addini ne kawai, yayin da shakali/siffar gwamnati take fuskantar sauyi da canji, wanda shi ne halin kowace al’umma, gwargwadon ci gaban wayewar kai. Saboda haka, abin da kawai za a iya cewa game da wannan al’amari shi ne, dole ne a ƙayyade shakali/siffar Gwamnatin Musulunci tare da yin la’akari da abubuwa uku tabbatattu a cikin Shari’ar Musulunci.”
Bayan haka, marigayi Allamah ya yi nuni da abubuwa uku da aka ambata, waɗanda za mu tattauna daga baya. Ya kuma bayyana a cikin risalarsa cewa, duk da sassaucin da Musulunci ya nuna wajen ƙayyade siffa da nau’in gwamnati, hakan ba yana nufin ya yi watsi da ƙa’idojin da suka tabbata a cikin Gwamnatin Musulunci ba, waɗanda a mahangar Allamah, guda uku ne. Saboda haka, muna ganin Musulunci yana ƙin wasu shakalolin gwamnati waɗanda ba su ƙunshi waɗannan abubuwa ba.
A wata ma’anar, abin da ya bambanta shakalin Gwamnatin Musulunci shi ne ba ta amincewa da kowane irin shakalin gwamnati ba, ko yaya aka same shi ko, duk da faɗin mahangarta da yalwar da’irar da take da.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda | 1 |
| 6 | Duk da haka, Imam Khumaini ya musanta sau da yawa wannan da’awar cewa Musulunci yana da wani takamaiman tsari na mulki. Lokacin da wakilin jaridar “The Guardian” ta Biritaniya ya tambaye shi cewa: “To, ya kai Ayatullah, kuna son ku kifar da tsarin sarautar da ake da shi, ku maye gurbinsa da tsarin jamhuriya. Wane irin tsarin jamhuriya kuke shirin kafawa? Shin zai yi kama da tsarin Amurka ne ko na Faransa?” Sai Imam ya amsa da cewa:
“Muna son kafa Jamhuriyar Musulunci, wadda ita ce gwamnati da ta dogara ga ra’ayoyin al’umma. Amma shakalin ƙarshe na wannan gwamnati, al’umma da kanta za ta ayyana ta bisa ga yanayi da buƙatun da ake ciki a yanzu a cikin al’ummarmu.”
A cikin amsar da ya bayar ga tambayar wakilin mujallar “Al-Mustaqbal” cewa: “Shin kuna son kafa gwamnatin Musulunci mai kama da gwamnatin da take a zamanin Imam Ali (A.S.)?” Imam ya ce:
“Gwamnatin Jamhuriyar Musulunci da muke burin kafawa tana yin koyi da tafarkin Annabi Mai Girma (S.) da Imam Ali (A.S.), kuma ta dogara ga ra’ayoyin al’umma. Za a ƙayyade shakalin gwamnati ne ta hanyar komawa ga ra’ayin al’umma.”
Idan muka ajiye waɗannan bayanai biyu a gefe, za mu ga cewa hanyar da Imam Khumaini ya bi wajen gudanar da ƙuri’ar jin ra’ayin jama’a kan shakalin gwamnati bayan nasarar Juyin Juya Halin Musulunci, tana nuni a sarari cewa takamaiman shakalin gwamnati — kamar Jamhuriyar Musulunci — bai samo asali kai tsaye daga Musulunci ba. Domin babu ma’anar gudanar da ƙuri’ar jama’a kan wani hukunci da ake cewa wajibi ne a tsarin da aka riga aka ayyana cewa zai yi aiki bisa Musulunci.
Idan muka amince da shakku cewa, saboda cikakken tsammanin Imam da kuma tabbataccen hasashensa cewa al’umma za ta kada ƙuri’a don goyon bayan Jamhuriyar Musulunci, wannan ƙuri’a ba komai ba ce face wani mataki na dogaro sosai da al’umma, da kuma wani matakin dabara da aka ɗauka a matsayin martani ga yanayin da ake ciki a ƙasashen duniya; to, idan muka amince da wannan, kalaman Imam cewa:
“Shakalin ƙarshe na wannan gwamnati an bar shi ga al’umma da kanta domin ta yanke hukunci a kansa bisa ga yanayi da buƙatun da ake ciki a yanzu a cikin al’ummarmu.”
suna nuna a sarari cewa bai goyi bayan ra’ayin cewa akwai shakali guda ɗaya tak na gwamnati a Musulunci wanda dole ne a bi a kowane zamani da kowane lokaci ba. Saboda haka, muna ganin cewa bai bar batun ƙayyade nau’in gwamnati ga ra’ayin al’umma kawai ba, har ma ya danganta shi da yanayi da buƙatun kowane mataki na lokaci.
Saboda abin da aka ambata, kuma tun da tambayar farko, wato: “Shin Musulunci yana da takamaiman shakali, ka’ida ko tsarin gwamnati?” tana da amsoshi biyu waɗanda a zahiri suke kama da masu karo da juna, babu makawa mu koma ga batun da muka yi nuni da shi a baya.
Da alama dai musantawa da tabbatarwar Imam ba su faru a wuri guda ba, kuma ba su shafi abu guda ba. Haɗa batun tabbatar da cewa Musulunci yana da wata ka’ida ta musamman game da gwamnati, tare da musanta cewa yana da ita, abu ne mai yiwuwa. Mun riga mun ambata cewa ana iya kallon wasu shakalolin gwamnati a matsayin shakali na musamman na gwamnati daga wata mahangar; daga wata mahangar kuma, ana iya ɗaukar su a matsayin ɗaya daga cikin shakalolii, ta hanyar kwatanta su da wasu abubuwa daban-daban.
Ana iya kallon su a matsayin wani nau’i mai faɗi wanda ya ƙunshi shakaloli daban-daban. Misali, duk da cewa dimokuraɗiyya tana wakiltar wani takamaiman shakali na gwamnati idan aka kwatanta da aristocracy, kuma Plato ya yi imani cewa aristocracy ita ce mafi kyawun nau’in gwamnati, yana kuma ƙin dimokuraɗiyya; duk da haka, wannan takamaiman shakalin gwamnati ba haka yake ba idan aka kwatanta da faɗin nau’o’in dimokuraɗiyya: dimokuraɗiyyar jari-hujja, dimokuraɗiyyar gurguzu, dimokuraɗiyya mai ’yanci, da dimokuraɗiyya mai ’yanci da adalci.
Haka nan lamarin yake game da tsarin mulki a Musulunci. | 1 |
| 7 | WACE GWAMNATI CE TAFI? Al'ummomi da Neman Mulki Mafi Kyawu.
KASHI NA SHIDA (8).
Shakalin Gwamnatin Musulumci.
Domin Amsa wannan tambayar cewa: Shin Musulunci ya gabatar da wani takamaiman shakalin gwamnati ko kuwa bai gabatar ba?.
Zamu dogara d Ra’ayin Imam Khumaini (Q.d) gun bayyana wannan. A tafiyar rayuwarsa ta tunani da siyasa, Imam Khumaini bai yi magana a kan batun Shakalin Gwamnatin Musulunci ba sai a wasu lokuta na musamman. Idan aka yi la’akari da yanayi na lokaci da wuri, wadanda a zahiri za'a iya kallon sun ci karo da juna, Shi kansa ya yi nuni da waɗannan matsayoyan a jere a cikin littafinsa mai suna “Kashful-Asrar”, yayin da yake mayar da martani ga shubuhohin da suke bayyana Shi’a da malaman addini a matsayin masu haifar da hargitsi da masu adawa da gwamnati.
Bayan haka, musamman a shekarun farko na gwagwarmayar da aka kira “lokacin ihuwa”, ya tsayu zuwa wani haddi don watsi da irin tsarin gwamnatin da ake da shi a lokacin, tare da bayyana wasu daga cikin shakalin Gwamnatin Musulunci. Daga baya kuma ya fara tattauna batun Walayatul-Faqih a cikin “Kitabul-Baie’”. A lokacin da ya biyo baya, ya ƙara yin bayani dalla-dalla game da shakalin Gwamnatin Musulunci, tare da kwatanta ta da sauran tsare-tsaren gwamnati masu kama da ita, yayin da yake amsa tambayoyin ’yan jarida na ƙasashen waje kafin da kuma bayan wasu watanni daga nasarar Juyin Juya Halin Musulunci, har a ƙarshe aka amince da tsarin gwamnatin da aka gabatar a cikin Kundin Tsarin Mulkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Tabbas, ana iya fahimtar sigar ƙarshe ta ka’idarsa ta hanyar kalaman da ya yi bayan nasarar Juyin Juya Halin Musulunci, da kuma ra’ayoyinsa a cikin shekarar ƙarshe ko shekaru biyu na ƙarshe na rayuwarsa.
Dangane da tambayar da aka gabatar a farkon wannan bincike kuwa, Imam Khumaini ya ba da amsarta ta hanyoyi daban-daban kuma masu bambancin matsayi. A wasu daga cikinsu ya tabbatar da cewa Musulunci yana da shakali da ka’idar gwamnati, yayin da a wasu amsoshin kuma ya musanta hakan.
Da farko za mu fara da waɗannan kalamai da suke tabbatar da samuwar wata ka’ida ta musamman game da Gwamnatin Musulunci:
“Musulunci yana da nasa tsarin zamantakewa, tattalin arziki da al’adu na musamman, kuma yana da dokoki da ƙa’idoji masu yawa waɗanda suka shafi dukkan fannoni da al’amuran rayuwar mutum da al’umma, kuma ba ya amincewa da wani abu daban da su a matsayin abin da zai tabbatar da farin cikin al’umma.”
Yana da kyau a yi nuni a nan cewa Imam Khumaini ya faɗi wannan magana ne a matsayin amsa ga tambayar da wakilin jaridar “The Times” ta London ya yi masa. Kamar yadda yake a fili, Imam bai yi magana game da nau’in tsarin na musamman ba, kuma bai yi nuni da shakalin wannan tsarin ba. Bayanin da ya yi kawai yana da alaƙa da yalwar dokokin Musulunci a fagen ibada da siyasa.
Ma’anar wannan ita ce, hakika Musulunci ya yi magana game da dokokin zamantakewa da na siyasa a lokaci guda, amma wannan ba lallai ne ya nuna cewa Musulunci yana da wani takamaiman shakalin gwamnati ba. Ko yaya dai, abin da zai iya kawar da ruɗanin da ke tattare da nau’in tsarin addini na musamman da aka ambata a wannan magana shi ne amsar da Imam ya bayar ga wata tambaya daga wannan wakilin jarida ɗin. Ya tambaye shi a sarari cewa: Wane irin gwamnati kuke son kafawa a Iran? Sai Imam ya amsa da cewa:
“Mun gabatar da tsarin Jamhuriyar Musulunci, kuma al’umma ta amince da shi tare da kada ƙuri’a a kansa ta hanyar zanga-zangar da suka gudanar. Gwamnati ce da ta dogara ga ra’ayin al’umma da kuma ƙa’idoji da ma’aunan Musulunci.”
Sai dai wannan magana da Imam ya yi ba ta wadatar da buƙata kamar wadda ta gabata ba. Na farko, saboda shakalin gwamnatin da ya ambata a amsar ba ita ce, a zahiri, takamaiman shakalin da ake nufi da Gwamnatin Musulunci ba. Na biyu kuma, saboda ya takaita ne kawai da ambaton shakaloli guda biyu waɗanda Gwamnatin Musulunci ta dogara da su, wato “dogaro da ra’ayin al’umma” da kuma “tsayuwa a kan ƙa’idoji da ma’aunan Musulunci.” | 1 |
| 8 | Ya ɗauki ‘ya’yansa, ‘yarsa, jikarsa, surukinsa, ‘ya’yansa; da yawa daga cikinsu sun samu raunuka, kuma Mai Girma Imam Jagora yana cikin wani yanayi da nake gaya muku yana da wahala, amma suna da ƙarfi. Wannan shi ne addini.
- Wanda yake a gaba shi ne mafi zuhudu, wanda yake a gaba shi ne mafi yawan taƙawa, wanda yake a gaba shi ne mafi tsantseni, wanda yake a gaba shi ne wanda rayuwarsa ta fi kama da ta talakawa.
Wannan ita ce wilayar Manzon Allah, wilayar Musa da Isa da Shu’aibu da Salih da Amirul-Mu’minin da Al-Hasan da Al-Husaini har zuwa zamaninmu; har zuwa zamaninmu, wilayar maraji’ai, fuqaha da malamai.
Saboda haka dole imani ya kasance, kamar yadda Sheikh al-Fayyad — Allah Ya jiƙan sa — ya ce, daga Allah Ta’ala yake; haka kuma wilayar faqihi, wato wilaya da imani tare da shi.
Muna fara yin imani da shi? Eh, muna yin imani da shi. Sannan mu kasance tare da shi, cikin umarninsa. A nan kada a shigar da kishin ƙasa, ƙabilanci, Larabci, Farisanci, Turkanci, ko kaɗan; addini ɗaya ne! Addini ɗaya ne, Manzon Allah ɗaya ne, al’ummarsa ɗaya ce, layinsa ɗaya ne; kada mu raba al’umma.
- Eh, akwai wasu kebantattun halaye waɗanda ake kiyayewa kuma ake girmamawa, amma hatta waɗannan kebantattun halayen dole ne su taimaka wa al’umma ɗaya. Wannan yana daga cikin nau’o’in gaggauta bayyanar Imam.
- Muna jiran jagora ɗaya wanda zai cika duniya, ba wanda zai cika ƙasa ba! Zai cika duniya da adalci kamar yadda aka cika ta da zalunci da danniya.
- Saboda haka dole imani da waliyyi ya kasance imani tare da shi, ba imani da shi kawai ba; ma’ana imani, biyayya, ƙauna, narkewa cikinsa, kariya, taimako, riko da umarni da makamantansu.
Wannan wilaya ɗaya ce, wannan shi ne adalcin Allah. Da muna zamanin Musa, wannan shi ne. Da muna zamanin Nuhu, wannan shi ne. Da muna zamanin Manzon Allah, wannan shi ne. Da muna zamanin Amirul-Mu’minin, haka yake, kuma a yau haka yake, har zuwa bayyanar Imam Zamaninmu. Lamari ɗaya ne.
- Wannan imani da shi da kasancewa tare da shi, imani ne da Imam Zamaninmu. Marja’i da waliyyin faqihi, wannan akida ce ta larura a kan ra’ayin wasu malamai. Wannan larura ce saboda gaibar Imam Zamaninmu. Mu muna son Imam ne ta hanyar waliyyi ko marja’i.
Imani ne da Imam Zamaninmu, tare da Amirul-Mu’minin, tare da Manzon Allah, domin mu tabbatar da Tauhidi da imani.
- Batun wilaya ba batun motsin zuciya ba ne, ko siyasa, ko sha’awa, ko son rai, ko muradi, ko maslaha, ko son zuciya, ko son duniya ba. A’a, lamari ne na akida, imani, addini, Musulunci, neman kusanci ga Allah, biyayya, sadaukarwa da shahada saboda Allah.
Wannan ita ce hanyar da muke imani da ita.
- Jagoran shahidi, Imam Khamenei — Allah Ya jiƙan sa — yana da wata magana da yayi a ranar 9/1/2016, yana cewa:
A bisa wannan fahimta: “Alkawarin biyayya ga fuqaha alkawarin biyayya ne ga Manzon Allah.”
- Yana cewa: “Wanda ya yi mubaya’a ga Imam Khomeini a yau, to haƙiƙa ya yi mubaya’a ga Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).”
- Wannan ba ta kebanta ga Imam Khomeini ba ne. Kafin shi da shekaru dubu, bayan shi da shekaru dubu, a yau, gobe; lamarin shi ne a zamanin gaiba, a cikin ma’iyya, dole mu bincika: wa za mu kasance tare da shi?
- Wasu suna cewa mu masu zaman kanmu ne, kuma maƙiya ma suna yaɗa wannan ra’ayi. Ba zai yiwu ba! Ba zai yiwu ba!
- Mai girma Imamush Shahid ya yi shekaru yana cewa a Iraki: “Ku bi Ayatullah al-Uzma Sayyid as-Sistani.”
Ma’ana, ku kasance tare da shi cikin umarninsa da shiryarwarsa game da Iraki. Babu wata girmamawa ta baki kawai, har ma ga wanda ba ya Taqlidi da shi. Batun ba batun taqlidi ba ne; batun biyayya ne... biyayya!
- Wannan ita ce haɗin kan magana. Kuma ina da yaƙinin cewa da mun ƙara samun biyayya da ma’iyya tare da marja’in da ra’ayoyin fuqaha a Najaf da Qum da waliyyin faqihi suka yi ittifaqi a kansa, da halinmu a yau bai kasance haka ba.
- Wannan shi ne nasara. Nasara tana nufin sunnonin Allah, taimakon Allah, nasarar Allah da tawfiƙin Allah.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda | 27 |
| 9 | - Saboda haka, tsakiyar ma’iyya tana kaiwa ga al’umma ɗaya, al’umma ɗaya. A nan zan yi magana a sarari, kuma zan sake maimaita wannan batu: dukkan taken ƙasa, na ƙabilanci, na jam’iyya da na tafiya, idan suna kaiwa kuma a cikin hanyar ƙarfafa... ƙarfafa al’umma Musulunci ɗaya, babu matsala a cikinsu.
- Amma duk wani taken, duk wani ra’ayi, duk wata ka’ida da take rarraba al’umma, wannan daga Shaiɗan ne, ko da kuwa mutane suna ɗaukarsa a matsayin taken mai tsarki; na ƙasa, na kabilanci... dukansu dole ne su karkata zuwa ga al’umma ɗaya, jagoranci ɗaya.
- Maƙiya suna raba mu domin su mallake mu. Ni kuma ina gaya muku: idan al’ummar Musulunci tayi ƙarfi, ƙasarmu tayi ƙarfi, ƙasar wancan da wancan da wancan tayi ƙarfi. Ƙasa tana ƙarfi ne da ƙarfin al’umma, amma ƙasashenmu suna raunana idan al’umma ta raunana. Wannan shi ne abin da Amurka take yi a yau da gobe.
- Batun wakilci, batun wilaya, batun marja’iyya a zamanin gaiba, ma’ana, a nan zan yi magana a sarari bisa ga waɗannan gabatarwa: cewa yin imani da hakan da kuma yarda da shi “da shi”, wato da faqihi ko marja’i, dole ne ya kai ga imani “tare da shi”; koyaushe mu kasance muna tsaye tare da hujjar Shari’a.
- A yau dole ne kowane Musulmi ya kasance a cikin sahun gaskiya, ba mai zaman kansa ba! A cikin sahu; yana halarta, yana yaƙi, yana faɗin gaskiya, yana bayar da kuɗin da yake da shi, yana sadaukar da abin da yake mallaka, yana kare Musulunci; domin ma’iyya ba za ta tabbata ba.
- Ma’iyya abu ce mai haɗari; domin idan azaba ta zo: {فَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا}... Wane suna ne yanzu, a zamaninmu, yake matsayin hujja? Wannan shi ne zai tsira, da waɗanda suke tare da shi; doka ɗaya ce! Wannan lamari ne mai haɗari, kuma dole mu kula da shi.
Kuma tabbas malamai da yawa suna ambaton wannan batu.
- A yau dole ne kowane Musulmi, kowane mumini ya kasance a cikin sahu ɗaya. Dukkanmu sahu ɗaya ne, da jagora ɗaya, waliyyi ɗaya, Imam ɗaya. Saboda haka malamai namu, kuma ina gaya wa matasa: maraji’ai sun yi ittifaqi, amma wasu daga cikin mabiyansu a wasu lokuta suna saɓawa kuma suna rarraba al’umma.
Duniyar Musulunci, ina magana ne gaba ɗaya; domin Allah ba Ya yarda da al’umma mai yawa da rarrabuwa, ba Ya yarda da ƙasa ta fuskar iyakokin ƙasa, ko jam’iyya, ko tafiya, ko ƙabilanci. Allah yana son al’umma ɗaya, ma’iyya ɗaya. Ka nemi hujja kuma ka kasance tare da shi, za ka tsira!
- Wannan shi ne abin da Alƙur’ani ya faɗa sarai. Waɗannan ba ayoyi ba ne na musamman ga Shu’aibu da Hud ba; da haka ne Alƙur’ani zai ƙare kuma ya gushe da mutuwar al’ummai da ƙabilu! Alƙur’ani yana raye har zuwa zamaninmu? Eh.
- Jarabawa ce mai wahala. Dole mutum ya kunna basira da lura sosai, kada ya rinjayu da yanayi da kafafen yaɗa labarai na Amurka masu son karkatarwa, masu son karkatarwa, Amurka uwar fasadi ce.
Saboda haka dole ne mu kasance tare da Manzon Allah da Ahlul Baiti a zamaninmu ta hanyar kasancewa tare da layin Manzon Allah. Ba a wadatu da motsin zuciya ba, ba a wadatu da imani “da shi” kawai ba; imani “tare da shi” da ci gabansa.
Ayatullah al-Uzma Sheikh Muhammad Ishaq al-Fayyad — Allah Ya jiƙan sa — yana cewa, kuma wannan magana ce mai muhimmanci da na karanta a Muharram, kuma idan Allah Ya ba ni lafiya da kuzari da dacewa zan sake maimaita ta: Wannan addininmu ne...
- Kamar yadda wilayar Manzon Allah da Imamai tsarkaka take daga Allah Ta’ala, wato wilayarsu daga Allah take, haka wilayar faqihi da ya cika sharuɗɗa a zamanin gaiba take; wilaya iri ɗaya ce daga Allah.
Allah ba Ya ba wanda ba ma’asumi ba wilaya, kuma bayan gaibar ma’asumi ba Ya bada wilaya ga wanda ba faqihi ba, marja’i, malami, mai tsoron Allah, mai tsantseni.
Wilayar faqihi ce, ba wilayar jahili ba ce. Ita ce alamar taƙawa, alamar tsantseni, alamar zuhudu, alamar sadaukarwa; ba son rai ba ne.
Wannan shi ne bambanci tsakanin tsarin dimokuraɗiyya da tsarin Musulunci; tsarin Musulunci tsarin Ali ne. Kuma a yau waliyyi faqihi shekaru da suka gabata yana ɗauke da ƙarfe a kan ‘ya’yansa da gidansa, kuma kun ga abin da ya biyo baya. | 21 |
| 10 | Saboda haka: {وَأَكْثَرُهُمْ لِلْحَقِّ كَارِهُونَ} — “Mafi yawansu masu ƙin gaskiya ne.” A kowane zamani masu gaskiya kaɗan ne; domin “tare da shi” abu ne mai wahala, amma “da shi” yana cikin hidimarka.
- Saboda haka Imam Husaini (aminci ya tabbata a gare shi) bai yarda da imani “da shi” kawai ba. Ya so imani “tare da shi”; mutum ya halarta. Wanda bai shiga tare da mu ba, ba zai riski nasara ba: “Duk wanda ya kasance mai bayar da ransa saboda mu, ya shirya kansa domin saduwa da Allah, to ya tafi tare da mu.” — “Tare da mu!”
- Domin idan ka bayar da kuɗi kawai, ko wanda ya ba da doki, kamar Ubaidullahi bn al-Hurr al-Ju’fi, ko wasu... wannan bai isa ba! Kasancewa tare da shi. Husaini yana son al’umma ta kasance mai imani “tare da shi”, ba wai mai imani “da shi” kawai ba.
- Wanda ya yi shiru bai shiga tare da Husaini ba, ko da yana son Husaini ko yana imani da shi, an la’ance shi! “Allah Ya la’anci al’ummar da ta ji wannan ta yarda da shi.” Akwai al’ummai, akwai mutanen da ba su shiga ba, ko da sun kasance masu imani, sai dai idan suna da uzuri na Shari’a, kamar mata da makamantansu; wannan wani bincike ne na daban, malamai ne suke tantance shi. A zahiri, wajibi ne a shiga tare da Imam Husaini; wadatuwa da imani da shi kawai bai isa ba.
- Alaƙar Musulmi, alaƙar muminai da Manzon Allah da layin Manzon Allah, alaƙar ma’iyya ce, ba kawai alaƙar imani da shi da ƙaunarsa ba. Saboda haka Alƙur’ani a nan ya gabatar da batun al’umma: {كُنتُمْ خَيْرَ أُمَّةٍ} — “Kun kasance mafificiyar al’umma.” Me ya sa al’umma? Domin ginshiƙi ɗaya ne, jagora ɗaya ne, Manzo ɗaya ne.
- Ina magana ne game da yanzu. Mu a yanzu, tun daga Adam har zuwa zamaninmu, a kowane lokaci akwai mutum ɗaya: jagora, hujja, Imam. Musa ya tafi: {اخْلُفْنِي فِي قَوْمِي} — “Ka maye gurbina cikin mutanena.” Annabi kuma a ƙarshen al’amari: {يَا أَيُّهَا الرَّسُولُ بَلِّغْ مَا أُنزِلَ إِلَيْكَ مِن رَّبِّكَ} — “Ya kai Manzo! Ka isar da abin da aka saukar maka daga Ubangijinka.” Game da me? Game da wanda yake mai iko, wanda yake jagora, ba wai ƙauna kawai ba. Haka da haka har zuwa zamaninmu.
- Dole ne ta fuskar hankali da Shari’a da waɗannan ayoyi, jagoranci ya kasance ɗaya ga dukkan al’ummar Musulmi ko ga dukkan bil’adama. Saboda haka malamai idan suna bayyana ma’anar mujtahidi da ya cika sharuɗɗa, kamar Ayatullah Mujaddid Sheikh Allama al-Muzaffar, Muhammad Rida al-Muzaffar, a cikin Aqa’idul Imamiyya, yana cewa: “Akidar mu game da mujtahidi da ya cika sharuɗɗa a zamanin gaiba ita ce cewa shi wakili ne... wakilin Imam ne a lokacin gaibarsa.”
- Wasu malamai suna cewa wannan wakilci ba na Musulmi ko ‘yan Shi’a kawai ba ne, a’a, na dukkan bil’adama ne; domin Imam shi ne jagoran bil’adama, Imamin bil’adama. Eh, wasu ba sa biyayya, wannan abu ne na dabi’a.
- Ma’anar al’umma ta samo asali ne daga ma’iyya ɗaya ga Imam ɗaya, Annabi ɗaya, jagora ɗaya, hujja ɗaya. Ba ya maimaituwa, ba ya ninkuwa. Wannan shi ne addini, wannan shi ne addinin Manzon Allah.
- A baya na kasance ina ambata a wasu darussa: mako guda kafin rasuwar Annabi (S.)... mako guda! Akwai ma’asumai biyar a Madina: Annabi (S.), Amirul-Mu’minin, Fatima az-Zahra, al-Hasan da al-Husaini; ma’asumai biyar. A wajenmu babu babba da ƙarami a cikin isma; duk ma’asumi ne.
- Amma jagora guda nawa ne? Ɗaya. Saboda haka idan wani dan ƙauye ya zo, misali, ya ga Amirul-Mu’minin, ya ce masa: “Ya Abal-Hasan, yanzu na Musulunta, yaya zan yi sallah?” Sai ya koya masa sallah, ba matsala; ya koya masa sallah, wannan al’amari ne na fatawa kamar yadda suke cewa.
- Idan ya ga Imam Hasan, ya ce masa: “Yaya zan yi alwala?” Sai ya koya masa alwala. Idan ya ga Imam Husaini, sai ya ce masa, misali: “Azumi, na ji cewa akwai azumi, yaya ake yin azumi?” Sai ya koya masa azumi.
- Amma idan wannan ba ƙauyen ya ce wa Amirul-Mu’minin: “Quraishawa sun zo da rundunarsu a ƙofar Madina, za mu yi yaƙi ko ba za mu yi ba?” Shin Amirul-Mu’minin zai amsa, ko kuwa ya ce masa: “Mu je mu ga Annabi”? Mu je mu ga Annabi; jagora ɗaya ne duk da kasancewar ma’asumai da yawa. | 15 |
| 11 | - Tabbas wannan ba ta kebanta ga waɗannan Annabawa uku ba ce. A fili yake. Wannan yana cikin zamanin Annabi da bayan Annabi; ba ta kebanta ga Manzanni da Annabawa, kuma ba ta kebanta ga Ahlul Baiti (aminci ya tabbata a gare su), a’a, wannan sunnah ce har zuwa tashin Alƙiyama.
Wace ce hujjar Shari’a? Kuma waɗanda suka yi imani tare da shi; waɗannan ne kawai suke tsira. Wannan abu ne mai haɗari ƙwarai, ƙwarai da gaske. Waɗannan ne kawai suke tsira a kowane zamani.
- Sanin hujja: Wane ne jagora? Waliyyi? A zamaninmu, marja’i? Waliyyi bisa ga...
Ba zan shiga cikin bayanai dalla-dalla ba, zan yi ishara da su daga baya. Haka kuma a Suratu Hud, aya ta 48, a labarin Nuhu (aminci ya tabbata a gare shi): {قِيلَ يَا نُوحُ اهْبِطْ بِسَلَامٍ مِنَّا وَبَرَكَاتٍ عَلَيْكَ وَعَلَىٰ أُمَمٍ مِمَّن مَّعَكَ} — “A ce: Ya Nuhu! Ka sauka da aminci daga gare Mu da albarka a kanka da kuma a kan al’ummomi daga waɗanda suke tare da kai.” Haka ma ma’iyya.
- Ɗan Nuhu, ɗan Annabi... ɗan Annabi bai tsira ba; domin bai zo tare da shi ba. Bai zo tare da shi ba, ya tafi ga halaka.
Haka kuma Allah Ta’ala yana cewa a Suratul Baƙara, wannan ma’iyya... Tabbas akwai ayoyi da yawa, na zaɓi wasu daga cikinsu: {حَتَّىٰ يَقُولَ الرَّسُولُ} — {أَمْ حَسِبْتُمْ أَن تَدْخُلُوا الْجَنَّةَ وَلَمَّا يَأْتِكُم مَّثَلُ الَّذِينَ خَلَوْا مِن قَبْلِكُم مَّسَّتْهُمُ الْبَأْسَاءُ وَالضَّرَّاءُ وَزُلْزِلُوا حَتَّىٰ يَقُولَ الرَّسُولُ وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ مَتَىٰ نَصْرُ اللَّهِ}.
- Tsira tana tare da Manzo, tare da hujja, tare da waliyyi. Babu wani wanda bai shiga jirgin waliyyi, ko Annabi, ko hujja, ko jagora a kowane zamani ba sannan ya tsira. Ba zai yiwu ba! Akwai nassoshi da yawa da suke magana a kan haka, kuma asali wannan aya tana magana ne game da ranar Alƙiyama.
- Abin da yake da matuƙar ban mamaki shi ne cewa Alƙur’ani bai ce: “آمن به” ba, alhali a harshen Larabci abin da ya dace shi ne a ce: “ya yi imani da shi.” Bai ce: “آمن به، والذين آمنوا به” ba, a’a, yana cewa: “والذين آمنوا معه” — “da waɗanda suka yi imani tare da shi!”
Wannan lamari ne mai ban mamaki.
- Wasu daga cikin mufassirai suna cewa, kuma wannan a bayyane yake: Ba za a iya wadatuwa da yin imani “da shi” kawai ba; dole ne imani ya kasance “tare da shi”; wato da shi kuma tare da shi! Ya shiga cikinsa, cikin rundunarsa, cikin layinsa, ya yi jihadi, ya kare hujjar Shari’a.
- Saboda haka ku kula: duk ayoyin suna cewa: “tare da shi, tare da shi, suka yi imani tare da shi”; babu “da shi”, babu “da shi”; duk suna magana ne game da imani... Ɗaya daga cikin manyan mufassirai yana cewa: Bai isa mutum ya yi imani da Annabawa kuma ya gaskata kiransu ba, a’a, dole ne ya kare su kuma ya basu kariya, wato ya kasance a cikin sahunsu.
- A kowane zamani: Musa, Shu’aibu, Hud, Lud, Salih, Annabin Musulunci, Amirul-Mu’minin, Imam Husaini, har zuwa zamaninmu kuma har zuwa tashin Alƙiyama. Saboda haka imani yana kasancewa tare da Annabi, tare da hujja, ba wai da shi kawai ba.
- Amma Alƙur’ani bai taɓa bayyana “imani tare da Allah” ba. Me yake cewa? “Imani da Allah.” Domin Allah, babu wanda yake cewa: “Ni ina tare da Allah.” Allah ba a ganinsa. Hujjarsa, halifarsa: {يَا دَاوُودُ إِنَّا جَعَلْنَاكَ خَلِيفَةً} — “Ya Dawuda! Lalle Mun sanya ka halifa.”
- A kowane lokaci akwai mutum ɗaya, kuma wajibi ne mu shiga sahunsa. Eh, imani da Allah. Dukkan ayoyi suna cewa: “imani da Allah, da...” Amma waɗannan ayoyi suna magana ne game da ma’iyya; wato ma’iyya ta zahiri, jiki yana nan, hankali yana nan, ƙarfi yana nan.
- Duk abin da mutum yake da shi na dukiya, ƙarfi, iko, ko wani abu... dukiya, ‘ya’ya, su kasance tare da hujja, tare da shi. Bai isa “da shi” ba. Ma’anarsa ita ce dole mutum ya kasance tare da hujjar Shari’a a kowane zamani da yake ciki.
- Matsalarmu ita ce: muna tare da Annabawa a tarihi, muna tare da Imamai a tarihi. Amma idan muka zo yanzu, sai mu wadatu da imani “da shi”; muna son shi. Shi wanene? Ko da mun san shi, galibi. | 14 |
| 12 | A kowane zamani dole ne mu nemi layin Manzon Allah, layin Annabawa, biyayyar Ahlul Baiti, wanda a zamaninmu yake cikin faqihi wanda ya cika sharuɗɗa da maraji’ai. Saboda haka, tsawon shekaru 1200 ‘yan Shi’a suna bin kuma suna kwaikwayon maraji’ai; wannan biyayya ce ga Manzon Allah. Domin bin maraji’ai ci gaba ne na haƙiƙa na biyayya ga Manzon Allah da layinsa na Ubangiji.
Daga wannan mahangar ne Alƙur’ani Mai Girma yake gabatar da wani muhimmin ra’ayi, wato ma’anar “al-ma’iyya” — kasancewa tare.
- Akwai ayoyi masu ban mamaki, ma’anoni masu ban mamaki a cikin Alƙur’ani game da “ma’iyya”! Wani lokaci yana cewa: “wa allazina ma’ahu” — waɗanda suke tare da shi, ko “tare da shi”.
Tabbas, biyayya ga Manzo ita ce ma’iyya tare da Manzo, kuma ci gabanta shi ne ma’iyya tare da Ahlul Baiti. Ma’iyya tare da Ahlul Baiti ci gabanta shi ne ma’iyya tare da wakilai huɗu ga wanda ya rayu a zamanin ƙaramar gaiba. Kuma ma’iyya tare da wakilai, Ahlul Baiti da Manzon Allah a zamaninmu ita ce kasancewa tare da fuqaha da maraji’ai.
Wannan ma’iyya tana da wahala. Wannan ci gaba ne, wannan shi ne ci gaba.
- Rahama da adalcin Allah suna bayyana wajen kiyaye wannan ci gaba na Ubangiji a cikin zamani daban-daban. Bayan Annabi (S.), akwai Amirul-Mu’minin, Al-Hasan, Al-Husaini da Imamai, har zuwa zamanin gaiba, inda aka kafa marja’iyya da fuqaha da suka cika sharuɗɗa a matsayin madadin da hanyar shiriya.
Saboda haka Alƙur’ani Mai Girma yana maimaita ma’anar “ma’iyya” da alaƙa da Annabawa da Manzanni. Maganar Alƙur’ani ba wani lamari ba ne na tarihi da ya ƙare, a’a, tana gudana kamar dare da rana, domin tabbatar da ci gaba da saƙon Allah, kamar yadda Allah Ya ce: {مُّحَمَّدٌ رَّسُولُ اللَّهِ ۚ وَالَّذِينَ مَعَهُ} — “Muhammad Manzon Allah ne, kuma waɗanda suke tare da shi.”
- {أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَمَاءُ بَيْنَهُمْ} — “Masu tsanani ne a kan kafirai, masu jinƙai ne a tsakaninsu.”
Ba Annabi kaɗai ba ne, har ma da waɗanda suke tare da shi!
Abin lura shi ne cewa bai raba siffofin ba; wato: {أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَمَاءُ بَيْنَهُمْ} — wannan ya shafi Annabi da waɗanda suke tare da shi. Wannan yana daga cikin al’amura masu wahala.
- A Suratu Hud, Alƙur’ani Mai Girma yana sake maimaita ma’iyya tare da Manzanni da dama, kuma yana tabbatar da cewa ceto, musamman ceto, Allah ne yake yi. Zan karanta ayoyin yanzu; yana magana da Annabi, yana cewa ceto ga Annabi ne, ga hujjar Shari’a, da waɗanda suka yi imani tare da shi. Ma’ana, waɗannan mabiyansa suna tsira ne ta hanyar binsa, ta hanyar ma’iyya, ba da kansu ba! Babu wani abu a addini da ake kira ‘yancin kai. Alƙur’ani yana tabbatar da ma’iyya, ba ‘yancin kai ba.
- A Suratu Hud, aya ta 58: Da farko Hud: {وَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا}. Akwai wata aya kuma: {جَعَلْنَا عَالِيَهَا سَافِلَهَا}. Ma’ana, lokacin da umarninmu ya zo, wato azaba, a duniya kafin lahira. Muna magana ne game da duniya kafin lahira. A duniya akwai azabobi da tasirinsu, kuma da yawa daga cikin wahalhalun jarabawarmu a duniyar Musulunci, a cikin al’ummar Musulunci, ciki har da watakila Iraki, sakamakon wasu azabobi ne. Mu ba ma’asumai ba ne, kuma al’ummai gaba ɗaya suna iya yin kuskure.
- A nan kuma: {وَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا} — “Sa’ad da umarninmu ya zo, Muka ceci...” Wa muka ceci? {هُودًا} — Hud; Annabi, jagora, hujja. {وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ بِرَحْمَةٍ مِنَّا} — “da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu.”
Tabbas wannan aya ta shafe mu; domin Alƙur’ani gaba ɗaya ya shafe mu. Wannan ba ta musamman ga Hud ba ce.
- Aya ta 66 kuma daga Suratu Hud: {فَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا صَالِحًا} — a nan Annabi Salih ne; {وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ بِرَحْمَةٍ مِنَّا} — “da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu.” Haka kuma a aya ta 94 daga Suratu Hud: {وَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا شُعَيْبًا وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ بِرَحْمَةٍ مِنَّا} — “Sa’ad da umarninmu ya zo, Muka ceci Shu’aibu da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu.” | 12 |
| 13 | WASU DAGA CIKIN JAWABIN SAYYID HASHIM aL-HAIDARI (H), A YAYIN BIKIN HAIHUWAR ANNABIN ALLAH (S):
- Bikin tunawa da haihuwar Manzon Allah (S), tare da abubuwan farin ciki da bukukuwan da suke tare da shi, ya kamata kuma ya zama an gabatar da wani cikakken rahoto ga Annabinmu, shugabanmu, mai cetonmu kuma jagoranmu; rahoton da zai bayyana ainihin matsayin imanimmu da ayyukanmu, da abin da muka gabatar wajen taimakon addininsa wanda shi ne addininmu, da kuma abin da muka cimma daga manyan manufofinsa.
- Shin Manzon Allah (S.) yana yarda da al’ummarsa alhali tana cikin rarrabuwa, ruɗani, dogaro ga wasu, rauni, gazawa, son duniya, yaɗuwar fasadi da lalata a wasu daga cikin al’ummarta a matsayin al’ummar Musulunci; luwadi, ƙwayoyi... Shin Manzon Allah yana yarda da al’ummarsa a haka?
Ina muke a matsayinmu na al’ummar Musulmi dangane da Musulunci? Ina muke a matsayinmu na al’ummar Manzon Allah dangane da Manzon Allah?
Allah Ta’ala yana cewa: {وَمَا أَرْسَلْنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا لِيُطَاعَ بِإِذْنِ اللَّهِ} — “Ba Mu aika wani Manzo ba face sai domin a yi masa biyayya da izinin Allah.”
Asalin samuwar Annabi shi ne a yi masa biyayya, domin biyayya. {وَمَا أَرْسَلْنَا} ya ƙunshi takaita; {وَمَا أَرْسَلْنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا لِيُطَاعَ بِإِذْنِ اللَّهِ}.
Shin mu al’umma ce mai biyayya ga Manzon Allah da addinin Allah a cikin hukunce-hukuncen Musulunci na mutum ɗaya, na zamantakewa, na siyasa, na tarbiyya, na iyali, na ƙabilanci da na al’umma?
- Biyayya ita ce ginshiƙin da ya zama dole na aiko Annabi (S.); Allah Ya aiko shi ne domin a yi masa biyayya, kuma manufar saƙon ta cika a cikinmu.
Cikar al’ummar Musulunci ba ta tabbata da kasancewa Musulmi a zahiri kawai ko ɗaga taken addini a fili ba; tana tabbata ne da cikakkiyar biyayya da aiwatar da hukunce-hukuncen Shari’a gaba ɗaya a kowane zamani da wuri. Kuma kamar yadda cikar al’umma take cikin mika wuya, haka faɗuwarta take cikin saɓo. Daga nan ne muhimmancin addu’ar: “Ya Allah, Ka azurta mu da ikon yin biyayya, Ka nisantar da mu daga saɓo.”
- A cikin Suratush-Shu’ara an maimaita aya mai albarka: {إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ * فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ} a kan harshen Annabawa biyar (Nuhu, Hud, Salih, Luɗ da Shu’aibu – aminci ya tabbata a gare su), domin ta bayyana cewa tsoron Allah da biyayya su ne jigon saƙonnin dukkan Annabawa.
Addini ba zaɓen wasu hukunce-hukunce ba ne bisa son rai da sha’awa; a’a, mika wuya ne gaba ɗaya. Allah bai halicci mutum ba face domin ya bi shiriyarsa. Amma dukiya, abubuwan more rayuwa da duniya gaba ɗaya ba su da wata daraja sai idan an yi amfani da su a hanyar lahira da addini, domin a tabbatar da asalin umarnin Allah: {فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ}.
- Allah Ya halicci bayi domin biyayya da bin hanya zuwa ga kamala: {إِلَّا لِيَعْبُدُونِ}. Babu ibada kuma babu taƙawa ba tare da bin Manzon Allah (S.) ba; domin shi ne yake tsara taswirar hanyar tafiya, kuma shi ne yake isar da Shari’a.
Biyayyar al’umma ga Annabi tana matsayin sake tayar da ita; kamar yadda Allah Ya aiko Manzo, haka al’umma take tashi daga gafalarta, kuma take tabbatar da ɗan Adamcinta ta hanyar mika wuya gare shi. Daga nan ne shiriya take cikin cikakkiyar biyayya kamar yadda Alƙur’ani Mai Girma ya tabbatar: {وَإِن تُطِيعُوهُ تَهْتَدُوا ۚ وَمَا عَلَى الرَّسُولِ إِلَّا الْبَلَاغُ الْمُبِينُ} — “Idan kun yi masa biyayya, za ku shiryu. Kuma babu abin da ke kan Manzo face isar da saƙo bayyananne.”
- Biyayya ga Manzon Allah (S.) ita ce ainihin biyayya ga Allah Ta’ala: {مَّن يُطِعِ الرَّسُولَ فَقَدْ أَطَاعَ اللَّهَ} — “Duk wanda ya yi biyayya ga Manzo, to, haƙiƙa ya yi biyayya ga Allah.”
Kuma tana ƙara tabbatar da ci gaba zuwa ga Ahlul Baiti tsarkaka: {يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَطِيعُوا اللَّهَ وَأَطِيعُوا الرَّسُولَ وَأُولِي الْأَمْرِ مِنكُمْ}.
Kada mu rayu da wannan nassi kamar wani abu da ya faru a tarihin baya kawai; wannan biyayya tana ci gaba a zamanin gaiba ta hanyar komawa ga fuqaha da maraji’ai waɗanda suka cika sharuɗɗa. | 17 |
| 14 | Sin texto... | 18 |
| 15 | TAMKAR GANGAR JIKI NE BA RUHI.....!!!
Jiya Alhamis, 27/8/2026, Ayatollah Abbas al-Ka'aby (H) a ofishin Wakilin Imam Khamenei a Iraq, a Karbala, ya gabatar da jawabi mai muhimmanci yayin da yake isar da sakon Imamul Qa'id Mujtaba Khamenei (D.z) na godiya ga al-Ummar Iraqi bisa halascin da suka nuna wajen raka gangar jikin Imamush Shaheed Khamenei (Q.).
Da yake magana akan muhimmancin Jagorancin Malami nagari a cikin ƙasa da al-Ummah, ya ce: "Usuluddeen da Furu'uddeen baki dayan su idan babu Jagoranci na gari, to tamkar gangar jiki ne, ba Ruhi. Da Jagoranci ne nagari karkashin tsarin Allah ne suke samun ma'ana kuma tasirinsu ke bayyana."
A yayin da yake magana kan zaɓen Sayyid Mujtaba Khamenei (Q.d), kuma ya ce: "Ku samu natsuwa, Sayyid Mujtaba Khamenei a zaɓinsa da aka yi, lalle akwai tagomashin Allah (T) a ciki da tagomashin Imam Sahibul Asri Wazzaman (A.S.)."
Ya ce: "Na farko, mu sani shi Mujtahidi Mudlaq ne, Mujtahidai, manyan malamai masana an kai musu rubutattun darussansa akan Dahara da darasi a Ta'arudul Adillah da ya gabatar, sun ce ba wai ya iya istinbadi da sanin makama ba a'a, yana da gogewa matuka a sha'anin Ijtihadi. Sannan ya shekara 20 yana bada Bahsul Kharij a gaban dalibai sama da 700."
Ya ce suna cikin dakin taron zaɓen Waliyul Faqih, ɗan Ayatollah Sheikh Makarimush Shirazy ya kira, ya ce a gaya masa ya wakilce shi a bayyana ra'ayinsa akan shi, yana goyon bayan zaɓen Sayyid Mujtaba. Haka shi ma Ayatollah Ja'afar Subuhany aka kira da sauransu, duk kansu akansa suke ishara, anan ne fa zukata suka karkata akansa.
Ya ce kamar kada a zaɓi Sayyid Mujtaba matsayin Waliyul Faqih sai ya zama hasken Walaya na bayyana a cikinsa da ayyukansa, kamar dai Mahaifinsa. Ya ce Sheikh Misbahu Yazdy ya ce: "Mun san Sayyid Imamush Shaheed Khamenei tsawon shekaru tun kafin a zaɓe shi, amma nan take hasken Walaya ya bayyana a shi da ayyukansa, ya kasance misdaqin wannan ayar:
«وَاصْطَنَعْتُكَ لِنَفْسِي»
To haka Imam Mujtaba Khamenei ya kasance."
Ya ce: "Ikonsa a tafiyarwa a fannin Soji da Tattalin Arziki ba ƙarami bane. Yace ina baku tabbaci, idan dama ta buɗe gaban Imam Mujtaba Khamenei, to zai canza lissafin Iran da ma Gabas ta Tsakiya baki ɗaya."
Ya ce yana isar da addu'a da godiya da sallamar Imam Mujtaba Khamenei zuwa ga mahalarta rakiyar Gangar Jikin Imamush Shaheed Khamenei a Iraq 🇮🇶.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda | 23 |
| 16 | Sin texto... | 18 |
| 17 | Amma wanda aka tabbatar cewa mahaifinsa Annabi ne, kamar Annabi Yusuf (A.S.) da sauran annabawa, to wannan yana buƙatar a yi la’akari da batun isma ta musamman da ya shafi annabawa.
Dangane da Abdul-Muɗɗalib da Abu Ɗalib.
An haifi Annabi (S) kuma ya girma a cikin zuri'a mai tauhidi da ɗaukakar ɗabi’u/halaye.
Ana iya ganin imanin kakansa Abdul-Muɗɗalib daga halayensa da addu’arsa lokacin da Abraha al-Habashi ya kai hari domin rusa Ka’aba; bai nemi taimakon gumaka ba, sai dai ya dogara ga Allah wajen kare Gidansa.[29]
Haka nan akwai abubuwan da suke nuna cewa Abdul-Muɗɗalib ya san wani abu game da matsayin Annabi (S) da makomarsa da ta shafi sama. Daga cikin hakan akwai neman ruwan sama da Annabi (S) tun yana jariri, saboda abin da ya sani game da matsayinsa a wurin Allah Mai arziki da azurtawa.[30]
Haka nan ya yi wa Ummu Ayman gargadi kada ta yi sakaci da shi tun yana ƙarami.[31]
Amma baffansa Abu Ɗalib ya ci gaba da kula da Annabi (S), ya kare shi, ya tallafa masa wajen isar da saƙon Allah da bayyana shi har zuwa ƙarshen rayuwarsa mai albarka, ya jurewa cutarwar Quraysh, kaurace musu da kuma killace shi a Shi’b.
An kuma ruwaito daga Abu Ɗalib (A.S.) abubuwa masu yawa da suke nuna tsananin kulawarsa da kare rayuwar Annabi (S).[32]
Saboda haka, ba daidai ba ne yaɗa magana cewa “iyayen Annabi (S) suna cikin wuta” domin hanya ta Ahlul baity da suke abokan tafiyar al-Qur'ani akwai hujjoji daga hankali, Alƙur’ani, hadisai da ijma’i da suke nuna tsarkin iyayen Annabi (S) daga shirka da kafurci, da kuma tsarkin nasabarsa daga zina.
Kuma wannan ba batu ne na kare wani mutum kawai ba daga tsatson; batu ne da yake da alaƙa da girmama matsayin Annabci da fahimtar hikimar Allah wajen zaɓar Manzonsa.
Allah bai bar wata kafa ta zargi a kan Manzonsa (S) ba. Ya tsarkake asalinsa, ya tsarkake tsatsonsa, ya tsarkake mahaifansa, kuma Ya ɗaukaka shi daga mafi kyawun tsatso zuwa mafi kyawun matsayi.
﴿اللَّهُ أَعْلَمُ حَيْثُ يَجْعَلُ رِسَالَتَهُ﴾
“Allah ne Mafi sani a inda Ya sanya saƙonsa.”
Allah Ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa Muhammad (S.) da Ahlulbaitinsa (A.S.), Ya sanya mu cikin masu riƙo da koyarwarsu da girmama matsayinsu.
Alhamdu lillahi Rabbil Alamin.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
Madogara:
[8] Ash-Shari’a, juzu’i na 3, shafi na 1417.
[9] Qutul-Qulub, juzu’i na 2, shafi na 145.
[10] A’lamun-Nubuwwa, shafi na 201.
[11] Majma’al-Bayan, juzu’i na 7, shafi na 357.
[12] Mutashabihul-Qur’an wa Mukhtalifuh, juzu’i na 2, shafi na 21.
[13] Ta’wilul-Ayat, juzu’i na 1, shafi na 396.
[14] Biharul-Anwar, juzu’i na 25, shafi na 17 da abin da ya biyo baya.
[15] Al-Khisal, shafi na 548.
[16] Kifayatul-Athar, shafi na 70.
[17] At-Tibyan, juzu’i na 4, shafi na 175.
[18] al-Ãmali, shafi na 183.
[19] Rawdatul-Wa’izin, shafi na 139.
[20] ad-Durrun-Nazim, shafi na 26.
[21] Iman Abi Talib, shafi na 57.
[22] Mir’atul-Uqul, juzu’i na 26, shafi na 549.
[23] Al-I’tiqadat, shafi na 354.
[24] Awa’ilul-Maqalat, shafi na 45.
[25] At-Tibyan, juzu’i na 4, shafi na 175.
[26] Biharul-Anwar, juzu’i na 12, shafi na 49.
[27] Awa’ilul-Maqalat, shafi na 45.
[28] Haqqul-Yaqin, shafi na 144.
[29] As-Siratun-Nabawiyya, juzu’i na 1, shafi na 33; Tarikhud-Dabari, juzu’i na 1, shafi na 553; Al-Kamil fit-Tarikh, juzu’i na 1, shafi na 444.
[30] As-Sira al-Halabiyya, juzu’i na 1, shafi na 189; Al-Milal wan-Nihal na ash-Shahrastani, juzu’i na 2, shafi na 240.
[31] Ad-dabaqatul-Kubra, juzu’i na 1, shafi na 118; Tarikh Madinat Dimashq, juzu’i na 3, shafi na 85; Al-Bidaya wan-Nihaya, juzu’i na 2, shafi na 343; As-Sira an-Nabawiyya, juzu’i na 1, shafi na 240.
[32] Usdul-Ghaba, juzu’i na 1, shafi na 19; Tarikhulmd-Dabari, juzu’i na 2, shafi na 64; Al-Bidaya wan-Nihaya, juzu’i na 3, shafi na 63; As-Sira an-Nabawiyya na Ibn Kathir, juzu’i na 1, shafi na 473. | 27 |
| 18 | 5. al-Fattal an-Naysaburi ya ruwaito daga Annabi (S): “Babu lokacin da iyaye biyu nawa suka haɗu ta zina. Allah Ya ci gaba da mayar da ni daga tsatso masu kyau zuwa mahaifu masu tsarki, ina mai shiryarwa kuma ana shiryar da ni, har Allah Ya ɗora mini amanar Annabci.”[19]
6. Yusuf bn Hatim ash-Shami ya ruwaito daga Ali (A.S.) cewa Annabi (S) ya ce: “Na fito ne daga aure, ban fito daga zina ba, tun daga Adam har zuwa lokacin da mahaifina da mahaifiyata suka haife ni; babu wani abu daga zina ta jahiliyya da ya same ni.”[20]
7. Sayyid Fakhar bn Ma’ad al-Musawi ya ruwaito daga Annabi (S): “Allah Ya ci gaba da mayar da ni daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki har Ya fitar da ni zuwa wannan duniyarku.”[21]
Allamah Majlisi ya ce: “Ina cewa: Hadisan da suke nuna Musuluncin iyayen Annabi (S) daga hanyoyin Shi’a suna da yawa sosai, har ma sun kai matsayin tawatur.”[22]
Dalilin Ijma’in Imamiyya.
Sheikh Saduq ya ce: “Imaninmu game da iyayen Annabi shi ne cewa su Musulmai ne daga Adam har zuwa mahaifinsa Abdullah, kuma Abu Ɗalib Musulmi ne, mahaifiyarsa Aminah bint Wahb kuma Musulma ce. Annabi (S) ya ce: ‘Na fito daga aure, ban fito daga zina ba, tun daga Adam.’ An kuma ruwaito cewa Abdul-Muɗɗalib ya kasance hujja, kuma Abu Ɗalib ya kasance wasiyyinsa.”[23]
Sheikh Mufid ya ce: “Imamiyya sun yi ittifaqi cewa iyayen Manzon Allah (S), daga Adam har zuwa Abdullah bn Abdul-Muɗɗalib, muminai ne ga Allah, masu tauhidi ne gare Shi. Sun kafa hujja da Alƙur’ani da hadisai.”[24]
Sheikh Abu Ja’afar aɗ-Ɗusi ya ce: “Abin da az-Zajjaj ya faɗa yana ƙarfafa abin da malamanmu suka ce: cewa Aazar ya kasance kakan Ibrahim ne ta bangaren mahaifiyarsa ko kuma baffansa; domin ya tabbata a wajenmu cewa iyayen Annabi (S) har zuwa Adam dukkaninsu masu tauhidi ne, babu wani kafiri a cikinsu. Hujjarsu ita ce ijma’in ɗa'ifar gaskiya, kuma babu saɓani a tsakaninsu a wannan mas’ala.”[25]
Allamah Majlisi ya ce: “Imamiyya sun yi ittifaqi cewa iyayen Manzon Allah (S) da dukkan kakanninsa har zuwa Adam (A.S.) Musulmai ne; har ma sun kasance daga cikin siddiqai: ko dai annabawa ne manzanni, ko kuma wasiyyai ma’asumai. Wataƙila wasu daga cikinsu ba su bayyana Musuluncinsu ba saboda taqiyya ko wata maslahar addini.”[26]
Haka kuma Sheikh Mufid ya ce: “Imamiyya sun yi ittifaqi cewa iyayen Manzon Allah (S) daga Adam har zuwa Abdullah bn Abdul-Muɗɗalib muminai ne ga Allah, masu tauhidi gare Shi. Sun kafa hujja da Alƙur’ani da hadisai. ... Kuma sun yi ijma’i cewa baffansa Abu Dalib (A.s) ya mutu yana mumini, kuma Aminah bint Wahb tana kan tauhidi, kuma za a tashe ta tare da muminai.”[27]
Shin wannan tsarki yana nufin rashin aikata kowane irin zunubi?
A nan ya kamata a fahimci ma’anar “tsarkin tsatso” daidai.
Mabiya Ahlulbaiti (A.S.) sun yi imani cewa iyayen annabawa da hujjojin Allah (A.S.) tsarkaka ne daga shirka da kafurci, haka nan tsarkaka ne ta fuskar nasaba; sun fito daga tsatso masu tsarki da mahaifu masu tsarki, kodayake wasu malamai sun yi nazari a kan ko wannan hukunci ya shafi dukkan annabawa ko Annabinmu Muhammad (S) ne kawai.
Sayyid Abdullah Shubbar ya ce: “Abin da ya shahara a wajen Imamiyya, har ma aka kawo ijma’i a kai, shi ne wajabcin tsarkake annabawa daga kafurcin iyaye da alfasharsu, domin kada a zarge su ko a kushe su da hakan, kuma kada mutane su nisance su; domin a al’ada, aibin da yake cikin iyaye yana komawa ga ’ya’ya... Amma a ganina akwai nazari a wannan, domin babu hujjar hankali tabbatacciya da ta wajabta hakan, kuma hujjar nakali ta inganta ne game da iyayen Annabi (S) kawai, ba sauran annabawa ba... Don haka tsayawa a nan shi ne mafi dacewa.”[28]
A bisa wannan, abin da ake nufi da tsarkin da ake magana a nan shi ne tsarki daga shirka da kufurci, ba lallai ba ne a ce dukkan kakannin annabawa sun kasance ma’asumai daga kowane irin kuskure da zunubi ba.
Saboda haka, idan aka ce wasu daga cikin kakannin annabawan Bani Isra’ila, kamar Yahuda da ’yan’uwansa, sun aikata kuskure ko zunubi, wannan ba ya saɓa wa ma’anar “tsatso mai tsarki”, domin ba a sharɗanta cewa dukkan iyayen annabawa su kasance ma’asumai daga kuskure ba. | 22 |
| 19 | NASABAR ANNABI (S): WANNAN ITACE MATSAYAR MABIYA MAKARANTAR AHLULBAITI (A.S.) GAME DA NASABAR ANNABI MUHAMMAD (S.) MAI GIRMA.
No (2).
Dalili na Alƙur’ani.
Daga cikin dalilan da suke nuna tsarkin iyayen Annabi (S) akwai faɗin Allah Maɗaukaki a cikin Suratul Shu’ara:
﴿الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُ * وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
“Wanda Yake ganin ka lokacin da kake tsayuwa, da jujjuyawarka a cikin masu sujada.” (Shu’ara: 218–219)
Malaman tafsiri da dama sun fahimci wannan aya da cewa tana nuni da tsarkin iyayen Annabi (S), daga Adam (A.S.) har zuwa mahaifinsa Abdullah.
1. al-Ajuri ya ce a tafsirin ayar: “Allah Ya ɗaukaka matsayin Annabinmu, Ya tsare shi daga auren jahiliyya, Ya riƙa mayar da shi cikin tsatson masu tsarki ta hanyar aure ingantacce tun daga Adam, ta hanyar sanya shi cikin tsatson annabawa da ’ya’yan annabawa, har Ya fitar da shi ta hanyar aure ingantacce.”[8]
2. Abu Ɗalib al-Makki ya ce:
“A cikin tafsiri: jujjuyawarka a cikin tsatson masu tsarki da mahaifu masu tsarki; babu wani lokaci da zina ta same ka. Haka aka ruwaito daga Annabi (S).”[9]
3. Al-Mawardi ya ce: “Amma game da tsarkin haihuwarsa, Allah Ya zaɓi Manzonsa daga mafi kyawun aure, Ya kare shi daga ƙazantar alfasha, Ya riƙa mayar da shi daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki. Ibn Abbas ya ce a cikin fassarar faɗin Allah: ﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾, wato: jujjuyawarka daga tsatso masu tsarki, daga uba zuwa uba, har Allah Ya sanya ka Annabi.”[10]
4. Sheikh aɗ-Ɗabarsi ya ce: “An ce ma’anarsa ita ce: jujjuyawarka a cikin tsatson masu tauhidi, daga annabi zuwa annabi, har Ya fitar da kai Annabi; daga Ibn Abbas, a wata ruwaya daga Aɗa’u da Ikrimah, kuma shi ne abin da aka ruwaito daga Abu Ja’afar da Abu Abdillah (A.S.): ‘A cikin tsatson annabawa, annabi bayan annabi, har Ya fitar da shi daga tsatson mahaifinsa, ta hanyar aure ba zina ba, tun daga Adam.’”[11]
5. Ibn Shahr Ashub ya ce: “A cikin ayar akwai dalili cewa iyayensa (A.S.) sun kasance Musulmai har zuwa Adam, kuma babu wani daga cikinsu da ya bauta wa wanin Allah. Da a ce ana nufin masu sujada ga gumaka, da ba a yi masa wannan ni’ima ba, domin yin wa mutum ni’ima ta hanyar kafurci abu ne mummuna.”[12]
6. Sayyid Sharafud-Din al-Istarabadi ya ruwaito daga Abu Ja’afar (A.S.) game da ayar:
﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
ya ce: “Yana ganin jujjuyawarsa a cikin tsatson annabawa, daga annabi zuwa annabi, har Ya fitar da shi daga tsatson mahaifinsa ta hanyar aure ba zina ba, tun daga Adam.”[13]
7. Allamah Majlisi ya ruwaito daga Imam al-Baqir (A.S.) cewa hasken Annabi (S) ya ci gaba da wucewa daga tsatso zuwa tsatso da mahaifa zuwa mahaifa, har ya kai ga Abdul-Muɗɗalib, inda ya rabu zuwa sassa biyu: wani sashe ya shiga Abdullah, wani sashe kuma ya shiga Abu Ɗalib. Wannan shi ne ma’anar:
﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
wato, a cikin tsatson annabawa da mahaifar matansu.[14]
Dalilin hadisai.
1. Sheikh as-Saduq ya ruwaito cewa Imam Ali (A.S.) ya ce: “Na rantse da Allah, kai ne wanda Allah ya tsarkake shi daga zina daga Adam har zuwa mahaifinka, da cewa: Ni da kai mun fito ne daga aure ba zina ba, daga Adam har zuwa Abdul-Muɗɗalib.”[15]
2. Al-Khazzaz al-Qummi ya ruwaito daga Anas bn Malik cewa Annabi (S) ya ce: “Allah Ya halicce ni ni da Ahlulbaitina daga haske guda kafin Ya halicci Adam da shekaru dubu bakwai. Sa’an nan Ya mayar da mu zuwa cikin tsatson Adam, sannan Ya ci gaba da mayar da mu daga tsatson masu tsarki zuwa mahaifai masu tsarki.”[16]
3. Sheikh aɗ-Ɗusi ya ruwaito daga Annabi (S): “Allah Ya riƙa mayar da ni daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki, bai gurɓata ni da ƙazantar jahiliyya ba.”
Ya ce: “Wannan hadisi ne da babu saɓani a ingancinsa.”[17]
4. Ya kuma ruwaito daga Annabi (S): “Ni da Ali mun kasance a gefen dama na Al’arshi muna tasbihi ga Allah shekaru dubu biyu kafin Ya halicci Adam. Lokacin da Ya halicci Adam, Ya sanya mu cikin tsatsonsa, sannan Ya ci gaba da mayar da mu daga tsatso zuwa tsatso a cikin tsatso masu tsarki da mahaifu masu tsarki, har muka kai ga tsatson Abdul-Muɗɗalib.”[18] | 26 |
| 20 | Sin texto... | 27 |
