ar
Feedback
TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

TASKAR KARATUKA DA AYYUKAN AL-ABDUL FANEEY AL-KANAWEEY🎥📚📗

الذهاب إلى القناة على Telegram

SHI'A IMAMIYYA ISNA ASHARIYYA

إظهار المزيد
2 289
المشتركون
+124 ساعات
-27 أيام
-930 أيام

جاري تحميل البيانات...

سحابة العلامات
لا توجد بيانات
هل تواجه مشاكل؟ يرجى تحديث الصفحة أو الاتصال بمدير الدعم الخاص بنا.
الإشارات الواردة والصادرة
---
---
---
---
---
---
جذب المشتركين
يوليو '26
يوليو '26
+28
في 0 قنوات
يونيو '26
+61
في 0 قنوات
Get PRO
مايو '26
+38
في 0 قنوات
Get PRO
أبريل '26
+16
في 0 قنوات
Get PRO
مارس '26
+18
في 0 قنوات
Get PRO
فبراير '26
+36
في 0 قنوات
Get PRO
يناير '26
+15
في 0 قنوات
Get PRO
ديسمبر '25
+40
في 0 قنوات
Get PRO
نوفمبر '25
+44
في 0 قنوات
Get PRO
أكتوبر '25
+29
في 0 قنوات
Get PRO
سبتمبر '25
+33
في 0 قنوات
Get PRO
أغسطس '25
+24
في 0 قنوات
Get PRO
يوليو '25
+60
في 0 قنوات
Get PRO
يونيو '25
+33
في 0 قنوات
Get PRO
مايو '25
+66
في 0 قنوات
Get PRO
أبريل '25
+43
في 0 قنوات
Get PRO
مارس '25
+60
في 0 قنوات
Get PRO
فبراير '25
+110
في 0 قنوات
Get PRO
يناير '25
+40
في 0 قنوات
Get PRO
ديسمبر '24
+68
في 0 قنوات
Get PRO
نوفمبر '24
+172
في 0 قنوات
Get PRO
أكتوبر '24
+185
في 0 قنوات
Get PRO
سبتمبر '24
+136
في 0 قنوات
Get PRO
أغسطس '24
+184
في 0 قنوات
Get PRO
يوليو '24
+72
في 0 قنوات
Get PRO
يونيو '24
+49
في 0 قنوات
Get PRO
مايو '24
+54
في 0 قنوات
Get PRO
أبريل '24
+52
في 0 قنوات
Get PRO
مارس '24
+92
في 0 قنوات
Get PRO
فبراير '24
+68
في 0 قنوات
Get PRO
يناير '24
+59
في 0 قنوات
Get PRO
ديسمبر '23
+51
في 0 قنوات
Get PRO
نوفمبر '23
+44
في 0 قنوات
Get PRO
أكتوبر '23
+55
في 0 قنوات
Get PRO
سبتمبر '23
+54
في 0 قنوات
Get PRO
أغسطس '23
+23
في 0 قنوات
Get PRO
يوليو '23
+59
في 0 قنوات
Get PRO
يونيو '23
+62
في 0 قنوات
Get PRO
مايو '23
+28
في 0 قنوات
Get PRO
أبريل '23
+33
في 0 قنوات
Get PRO
مارس '23
+58
في 0 قنوات
Get PRO
فبراير '23
+49
في 0 قنوات
Get PRO
يناير '23
+42
في 0 قنوات
Get PRO
ديسمبر '22
+39
في 0 قنوات
Get PRO
نوفمبر '22
+20
في 0 قنوات
Get PRO
أكتوبر '22
+24
في 0 قنوات
Get PRO
سبتمبر '22
+7
في 0 قنوات
Get PRO
أغسطس '22
+16
في 0 قنوات
Get PRO
يوليو '22
+14
في 0 قنوات
Get PRO
يونيو '22
+37
في 0 قنوات
Get PRO
مايو '22
+52
في 0 قنوات
Get PRO
أبريل '22
+527
في 0 قنوات
التاريخ
نمو المشتركين
الإشارات
القنوات
25 يوليو+1
24 يوليو+3
23 يوليو+2
22 يوليو+1
21 يوليو+1
20 يوليو+1
19 يوليو+5
18 يوليو+2
17 يوليو+1
16 يوليو+1
15 يوليو0
14 يوليو0
13 يوليو+1
12 يوليو0
11 يوليو+3
10 يوليو+1
09 يوليو+1
08 يوليو0
07 يوليو+1
06 يوليو0
05 يوليو+1
04 يوليو+1
03 يوليو0
02 يوليو+1
01 يوليو0
منشورات القناة
SHAHADAR AMMAR BIN YASIR DA KHUZAIMATU BIN THABIT DA HASHIMUL MIRƘAL (R.T.A) A YAƘIN SIFFIN TARE DA IMAM ALI (A.S.) Sunyi Shahada a rana mai kamar yau , 9 ga watan Safar shekara ta 37 bayan hijira , lokacin da suke yaki a cikin rundunar Imam Ali (a.s.) a yaƙin Siffin da aka yi da rundunar Azzalumai ta mutanen Sham . -Ammar bn Yasir ya kasance ɗaya daga cikin manyan Sahabban Manzon Allah (s) masu daraja , wanda Annabi yayi masa bushara da cewa rundunar Azzalumai ce za ta kasheshi , kuma hakan ta faru bayan shekaru masu yawa da komawar Annabi ga Ubangijinsa , inda Ammar Bn Yasir yayi shahada a hannun rundunar Azzaluman Sham (Rundunar Mu'awiyah ɗan Abi Sufyan ) . Shahadar Ammar Bin Yasir tana daga cikin Mu'ujizozin da Annabi ya bada labarinsu , kuma tana tabbatar da kasancewar rundunar Sarkin Sham Mu'awiyah , a matsayin Azzaluman ƴan Ta'adda. - Khuzaimatu bin Thabit Al-ansari , wanda ake ma laƙabi da Zush shadataini (ma'abocin sheda biyu ) , shima yana daga cikin manyan Sahabbai managarta , da suka Sallamawa Annabi da iyalan gidansa , kuma suka tsaya tsayin daka a bayan Annabi (s) wajen kare iyalansa , tun daga Saƙifa har ranar da yayi shahada a tare da Imam Ali (a.s.) lokacin yaƙin Siffin a rana mai kamar yau .Kuma ya kasance mawaƙi da ya yawaita yabon Imam Ali da bayanin matsayinsa da falalarsa . - Shima Hashim bn Utbatu bn Abi Waƙkas , wanda aka fi sani da Almirƙal yana daga cikin Sahabban da suka bawa Musulunci gudummawa tun ran gini , kuma ya kasance cikin rundunar Imam Ali (a.s) a yaƙin Siffin , a lokacin da Alharis Bn Munzir ya lallaɓo ya sokeshi a cikinsa . ✍️Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv

2
masoyansu. Amma muna jefa kule ga duk masu ra'ayin biyu da su kawo inda Sayyid Khumaini ko Sayyid Khamene'i (R) suka ce ku dena yarda ana ce muku Shi'a don kar kai ya rarrabu ! Amma dai mun san sun hana amfani da sunan Shi'a wajen kawo rarrabuwar kai da rikici. Idan ban manta ba a jawabin Sayyid shugaban Kudu (Allah ya jiƙan shi) na ranar Ƙudus ɗin shekarar 2013 , yana bugar ƙirji da karsashi yana faɗawa duniya : Mu ne rundunar ...tawagar Musuluncin Shi'a Imamiyya Ithna Ashariyya ... Mu ne Shi'ar Ali ɗan Abi Ɗalib a duniya . ونحن حزب ...الحزب الإسلامي الشيعي الإمامي الإثني عشر .... نحن شيعة علي بن أبي طالب في العالم . Kuma ban jin akwai wanda zai ce bai fahimci gw@gwarmaya ko fikra ingantacciya ba sai ɗan son zuciya . 7 . Don haka zance na gaskiya da adalci bisa dai-daito kar a kore sunan Musulmi ko a kore na Shi'a domin duka suna da asali mai kyau , bari dai a tashi a yaƙi amfani da su wajen kawo rikici ko rabuwar kai shi ne mafita. Domin ba sunan Shi'anci ba ita kanta kalmar Musulmi ɗin ana iya amfani da ita a kawo rarrabuwar kai , kenan itama kalmar Musulmin sai mu dena kiran kanmu da ita ? 8 . Kuma duk yanda ka kai ga dena kiran kanka Shi'a matuƙar ka yarda da aƙidar to ba za kaga kuɓuta ba , tunda dai za a dinga ganinka da ayyuka da taken su , bari ma dai za a tuhumeka da mai taƙiyya ne ko mai raina wayo . Don haka muna tare da hana amfani da sunan Shi'a wajen kawo rarrabuwar kai da rikici , amma bama tare dena amfani da sunan Shi'a da da'awar neman haɗin kai ko cimma manufa , kuma hakan ba ya nuna bama tare da haɗin kai ko kusanto da juna . Wannan ra'ayina ne kuma kowa yana da ikon faɗin albarkacin bakinsa . Ni nake da alhakin rubutuna mai karatu kuma shi ne zai ɗauki alhakin duk fahimtar da yayi min . ✍️Masoyin Al-shaikhul Mufid Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 9 / Safarul Khair / 1448H - 24 / 7 / 2026 miladiyya.
43
3
BA HANA AMFANI DA SUNAN SHI'A BANE MAFITA HANA AMFANI DA SUNAN SHI'A WAJEN RARRABA KAN MUSULMI SHI NE DAI-DAI !!! 1 . Tabbas Allah Ta'ala ya siffanta Annabi Ibrahim da sauran Annabawa (A.S) da musulmi , amma hakan ba ya nuna cewa su ba muminai ba ne , ko su ba mukhlasai ba ne , ko su ba hanifai bane .... Kamar yanda a wata ayar ya kira Annabi Ibrahim da Shi'a, domin - bisa zance na tahƙiƙi a wurin malamai - sifa ba ta da mafhumi kamar laƙabi take mafhumi su ba hujja bane. Shi yasa Allahn da ya siffanta su da Musulmi shi ne kuma a wasu ayoyin ya siffanta su da Mukhlasai, a wasu ayoyin kuma hanifai , a wasu ayoyin kuma da Muminai da sauran siffofi masu girma ..saboda yawaitar suna ko sifa yana nuna daraja da ɗaukakar ma'abocinsu. 2 . Kamar yanda siffanta Musulmi da wannan sifa ko laƙabi ba ya nuna haramci ko rashin kyautatuwar siffanta su da wani suna bayan wannan ko kuma yana kore ya zama suna da wani laƙabi ko suna na daban , ƙa'ida ce zaunanniya ta hankali cewa "Tabbatar da wani abu ba ya kore waninsa" إثبات الشيء لا ينفي غيره kowanne abu da mahallinsa. 3 . Ko da an ɗauka kalmar Musulmi sunan yanka ne ga duk wanda yayi kalmar shahada biyu , hakan ba ya hana ya zama sunaye da laƙubba da matakai mabanbanta , domin shi Musulunci ba komai bane face maudhu'i na hukunce-hukunce kamar haramta jinin mutum da dukiyarsa da halascin aurensa da sauran su . 4 . Bugu da ƙari dalilai masu tarin yawa - bayan Alƙur'ani - sun tabbatar da wani suna ko laƙabi ga wasu Musulmi saboda daraja ko hususiyarsu , kamar Muminai , ƴan Shi'a ,Rofidhawa ... Kuma shi sunan ƴan Shi'a halsataccen suna ne garesu daga Annabi (Saww) da iyalan gidansa tsarkaka , bari ma ya tabbata a hadisai masu tarin yawa suna kiran mabiyansu da ƴan Shi'a , suna masu cewa ƴan Shi'ar mu kaza da kaza , ƴan Shi'ar mu su ne masu kaza , kuma ba wai kawai siffantasu suke da haka ba a muƙamin magana sun ayyana musu waɗannan sunaye ne kai tsaye. Domin kuwa ya zo a hadisai masu tarin yawa lokacin da wasu maƙiya Shi'a suka matsa da tsokanar ƴan Shi'a ko kiran ƴan Shi'a da sunansu na Rafidha , sun kawowa Imam Muhammadul Baƙir (AS) koke wata rana sai yace : Nima Rafhidi ne kuma ina daga cikin su , a wani hadisi an bayyana musu tun zamanin Annabi Musa (A.S) ake kiran waɗanda suka kangarewa ɓarna da wannan suna , a wani hadisi na Allah ne ya kira su da wannan sunan. 5 . Don haka idan muka ce za mu dena kiran kanmu da sunan da Allah da Manzon Allah (SAWW) da limaman shiriya suka raɗa mana - saboda kauda saɓani ko haɗin kai - to ai ba iya suna ba gaba ɗaya aƙidar za mu dena yi ; saboda ba sunan bane matsalar abinda aka sawa sunan ne matsala kenan , shi suna take ne mai bada labari , don ka ce a dena kiran ka Shi'a amma ka ci-gaba da Aƙida , ibada da mu'amala irin na Shi'a bata sauya zani ba , ba cinya ba kafar baya kenan. Dole ka dena zaman Ashura ; don shima take ne na Shi'a a duniya , dole ka dena magana irin ta Shi'a ko saka.kaya irin na Shi'a ko malaman Shi'a , dole ka dena komai ka koma kamar zamanin da aka saukar da aya ta farko ga Annabi (SAWW) kafin a fara saukar da hukunce-hukunce. Kainko ka koma hakan saɓani ba zai kau ba domin sunnar Allah ce a cikin halitta , ba za su gushe ba suna masu saɓani ... na'am hakan ba zai hana ayi ƙoƙarin haɗin kai da kusanto da juna , amma haɗin kai ba ya nufin kowa ya shafe "Huwiyyarsa" gaba ɗaya. 6 . Wannan ya nuna mana shi sunan Shi'a a kankin kansa ba shi bane matsala idan ana so a yi da'awa ga mutane , amfani da sunan Shi'ar wajen kawo rarrabuwa shi ne illah kuma shi ya kamata a kira a hana su , kuma wannan itace fikirar malaman Shi'a kaf ɗinsu (Musamman Sayyidunal Khumaini da Sayyid Khamene'i Allah ya ƙara musu yarda) bayanan su da littattafan su cike suke da hakan. Tabbas duk wanda ya koma maganganun waɗannan jagororin fikrar Musulunci zai ga suna bayani a kan haɗarin fakewa da sunan Shi'a ko aƙidar Shi'a wajen kawo rarrabar Musulmi , amma ba za ka samu suna cewa ku dena kiran kanmu Shi'a , abu ne da ba zai taɓa yiwuwa ba su faɗi hakan , duk da wasu maƙiyansu suna tuhumarsu da hakan saboda suma basu fahimce su ba kamar wasu
34
4
Imam Hassan (a.s) ya rayu tsawon shekaru 47 , tare da Imamancin Shekaru goma , tun bayan Shahadar mahaifinsa Imam Ali (a.s.) a shakara ta Arba'in (40) bayan hijira , shi kuma Imam Hassan ya rasu a ranar bakwai ga watan Safar shekara ta Hamsin bayan Hijira , A wata ruwayar kuma ; 28 ga watan Safar ne ranar shahadar Imam Hassan (a.s.) . السلام عليك أيها المظلوم الشهيد ورحمة الله وبركاته ومغفرته ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 7 / Safar/ 1444H - 24/8/2023 Miladiyya
58
5
SHAHADAR IMAM HASSAN AL-MUJTABA (A.S.) A ranar bakwai ga watan Safar , shekara ta 50 bayan Hijira , babban jikan Manzon Allah (saww) , limami na biyu daga jerin Limaman shiriya, Karimu Ahlil baiti , Imam Hassan ɗan Imam Ali da Sayyida Fatima (a.s) yayi shahada a garin Madina . Tun bayan yarjejeniyar da akayi tsakanin Imam Hassan (a.s) da Mu'awiyah ɗan Abi Sufyan (L), Mu'awiya ya cigaba da warware waɗannan sharuddan da aka gindaya masa , har ta kai ga yazo ya amshi caffa ga ɗansa Yazidu , a matsayin yarima mai jiran gado , wanda hakan ya saɓawa yarjejeniyar da akayi dashi. Daga cikin Sharuɗɗan shine zai ci gaba da gudanar da harkar Gwamanti , idan ya mutu to al'amari zai dawo wajen masu shi ko Imam Hassan ko Imam Hussain (a.s.) , amma bai iya cika wannan alƙawari ba . Abul Faraj ya rawaito cewa : Tun sanda aka gama sulhu tsakanin Imam Hassan (a.s) da Mu'awiyah (L), sai Mu'awiyah ya tara wasu mutanensa yace musu ; Sulhun da muka yi da Hassan na takeshi a ƙarƙashin ƙafata , kuma Ni ai ba don Sallah ko Azumi Ko Zakka da Hajji nake wannan rigimar ba , mulkin nan na kakannina nakeso , kuma gashi ya dawo hannuna . Ta ɓangaren Imam Hassan (a.s ) ya shagaltu da ibada da shiryar da mutane da karantar dasu Addini na haƙika , sai ya zama Gwamanti tana hannun Mu'awiya , mutanen Allah da zuciyoyinsu suna tare da Imam Hassan (a.s) , hakan ya cigaba da ƙuntatawa Mu'awiyah (L) sosai , daga nan ya shiga kokarin ganin ya kawar da Imam Hassan (a s.) baki ɗaya don mulki ya cigaba a zuriyarsa yadda ya tsara ba tare da cikas gareshi ba . Yayi ta sawa ana bawa Imam Hassan (a.s) guba yana sha , amma Allah yana tseratar da Imam Hassan (a.s.) daga sharrinsa , sai a ƙarshe da ajalin Imam Hassan (a.s) yayi , Mu'awiya ya biya matar Imam Hassan (a.s) don ta shayar dashi guba ƴar Rum, tare da yi mata alƙawuran da bai cika mata ba , kamar aura mata Yazidu da samun ɗinbin dukiya mai yawa . Haka ko tayi masa abinda yake so , ta shayar da Imam Hassan (a.s) wannan guba da Mu'awiya (L) ya bata , lokacin da Imam Hassan (a.s) yake ƙoƙarin bude baki yayin da yayi Azumi . Daga nan ne wannan gubar ƴar Rum ta kwantar da Imam Hassan (a.s) na ƴan wasu kwanaki , tana yawo cikin jininsa da jijiyarsa da namansa , har ta kai ga ta fara farfasa masa ƴaƴan hanjinsa ! Imam Hassan (a.s) ya dinga aman jininsa da hantarsa saboda ƙarfin wannan gubar da tasirinta, daga ƙarshe yayi wasiyyoyi ga ɗan uwansa Imam Hussain (a.s) , sannan ya koma ga Ubangijinsa a matsayin shahidi abun zalunta .Allahu Akbar !!! An rawaito cewa ; Lokacin da Imam Hussain (a s.) ya ɗauki gawar Imam Hassan mai tsarki, da nufin binneta a maƙabartar Baki'u kamar yanda Imam Hassan (a.s) yayi masa wasiyya , cewa ya fara kaishi wurin Annabi kakansa suyi bankwana , sannan ya tafi dashi can ya binne shi a kusa da kakarsa Sayyida Fatima Bintu Asad. Sai Marwan Binil Hakam (L) ya ɗebo yaransa Umayyawa suka tare Imam Hussain (a.s) a hanya , suna tsammanin zai binneshi kusa da Annabi (saww) ne , suna cewa ai muma ba'a bari mun binne Usman bn Affan a kusa da Annabi ba don haka kuma baku isa ba . Da labari ya isa ga matar Manzon Allah (saww) , Aisha bintu Abi Bakr, sai ta hayo kan Alfadara kamar yanda ta hau raƙumi a yaƙin Jamal , tazo tana cewa ; Nima bazan yardaa ku binne min wanda banaso ba a ɗaƙina ba sam , wuri ya yamuste da rikici da hayaniya , har ta kai ga an fara harbin gawar Imam Hassan (a.s) da kibiya ! Sai Imam Hussain (a.s) ya aiwatar da wasiyyar ɗan uwansa Imam Hassan (a.s) , ta kar ya bari a sheƙar da jini a lokacin jana'izarsa , take suka juya aka tafi can Maƙabartar Baƙiy , aka binne Imam Hassan kusa da kakarsa Sayyida Fadima Bintu Asad (Mahaifiyar Imam Ali ) tsira da Amincin Allah su ƙara dawwama a gare su baki ɗaya . Kafin Imam Hasan (a.s) ya cika , a ko da yaushe Imam Husain (a.s.) yana shiga wajensa , har suyi ta kuka da jimamin halin da suka shiga tun bayan rashin kakansu Annabi da Mahaifansu , Imam Hasan (a.s) ya kasance yana cewa ; Wannan ne abinda kakanmu Manzon Allah (a.s) yace zai samemu , lallai ya gaskata a cikin zancensa .
60
6
"Duk al'umar da suka zaɓi shiru da ɗaukar ƙasƙanci tabbas za su zama bayin azzalumai" ✍️Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
"Duk al'umar da suka zaɓi shiru da ɗaukar ƙasƙanci tabbas za su zama bayin azzalumai" ✍️Al-Abdul Faneey Al-kanaweey
76
7
ISOWAR IYALAN GIDAN MAZON ALLAH (SAWW) CIKIN GARIN SHAM !!! A ranar 1 ga watan Safar ɗin shekara ta 61H , sojojin Umayyawa suka shigo da ayarin zuriyar Manzon Allah cikin garin Sham ta ƙofar "Bab al-Sa’at (Bab Touma) inda kan Imam Husain (a.s) yake sahun gaba a tsire a kan dogon mashi da sauran kawukan da aka yanke a Karbala , dama jerin gwanon mata da yara na daga zuriyar Annabi (saww) , sun shiga gaban Imam Ali Zainul Abidin (a.s) a lokacin da aka ɗaure hannunsa da sarƙoki . Daga ɓangaren mutanen garin Sham kuwa , sun caɓa ado sun fito tarbarsu da kiɗe-kiɗe da raye-raye da murna da farin ciki , fiye da yadda suke yi ranar Idi , masu jifa nayi , masu zagi nayi , masu ihu da shewa nayi ta ko ina . السلام على جبل الصبر زينب 😭 ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
121
8
SHAHADAR BABBAN SAHABIN ANNABI HUZAIFATU IBNUL YAMAN (R.T.A) A ranar 28 ga watan Muharram , shekara ta 36 bayan hijirar Annabi (s) , babban sahabin nan Huzaifatul yamani yayi wafati. GA TAƘAITACCEN TARIHINSA : Shine Abu Abdillah , Huzaifah bin Hisal (Husayl) bin Jabir bin Amr bin Rabi'ah. Mahaifinsa kuwa shine Husail bin Jabir , shahararren sahabi . Mahaifiyarsa itace : Al-Rubab bint Ka'ab bin Adi bin Abdul Ashal, daga Ƙabilar Aus , mutuniyar Madina . Ƴa'yansa: Su ne Sa'ad bin Huzaifa bin Al-Yaman, wasu suka ce Saeed ne sunansa , Sai Safwan bin Huzaifa bin Al-Yaman , Da Husail bin Huzaifa bin Al-Yaman. Da Abu Ubaidah bn Hudhaifa bn Al-Yaman, wanda shine Bilal . An ruwaito cewa an kashe Sa'ad ko Sa’eed da ɗan uwansa Safwan ‘ya’yan Huzaifa bin Al-Yaman tare da Imam Ali (a.s) a Siffin, kuma sun yi mubaya’a ga Imam Ali (a.s). bisa wasiyyar mahaifinsu. Huzaifa yana daga cikin fitattun manyan sahabban manzon Allah (saw) masu daraja , shine ma'abocin sirrin Annabi , kuma mafi sanin mutane akan lamarin munafukai , domin shi Annabi yake sanarwa da sunayen munafukai . Ya halarci yaƙin Uhudu da sauran yakoƙin da suka biyo baya , kuma yana daga cikin wadanda suka yi tsayin daka a kan imaninsu , suka tabbata a bayan wafatin Manzon Allah (saww) . Ya kasance tare da Imam Ali (a.s.) kasancewa ta gaskiya , kuma yana daga cikin tsirarun mutanen da suka halarci jana'izar Sayyida Fatimatuz Zahra (a.s) , ya kuma tsaya akan gawarsa Mai tsarki yayi mata sallah . Ya yi Gwamnan garin Mada'in a zamanin Umar da Usman, kuma ya yi rashin lafiya a farkon halifancin Amirul Muminina Imam Ali (a.s), dauk da wannan bai iya yin shiru ba , ya kasance yana faɗar falaloli da darajojin Imam Ali , har ya hau mimbari yana halin rashin lafiyarsa , ya yabi Imam Ali , yayi masa kirari , sannan yace : Wallahi Ali yana kan gaskiya a ƙarshe da farko . Ya kuma ce : Ali ne mafi alherin mutane bayan Annabinku. Ya karɓarwa Imam Ali bai'a , kuma shima da kansa ya yi masa mubaya'a, ya kuma yi wasiyya ga 'ya'yansa, yana mai jaddada cewa kada su yi kasa a gwiwa wajen bin Imam Ali (a.s.) ko bayan ransa . Huzaifa yana da tarin matsayi da daraja da falala a cikin wannan al'umma , ya isheshi matsayi da daraja kasancewarsa cikin keɓantattun Imam Ali (a.s.) , sannan mataimakinsa tun a farkon al'amari ta yadda dashi akayi jana'izar Sayyida Fadima (a.s.) . An karɓo daga Manzon Allah (saww) ya ce: “Huzaifa ɗan Yaman yana daga cikin zaɓaɓɓun Allah Arrahamanu . Sannan Annabi ya haɗashi ƴan uwantaka da Ammar bn Yasir a Madina . Bayan wafatinsa an binne shi a garin Mada'in dake ƙasar Iraƙi , a yanzu haka ƙabarinsa yana kusa da ƙabarin Sahabin nan Salmanul Farisi , dama Abdullahi bin Jabirul Ansari da Aliyuɗdahir . A shekarar 1933 aka dakko Huzaifa aka dawo dashi wannan wurin da yake a yanzu , aka sake binne shi saboda matsalar ambaliyar ruwan Dijla, a lokacin anga gawarsu lafiya kalau tana haske da sheƙi kamar ranar aka binne su , duk an share sama da shekaru dubu da yi musu binnewar farko , anyi gagarumin taro a kasar Iraki ranar da aka kawo su kusa da Salmanul Muhammadi , kuma manyan karamomi sun bayyana ga mutane . Sannan har yanzu suna wurin ana ci gaba da ziyararsu a unguwar da katangar Kisra take . ✍️ Khadimu ã'atabi ãli Muhammad Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 28/ Almuharramul Haraam - 27/8/2022
136
9
Ba a Karbala gwagwarmayar ta fara ba kuma ba ta ƙare da kashe Imam Husaini ba !!! https://t.me/tafarkintsiratv
Ba a Karbala gwagwarmayar ta fara ba kuma ba ta ƙare da kashe Imam Husaini ba !!! https://t.me/tafarkintsiratv
102
10
SHAHADAR IMAM ALIYU ZAINUL ABIDIN (ALAIHIS SALÃM) Ya zo a hadisi cewa Imam Ali Zainul Abidin (a.s) ya yi kukan shakara 25 ko 40 saboda kisan gillar da aka yiwa mahaifinsa Imam Husaini ( Alaihis salãm) da danginsa a Karbala. Wata rana wani daga cikin barorinsa ya gan shi ya jiƙe fuskarsa da gamunsa mai albarka da hawaye sai yace masa : Ya shugabana shin lokaci bai yi bane da baƙin cikinka zai yanke haka nan kukanka ya ƙaranta ? Sai Imam Sajjad yace da shi : Kayi hattara! Lallai Ya'aƙubu ɗan Ishaƙ ɗan Ibrahim ya kasance Annabi ɗan Annabi kuma yana da ƴaƴa goma sha biyu , sai Allah ya fakar da guda ɗayansu , amma sai da kansa yayi furfura saboda baƙin ciki , haka nan bayansa ya ranƙwafa saboda damuwa da ƙunci kuma ganinsa ya tafi saboda kuka alhalin ɗan nasa yana raye a gidan Duniya , Ni kuma naga babana da ɗan uwana tare da mutum sha bakwai daga dangina an musu kisan gilla ta yaya baƙin cikinna zai yanke kuma na dena kuka ?! An ruwaito tun bayan waƙi'ar Karbala ba a taɓa ajiye abinci da ruwa gabansa ba face sai ya jiƙa shi da hawaye saboda abinda aka yiwa mahaifinsa da danginsa a saharar Karbala . A wani hadisin Imam Ja'afar Assadiƙ (A.S) yana cewa : Al-bakka'ūn (Masu yawan kuka a duniya) biyar ne , Adamu , Ya'aƙubu , Yusufu , Faɗimatu bintu Muhammad da Aliyu bin Husaini (a.s) . Tabbas Imam Ali Zainul Abidin (a.s) ya tsaya tsayin daga wajen raya al'amarin Ashura da Karbala da kuma sanar da Musulmi har tashin alkiyama mazlumiyyar su (Ahlul Baiti) ta hanyar amfani da salo daban-daban da kuma matakai mabanbanta duk da yanayin da ya sami kansa mai wahala , bugu da ƙari ya sadaukar da rayuwarsa wajen isar da saƙon Musulunci na haƙiƙa da sanar da duniya matsayinsu hatta a cikin salo na addu'a da munajati , kuma yakan sayi bayi ya ƴanta su sannan ya sanya su bazama sassan duniya domin karantarwa bayan ya raine su , in ko ana maganar gudun duniya , sanin Allah , jarumta , kyauta , ibada , sadaka , da duk wani halin girma da tadojin kirki shi maƙura ne . Imam Sajjad (a.s) ya yi shahada a garin Madina mai girma a ranar 25 ga watan Al-Muharram ɗin shakara ta 95 bayan hijira , watau shakara 35 da waƙi'ar Karbala . ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
150
11
"سليل الكرام" غاب نجمٌ وصفوةٌ في الأنامِ خمنئيُّ العلى سليلُ الكرامِ ليس يسلي الفؤادَ عن حرّ حزني غيرَ يوم الظّهورِ والانتقامِ يا لها من فجيئةٍ كدتُ أسقى من لظى شجوها كؤوسُ الحِمامِ كيف غطّى التّرابُ وجهَك يا من شرّف الأرضَ بالصّلا والصّيامِ كيف يخبو نور النّضال وقد كا ن منارًا لنا مدى الأعوامِ آيةَ الله كنتَ في الففهِ والفكـ ـر وصونِ البلادِ دون انخرامِ يا ملاذَ الضّعيفِ شرقًا وغربًا من بكتْ فقدَه عيونُ الغمامِ كلّ شبرٍ بكاكَ في الأرض شجوًا من زُبى قدسِنا لدار السّلامِ أيّ شوقٍ يجتاحني وحنينٍ لشهيدٍ أذلّ جيشَ الطّغامِ قد ملأتَ الفؤادَ حبّا وفخرًا راسخًا في الحشا كشدّ العظامِ كنتَ في المكرماتِ رمزًا عزيزًا وصراطًا للحقّ يومَ الصّدامِ فقدكم ثلمةٌ عديمةُ سدّ غرق الكونُ بعدها في الظّلامِ من لنا سيّدي فتي الحربُ عادتْ كيف نقضي على حبالِ الخصامِ ! أيّها القائدُ العظيمُ سلامٌ من قلوبٍ تذوبُ قبل الكلامِ قد رثتكَ الأحرارُ من كلّ أرضٍ يا زعيمَ النّضال بينَ الأنامِ موضعُ العهد في القلوبِ حصينٌ ثابت لا يزولُ حتّى الختامِ ليس من شأننِا التراجعُ حتّى لو رُمينا بجمرةٍ وسهامِ نحن ماضون مثلما كنتَ تبغي ومصرّون في شديد اعتزامِ في سبيلِ الهدى ندوسُ المنايا ونصونُ الطّريقَ من كلّ رامِ في أمانِ الإلهِ يا بن عليٍّ وابن ياسين بلسمَ الأسقامِ ذا وداعي والدّمعُ يجري بدَفقٍ ولهيبِ الأسى وهجرِ المنامِ ذا وداعي بصرخةٍ وعويلِ في قريضِ الرّثا ودمعِ القلامِ نمْ قريرَ العينينِ فالنّهجُ باقٍ في قلوبِ الرّجال والأعلامِ وعليك السّلام ثمّ التّحايا يا رئيسَ النّضالِ نجلَ الكرامِ ✍️خادم العترة الطّاهرة ️ العبد الفاني الكنوي ٢٤ / المحرم الحرام / ١٤٤٨هـ
129
12
ƘARYA FURE TAKE BATA ƳAƳA Wai ƴan Shi'a suna yin murna da kashe Imam Ali in ji wani mabiyin addinin Wahhabiyawa! 🎙️ https://
ƘARYA FURE TAKE BATA ƳAƳA Wai ƴan Shi'a suna yin murna da kashe Imam Ali in ji wani mabiyin addinin Wahhabiyawa! 🎙️ https://t.me/tafarkintsiratv
127
13
TUNAWA DA HARIN SAMARRA A ranar 23 ga watan Al-muharram shekara ta 1427 bayan hijira , dai-dai da (22 ga watan Fabrairu , 2006 AD). Ƴan ta'addan Wahhabiyawa masu kafirta mutane suka kai harin bama-bamai a garin Samarra dake ƙasar Iraki , inda suka rusa ƙubbar zinare dake ƙabarin Imam Aliyul Hadi da Imam Hasan Al-askari da Sayyida Narjis da Sayyida Hakima suke kwance , tare da abubuwan tarihi masu muhimmanci da daraja , suka yi mummunar ɓarna da aikin ta'addanci . Garin Samarra , gari ne mai cike da abubuwan tarihi , a nan kurkukun da aka saka Imam Aliyul Hadi da Imam Askari (A.S) take , wanda duk mai imani in yaga wannan kurkuku sai ya zuba hawaye , da gidansu Imam Mahdi (a.j.)anan garin yake shima . Kuma dama nan ne babban birnin Daular Abbasiyyawa L da cibiyarsu , anan suka ci karensu ba babbaka na tsawon shekaru bayan sun baro birnin Bagadaza . Alhamdulillahi , duk waɗanda suka yi ta shirya wannan shegantakar garin ya gagare su zama kuma ga ƴan Shi'a ba ci gaba da zuwa ziyara . ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
130
14
SHAHIDI NA FARKO BAYAN WAƘI'AR KARBALA (ABDULLAHI BIN AFIF AL-AZDI) - Me ka sani game dashi ??? Abdullahi bin Afif Al-Azdi Al-Ghamidi (Allah ya kara masa yarda) , yana daga cikin manyan sahabban Amirul Muminin Ali bin Abi Ɗalib (a.s.), ya rasa idonsa na hagu a yakin Jamal dana dama a yakin Siffin yana cikin rundunar Imam Ali , bayan da ya rasa idanuwansa biyu sai ya shagaltu da bautar Allah tsantsa , kuma ya kasance daga cikin manyan bayin Allah masu zuhudu a garin Kufa . Ya kasance a cikin masallacin Kufa majlisin da Ibnu Ziyad (Allah Ya la'ance shi) ya shirya , lokacin da aka kawo Imam Sajjad da Sayyiida Zainab da sauran zuriyar Annabi (s) kufa , a matsayin ribattatun yaƙi da fursunonin Yazidu L , bayan an kashe Imam Hussain da kwana biyu . Sai Gwmanan Kufa Ibnu Ziyad (L) yace : Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya bayyanar da gaskiya da mutanenta, ya taimaki Amirul Muminin (ma'ana Yazidu ) da mabiyansa, kuma ya kashe makaryaci dan makaryaci (yana nufin Amirul Muminin Imam Ali da Imam Hussein ) , wai sune maƙaryata ! Jin haka ke da wuya sai Abdullahi bin Afif ya tashi a tsakiyar mutane ya cewa Ibnu Ziyad : Ya kai ɗan Marjana yi mana shiru , Kai da mahaifinka da wanda ya jiɓintaka da mahaifinsa ne maƙaryata , ya kai makiyin Allah, ka kashe ‘ya’yan Annabawa (zuriyar Annabi ) kuma kana faɗin waɗannan kalmomi a kan mimbarin muminai? (Kana magana irin ta mutanen kirki bayan aikin da kayi) . A lokacin ne sojojin Ibnu Ziyad sukayi kansa za su kamashi , sai ƙabilarsa suka hana su ta hanyar rufeshi da tada hayaniya a masallacin , ko da suka fitar da shi daga Masallacin , da ya isa gidansa sai sojojin Ibnu Ziyad suka kewaye gidansa suka karya ƙofa suka far masa. Duk da kasancewarsa makaho amma yayi yaƙi irin na mazaje , yana da wata ƴa mace mai suna "Safiyya" wacce ta dinga taya shi faɗa a cikin gidan , tana ce masa : Baba gasu nan ta damanka, Baba gasu nan ta bayanka, ko kuma daga gabanka, shi kuma yana kai sara duk ta inda tace masa ya kai sara ko duka , tana tayashi ita da wani ɗansa Namiji guda ɗaya ga shekarunsa sun ja , ya tsufa sosai . Daga baya suka kara yawa har suka kashe ɗiyarsa Safiyya da dansa Namijin , sannan suka kama Abdullahi bin Afif suka kai shi fadar Ibnu Ziyad . Ko da ya isa fadar , sai Ibnu Ziyad yace masa : Godiya ta tabbata ga Ubangijin daya wulakantaka , sai Abdullahi bin Afif ya mayar masa da martani cikin waƙa yana cewa : يا عدو الله ، وبماذا أخزاني الله ؟ والله لو فرج لي عن بصري ضاق عليك موردي ومصدري وكنت منـكم قـد شفيـت غلتي إن لم يكن ذا اليـوم قومي تخفـر أم كيف لي والأصبحي قـد أتى فـي جيشـه إلى لقا الـغضنفـر لـو بارزونـي واحـداً فواحـداً أفنيتـم بمـوردي ومصـدري يا ويحكم والسيف أبـدا مشرفـاً لا ينبغـي إلا مقـر الحنجـر ويح ابن مرجان الدعي وقد أتى ويزيد إذ يؤتى بهم في المحشر والحكـم فـيه للإله وخصمهـم خير البرية أحمد مـع حيـدر Ya cigaba da ce masa : Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai , na kasance ina roƙon Allah Ubangijina Ya ba ni shahada tun kafin mahaifiyarka ta haifeka ........ Bayan na makance sai na fidda rai daga samun shahada, amma yanzu Alhamdulillahi Allah ya azurtani da ita , ya nunan ya daɗe da amsar addu'ata . Sai Ibnu Ziyad (Allah Ya tsine masa) yace : Kuje ku sare min kansa ! Sai kuwa aka je aka sare wuyansa kuma aka gicciye shi .😭 Ya yi shahada ne a ranar 12 ga watan Muharram, wata ruwayar kuma ance a ranar 13 ga Muharram ne , shekara ta 61 bayan hijira . Amincin Allah ya tabbata a gare shi ranar da aka haife shi, da ranar da ya yi shahada, da ranar da za a tashe shi rayuwa kuma ƴantacce. ✍️ Khâdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey 12/ Almuharramul Haraam - 11 /8/2022 .
140
15
Idan ka zama Bahusaine to tabbas za ka zama Bakarbale , amma idan tunanin ka a kullum iya zama Bakarbale ne to ba lallai ka z
Idan ka zama Bahusaine to tabbas za ka zama Bakarbale , amma idan tunanin ka a kullum iya zama Bakarbale ne to ba lallai ka zama Bahusaine ba a ko da yaushe. ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
156
16
AIKA KAN IMAM HUSAINI (A.S) TARE DA SAURAN KAWUKAN SHAHIDAN KARBALA ZUWA GA YAZIDU (L) - LABARAN ASHURA DA KARBALA (HANYAR SHAM) A ranar 19 ga watan Almuharram ɗin shekara ta 61H , gwamnan Kufa la'ananne Ibnu Ziyad ya aika da kan Imam Husaini (a.s) tare da sauran iyalan Manzon Allah (saww) zuwa ga ubangidansa Yazidu ɗan Sarkin Sham Mu'awiyah (L) , bayan da aka kawo su birnin Kufa daga Karbala a ranar 12 ga watan Almuharram na shekarar. Tunda farko dai Ibnu Ziyad ya aikawa ubangijinsa Yazidu (L) labarin ya zartar da umarnin sa na kashe Imam Husaini (a.s) kuma zuriyar sa da kawukan waɗanda suka kashe suna tare dashi a Kufa , sai Yazidu (L) ya bada umarnin a ɗoro masa su a sirada a kai su Sham . To bayan hakan ne a ranar 19 ga Al-Muharram ɗin shekarar ya aike masa da su , an fita da tawagar Iyalan Manzon Allah (saww) daga Kufa tare da kan Imam Husaini (a.s) tsire bisa mashi ana yawo dasu gari-gari cikin Sahara don kai su ga Yazidu (L) ɗan masu cin hanta Babu shakka karamomi sun bayyana a tattare da kan Imam Husaini (a.s) yayin da ake yawo dashi bisa mashi, karamomi ne masu ɗimauta hankali da sanya tunani ga masu neman shiriya . السلام عليك يا قتيل العبرات ✍️ Khadimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
166
17
Wasu mutanen suna fara rayuwa ne daga sanda suka mutu , wasu kuma suna mutuwa ne a sanda suke raye . Fi amanillah , Sayyidana
Wasu mutanen suna fara rayuwa ne daga sanda suka mutu , wasu kuma suna mutuwa ne a sanda suke raye . Fi amanillah , Sayyidana . ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
177
18
ƁULLAR FITINA TA FARA TUN RANAR DA AKA FARA KARATUN HADISAN FIƘHU GA GAME GARIN MUTANE !!! Yaɗa karatun littattafan hadisan hukunce-hukunce a cikin game garin mutane da al'uma na daga cikin manyan kusakurai da fitintinun da Izala da Salafawa suka kawo cikin al'umarmu , domin kafin su a zaurukan ilmi muka san ana karanta su ba ga kowa da kowa ba. Kafin bayyanar su cikin mutanen mu su Lahalari, Ishmawiy , Iziyya , Mukhtasar da Askari aka sani ana koyawa mutane da ɗaliban ilmi , amma manyan littattafan hadisi na Sunanu ba na kowa bane. Abinda suka yi tamkar likita ne rana tsaka ya fito kan titi yana kiran mutane yana cewa kuzo na koya muku yanda ake haɗa magani da aikin likitanci. Saboda su littattafin hadisan hukuncen-hukuce kayan aikin manyan malamai da rantsattsun ɗaliban ilmi ne , wanin su kuma ana karanta masa hukunci da fatawa ne yaje yayi aiki da su tunda shi mai taklidi ne ba mujtahidi , ana ba shi sakamakon da aka fitar daga matakin tacewa da gyarawa kamar yanda likita yake ba shi magani bayan ya gano cutarsa da yanda zai maganceta. Idan ana so a sanar da mutane to a karantar da su fiƙhu ko aƙida ta hanyar matanonin fiƙhu ko aƙida da aka rubuta , shi yafi kusa da zaman lafiya da aminci. Amma ba laifi bane - bari ma abu ne mai kyau - a dinga karantar da al'uma littattafan hadisai da suka shafi tarihi , aƙida , gyaran zuciya da sauran su . Amma me kake tsammani idan aka kawowa game garin mutane litattafan da malamai kansu suna kai ruwa rana a tsakaninsu da gwabzawa a kan fahimtar su da aiki da su ?! ✍️ Khãdimul Ashrãf Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv
191
19
Kai bari ma ƴan Shi'a sunyi ƙaranci a kufa tun bayan Imam Ali (a.s.) ,da Ziyadu bn Abihi yazo duk ya koresu ya matsa musu , wasu suka koma Yaman wasu Khorasan.... , har Imam Hassan (a.s.) yayi masa muguwar addu'a saboda yadda ya matsawa mabiyansa , Ɗabarani ya rawaito haka cikin (المعجم الكبير lambar ruwaya ta 2690 ) yace : كان زياد يتتبع شيعة علي رضي الله عنه ، فيقتلهم، فبلغ ذلك الحسن بن علي رضي الله عنه فقال: اللهم تفرد بموته؛ فإن القتل كفارة. Kuma ko sanda aka kashe Imam Husaini (a.s) kusan duk wani babban ɗan Shi'a da kasani yana kurkuku , haka sauran ƴan Shi'a duk an tsare su , wanda suka rage sun gudu ko sun ɓuya , wasu kuma sun iya fita daga Kufan duk da dokar kulle da aka sa , sukaje sukayi shahada tare da Imam Hussain (a.s.) . In kuma sunce ƴan Shi'ar Kufa ne suka kashe Imam Husain (a.s) ya za suyi da ƴan Kufa dayawa da sukayi shahada tare da Imam Husain ? Irin su Habib bn Muzahir da Muslm ɗan Ausaja'i ? 3 . Babu wani ingantaccen dalili da za su iya kawowa da yake tabbatar da cewa Shimru da sauran waɗanda suka kashe Imam Husain (a.s) ƴan Shi'a ne, babu . In kuma akwai muna ƙalubalantar su su kawo mana shi ! Daga nan har tashin Alkiyama , hasali ma wannan maganar sabuwa ce kwana nan aka fara fito da ita dan a ɓata Shi'a Amma babu wani magabacin su akanta . 4. Waɗanda suka kashe Imam Hussain (a.s) sune ƴan Shi'ar Âli Abi Sufyan, wanda Imam Husain (a.s) ya faɗi hakan da kansa kafin a kashe shi , Alkhawarizimi ya rawaito a cikin(مقتل الحسين juzu'i na 2 shafi 38) cewa Imam Husain (a.s) yana ce musu a wata huɗubar sa : Kaiconku ya ku ƴan Shi'ar iyalan Abu Sufyan , in kun kasance baku da Addini kuma bakwa tsoron tashin Alkiyama, to ku zamo ƴantattu a duniyarku mana , ku koma ga nasabarku da asalinku In kun kasance larabawa kamar yanda kuke tsammani . Lafazin shine : وَيْحَكُمْ يَا شِيْعَةِ آَلِ أَبِي سُفْيَان. إِنْ لَمْ يَكُنْ لَكُمْ دِيْنٌ وَكُنْتُمْ لَا تَخَافُوْنَ يَوْمَ المَعَادِ فَكُوْنُوا أَحْرَارَاً فِيْ دُنْيَاكُمْ هَذِهِ، وَارْجِعُوا إِلَى أَحْسَابِكُمْ إِنْ كُنْتُمْ عُرُبَاً كَمَا تَزْعُمُوْنَ.. Imam Hussain yana fada ɓaro-ɓaro cewa ƴan Shi'ar Ali Abu Sufyan ne suka zo kasheshi , bai ce ƴan Shi'ata ba ko ƴan Shi'ar babana a misali . 5. Bugu da ƙari su da kansu wanda suka zo kasheshi sun faɗa suka ce masa : Hussaini ! Mun zo yakarka ne saboda haushin Babanka da ƙinsa da muke yi . Duba littafin (ينابع المودة j:3 shafi na 80 ) inda suke cewa : إِنَّا نَقْتُلُكَ بُغْضَاً لِأَبِيْكَ..... Tunda suka faɗi haka magana kuwa ta ƙare , domin ba ta yadda za'a yi ɗan Shi'a ya faɗi haka sam , in ko ya faɗa ba fita daga Shi'a ba ya kafirta gaba ɗaya , kuma mun riga munyi ta'arifin ɗan Shi'a a wajen Malaman Aƙida da Firaqu . Waɗannan kadan ne daga cikin dalilan da suke tabbatar da jahilci ko wautar masu cewa ; Ƴan Shi'a ne suka kashe Imam Husain (a.s) ko Shimru da Sinanu bn Anas da Shabas ƴan Shi'a ne , kamar dai yanda kagani . Akwai dalilai da yawa da suka sa suke kawo wannan shubhar da wautar ,wanda su kansu suna buƙatar dogon bayani amma daga cikin ; Suna yin hakan saboda ƙinsu da ƴan Shi'a ko ƙiyayyarsu ga Ahlul Baiti (a.s.) , da ƙoƙarin rufe mummunan aikin Yazidu da jama'arsa (L), saboda tona lamarin Yazidu yana nufin tona asiri babansa (Mu'awiyah) , dama wanɗanda suka kawo babansa (Mutanen Saƙifa kenan ) , daga nan kuma Addinsu ya rushe gaba ɗaya , shi yasa duk yadda zasu yi suna ƙoƙarin suga sun kare Yazidu (L), sun wautar da hankalin miskinan mutane daga hakikanin gaskiya , tare da sun san Yazidu Fasikin ne , ɗan giya , mai wasa da birrai , babu mai musa haka sai munkiri marashin rabo . Muna rokon Allah ya kara tsinewa makasan Imam Husain (a.s) , da duk wanda ke da hannu ko yaji daɗi ko yarda da abunda akayi , Allah ka ƙara ninka azaba madawwamiya akansu . Wassalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu 👏 ✍️Khadimul Itrah Al-Abdul Faneey Al-kanaweey https://t.me/tafarkintsiratv 11 /Almuharramul Haraam - 10 / 8/2022 .
158
20
SHIN ƳAN SHI'A NE SUKA KASHE IMAM HUSAIN (A.S) SANNAN SUKE KUKAN KASHESHI ? KUMA DA GASKE NE SHIMRU BIN ZHUL-JAUSHANIN ƊAN SHI'A NE ? Daga cikin shubha da wautar da wasu maƙiya ƴan Shi'a kanyi saboda jahilci ko ƙin gaskiya , sukan yi ƙoƙarin nuna cewa ; Ai shimru ɗan Zhul-Jaushan ɗan Shi'a ne , kuma shine wanda ya danne Imam Hussain ya yankashi , dan haka ƴan Shi'a ne suka kashe Imam Hussain (a.s.) . Abun dariya da takaici ! Dalilinsu na faɗar haka saboda shimru ya taɓa zama sojan Imam Ali (a.s.) a lokacin da Imam ya amshi Gwamnati , ko kuma ai shi Shimru mutumin Kufa ne , don haka ɗan Shi'a ne . Sai dai wannan magana cike take da wauta da jahilci da son rai, amma kafin mu warwareta , zamu so mu san menene ma'anar "Shi'a" da ɗan Shi'a Kalmar Shi'a a tsabar larabci tana nufin mabiya ko mataimaka , su ko malaman Aƙida da masana firaqu a isɗilahinsu ɗan Shi'a shine : Duk wanda yabi Ali ɗan Abi Dalib (a.s.) ya mara masa baya , kuma ya ƙudirceshi a matsayin Imami da Khalifa a bayan Manzon Allah kai tsaye , da Nassi bayyananne daga Annabi ko ɓoyayye . Idan mutum ya koma cikin duk litattafan Aƙida dana Malaman Firaqu zai samu haka , kamar Littafin (مقالة الإسلامين) na Abul Hasanul Ash'ari , ko (الملل والنحل ) Na Abul Fathi Ash- shahrustani da wasunsu zai sami hakan , daga ɓangren Shi'a ka duba littafin (أوائل المقالات) Na Sheik Almufid, in ma luga ne duba (لسان العرب ) Na Ibnul Manzur , zaka sami duk sunyi bayanin ma'anar Shi'a da ɗan Shi'a da irin abinda muka faɗa , tare da karin lafazai ko ragi domin lura (إعتبار ) . Kar na tsawaita mu koma kan batunmu na asali , shin Shimru da mutanen sa kamar Sinanu bn Anas da Ibnu Ziyadin L ƴan Shi'a ne ? Amsa cikin sauƙi itace : A'a , basu da alakar kusa ko ta nesa da Shi'anci , duk wnada yake da'awar haka don yayiwa ƴan Shi'a sharrin sun kashe Imam Hussain (a.s.) ne , jahili ne ko wawa , dalili akan haka shine : 1 . Kasancewar mutum (Kamar Shimru ) a rundunar Imam Ali (a.s) bashi ke nuna dole ya zama ɗan Shi'a ne shi , duk wanda yasan tarihi da ilmi baya buƙatar dogon nazari da tunani wajen sanin haka , in kuma ba haka ba zamuce masa shin Khawariju ƴan Shi'a ne ? Ko duk wanda yake cikin rundunar sojin Najeriya Musulmi ne ko Kirista ne shi ? Imam Ali (a.s.) yazo ya karɓi Gwamnati da take da rundunar soji da mutane mabanbantan ra'ayi da tunani da aƙida , don haka ma mafi yawansu ba ƴan Shi'arsa bane , sun dai yi masa mubaya'a a matsayin Khalifa ne kamar wanda suka gabace shi , suna aikin Gwamnati a ƙarƙashin sa yana biyansu albashi shikkenan....amma basa kallonsa da irin kallon da ƴan Shi'a suke masa , cewa shine Imami, Khalifan Annabi na farko ma'asumi ne da sauransu , shi yasa sau dayawa zai yi magana su juya masa baya ko su masa taurin kai , ko su saɓa masa a ra'ayi , koma su yi masa tawaye da bore , wanda shi wannan Shimrun da ire -irensa suna daga cikin wanɗanda suka yiwa Imam Ali tawaye , suka bar rundunar sa . Don haka kasancewar mutum soja a rundunar Gwamnatin Imam Ali (a.s) bashi ke nuna shi ɗan Shi'a bane sam , kamar yanda ba kowanne sojan Gwamantin Najeriya bane a yanzu , yake son Buhari ko Gwamantinsa ko yake yin "APC" ko yake tare da Addinin Buhari ko Aƙidarsa , shima Shimru ba kowa bane face game garin Musulmi , in kaso kace irin ƴan Iskan garin nan ! Wanda daga ƙarshe ya zama karen Banu Umayyah har ya kashe Imam Husain (a.s.) . 2 . Kasancewar mutum ɗan garin kufa baya nuna cewa shi ɗan Shi'a ne , kamar yanda kasancewar mutum ɗan garin Kano baya nuna shi ɗan kasuwa ne dole , Ibnu Taimiyya yana faɗa a cikin littafinsa Minhajussunah (J:4shafi 554 ): وكانت الكوفة بها قوم من الشيعة المنتصرين للحسين، وكان رأسهم المختار بن أبي عبيد الكذاب، وقوم من الناصبة المبغضين لعلي رضي الله عنه وأولاده ومنهم الحجاج بن يوسف الثقفي... Ma'ana : A kufa akwai ƴan Shi'a da suka taimaki Imam Husain, wanda shugabansu shine Mukhtar Assaqafi, kuma a kufa akwai Nasibawa maƙiya Ali (R) da ƴaƴansa kamar su Hajjaj bin Yusuf Assaqafi .
132