📚🖍Darul Fikr Na Mahdi Sanda 📚🖍
Open in Telegram
وَأَعِدُّوا لَهُم مَّا اسْتَطَعْتُم مِّن قُوَّةٍ.......! #Fikira_Ruhi_Jiki. #Kai_Da_Jama'a.
Show more803
Subscribers
No data24 hours
-27 days
-630 days
Posts Archive
Ya ɗauki ‘ya’yansa, ‘yarsa, jikarsa, surukinsa, ‘ya’yansa; da yawa daga cikinsu sun samu raunuka, kuma Mai Girma Imam Jagora yana cikin wani yanayi da nake gaya muku yana da wahala, amma suna da ƙarfi. Wannan shi ne addini.
- Wanda yake a gaba shi ne mafi zuhudu, wanda yake a gaba shi ne mafi yawan taƙawa, wanda yake a gaba shi ne mafi tsantseni, wanda yake a gaba shi ne wanda rayuwarsa ta fi kama da ta talakawa.
Wannan ita ce wilayar Manzon Allah, wilayar Musa da Isa da Shu’aibu da Salih da Amirul-Mu’minin da Al-Hasan da Al-Husaini har zuwa zamaninmu; har zuwa zamaninmu, wilayar maraji’ai, fuqaha da malamai.
Saboda haka dole imani ya kasance, kamar yadda Sheikh al-Fayyad — Allah Ya jiƙan sa — ya ce, daga Allah Ta’ala yake; haka kuma wilayar faqihi, wato wilaya da imani tare da shi.
Muna fara yin imani da shi? Eh, muna yin imani da shi. Sannan mu kasance tare da shi, cikin umarninsa. A nan kada a shigar da kishin ƙasa, ƙabilanci, Larabci, Farisanci, Turkanci, ko kaɗan; addini ɗaya ne! Addini ɗaya ne, Manzon Allah ɗaya ne, al’ummarsa ɗaya ce, layinsa ɗaya ne; kada mu raba al’umma.
- Eh, akwai wasu kebantattun halaye waɗanda ake kiyayewa kuma ake girmamawa, amma hatta waɗannan kebantattun halayen dole ne su taimaka wa al’umma ɗaya. Wannan yana daga cikin nau’o’in gaggauta bayyanar Imam.
- Muna jiran jagora ɗaya wanda zai cika duniya, ba wanda zai cika ƙasa ba! Zai cika duniya da adalci kamar yadda aka cika ta da zalunci da danniya.
- Saboda haka dole imani da waliyyi ya kasance imani tare da shi, ba imani da shi kawai ba; ma’ana imani, biyayya, ƙauna, narkewa cikinsa, kariya, taimako, riko da umarni da makamantansu.
Wannan wilaya ɗaya ce, wannan shi ne adalcin Allah. Da muna zamanin Musa, wannan shi ne. Da muna zamanin Nuhu, wannan shi ne. Da muna zamanin Manzon Allah, wannan shi ne. Da muna zamanin Amirul-Mu’minin, haka yake, kuma a yau haka yake, har zuwa bayyanar Imam Zamaninmu. Lamari ɗaya ne.
- Wannan imani da shi da kasancewa tare da shi, imani ne da Imam Zamaninmu. Marja’i da waliyyin faqihi, wannan akida ce ta larura a kan ra’ayin wasu malamai. Wannan larura ce saboda gaibar Imam Zamaninmu. Mu muna son Imam ne ta hanyar waliyyi ko marja’i.
Imani ne da Imam Zamaninmu, tare da Amirul-Mu’minin, tare da Manzon Allah, domin mu tabbatar da Tauhidi da imani.
- Batun wilaya ba batun motsin zuciya ba ne, ko siyasa, ko sha’awa, ko son rai, ko muradi, ko maslaha, ko son zuciya, ko son duniya ba. A’a, lamari ne na akida, imani, addini, Musulunci, neman kusanci ga Allah, biyayya, sadaukarwa da shahada saboda Allah.
Wannan ita ce hanyar da muke imani da ita.
- Jagoran shahidi, Imam Khamenei — Allah Ya jiƙan sa — yana da wata magana da yayi a ranar 9/1/2016, yana cewa:
A bisa wannan fahimta: “Alkawarin biyayya ga fuqaha alkawarin biyayya ne ga Manzon Allah.”
- Yana cewa: “Wanda ya yi mubaya’a ga Imam Khomeini a yau, to haƙiƙa ya yi mubaya’a ga Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).”
- Wannan ba ta kebanta ga Imam Khomeini ba ne. Kafin shi da shekaru dubu, bayan shi da shekaru dubu, a yau, gobe; lamarin shi ne a zamanin gaiba, a cikin ma’iyya, dole mu bincika: wa za mu kasance tare da shi?
- Wasu suna cewa mu masu zaman kanmu ne, kuma maƙiya ma suna yaɗa wannan ra’ayi. Ba zai yiwu ba! Ba zai yiwu ba!
- Mai girma Imamush Shahid ya yi shekaru yana cewa a Iraki: “Ku bi Ayatullah al-Uzma Sayyid as-Sistani.”
Ma’ana, ku kasance tare da shi cikin umarninsa da shiryarwarsa game da Iraki. Babu wata girmamawa ta baki kawai, har ma ga wanda ba ya Taqlidi da shi. Batun ba batun taqlidi ba ne; batun biyayya ne... biyayya!
- Wannan ita ce haɗin kan magana. Kuma ina da yaƙinin cewa da mun ƙara samun biyayya da ma’iyya tare da marja’in da ra’ayoyin fuqaha a Najaf da Qum da waliyyin faqihi suka yi ittifaqi a kansa, da halinmu a yau bai kasance haka ba.
- Wannan shi ne nasara. Nasara tana nufin sunnonin Allah, taimakon Allah, nasarar Allah da tawfiƙin Allah.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
- Saboda haka, tsakiyar ma’iyya tana kaiwa ga al’umma ɗaya, al’umma ɗaya. A nan zan yi magana a sarari, kuma zan sake maimaita wannan batu: dukkan taken ƙasa, na ƙabilanci, na jam’iyya da na tafiya, idan suna kaiwa kuma a cikin hanyar ƙarfafa... ƙarfafa al’umma Musulunci ɗaya, babu matsala a cikinsu.
- Amma duk wani taken, duk wani ra’ayi, duk wata ka’ida da take rarraba al’umma, wannan daga Shaiɗan ne, ko da kuwa mutane suna ɗaukarsa a matsayin taken mai tsarki; na ƙasa, na kabilanci... dukansu dole ne su karkata zuwa ga al’umma ɗaya, jagoranci ɗaya.
- Maƙiya suna raba mu domin su mallake mu. Ni kuma ina gaya muku: idan al’ummar Musulunci tayi ƙarfi, ƙasarmu tayi ƙarfi, ƙasar wancan da wancan da wancan tayi ƙarfi. Ƙasa tana ƙarfi ne da ƙarfin al’umma, amma ƙasashenmu suna raunana idan al’umma ta raunana. Wannan shi ne abin da Amurka take yi a yau da gobe.
- Batun wakilci, batun wilaya, batun marja’iyya a zamanin gaiba, ma’ana, a nan zan yi magana a sarari bisa ga waɗannan gabatarwa: cewa yin imani da hakan da kuma yarda da shi “da shi”, wato da faqihi ko marja’i, dole ne ya kai ga imani “tare da shi”; koyaushe mu kasance muna tsaye tare da hujjar Shari’a.
- A yau dole ne kowane Musulmi ya kasance a cikin sahun gaskiya, ba mai zaman kansa ba! A cikin sahu; yana halarta, yana yaƙi, yana faɗin gaskiya, yana bayar da kuɗin da yake da shi, yana sadaukar da abin da yake mallaka, yana kare Musulunci; domin ma’iyya ba za ta tabbata ba.
- Ma’iyya abu ce mai haɗari; domin idan azaba ta zo: {فَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا}... Wane suna ne yanzu, a zamaninmu, yake matsayin hujja? Wannan shi ne zai tsira, da waɗanda suke tare da shi; doka ɗaya ce! Wannan lamari ne mai haɗari, kuma dole mu kula da shi.
Kuma tabbas malamai da yawa suna ambaton wannan batu.
- A yau dole ne kowane Musulmi, kowane mumini ya kasance a cikin sahu ɗaya. Dukkanmu sahu ɗaya ne, da jagora ɗaya, waliyyi ɗaya, Imam ɗaya. Saboda haka malamai namu, kuma ina gaya wa matasa: maraji’ai sun yi ittifaqi, amma wasu daga cikin mabiyansu a wasu lokuta suna saɓawa kuma suna rarraba al’umma.
Duniyar Musulunci, ina magana ne gaba ɗaya; domin Allah ba Ya yarda da al’umma mai yawa da rarrabuwa, ba Ya yarda da ƙasa ta fuskar iyakokin ƙasa, ko jam’iyya, ko tafiya, ko ƙabilanci. Allah yana son al’umma ɗaya, ma’iyya ɗaya. Ka nemi hujja kuma ka kasance tare da shi, za ka tsira!
- Wannan shi ne abin da Alƙur’ani ya faɗa sarai. Waɗannan ba ayoyi ba ne na musamman ga Shu’aibu da Hud ba; da haka ne Alƙur’ani zai ƙare kuma ya gushe da mutuwar al’ummai da ƙabilu! Alƙur’ani yana raye har zuwa zamaninmu? Eh.
- Jarabawa ce mai wahala. Dole mutum ya kunna basira da lura sosai, kada ya rinjayu da yanayi da kafafen yaɗa labarai na Amurka masu son karkatarwa, masu son karkatarwa, Amurka uwar fasadi ce.
Saboda haka dole ne mu kasance tare da Manzon Allah da Ahlul Baiti a zamaninmu ta hanyar kasancewa tare da layin Manzon Allah. Ba a wadatu da motsin zuciya ba, ba a wadatu da imani “da shi” kawai ba; imani “tare da shi” da ci gabansa.
Ayatullah al-Uzma Sheikh Muhammad Ishaq al-Fayyad — Allah Ya jiƙan sa — yana cewa, kuma wannan magana ce mai muhimmanci da na karanta a Muharram, kuma idan Allah Ya ba ni lafiya da kuzari da dacewa zan sake maimaita ta: Wannan addininmu ne...
- Kamar yadda wilayar Manzon Allah da Imamai tsarkaka take daga Allah Ta’ala, wato wilayarsu daga Allah take, haka wilayar faqihi da ya cika sharuɗɗa a zamanin gaiba take; wilaya iri ɗaya ce daga Allah.
Allah ba Ya ba wanda ba ma’asumi ba wilaya, kuma bayan gaibar ma’asumi ba Ya bada wilaya ga wanda ba faqihi ba, marja’i, malami, mai tsoron Allah, mai tsantseni.
Wilayar faqihi ce, ba wilayar jahili ba ce. Ita ce alamar taƙawa, alamar tsantseni, alamar zuhudu, alamar sadaukarwa; ba son rai ba ne.
Wannan shi ne bambanci tsakanin tsarin dimokuraɗiyya da tsarin Musulunci; tsarin Musulunci tsarin Ali ne. Kuma a yau waliyyi faqihi shekaru da suka gabata yana ɗauke da ƙarfe a kan ‘ya’yansa da gidansa, kuma kun ga abin da ya biyo baya.
Saboda haka: {وَأَكْثَرُهُمْ لِلْحَقِّ كَارِهُونَ} — “Mafi yawansu masu ƙin gaskiya ne.” A kowane zamani masu gaskiya kaɗan ne; domin “tare da shi” abu ne mai wahala, amma “da shi” yana cikin hidimarka.
- Saboda haka Imam Husaini (aminci ya tabbata a gare shi) bai yarda da imani “da shi” kawai ba. Ya so imani “tare da shi”; mutum ya halarta. Wanda bai shiga tare da mu ba, ba zai riski nasara ba: “Duk wanda ya kasance mai bayar da ransa saboda mu, ya shirya kansa domin saduwa da Allah, to ya tafi tare da mu.” — “Tare da mu!”
- Domin idan ka bayar da kuɗi kawai, ko wanda ya ba da doki, kamar Ubaidullahi bn al-Hurr al-Ju’fi, ko wasu... wannan bai isa ba! Kasancewa tare da shi. Husaini yana son al’umma ta kasance mai imani “tare da shi”, ba wai mai imani “da shi” kawai ba.
- Wanda ya yi shiru bai shiga tare da Husaini ba, ko da yana son Husaini ko yana imani da shi, an la’ance shi! “Allah Ya la’anci al’ummar da ta ji wannan ta yarda da shi.” Akwai al’ummai, akwai mutanen da ba su shiga ba, ko da sun kasance masu imani, sai dai idan suna da uzuri na Shari’a, kamar mata da makamantansu; wannan wani bincike ne na daban, malamai ne suke tantance shi. A zahiri, wajibi ne a shiga tare da Imam Husaini; wadatuwa da imani da shi kawai bai isa ba.
- Alaƙar Musulmi, alaƙar muminai da Manzon Allah da layin Manzon Allah, alaƙar ma’iyya ce, ba kawai alaƙar imani da shi da ƙaunarsa ba. Saboda haka Alƙur’ani a nan ya gabatar da batun al’umma: {كُنتُمْ خَيْرَ أُمَّةٍ} — “Kun kasance mafificiyar al’umma.” Me ya sa al’umma? Domin ginshiƙi ɗaya ne, jagora ɗaya ne, Manzo ɗaya ne.
- Ina magana ne game da yanzu. Mu a yanzu, tun daga Adam har zuwa zamaninmu, a kowane lokaci akwai mutum ɗaya: jagora, hujja, Imam. Musa ya tafi: {اخْلُفْنِي فِي قَوْمِي} — “Ka maye gurbina cikin mutanena.” Annabi kuma a ƙarshen al’amari: {يَا أَيُّهَا الرَّسُولُ بَلِّغْ مَا أُنزِلَ إِلَيْكَ مِن رَّبِّكَ} — “Ya kai Manzo! Ka isar da abin da aka saukar maka daga Ubangijinka.” Game da me? Game da wanda yake mai iko, wanda yake jagora, ba wai ƙauna kawai ba. Haka da haka har zuwa zamaninmu.
- Dole ne ta fuskar hankali da Shari’a da waɗannan ayoyi, jagoranci ya kasance ɗaya ga dukkan al’ummar Musulmi ko ga dukkan bil’adama. Saboda haka malamai idan suna bayyana ma’anar mujtahidi da ya cika sharuɗɗa, kamar Ayatullah Mujaddid Sheikh Allama al-Muzaffar, Muhammad Rida al-Muzaffar, a cikin Aqa’idul Imamiyya, yana cewa: “Akidar mu game da mujtahidi da ya cika sharuɗɗa a zamanin gaiba ita ce cewa shi wakili ne... wakilin Imam ne a lokacin gaibarsa.”
- Wasu malamai suna cewa wannan wakilci ba na Musulmi ko ‘yan Shi’a kawai ba ne, a’a, na dukkan bil’adama ne; domin Imam shi ne jagoran bil’adama, Imamin bil’adama. Eh, wasu ba sa biyayya, wannan abu ne na dabi’a.
- Ma’anar al’umma ta samo asali ne daga ma’iyya ɗaya ga Imam ɗaya, Annabi ɗaya, jagora ɗaya, hujja ɗaya. Ba ya maimaituwa, ba ya ninkuwa. Wannan shi ne addini, wannan shi ne addinin Manzon Allah.
- A baya na kasance ina ambata a wasu darussa: mako guda kafin rasuwar Annabi (S.)... mako guda! Akwai ma’asumai biyar a Madina: Annabi (S.), Amirul-Mu’minin, Fatima az-Zahra, al-Hasan da al-Husaini; ma’asumai biyar. A wajenmu babu babba da ƙarami a cikin isma; duk ma’asumi ne.
- Amma jagora guda nawa ne? Ɗaya. Saboda haka idan wani dan ƙauye ya zo, misali, ya ga Amirul-Mu’minin, ya ce masa: “Ya Abal-Hasan, yanzu na Musulunta, yaya zan yi sallah?” Sai ya koya masa sallah, ba matsala; ya koya masa sallah, wannan al’amari ne na fatawa kamar yadda suke cewa.
- Idan ya ga Imam Hasan, ya ce masa: “Yaya zan yi alwala?” Sai ya koya masa alwala. Idan ya ga Imam Husaini, sai ya ce masa, misali: “Azumi, na ji cewa akwai azumi, yaya ake yin azumi?” Sai ya koya masa azumi.
- Amma idan wannan ba ƙauyen ya ce wa Amirul-Mu’minin: “Quraishawa sun zo da rundunarsu a ƙofar Madina, za mu yi yaƙi ko ba za mu yi ba?” Shin Amirul-Mu’minin zai amsa, ko kuwa ya ce masa: “Mu je mu ga Annabi”? Mu je mu ga Annabi; jagora ɗaya ne duk da kasancewar ma’asumai da yawa.
- Tabbas wannan ba ta kebanta ga waɗannan Annabawa uku ba ce. A fili yake. Wannan yana cikin zamanin Annabi da bayan Annabi; ba ta kebanta ga Manzanni da Annabawa, kuma ba ta kebanta ga Ahlul Baiti (aminci ya tabbata a gare su), a’a, wannan sunnah ce har zuwa tashin Alƙiyama.
Wace ce hujjar Shari’a? Kuma waɗanda suka yi imani tare da shi; waɗannan ne kawai suke tsira. Wannan abu ne mai haɗari ƙwarai, ƙwarai da gaske. Waɗannan ne kawai suke tsira a kowane zamani.
- Sanin hujja: Wane ne jagora? Waliyyi? A zamaninmu, marja’i? Waliyyi bisa ga...
Ba zan shiga cikin bayanai dalla-dalla ba, zan yi ishara da su daga baya. Haka kuma a Suratu Hud, aya ta 48, a labarin Nuhu (aminci ya tabbata a gare shi): {قِيلَ يَا نُوحُ اهْبِطْ بِسَلَامٍ مِنَّا وَبَرَكَاتٍ عَلَيْكَ وَعَلَىٰ أُمَمٍ مِمَّن مَّعَكَ} — “A ce: Ya Nuhu! Ka sauka da aminci daga gare Mu da albarka a kanka da kuma a kan al’ummomi daga waɗanda suke tare da kai.” Haka ma ma’iyya.
- Ɗan Nuhu, ɗan Annabi... ɗan Annabi bai tsira ba; domin bai zo tare da shi ba. Bai zo tare da shi ba, ya tafi ga halaka.
Haka kuma Allah Ta’ala yana cewa a Suratul Baƙara, wannan ma’iyya... Tabbas akwai ayoyi da yawa, na zaɓi wasu daga cikinsu: {حَتَّىٰ يَقُولَ الرَّسُولُ} — {أَمْ حَسِبْتُمْ أَن تَدْخُلُوا الْجَنَّةَ وَلَمَّا يَأْتِكُم مَّثَلُ الَّذِينَ خَلَوْا مِن قَبْلِكُم مَّسَّتْهُمُ الْبَأْسَاءُ وَالضَّرَّاءُ وَزُلْزِلُوا حَتَّىٰ يَقُولَ الرَّسُولُ وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ مَتَىٰ نَصْرُ اللَّهِ}.
- Tsira tana tare da Manzo, tare da hujja, tare da waliyyi. Babu wani wanda bai shiga jirgin waliyyi, ko Annabi, ko hujja, ko jagora a kowane zamani ba sannan ya tsira. Ba zai yiwu ba! Akwai nassoshi da yawa da suke magana a kan haka, kuma asali wannan aya tana magana ne game da ranar Alƙiyama.
- Abin da yake da matuƙar ban mamaki shi ne cewa Alƙur’ani bai ce: “آمن به” ba, alhali a harshen Larabci abin da ya dace shi ne a ce: “ya yi imani da shi.” Bai ce: “آمن به، والذين آمنوا به” ba, a’a, yana cewa: “والذين آمنوا معه” — “da waɗanda suka yi imani tare da shi!”
Wannan lamari ne mai ban mamaki.
- Wasu daga cikin mufassirai suna cewa, kuma wannan a bayyane yake: Ba za a iya wadatuwa da yin imani “da shi” kawai ba; dole ne imani ya kasance “tare da shi”; wato da shi kuma tare da shi! Ya shiga cikinsa, cikin rundunarsa, cikin layinsa, ya yi jihadi, ya kare hujjar Shari’a.
- Saboda haka ku kula: duk ayoyin suna cewa: “tare da shi, tare da shi, suka yi imani tare da shi”; babu “da shi”, babu “da shi”; duk suna magana ne game da imani... Ɗaya daga cikin manyan mufassirai yana cewa: Bai isa mutum ya yi imani da Annabawa kuma ya gaskata kiransu ba, a’a, dole ne ya kare su kuma ya basu kariya, wato ya kasance a cikin sahunsu.
- A kowane zamani: Musa, Shu’aibu, Hud, Lud, Salih, Annabin Musulunci, Amirul-Mu’minin, Imam Husaini, har zuwa zamaninmu kuma har zuwa tashin Alƙiyama. Saboda haka imani yana kasancewa tare da Annabi, tare da hujja, ba wai da shi kawai ba.
- Amma Alƙur’ani bai taɓa bayyana “imani tare da Allah” ba. Me yake cewa? “Imani da Allah.” Domin Allah, babu wanda yake cewa: “Ni ina tare da Allah.” Allah ba a ganinsa. Hujjarsa, halifarsa: {يَا دَاوُودُ إِنَّا جَعَلْنَاكَ خَلِيفَةً} — “Ya Dawuda! Lalle Mun sanya ka halifa.”
- A kowane lokaci akwai mutum ɗaya, kuma wajibi ne mu shiga sahunsa. Eh, imani da Allah. Dukkan ayoyi suna cewa: “imani da Allah, da...” Amma waɗannan ayoyi suna magana ne game da ma’iyya; wato ma’iyya ta zahiri, jiki yana nan, hankali yana nan, ƙarfi yana nan.
- Duk abin da mutum yake da shi na dukiya, ƙarfi, iko, ko wani abu... dukiya, ‘ya’ya, su kasance tare da hujja, tare da shi. Bai isa “da shi” ba. Ma’anarsa ita ce dole mutum ya kasance tare da hujjar Shari’a a kowane zamani da yake ciki.
- Matsalarmu ita ce: muna tare da Annabawa a tarihi, muna tare da Imamai a tarihi. Amma idan muka zo yanzu, sai mu wadatu da imani “da shi”; muna son shi. Shi wanene? Ko da mun san shi, galibi.
A kowane zamani dole ne mu nemi layin Manzon Allah, layin Annabawa, biyayyar Ahlul Baiti, wanda a zamaninmu yake cikin faqihi wanda ya cika sharuɗɗa da maraji’ai. Saboda haka, tsawon shekaru 1200 ‘yan Shi’a suna bin kuma suna kwaikwayon maraji’ai; wannan biyayya ce ga Manzon Allah. Domin bin maraji’ai ci gaba ne na haƙiƙa na biyayya ga Manzon Allah da layinsa na Ubangiji.
Daga wannan mahangar ne Alƙur’ani Mai Girma yake gabatar da wani muhimmin ra’ayi, wato ma’anar “al-ma’iyya” — kasancewa tare.
- Akwai ayoyi masu ban mamaki, ma’anoni masu ban mamaki a cikin Alƙur’ani game da “ma’iyya”! Wani lokaci yana cewa: “wa allazina ma’ahu” — waɗanda suke tare da shi, ko “tare da shi”.
Tabbas, biyayya ga Manzo ita ce ma’iyya tare da Manzo, kuma ci gabanta shi ne ma’iyya tare da Ahlul Baiti. Ma’iyya tare da Ahlul Baiti ci gabanta shi ne ma’iyya tare da wakilai huɗu ga wanda ya rayu a zamanin ƙaramar gaiba. Kuma ma’iyya tare da wakilai, Ahlul Baiti da Manzon Allah a zamaninmu ita ce kasancewa tare da fuqaha da maraji’ai.
Wannan ma’iyya tana da wahala. Wannan ci gaba ne, wannan shi ne ci gaba.
- Rahama da adalcin Allah suna bayyana wajen kiyaye wannan ci gaba na Ubangiji a cikin zamani daban-daban. Bayan Annabi (S.), akwai Amirul-Mu’minin, Al-Hasan, Al-Husaini da Imamai, har zuwa zamanin gaiba, inda aka kafa marja’iyya da fuqaha da suka cika sharuɗɗa a matsayin madadin da hanyar shiriya.
Saboda haka Alƙur’ani Mai Girma yana maimaita ma’anar “ma’iyya” da alaƙa da Annabawa da Manzanni. Maganar Alƙur’ani ba wani lamari ba ne na tarihi da ya ƙare, a’a, tana gudana kamar dare da rana, domin tabbatar da ci gaba da saƙon Allah, kamar yadda Allah Ya ce: {مُّحَمَّدٌ رَّسُولُ اللَّهِ ۚ وَالَّذِينَ مَعَهُ} — “Muhammad Manzon Allah ne, kuma waɗanda suke tare da shi.”
- {أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَمَاءُ بَيْنَهُمْ} — “Masu tsanani ne a kan kafirai, masu jinƙai ne a tsakaninsu.”
Ba Annabi kaɗai ba ne, har ma da waɗanda suke tare da shi!
Abin lura shi ne cewa bai raba siffofin ba; wato: {أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَمَاءُ بَيْنَهُمْ} — wannan ya shafi Annabi da waɗanda suke tare da shi. Wannan yana daga cikin al’amura masu wahala.
- A Suratu Hud, Alƙur’ani Mai Girma yana sake maimaita ma’iyya tare da Manzanni da dama, kuma yana tabbatar da cewa ceto, musamman ceto, Allah ne yake yi. Zan karanta ayoyin yanzu; yana magana da Annabi, yana cewa ceto ga Annabi ne, ga hujjar Shari’a, da waɗanda suka yi imani tare da shi. Ma’ana, waɗannan mabiyansa suna tsira ne ta hanyar binsa, ta hanyar ma’iyya, ba da kansu ba! Babu wani abu a addini da ake kira ‘yancin kai. Alƙur’ani yana tabbatar da ma’iyya, ba ‘yancin kai ba.
- A Suratu Hud, aya ta 58: Da farko Hud: {وَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا}. Akwai wata aya kuma: {جَعَلْنَا عَالِيَهَا سَافِلَهَا}. Ma’ana, lokacin da umarninmu ya zo, wato azaba, a duniya kafin lahira. Muna magana ne game da duniya kafin lahira. A duniya akwai azabobi da tasirinsu, kuma da yawa daga cikin wahalhalun jarabawarmu a duniyar Musulunci, a cikin al’ummar Musulunci, ciki har da watakila Iraki, sakamakon wasu azabobi ne. Mu ba ma’asumai ba ne, kuma al’ummai gaba ɗaya suna iya yin kuskure.
- A nan kuma: {وَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا} — “Sa’ad da umarninmu ya zo, Muka ceci...” Wa muka ceci? {هُودًا} — Hud; Annabi, jagora, hujja. {وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ بِرَحْمَةٍ مِنَّا} — “da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu.”
Tabbas wannan aya ta shafe mu; domin Alƙur’ani gaba ɗaya ya shafe mu. Wannan ba ta musamman ga Hud ba ce.
- Aya ta 66 kuma daga Suratu Hud: {فَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا صَالِحًا} — a nan Annabi Salih ne; {وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ بِرَحْمَةٍ مِنَّا} — “da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu.” Haka kuma a aya ta 94 daga Suratu Hud: {وَلَمَّا جَاءَ أَمْرُنَا نَجَّيْنَا شُعَيْبًا وَالَّذِينَ آمَنُوا مَعَهُ بِرَحْمَةٍ مِنَّا} — “Sa’ad da umarninmu ya zo, Muka ceci Shu’aibu da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu.”
WASU DAGA CIKIN JAWABIN SAYYID HASHIM aL-HAIDARI (H), A YAYIN BIKIN HAIHUWAR ANNABIN ALLAH (S):
- Bikin tunawa da haihuwar Manzon Allah (S), tare da abubuwan farin ciki da bukukuwan da suke tare da shi, ya kamata kuma ya zama an gabatar da wani cikakken rahoto ga Annabinmu, shugabanmu, mai cetonmu kuma jagoranmu; rahoton da zai bayyana ainihin matsayin imanimmu da ayyukanmu, da abin da muka gabatar wajen taimakon addininsa wanda shi ne addininmu, da kuma abin da muka cimma daga manyan manufofinsa.
- Shin Manzon Allah (S.) yana yarda da al’ummarsa alhali tana cikin rarrabuwa, ruɗani, dogaro ga wasu, rauni, gazawa, son duniya, yaɗuwar fasadi da lalata a wasu daga cikin al’ummarta a matsayin al’ummar Musulunci; luwadi, ƙwayoyi... Shin Manzon Allah yana yarda da al’ummarsa a haka?
Ina muke a matsayinmu na al’ummar Musulmi dangane da Musulunci? Ina muke a matsayinmu na al’ummar Manzon Allah dangane da Manzon Allah?
Allah Ta’ala yana cewa: {وَمَا أَرْسَلْنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا لِيُطَاعَ بِإِذْنِ اللَّهِ} — “Ba Mu aika wani Manzo ba face sai domin a yi masa biyayya da izinin Allah.”
Asalin samuwar Annabi shi ne a yi masa biyayya, domin biyayya. {وَمَا أَرْسَلْنَا} ya ƙunshi takaita; {وَمَا أَرْسَلْنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا لِيُطَاعَ بِإِذْنِ اللَّهِ}.
Shin mu al’umma ce mai biyayya ga Manzon Allah da addinin Allah a cikin hukunce-hukuncen Musulunci na mutum ɗaya, na zamantakewa, na siyasa, na tarbiyya, na iyali, na ƙabilanci da na al’umma?
- Biyayya ita ce ginshiƙin da ya zama dole na aiko Annabi (S.); Allah Ya aiko shi ne domin a yi masa biyayya, kuma manufar saƙon ta cika a cikinmu.
Cikar al’ummar Musulunci ba ta tabbata da kasancewa Musulmi a zahiri kawai ko ɗaga taken addini a fili ba; tana tabbata ne da cikakkiyar biyayya da aiwatar da hukunce-hukuncen Shari’a gaba ɗaya a kowane zamani da wuri. Kuma kamar yadda cikar al’umma take cikin mika wuya, haka faɗuwarta take cikin saɓo. Daga nan ne muhimmancin addu’ar: “Ya Allah, Ka azurta mu da ikon yin biyayya, Ka nisantar da mu daga saɓo.”
- A cikin Suratush-Shu’ara an maimaita aya mai albarka: {إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ * فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ} a kan harshen Annabawa biyar (Nuhu, Hud, Salih, Luɗ da Shu’aibu – aminci ya tabbata a gare su), domin ta bayyana cewa tsoron Allah da biyayya su ne jigon saƙonnin dukkan Annabawa.
Addini ba zaɓen wasu hukunce-hukunce ba ne bisa son rai da sha’awa; a’a, mika wuya ne gaba ɗaya. Allah bai halicci mutum ba face domin ya bi shiriyarsa. Amma dukiya, abubuwan more rayuwa da duniya gaba ɗaya ba su da wata daraja sai idan an yi amfani da su a hanyar lahira da addini, domin a tabbatar da asalin umarnin Allah: {فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ}.
- Allah Ya halicci bayi domin biyayya da bin hanya zuwa ga kamala: {إِلَّا لِيَعْبُدُونِ}. Babu ibada kuma babu taƙawa ba tare da bin Manzon Allah (S.) ba; domin shi ne yake tsara taswirar hanyar tafiya, kuma shi ne yake isar da Shari’a.
Biyayyar al’umma ga Annabi tana matsayin sake tayar da ita; kamar yadda Allah Ya aiko Manzo, haka al’umma take tashi daga gafalarta, kuma take tabbatar da ɗan Adamcinta ta hanyar mika wuya gare shi. Daga nan ne shiriya take cikin cikakkiyar biyayya kamar yadda Alƙur’ani Mai Girma ya tabbatar: {وَإِن تُطِيعُوهُ تَهْتَدُوا ۚ وَمَا عَلَى الرَّسُولِ إِلَّا الْبَلَاغُ الْمُبِينُ} — “Idan kun yi masa biyayya, za ku shiryu. Kuma babu abin da ke kan Manzo face isar da saƙo bayyananne.”
- Biyayya ga Manzon Allah (S.) ita ce ainihin biyayya ga Allah Ta’ala: {مَّن يُطِعِ الرَّسُولَ فَقَدْ أَطَاعَ اللَّهَ} — “Duk wanda ya yi biyayya ga Manzo, to, haƙiƙa ya yi biyayya ga Allah.”
Kuma tana ƙara tabbatar da ci gaba zuwa ga Ahlul Baiti tsarkaka: {يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَطِيعُوا اللَّهَ وَأَطِيعُوا الرَّسُولَ وَأُولِي الْأَمْرِ مِنكُمْ}.
Kada mu rayu da wannan nassi kamar wani abu da ya faru a tarihin baya kawai; wannan biyayya tana ci gaba a zamanin gaiba ta hanyar komawa ga fuqaha da maraji’ai waɗanda suka cika sharuɗɗa.
TAMKAR GANGAR JIKI NE BA RUHI.....!!!
Jiya Alhamis, 27/8/2026, Ayatollah Abbas al-Ka'aby (H) a ofishin Wakilin Imam Khamenei a Iraq, a Karbala, ya gabatar da jawabi mai muhimmanci yayin da yake isar da sakon Imamul Qa'id Mujtaba Khamenei (D.z) na godiya ga al-Ummar Iraqi bisa halascin da suka nuna wajen raka gangar jikin Imamush Shaheed Khamenei (Q.).
Da yake magana akan muhimmancin Jagorancin Malami nagari a cikin ƙasa da al-Ummah, ya ce: "Usuluddeen da Furu'uddeen baki dayan su idan babu Jagoranci na gari, to tamkar gangar jiki ne, ba Ruhi. Da Jagoranci ne nagari karkashin tsarin Allah ne suke samun ma'ana kuma tasirinsu ke bayyana."
A yayin da yake magana kan zaɓen Sayyid Mujtaba Khamenei (Q.d), kuma ya ce: "Ku samu natsuwa, Sayyid Mujtaba Khamenei a zaɓinsa da aka yi, lalle akwai tagomashin Allah (T) a ciki da tagomashin Imam Sahibul Asri Wazzaman (A.S.)."
Ya ce: "Na farko, mu sani shi Mujtahidi Mudlaq ne, Mujtahidai, manyan malamai masana an kai musu rubutattun darussansa akan Dahara da darasi a Ta'arudul Adillah da ya gabatar, sun ce ba wai ya iya istinbadi da sanin makama ba a'a, yana da gogewa matuka a sha'anin Ijtihadi. Sannan ya shekara 20 yana bada Bahsul Kharij a gaban dalibai sama da 700."
Ya ce suna cikin dakin taron zaɓen Waliyul Faqih, ɗan Ayatollah Sheikh Makarimush Shirazy ya kira, ya ce a gaya masa ya wakilce shi a bayyana ra'ayinsa akan shi, yana goyon bayan zaɓen Sayyid Mujtaba. Haka shi ma Ayatollah Ja'afar Subuhany aka kira da sauransu, duk kansu akansa suke ishara, anan ne fa zukata suka karkata akansa.
Ya ce kamar kada a zaɓi Sayyid Mujtaba matsayin Waliyul Faqih sai ya zama hasken Walaya na bayyana a cikinsa da ayyukansa, kamar dai Mahaifinsa. Ya ce Sheikh Misbahu Yazdy ya ce: "Mun san Sayyid Imamush Shaheed Khamenei tsawon shekaru tun kafin a zaɓe shi, amma nan take hasken Walaya ya bayyana a shi da ayyukansa, ya kasance misdaqin wannan ayar:
«وَاصْطَنَعْتُكَ لِنَفْسِي»
To haka Imam Mujtaba Khamenei ya kasance."
Ya ce: "Ikonsa a tafiyarwa a fannin Soji da Tattalin Arziki ba ƙarami bane. Yace ina baku tabbaci, idan dama ta buɗe gaban Imam Mujtaba Khamenei, to zai canza lissafin Iran da ma Gabas ta Tsakiya baki ɗaya."
Ya ce yana isar da addu'a da godiya da sallamar Imam Mujtaba Khamenei zuwa ga mahalarta rakiyar Gangar Jikin Imamush Shaheed Khamenei a Iraq 🇮🇶.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
Amma wanda aka tabbatar cewa mahaifinsa Annabi ne, kamar Annabi Yusuf (A.S.) da sauran annabawa, to wannan yana buƙatar a yi la’akari da batun isma ta musamman da ya shafi annabawa.
Dangane da Abdul-Muɗɗalib da Abu Ɗalib.
An haifi Annabi (S) kuma ya girma a cikin zuri'a mai tauhidi da ɗaukakar ɗabi’u/halaye.
Ana iya ganin imanin kakansa Abdul-Muɗɗalib daga halayensa da addu’arsa lokacin da Abraha al-Habashi ya kai hari domin rusa Ka’aba; bai nemi taimakon gumaka ba, sai dai ya dogara ga Allah wajen kare Gidansa.[29]
Haka nan akwai abubuwan da suke nuna cewa Abdul-Muɗɗalib ya san wani abu game da matsayin Annabi (S) da makomarsa da ta shafi sama. Daga cikin hakan akwai neman ruwan sama da Annabi (S) tun yana jariri, saboda abin da ya sani game da matsayinsa a wurin Allah Mai arziki da azurtawa.[30]
Haka nan ya yi wa Ummu Ayman gargadi kada ta yi sakaci da shi tun yana ƙarami.[31]
Amma baffansa Abu Ɗalib ya ci gaba da kula da Annabi (S), ya kare shi, ya tallafa masa wajen isar da saƙon Allah da bayyana shi har zuwa ƙarshen rayuwarsa mai albarka, ya jurewa cutarwar Quraysh, kaurace musu da kuma killace shi a Shi’b.
An kuma ruwaito daga Abu Ɗalib (A.S.) abubuwa masu yawa da suke nuna tsananin kulawarsa da kare rayuwar Annabi (S).[32]
Saboda haka, ba daidai ba ne yaɗa magana cewa “iyayen Annabi (S) suna cikin wuta” domin hanya ta Ahlul baity da suke abokan tafiyar al-Qur'ani akwai hujjoji daga hankali, Alƙur’ani, hadisai da ijma’i da suke nuna tsarkin iyayen Annabi (S) daga shirka da kafurci, da kuma tsarkin nasabarsa daga zina.
Kuma wannan ba batu ne na kare wani mutum kawai ba daga tsatson; batu ne da yake da alaƙa da girmama matsayin Annabci da fahimtar hikimar Allah wajen zaɓar Manzonsa.
Allah bai bar wata kafa ta zargi a kan Manzonsa (S) ba. Ya tsarkake asalinsa, ya tsarkake tsatsonsa, ya tsarkake mahaifansa, kuma Ya ɗaukaka shi daga mafi kyawun tsatso zuwa mafi kyawun matsayi.
﴿اللَّهُ أَعْلَمُ حَيْثُ يَجْعَلُ رِسَالَتَهُ﴾
“Allah ne Mafi sani a inda Ya sanya saƙonsa.”
Allah Ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa Muhammad (S.) da Ahlulbaitinsa (A.S.), Ya sanya mu cikin masu riƙo da koyarwarsu da girmama matsayinsu.
Alhamdu lillahi Rabbil Alamin.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
Madogara:
[8] Ash-Shari’a, juzu’i na 3, shafi na 1417.
[9] Qutul-Qulub, juzu’i na 2, shafi na 145.
[10] A’lamun-Nubuwwa, shafi na 201.
[11] Majma’al-Bayan, juzu’i na 7, shafi na 357.
[12] Mutashabihul-Qur’an wa Mukhtalifuh, juzu’i na 2, shafi na 21.
[13] Ta’wilul-Ayat, juzu’i na 1, shafi na 396.
[14] Biharul-Anwar, juzu’i na 25, shafi na 17 da abin da ya biyo baya.
[15] Al-Khisal, shafi na 548.
[16] Kifayatul-Athar, shafi na 70.
[17] At-Tibyan, juzu’i na 4, shafi na 175.
[18] al-Ãmali, shafi na 183.
[19] Rawdatul-Wa’izin, shafi na 139.
[20] ad-Durrun-Nazim, shafi na 26.
[21] Iman Abi Talib, shafi na 57.
[22] Mir’atul-Uqul, juzu’i na 26, shafi na 549.
[23] Al-I’tiqadat, shafi na 354.
[24] Awa’ilul-Maqalat, shafi na 45.
[25] At-Tibyan, juzu’i na 4, shafi na 175.
[26] Biharul-Anwar, juzu’i na 12, shafi na 49.
[27] Awa’ilul-Maqalat, shafi na 45.
[28] Haqqul-Yaqin, shafi na 144.
[29] As-Siratun-Nabawiyya, juzu’i na 1, shafi na 33; Tarikhud-Dabari, juzu’i na 1, shafi na 553; Al-Kamil fit-Tarikh, juzu’i na 1, shafi na 444.
[30] As-Sira al-Halabiyya, juzu’i na 1, shafi na 189; Al-Milal wan-Nihal na ash-Shahrastani, juzu’i na 2, shafi na 240.
[31] Ad-dabaqatul-Kubra, juzu’i na 1, shafi na 118; Tarikh Madinat Dimashq, juzu’i na 3, shafi na 85; Al-Bidaya wan-Nihaya, juzu’i na 2, shafi na 343; As-Sira an-Nabawiyya, juzu’i na 1, shafi na 240.
[32] Usdul-Ghaba, juzu’i na 1, shafi na 19; Tarikhulmd-Dabari, juzu’i na 2, shafi na 64; Al-Bidaya wan-Nihaya, juzu’i na 3, shafi na 63; As-Sira an-Nabawiyya na Ibn Kathir, juzu’i na 1, shafi na 473.
5. al-Fattal an-Naysaburi ya ruwaito daga Annabi (S): “Babu lokacin da iyaye biyu nawa suka haɗu ta zina. Allah Ya ci gaba da mayar da ni daga tsatso masu kyau zuwa mahaifu masu tsarki, ina mai shiryarwa kuma ana shiryar da ni, har Allah Ya ɗora mini amanar Annabci.”[19]
6. Yusuf bn Hatim ash-Shami ya ruwaito daga Ali (A.S.) cewa Annabi (S) ya ce: “Na fito ne daga aure, ban fito daga zina ba, tun daga Adam har zuwa lokacin da mahaifina da mahaifiyata suka haife ni; babu wani abu daga zina ta jahiliyya da ya same ni.”[20]
7. Sayyid Fakhar bn Ma’ad al-Musawi ya ruwaito daga Annabi (S): “Allah Ya ci gaba da mayar da ni daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki har Ya fitar da ni zuwa wannan duniyarku.”[21]
Allamah Majlisi ya ce: “Ina cewa: Hadisan da suke nuna Musuluncin iyayen Annabi (S) daga hanyoyin Shi’a suna da yawa sosai, har ma sun kai matsayin tawatur.”[22]
Dalilin Ijma’in Imamiyya.
Sheikh Saduq ya ce: “Imaninmu game da iyayen Annabi shi ne cewa su Musulmai ne daga Adam har zuwa mahaifinsa Abdullah, kuma Abu Ɗalib Musulmi ne, mahaifiyarsa Aminah bint Wahb kuma Musulma ce. Annabi (S) ya ce: ‘Na fito daga aure, ban fito daga zina ba, tun daga Adam.’ An kuma ruwaito cewa Abdul-Muɗɗalib ya kasance hujja, kuma Abu Ɗalib ya kasance wasiyyinsa.”[23]
Sheikh Mufid ya ce: “Imamiyya sun yi ittifaqi cewa iyayen Manzon Allah (S), daga Adam har zuwa Abdullah bn Abdul-Muɗɗalib, muminai ne ga Allah, masu tauhidi ne gare Shi. Sun kafa hujja da Alƙur’ani da hadisai.”[24]
Sheikh Abu Ja’afar aɗ-Ɗusi ya ce: “Abin da az-Zajjaj ya faɗa yana ƙarfafa abin da malamanmu suka ce: cewa Aazar ya kasance kakan Ibrahim ne ta bangaren mahaifiyarsa ko kuma baffansa; domin ya tabbata a wajenmu cewa iyayen Annabi (S) har zuwa Adam dukkaninsu masu tauhidi ne, babu wani kafiri a cikinsu. Hujjarsu ita ce ijma’in ɗa'ifar gaskiya, kuma babu saɓani a tsakaninsu a wannan mas’ala.”[25]
Allamah Majlisi ya ce: “Imamiyya sun yi ittifaqi cewa iyayen Manzon Allah (S) da dukkan kakanninsa har zuwa Adam (A.S.) Musulmai ne; har ma sun kasance daga cikin siddiqai: ko dai annabawa ne manzanni, ko kuma wasiyyai ma’asumai. Wataƙila wasu daga cikinsu ba su bayyana Musuluncinsu ba saboda taqiyya ko wata maslahar addini.”[26]
Haka kuma Sheikh Mufid ya ce: “Imamiyya sun yi ittifaqi cewa iyayen Manzon Allah (S) daga Adam har zuwa Abdullah bn Abdul-Muɗɗalib muminai ne ga Allah, masu tauhidi gare Shi. Sun kafa hujja da Alƙur’ani da hadisai. ... Kuma sun yi ijma’i cewa baffansa Abu Dalib (A.s) ya mutu yana mumini, kuma Aminah bint Wahb tana kan tauhidi, kuma za a tashe ta tare da muminai.”[27]
Shin wannan tsarki yana nufin rashin aikata kowane irin zunubi?
A nan ya kamata a fahimci ma’anar “tsarkin tsatso” daidai.
Mabiya Ahlulbaiti (A.S.) sun yi imani cewa iyayen annabawa da hujjojin Allah (A.S.) tsarkaka ne daga shirka da kafurci, haka nan tsarkaka ne ta fuskar nasaba; sun fito daga tsatso masu tsarki da mahaifu masu tsarki, kodayake wasu malamai sun yi nazari a kan ko wannan hukunci ya shafi dukkan annabawa ko Annabinmu Muhammad (S) ne kawai.
Sayyid Abdullah Shubbar ya ce: “Abin da ya shahara a wajen Imamiyya, har ma aka kawo ijma’i a kai, shi ne wajabcin tsarkake annabawa daga kafurcin iyaye da alfasharsu, domin kada a zarge su ko a kushe su da hakan, kuma kada mutane su nisance su; domin a al’ada, aibin da yake cikin iyaye yana komawa ga ’ya’ya... Amma a ganina akwai nazari a wannan, domin babu hujjar hankali tabbatacciya da ta wajabta hakan, kuma hujjar nakali ta inganta ne game da iyayen Annabi (S) kawai, ba sauran annabawa ba... Don haka tsayawa a nan shi ne mafi dacewa.”[28]
A bisa wannan, abin da ake nufi da tsarkin da ake magana a nan shi ne tsarki daga shirka da kufurci, ba lallai ba ne a ce dukkan kakannin annabawa sun kasance ma’asumai daga kowane irin kuskure da zunubi ba.
Saboda haka, idan aka ce wasu daga cikin kakannin annabawan Bani Isra’ila, kamar Yahuda da ’yan’uwansa, sun aikata kuskure ko zunubi, wannan ba ya saɓa wa ma’anar “tsatso mai tsarki”, domin ba a sharɗanta cewa dukkan iyayen annabawa su kasance ma’asumai daga kuskure ba.
NASABAR ANNABI (S): WANNAN ITACE MATSAYAR MABIYA MAKARANTAR AHLULBAITI (A.S.) GAME DA NASABAR ANNABI MUHAMMAD (S.) MAI GIRMA.
No (2).
Dalili na Alƙur’ani.
Daga cikin dalilan da suke nuna tsarkin iyayen Annabi (S) akwai faɗin Allah Maɗaukaki a cikin Suratul Shu’ara:
﴿الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُ * وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
“Wanda Yake ganin ka lokacin da kake tsayuwa, da jujjuyawarka a cikin masu sujada.” (Shu’ara: 218–219)
Malaman tafsiri da dama sun fahimci wannan aya da cewa tana nuni da tsarkin iyayen Annabi (S), daga Adam (A.S.) har zuwa mahaifinsa Abdullah.
1. al-Ajuri ya ce a tafsirin ayar: “Allah Ya ɗaukaka matsayin Annabinmu, Ya tsare shi daga auren jahiliyya, Ya riƙa mayar da shi cikin tsatson masu tsarki ta hanyar aure ingantacce tun daga Adam, ta hanyar sanya shi cikin tsatson annabawa da ’ya’yan annabawa, har Ya fitar da shi ta hanyar aure ingantacce.”[8]
2. Abu Ɗalib al-Makki ya ce:
“A cikin tafsiri: jujjuyawarka a cikin tsatson masu tsarki da mahaifu masu tsarki; babu wani lokaci da zina ta same ka. Haka aka ruwaito daga Annabi (S).”[9]
3. Al-Mawardi ya ce: “Amma game da tsarkin haihuwarsa, Allah Ya zaɓi Manzonsa daga mafi kyawun aure, Ya kare shi daga ƙazantar alfasha, Ya riƙa mayar da shi daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki. Ibn Abbas ya ce a cikin fassarar faɗin Allah: ﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾, wato: jujjuyawarka daga tsatso masu tsarki, daga uba zuwa uba, har Allah Ya sanya ka Annabi.”[10]
4. Sheikh aɗ-Ɗabarsi ya ce: “An ce ma’anarsa ita ce: jujjuyawarka a cikin tsatson masu tauhidi, daga annabi zuwa annabi, har Ya fitar da kai Annabi; daga Ibn Abbas, a wata ruwaya daga Aɗa’u da Ikrimah, kuma shi ne abin da aka ruwaito daga Abu Ja’afar da Abu Abdillah (A.S.): ‘A cikin tsatson annabawa, annabi bayan annabi, har Ya fitar da shi daga tsatson mahaifinsa, ta hanyar aure ba zina ba, tun daga Adam.’”[11]
5. Ibn Shahr Ashub ya ce: “A cikin ayar akwai dalili cewa iyayensa (A.S.) sun kasance Musulmai har zuwa Adam, kuma babu wani daga cikinsu da ya bauta wa wanin Allah. Da a ce ana nufin masu sujada ga gumaka, da ba a yi masa wannan ni’ima ba, domin yin wa mutum ni’ima ta hanyar kafurci abu ne mummuna.”[12]
6. Sayyid Sharafud-Din al-Istarabadi ya ruwaito daga Abu Ja’afar (A.S.) game da ayar:
﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
ya ce: “Yana ganin jujjuyawarsa a cikin tsatson annabawa, daga annabi zuwa annabi, har Ya fitar da shi daga tsatson mahaifinsa ta hanyar aure ba zina ba, tun daga Adam.”[13]
7. Allamah Majlisi ya ruwaito daga Imam al-Baqir (A.S.) cewa hasken Annabi (S) ya ci gaba da wucewa daga tsatso zuwa tsatso da mahaifa zuwa mahaifa, har ya kai ga Abdul-Muɗɗalib, inda ya rabu zuwa sassa biyu: wani sashe ya shiga Abdullah, wani sashe kuma ya shiga Abu Ɗalib. Wannan shi ne ma’anar:
﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
wato, a cikin tsatson annabawa da mahaifar matansu.[14]
Dalilin hadisai.
1. Sheikh as-Saduq ya ruwaito cewa Imam Ali (A.S.) ya ce: “Na rantse da Allah, kai ne wanda Allah ya tsarkake shi daga zina daga Adam har zuwa mahaifinka, da cewa: Ni da kai mun fito ne daga aure ba zina ba, daga Adam har zuwa Abdul-Muɗɗalib.”[15]
2. Al-Khazzaz al-Qummi ya ruwaito daga Anas bn Malik cewa Annabi (S) ya ce: “Allah Ya halicce ni ni da Ahlulbaitina daga haske guda kafin Ya halicci Adam da shekaru dubu bakwai. Sa’an nan Ya mayar da mu zuwa cikin tsatson Adam, sannan Ya ci gaba da mayar da mu daga tsatson masu tsarki zuwa mahaifai masu tsarki.”[16]
3. Sheikh aɗ-Ɗusi ya ruwaito daga Annabi (S): “Allah Ya riƙa mayar da ni daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki, bai gurɓata ni da ƙazantar jahiliyya ba.”
Ya ce: “Wannan hadisi ne da babu saɓani a ingancinsa.”[17]
4. Ya kuma ruwaito daga Annabi (S): “Ni da Ali mun kasance a gefen dama na Al’arshi muna tasbihi ga Allah shekaru dubu biyu kafin Ya halicci Adam. Lokacin da Ya halicci Adam, Ya sanya mu cikin tsatsonsa, sannan Ya ci gaba da mayar da mu daga tsatso zuwa tsatso a cikin tsatso masu tsarki da mahaifu masu tsarki, har muka kai ga tsatson Abdul-Muɗɗalib.”[18]
Wannan kuwa zai raunana tasirin da’awa a zukatan mutane, kuma ya saɓawa manufar da aka aiko Annabi domin ita, wato shiryar da mutane cikin mafi cikar hanya da bayani.
Saboda haka, hankali mai inganci yana hukunci da wajabcin tsarkake jerin nasabar Annabi daga shirka, kafurci da zina, domin kare matsayin Annabci daga abin zargi, da kuma kare manufar aiko Manzo daga duk abin da zai saɓa mata.
Saboda haka, cewa iyayen Annabi da kakanninsa (A.S.) tsarkaka ne shi ne abin da hikimar Allah take buƙata kuma ta hukumta, kuma hankali lafiyayye yana taimakawa wurin tabbatar da hakan, domin kare matsayin Annabci da tabbatar da babbar manufar saƙon Allah: shiryar da halittu zuwa tauhidin Allah Maɗaukaki.
Abul-Futuh ar-Razi ya ce:
“Amma abin da suka ce: An tabbatar cewa iyayen Annabi (S) har zuwa Adam dukkaninsu muminai ne, to wannan yana da hujjar hankali... domin an sani cewa akasin haka zai sa mutane su nisance su, ya karkatar da mutane daga amsa kiransu, karɓar maganarsu da bin umarninsu. Da sun kira kafirai zuwa Musulunci, kafirai su ce musu: Wannan aibin yana cikinku, a cikin nasabarku da iyayenku. Na biyu kuma: Allah Ya siffanta mushrikai da ƙazanta, kuma wanda Allah Ya aiko domin tsarkake ƙazanta bai dace a haife shi daga ƙazanta ba.”[7]
Saboda haka, Allah Maɗaukaki bai bar wata kafa ta zargi ko hujjar kamawa da za a yi amfani da ita wajen ƙalubalantar Manzonsa (S) ba, domin hikimarsa ta tanadi cewa Manzon da aka aiko domin ya kira mutane zuwa tauhidi ya kasance daga tsatson masu tauhidi, cikin aure na halal, ba daga zina ko shirka ba.
Masadir:
[1] Manaqib Al Abi Dalib, Ibn Shahr Ashub, juzu’i na 1, shafi na 134.
[2] Muntahal-Amal, Sheikh Abbas al-Qummi, juzu’i na 1, shafi na 9.
[3] Kanzul-Fawa’id, Abul-Fath al-Karajki, shafi na 170.
[4] Nahjul-Balagha, Khudbar Imam Ali (A.S.), juzu’i na 2, shafi na 195.
[5] Tafsir Majma’ al-Bayan, Sheikh aɗ-Ɗabarsi, juzu’i na 7, shafi na 358.
[6] Muntahal-Amal, Sheikh Abbas al-Qummi.
[7] Rawdul-Jinan, juzu’i na 7, shafi na 340–341
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
NASABAR ANNABI (S): WANNAN ITACE MATSAYAR MABIYA MAKARANTAR AHLULBAITI (A.S.) GAME DA NASABAR ANNABI MUHAMMAD (S.) MAI GIRMA.
No (1).
Annabi Muhammad (S.) ya kasance ɗane ga wata zuri'a da suka kasance a kan tauhidi, tare da maɗaukakan ɗabi’u, matsayi da daraja.
Shi ne Abul-Qasim Muhammad (S.), ɗan Abdullah ɗan Abdul-Muɗɗalib ɗan Hashim ɗan Abd Manaf ɗan Qusayy ɗan Kilab ɗan Murrah ɗan Ka’ab ɗan Lu’ayy ɗan Galib ɗan Fihr ɗan Malik ɗan an-Nadr ɗan Kinanah ɗan Khuzaymah ɗan Mudrikah ɗan Ilyas ɗan Mudar ɗan Nizar ɗan Ma’ad ɗan Adnan.
An ruwaito daga Annabi (S) cewa:
“Idan nasabata ta kai ga Adnan, to ku tsaya.”[1]
Allamah Majlisi (R.) ya ce:
“Ka sani cewa ijma’in malaman Imamiyya ya tabbata a kan cewa mahaifin Manzon Allah (S), mahaifiyarsa, da dukkan kakanninsa maza da mata har zuwa Adam (A.S.), dukkaninsu Musulmai ne, kuma haskensa (S) bai zauna a cikin tsatson ko mahaifar mushrikai ba. Babu wani shakku a cikin nasabarsa (S), da nasabar kakanninsa maza da mata, kuma hadisai masu yawa daga bangaren Shi’a da Ahlus-Sunnah suna nuna waɗannan ma’anoni.”[2]
Saboda haka, Annabi (S) tsarkakke ne daga ƙazantar iyaye da alfashar mata; domin babu cikin kakanninsa maza da mata da ya taba kusantar zina ko fasikanci. Wannan shi ne abin da Musulmai nagari suka yi ittifaqi a kai, kuma Manzon Allah (S) ya bayyana hakan a cikin hadisai da aka ruwaito daga bangaren Sunni da Shi’a. Ya ce:
“An riƙa ɗauka ta daga tsatso masu tsarki zuwa mahaifu masu tsarki, ta hanyar aure ba zina ba.”[3]
Imam Ali (A.S.) ya ce:
“Ina shaida cewa Muhammad bawansa ne (Allah) kuma Manzonsa ne, kuma shugaban bayinsa. A duk lokacin da Allah Ya raba halittu gida biyu, Ya kan sanya shi a cikin mafi alherin bangarorin biyu ne. Babu mazinaci da ya shiga cikin asalinsa, kuma babu fasiki da ya shiga cikin tsatsonsa.”[4]
Haka nan Imam as-Sadiq (A.S.) ya bayyana ma’anar ayar Allah:
﴿وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ﴾
da cewa:
“A cikin tsatson annabawa, annabi bayan annabi, har Allah Ya fitar da shi daga tsatson mahaifinsa ta hanyar aure ba zina ba, tun daga Adam.”[5]
Allamah Majlisi ya ƙara da cewa:
“A’a, hadisai masu yawa suna bayyana cewa kakanninsa (S) dukkaninsu annabawa ne da wasiyyai kuma maɗauka shari’ar Allah. ’Ya’yan Isma’il (A.S.) ne waɗanda su ne kakanninsa (S) sun kasance wasiyyai na Ibrahim (A.S.), shugabannin Makka kuma masu kula da Ka’aba. Gyara da raya Ka’aba an damƙa musu, kuma sun kasance mafaka ga halittu gaba ɗaya. A cikinsu akwai addinin Ibrahim, kuma su ne masu kiyaye wannan shari’a; ɗaya yana wasilci da ita ga ɗaya, kamar yadda ɗaya yake ajiyewa ɗayan kayan gado na annabawa, har suka kai ga Abdul-Muɗɗalib, wanda ya sanya Abu ɗalib ya zama wasiyyinsa. Abu ɗalib kuwa ya miƙa kayan gado na annabawa da amana ga mai kiyaye saƙon Allah (S).”[6]
Don haka, Annabi (S.) ɗane na zuriya mafi daraja a cikin Larabawa ne, magajin mafi ɗaukakar zuri'a wadda ta mallaki girma, daraja, ƙarfi da matsayi wanda wasu ba su kai gare shi ba.
Dalili na hankali kan tsarkin iyayen Annabi (S).
Babu shakka a cikin Aqidar mabiya Makarantar Ahlulbaiti (A.S.) cewa iyayen Annabi mai girma (S) tsarkaka ne daga shirka, kufurci da duk abin da ya saɓa wa imani, haka nan mahaifa da kakannin da hasken Annabi (S) ya ratsa cikinsu sun kasance tsarkaka.
To daga cikin dalilan hakan akwai dalilin hankali kamar haks.
In mukayi nazarin manufar aiko Annabi (S) ita ce shiryar da mutane zuwa tauhidi, kafa hujja a kansu, da kawar da shubuhohi da za a iya gabatarwa a kan da’awar Musulunci da abin ya shafeta duka.
Abu ne sananne cewa daga cikin muhimman abubuwan da suke taimakawa nasarar da’awar mai kira akwai cikar halayensa, lafiyar matsayinsa a cikin al’umma, da rashin wani abu da za a yi amfani da shi wajen kushe shi ko saƙonsa.
Da ace _ Allah Ya kiyaye_iyayen Annabi ko kakanninsa sun kasance mushrikai ko mazinata, wannan da ya zama abin da masu adawa za su yi amfani da shi wajen zagi da suka. Da za su iya cewa:
“Ta yaya yake kiran mutane zuwa tauhidi alhali irin wannan ne yanayin iyayensa da kakanninsa?”
Idan ba mu iya kare matsayar Marja’iyyarmu da dalili da ilimi ba, kada mu mayar da rauni wajen bayanin hujja zuwa hanyar kushe da bata sauran malamai.
Muqallidi na gaskiya ba shine wanda yake cewa: “Marja’ina ne kawai yake daidai ba, sauran duk suna kan ɓata”. Muqallid na gaskiya shi ne wanda ya san darajar Marja’iyyarsa, ya fahimci cewa hukuncin Mujtahidi yana da tsarin ilimi da dalilai a bayansa, kuma ya san yadda zai kare fahimtarsa ba tare da ya wulakanta sauran malamai ba.
Mu shagaltu da sauke wazifofin da Allah ya rataya mana, shine tafarkin tsira.
Allah mana afuwa da muda Malamanmu, iyaye, iyalai, makusanta, abokai ya suturtamu baki daya.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
Sau da yawa abin da ke cutar da mu, Muqallidai, har ma ya kai ga cutar da Jihar da muke komawa gare ta, shi ne i‘tiqadinmu cewa: fahimtar Marja’iyyarmu ita ce kaɗai daidai; bayan fahimtarta kuma duk sauran fahimtoci kuskure ne. Sai kuma mu kasa bayanin fahimtar Marja’iyyarmu sai mun kushe wata fahimta, mun soke ta, ko mun bata ta. Lallai wannan hali ne da son rai ke jagoranta ga wanda ya sani, da rashin sani ke jagoranta ga wanda bai sani ba.
Mu sani cewa Mujtahidi wanda ya cika sharuddan ijtihadi, idan ya fitar da hukunci a kowace mas’ala, yana yin hakan ne bisa sanannun ƙa’idojin ilimi da suke hannun kowane Mujtahidi. Ba wai Marja’in yana da wata ƙa’ida tasa ta daban, boyayya ga sauran Mujtahidai ba ne. Abin da ke faruwa shi ne: dalilin da wannan Marja’i ya dora hannu a kansa, shi ma wani Marja’in zai iya dora hannu a kansa; sai dai kowannensu ya iya samun fahimta daban game da nassi ko ƙa’idar da ya dogara da ita.
Wannan fahimta kuwa tana kasancewa ne bisa doron ilimi da ƙa’idojin ilimi, ba bisa son rai ba. Sauran Mujtahidai da kansu suna fahimtar cewa wannan fahimtar ta ginu ne bisa dalilai da ƙa’idojin ilimi. Haka nan, da zarar aka ji hukunci ko matsayar wani Mujtahidi a kan wata mas’ala, sauran Mujtahidai da ma’abota ƙwarewa a ilimi suna iya gane ta inda ya bi da kuma yadda ya kai ga wannan natija.
Saboda haka, kada ka ɗauka cewa Marja’i ya bar wata matsaya ne saboda son zuciya, ko kuma ya riƙi wata matsaya ne saboda wani na kusa da shi ko wani dalili na kashin kansa, wannan duk wanda yasan dabi'a ta tafarkin karatu yasan wannan.
Babban dalili a kan haka shi ne yadda za ka ga ɗalibi ya saba wa malaminsa a wasu al’amuran ilimi, ko kuma malami ya saba wa ɗalibinsa. Ana ɗaukar wannan a matsayin abu na al’ada a cikin tafarkin ilimi. Malamin bai ɗauki ɗalibin a matsayin abokin gaba ba, ɗalibin kuma bai zagi malaminsa ba. A’a, haka hanyar ilimi take tun asali: ana samun bambancin fahimta yayin da kowa yake dogaro da dalili da ƙa’idojin ilimi.
Misali, za ka samu Imamush-Shahid Sayyid Khamenei (Quddisa sirruhu) ya saba da Imam Khomeini (Quddisa sirruhu) a kan batun ganin wata da ido tsura. Imam Khomeini yana ganin cewa ganin wata yana buƙatar gani na kai tsaye da ido, yayin da Sayyid Khamenei yake ganin cewa ban da gani da ido kai tsaye, ana iya tabbatar da ganin wata ta hanyar telescope. Wannan sanannen sabani ne na ilimi. To, shin wannan ya kamata ya zama dalilin suka, zagi da cin mutunci tsakanin masu bin waɗannan ra’ayoyi da Muqallidansu?.
Haka nan za ka samu Sayyid Sistani (D.z) ya saba da Malaminsa, Sayyid al-Khu’i (Quddisa sirruhu), a kan batun اتحاد الأفق. Sayyid al-Khu'i na da wannan fahimta a mas’alar, yayin da Sayyid Sistani yake ganin sabani da bambancin افق a wannan batu.
Akwai daruruwan irin waɗannan sabani tsakanin manyan malamai, amma ba za ka ga malamai suna ɗaukar juna a matsayin batattu saboda irin wannan bambancin ba. Maimakon haka, suna girmama juna matuƙa, domin sun san cewa wannan sabani na iya kasancewa cikin iyakar fahimtar dalilai da ƙa’idojin ilimi.
To, abin mamaki shi ne ka ga mu, Muqallidai, muna kushe su, muna jefa musu zargi, muna jingina musu jahilci, rashin wayewa da makamantansu.
Wai wanda bai san gaba ɗaya inda Addini yasa gaba ba, shi ne yake tuhumar da sukar wanda a fagen ilimin Addini Imaminsa na Zamani (A.J.F) ne kawai a gabansa!.
Wanda baya kiyaye Sallah yadda ya kamata, baya kiyaye haƙƙin mutane, kuma baya tsayawa kan abin da Addini ya wajabta, shi ne zai ɗauki kansa a matsayin mai cancantar sukar wanda yake cikin alamomin taƙawa da ilimi?
Mu yi tunani sosai: idan Allah Ya gurfanar da mu tare da su a gabansa, aka yi mana hisabi a kan hakkokinsu da aka keta ta hanyar zagi, suka, ƙazafi ko cin mutunci, muna ganin za mu iya ɗaukar wannan nauyi?.
Saboda haka, mu koyi girmama Mujtahidai, Malamai, mu fahimci yanayin sabanin ilimi, kuma kada mu mayar da bambancin fahimta a cikin ijtihadi ya zama dalilin gaba, ƙiyayya da cin mutunci.
AKAN MARJA'IYYA DA MOTSIN MUSULUMCI: da Jahbhatul Muqawama ka Fahimci wannan.....!!!!
Marji’iyyah matsayi ne mai ƙima, matsayi mai girma da tsarki a zamanin Gaibar Sahibul-Asri waz-Zaman (A.s.), ba ya halatta a kushe ko a soke wannan matsayi. Ko da ka ga wani tasarrufi daga Marji’iyyah da ba ka fahimta ba, ko kuma ba ka samu natsuwa da shi ba, ka sani cewa rashin fahimtarka ko rashin natsuwarka bai zama dalilin kuskurar da su, ko ka soke wannan matsayi, domin shin ka kewaye sanin abinda ya kaisu ga wannan matsayin da suka tsaya kansa akan wata mas'ala?, Marji'ai suna daukar matsaya ne a komai dai-dai da abinda suka Fahimta ne daga Nassosa na Shari'a, abinda ya hau kanka muqallidi shine ainihin zabar mar'ja'i a cikin Maraji'ai da a'alamiyyarsa ta bayyana gare ka ta hanyar masu experience akan haka da ka natsu da su sai ka bi.
Ita Marji’iyyah matsayi ne da babu mai kaiwa gare shi sai wanda ya kai darajar Ijtihadi, yake mumini, yake adali wato wanda aka shaida masa da’a ga Allah (T) kuma ba a shaida masa sabon Allah a zahiri ba, ba ya bin duniya da gudu, tare da sauran sharuddan da ake buƙata. Idan aka rasa ɗaya daga cikin waɗannan sharudda, ko da mutum ya kai matsayin Ijtihadi, to ya sauka daga wannan matsayin.
Wannan ita ce hanya guda tilo da dalilan hankali da Shari’a suka tabbatar da ita cewa, a zamanin Gaibar Sahibul-Asri waz-Zaman (A.s.), ita ce za a bi wajen sanin hukuncin Allah (S) ta hanyar Al-Qur’ani da Sunnah. Mu sani cewa Marji'iyya babu inda a shi'a akace Annabci ce ko Imamanci ce ba, kuma ba in da aka ce Marja'i na gaba da Annabi ko Imami, babu wannan ko kusa ko nesa.
Don haka abinda nake son cewa shine: Wanda duk da sunan Marji’iyyah ya kushe ko ya soke Motsin Musulunci da Jabhatul Muqawama a faɗin duniya, Marji’iyyah ta barranta daga gare shi. Haka nan, wanda saboda Motsin Musulunci ko Jabhatul Muqawama ya kushe ko ya soke Marji’iyyah, to Motsin Musulunci da Jabhatul Muqawama sun barranta kansu daga gare shi.
Mu sani cewa Marji’iyyah da Motsin Musulunci da Jabhatul Muqawama ba abubuwa biyu ne masu cin karo da juna ba, kuma ba kishiyoyin juna ba ne. Babu wani Motsin Musulunci na gaskiya ko Jabhatul Muqawama da a zamanin Gaiba, ya juyawa Marji’iyyah baya ko ya ƙi yin biyayya gare ta, yaki girmama ra'ayinta, matuƙar yana cikin Makarantar Ahlul-Baiti (A.s.), zaka tarar da suna komawa wani Marja'i ne suna aiki dai-dai da fatawowinsa da taujihaat dinsa tare da girmama sauran maraji'an.
Hauzah ilmiyya, wadda ke kyankyashe Maraji’ai, mu sani cewa tana daga cikin manyan ginshiƙan wanzuwar tafarkin Ahlul-Baiti (A.s.). Haka nan, jagororin Jabhatul Muqawama da kansu sun fito ne daga wannan makaranta ta ilimi kuma suna cikin wannan tafarki.
Don haka, idan ka ji kana ƙiyayya da Marji’iyyah, to ka sani cewa maƙiyi ba-amurke, ba-Sahyuniye ya yi nasara a kanka.
Idan kuma ka ji kana ƙiyayya da Motsin Musulunci da Jabhaatul Muqawama, to ka sani cewa maƙiyi ba-amurke, ba-Sahyuniye ya yi nasara a kanka. Don haka ayi muraji'ar afkaar da Imani kar a tauye ko a wuce gona da iri, a bar komai a Muhallinsa, kuma kowa ya tsaya matsayinsa.
_Mahdi Dahiru Sanda
https://t.me/Mahdisanda
