ru
Feedback
📚🖍Darul Fikr Na Mahdi Sanda 📚🖍

📚🖍Darul Fikr Na Mahdi Sanda 📚🖍

Открыть в Telegram

وَأَعِدُّوا لَهُم مَّا اسْتَطَعْتُم مِّن قُوَّةٍ.......! #Fikira_Ruhi_Jiki. #Kai_Da_Jama'a.

Больше
810
Подписчики
Нет данных24 часа
Нет данных7 дней
-430 день
Архив постов
Sai dai abin lura shi ne cewa halaccin mulki daga Allah a tunanin Musulunci, da kuma a gwamnatin Manzon Allah (S.) ko ta Amirul Muminina (A.S.), bai taɓa zama wata hanya ta tauye wa mutane haƙƙinsu na bayyana ra'ayi ko rage muhimmancin ra'ayoyinsu ba. Akasin haka ne ma idan aka kwatanta da gwamnatocin kama-karya ko gwamnatocin Kiristanci na Yamma, waɗanda suke ɗora halaccin mulki daga Allah a matsayin kishiyar ra'ayin jama'a, kuma suke sanya shugabannin da Allah Ya zaɓa a gaban jama'a. Amma a tunanin Musulunci, Allah ba ya taɓa kasancewa a gefen da yake gaba da jama'a. Batu na gaba da za a tattauna dangane da tsarin gwamnatin Musulunci shi ne yadda nufin jama'a da nufin Allah suke daidaituwa kuma suke jituwa a cikin gwamnatin Musulunci. A gaskiya, duk da cewa halaccin mulki daga Ubangiji na iya kasancewa yana ɗauke da wani bangare mai kyau (idan faɗin haka ya inganta), kuma gwamnatin da Allah Ya yarda da ita, kamar gwamnatin Manzon Allah (S.) ko ta Imam (A.S), ita ce mafi alherin gwamnatoci, amma wannan batu ya kasance ana amfani da shi ta hanyar da ba ta dace ba a tsawon tarihi daga gwamnatocin zalunci da kama-karya. A cikin kundin tsarin mulkin Iran da aka rubuta bayan juyin juya halin dokokin da ka sani da Al-mashruɗa a farkon ƙarni na baya, wanda ya amince da tsarin sarauta a matsayin tsarin mulki, an rubuta cewa: Sarauta amana ce daga Allah da Ya ajiye... Haka kuma jam'iyyar Rastakhiz ta yi ƙoƙarin yaɗa wannan ra'ayi ta cikin bayananta, tana cewa gwamnatin Shahanshahi (sarauta) tana da tushene daga Ubangiji. To ya zama dole a nan a lura cewa wasu daga cikin waɗannan gwamnatoci sun yi ƙoƙarin amfani da wasu malaman addini da kuma riƙe wasu siffofin addini domin ƙarfafa riƙonsu da mulki, kuma suna amfani da maganar halaccin mulki daga Allah a matsayin hanyar cimma manufarsu. Mirza Na'ini ya yi bayani sarai game da amfani da addini wajen ƙarfafa ginshiƙan mulkin kama-karya a cikin shahararren littafinsa Tanbihul-Ummah wa Tanzihul-Millah, wanda ake ɗauka a matsayin ra'ayinsa na musamman game da gwamnatin tsarin mulki. A cikinsa ya bayyana nau'o'in gwamnatoci, sannan ya raba gwamnatin kama-karya zuwa nau'i biyu: gwamnatin kama-karya ta siyasa, wadda ita ce gwamnatin da azzalumai suke jagoranta a al'ummomi daban-daban; da kuma gwamnatin kama-karya ta addini, wato amfani da addini wajen danniya, inda mutum ɗaya ko wasu mutane suke tilasta zaluncinsu a kan al'umma. A ra'ayin Mirza Na'ini, wannan nau'i na biyu shi ne mafi muni daga cikin dukkan nau'o'in gwamnatoci. Sakamakon da za mu iya fitarwa daga wannan taƙaitaccen bayani shi ne cewa ana iya fassara halaccin mulki daga Ubangiji ta fuska biyu: ta fuska ɗaya a matsayin irin halaccin mulkin da ake buƙata, kuma ta wata fuska a matsayin irin halaccin mulkin da ba a buƙata. _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda

WACE GWAMNATI CE TAFI? Al'ummomi da Neman Mulki Mafi Kyawu. KASHI NA BIYAR (5) Nazariya ta Uku akan Tushen Halascin Gwamnati: Nazariyyar halaccin mulki daga Ubangiji. Ana ɗaukar ra'ayi na uku (Nazariyyar halaccin mulki daga Ubangiji) a matsayin ɗaya daga cikin muhimman ra'ayoyin tarihi game da tushen halaccin mulki a ƙasashe daban-daban na duniya. Masu wannan ra'ayi suna ganin cewa kafa gwamnati tana samo asali ne daga nufin Allah, kuma gwamnati tana da siffar addini da sama. Haka kuma, biyayya ga umarnin mai mulki a irin wannan gwamnati tana nufin biyayya ga umarnin Allah Madaukakin Sarki, saboda haka, saɓawa umarnin mai mulki yana nufin saɓa wa umarnin Allah da hukunce-hukuncensa. A takaice dai, ma'aunin halaccin mulki a wannan ra'ayi shi ne nufin Allah Maɗaukaki. Sai dai akwai manyan saɓani tsakanin masu wannan ra'ayi dangane da yadda ake aiwatar da shi a tsarin gwamnatoci. Kuma Saboda zurfin tasirin addini da ƙarfinsa a tsakanin al'ummomi daban-daban, wasu masu iko da suke neman dalilan da za su ba su damar rinjayar mutane, sun sami abin da suke nema a cikin wannan ra'ayi. A zamanin da, Fir'aunonin Masar suna da nau'i biyu na mulki: mulkin ubangiji da mulkin sarki. Wato, mai mulki (ko Fir'auna) yana ɗaukar kansa a matsayin Ubangiji, kuma a lokaci guda yana wakiltar ɗan ubangijin da ya yi mulki kafin shi. Kiristoci kuma suna imani cewa Annabi Isa (A.S.) yana da sifar Ubangijantaka kuma shi ɗan Allah ne (Allah Ya Mana Tsari). Duk da haka, babban ma'anar tushen mulki daga Ubangiji ita ce Allah ne ke zaɓar mai mulki, ta hanyar wahayi ko ilhami, kuma dokoki da umarnin gwamnati suna fitowa ne daga Allah Madaukakin Sarki. Saboda Allah Shi ne Masani, Mai Hikima, Mai Gane halin bayinsa kuma Mai Tausayi gare su, Shi ne ya fi kowa sanin abin da yake maslaharsu gaba ɗaya. Saboda haka Shi ne ke zaɓar mai mulki da kuma dokokin da za su tabbatar da farin cikin ɗan Adam kuma su jagoranci mutane ta hanya mafi kyau. Abin lura shi ne cewa Church ta yi aiki wajen tabbatar da wannan ra'ayi, har ta kai ga cewa a aikace an kawar da gwamnatocin da ba na Kiristanci ba, aka maye gurbinsu da gwamnatocin addini. Abin takaici kuwa, wannan ra'ayi ya kasance a tsawon tarihin Kiristanci yana ƙarfafa ginshiƙan mulkin kama-karya da zaluncin masu mulki, tare da murƙushe haƙƙin al'umma har ta kai ga cewa mutane ba su da ikon ko tambayar abin da mai mulki yake yi. Masu wannan ra'ayi suna yaɗa cewa sarki inuwa ce ta Allah a doron ƙasa, kuma dukkan sarakuna Allah ne Ya ɗora musu alhakin tafiyar da al'amuran al'umma. Saboda haka ba su da alhakin ba wa kowa amsa face Allah Shi kaɗai, kuma wannan aiki da aka ɗora musu shi ne yake ba mulkinsu halacci, abin da ya rage wa mutane shi ne kawai su yi musu biyayya. Wasu kuma suna ganin cewa halaccin gwamnatocin kama-karya da suka yi mulki a baya a Iran ya samo asali ne daga kasancewarsu masu tushe daga Ubangiji, domin Allah ne Ya zaɓi sarakuna Ya kuma naɗa su, kuma Allah ne Ya sanya a cikin halittarsu ainihin sarauta. Har ila yau, tunanin Musulunci ma yana ƙunshe da wani ra'ayi mai kama da wannan dangane da tushen halaccin mulki. Ta fuskar tarihi, idan muka dubi gwamnatin Manzon Allah Maɗaukaki (S.) da ta Imami Ma'asumi (A.S.) a cikin al'ummar Musulmi, kuma muka nazarci ayoyin Alƙur'ani da suka yi magana game da mulkinsu, za mu ga cewa wakilcin Allah da aka ba su shi ne yake ba mulkinsu halacci, kuma shi ne yake tabbatar musu da ƙarfi wajen ci gaba da wannan wakilci. Duk da haka, sun kasance suna ba ra'ayin mutane muhimmanci sosai, suna kuma yin shawara da su, musamman a yaƙe-yaƙe da sauran al'amura. Hakika, Alƙur'ani Mai Girma ya jaddada a wurare da dama wajibcin yi wa Manzon Allah (S.) biyayya, kuma ya haɗa biyayyarsa da biyayya ga Allah Maɗaukaki, inda Allah Ya ce: {Ku yi biyayya ga Allah, kuma ku yi biyayya ga Manzo}.Haka kuma, Manzon Allah Maɗaukaki (S.) ya naɗa Imam Ali (A.S.) a matsayin halifansa bayansa a Hadisin Ghadir Khumm, kuma babu shakka wannan naɗin aiwatar da umarnin Allah ne, kamar yadda Ya ce: {Ya kai Manzo! Ka isar da abin da aka saukar maka daga Ubangijinka}.

Sai dai abin lura shi ne cewa halaccin mulki daga Allah a tunanin Musulunci, da kuma a gwamnatin Manzon Allah (S.) ko ta Amirul Muminina (A.S.), bai taɓa zama wata hanya ta tauye wa mutane haƙƙinsu na bayyana ra'ayi ko rage muhimmancin ra'ayoyinsu ba. Akasin haka ne ma idan aka kwatanta da gwamnatocin kama-karya ko gwamnatocin Kiristanci na Yamma, waɗanda suke ɗora halaccin mulki daga Allah a matsayin kishiyar ra'ayin jama'a, kuma suke sanya shugabannin da Allah Ya zaɓa a gaban jama'a. Amma a tunanin Musulunci, Allah ba ya taɓa kasancewa a gefen da yake gaba da jama'a. Batu na gaba da za a tattauna dangane da tsarin gwamnatin Musulunci shi ne yadda nufin jama'a da nufin Allah suke daidaituwa kuma suke jituwa a cikin gwamnatin Musulunci. A gaskiya, duk da cewa halaccin mulki daga Ubangiji na iya kasancewa yana ɗauke da wani bangare mai kyau (idan faɗin haka ya inganta), kuma gwamnatin da Allah Ya yarda da ita, kamar gwamnatin Manzon Allah (S.) ko ta Imam (A.S), ita ce mafi alherin gwamnatoci, amma wannan batu ya kasance ana amfani da shi ta hanyar da ba ta dace ba a tsawon tarihi daga gwamnatocin zalunci da kama-karya. A cikin kundin tsarin mulkin Iran da aka rubuta bayan juyin juya halin dokokin da ka sani da Al-mashruɗa a farkon ƙarni na baya, wanda ya amince da tsarin sarauta a matsayin tsarin mulki, an rubuta cewa: Sarauta amana ce daga Allah da Ya ajiye... Haka kuma jam'iyyar Rastakhiz ta yi ƙoƙarin yaɗa wannan ra'ayi ta cikin bayananta, tana cewa gwamnatin Shahanshahi (sarauta) tana da tushene daga Ubangiji. To ya zama dole a nan a lura cewa wasu daga cikin waɗannan gwamnatoci sun yi ƙoƙarin amfani da wasu malaman addini da kuma riƙe wasu siffofin addini domin ƙarfafa riƙonsu da mulki, kuma suna amfani da maganar halaccin mulki daga Allah a matsayin hanyar cimma manufarsu. Mirza Na'ini ya yi bayani sarai game da amfani da addini wajen ƙarfafa ginshiƙan mulkin kama-karya a cikin shahararren littafinsa Tanbihul-Ummah wa Tanzihul-Millah, wanda ake ɗauka a matsayin ra'ayinsa na musamman game da gwamnatin tsarin mulki. A cikinsa ya bayyana nau'o'in gwamnatoci, sannan ya raba gwamnatin kama-karya zuwa nau'i biyu: gwamnatin kama-karya ta siyasa, wadda ita ce gwamnatin da azzalumai suke jagoranta a al'ummomi daban-daban; da kuma gwamnatin kama-karya ta addini, wato amfani da addini wajen danniya, inda mutum ɗaya ko wasu mutane suke tilasta zaluncinsu a kan al'umma. A ra'ayin Mirza Na'ini, wannan nau'i na biyu shi ne mafi muni daga cikin dukkan nau'o'in gwamnatoci. Sakamakon da za mu iya fitarwa daga wannan taƙaitaccen bayani shi ne cewa ana iya fassara halaccin mulki daga Ubangiji ta fuska biyu: ta fuska ɗaya a matsayin irin halaccin mulkin da ake buƙata, kuma ta wata fuska a matsayin irin halaccin mulkin da ba a buƙata. _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda

WACE GWAMNATI CE TAFI? Al'ummomi da Neman Mulki Mafi Kyawu. KASHI NA BIYAR (5) Nazariya ta Uku akan Tushen Halascin Gwamnati: Nazariyyar halaccin mulki daga Ubangiji. Ana ɗaukar ra'ayi na uku (Nazariyyar halaccin mulki daga Ubangiji) a matsayin ɗaya daga cikin muhimman ra'ayoyin tarihi game da tushen halaccin mulki a ƙasashe daban-daban na duniya. Masu wannan ra'ayi suna ganin cewa kafa gwamnati tana samo asali ne daga nufin Allah, kuma gwamnati tana da siffar addini da sama. Haka kuma, biyayya ga umarnin mai mulki a irin wannan gwamnati tana nufin biyayya ga umarnin Allah Madaukakin Sarki, saboda haka, saɓawa umarnin mai mulki yana nufin saɓa wa umarnin Allah da hukunce-hukuncensa. A takaice dai, ma'aunin halaccin mulki a wannan ra'ayi shi ne nufin Allah Maɗaukaki. Sai dai akwai manyan saɓani tsakanin masu wannan ra'ayi dangane da yadda ake aiwatar da shi a tsarin gwamnatoci. Kuma Saboda zurfin tasirin addini da ƙarfinsa a tsakanin al'ummomi daban-daban, wasu masu iko da suke neman dalilan da za su ba su damar rinjayar mutane, sun sami abin da suke nema a cikin wannan ra'ayi. A zamanin da, Fir'aunonin Masar suna da nau'i biyu na mulki: mulkin ubangiji da mulkin sarki. Wato, mai mulki (ko Fir'auna) yana ɗaukar kansa a matsayin Ubangiji, kuma a lokaci guda yana wakiltar ɗan ubangijin da ya yi mulki kafin shi. Kiristoci kuma suna imani cewa Annabi Isa (A.S.) yana da sifar Ubangijantaka kuma shi ɗan Allah ne (Allah Ya Mana Tsari). Duk da haka, babban ma'anar tushen mulki daga Ubangiji ita ce Allah ne ke zaɓar mai mulki, ta hanyar wahayi ko ilhami, kuma dokoki da umarnin gwamnati suna fitowa ne daga Allah Madaukakin Sarki. Saboda Allah Shi ne Masani, Mai Hikima, Mai Gane halin bayinsa kuma Mai Tausayi gare su, Shi ne ya fi kowa sanin abin da yake maslaharsu gaba ɗaya. Saboda haka Shi ne ke zaɓar mai mulki da kuma dokokin da za su tabbatar da farin cikin ɗan Adam kuma su jagoranci mutane ta hanya mafi kyau. Abin lura shi ne cewa Church ta yi aiki wajen tabbatar da wannan ra'ayi, har ta kai ga cewa a aikace an kawar da gwamnatocin da ba na Kiristanci ba, aka maye gurbinsu da gwamnatocin addini. Abin takaici kuwa, wannan ra'ayi ya kasance a tsawon tarihin Kiristanci yana ƙarfafa ginshiƙan mulkin kama-karya da zaluncin masu mulki, tare da murƙushe haƙƙin al'umma har ta kai ga cewa mutane ba su da ikon ko tambayar abin da mai mulki yake yi. Masu wannan ra'ayi suna yaɗa cewa sarki inuwa ce ta Allah a doron ƙasa, kuma dukkan sarakuna Allah ne Ya ɗora musu alhakin tafiyar da al'amuran al'umma. Saboda haka ba su da alhakin ba wa kowa amsa face Allah Shi kaɗai, kuma wannan aiki da aka ɗora musu shi ne yake ba mulkinsu halacci, abin da ya rage wa mutane shi ne kawai su yi musu biyayya. Wasu kuma suna ganin cewa halaccin gwamnatocin kama-karya da suka yi mulki a baya a Iran ya samo asali ne daga kasancewarsu masu tushe daga Ubangiji, domin Allah ne Ya zaɓi sarakuna Ya kuma naɗa su, kuma Allah ne Ya sanya a cikin halittarsu ainihin sarauta. Har ila yau, tunanin Musulunci ma yana ƙunshe da wani ra'ayi mai kama da wannan dangane da tushen halaccin mulki. Ta fuskar tarihi, idan muka dubi gwamnatin Manzon Allah Maɗaukaki (S.) da ta Imami Ma'asumi (A.S.) a cikin al'ummar Musulmi, kuma muka nazarci ayoyin Alƙur'ani da suka yi magana game da mulkinsu, za mu ga cewa wakilcin Allah da aka ba su shi ne yake ba mulkinsu halacci, kuma shi ne yake tabbatar musu da ƙarfi wajen ci gaba da wannan wakilci. Duk da haka, sun kasance suna ba ra'ayin mutane muhimmanci sosai, suna kuma yin shawara da su, musamman a yaƙe-yaƙe da sauran al'amura. Hakika, Alƙur'ani Mai Girma ya jaddada a wurare da dama wajibcin yi wa Manzon Allah (S.) biyayya, kuma ya haɗa biyayyarsa da biyayya ga Allah Maɗaukaki, inda Allah Ya ce: {Ku yi biyayya ga Allah, kuma ku yi biyayya ga Manzo}.Haka kuma, Manzon Allah Maɗaukaki (S.) ya naɗa Imam Ali (A.S.) a matsayin halifansa bayansa a Hadisin Ghadir Khumm, kuma babu shakka wannan naɗin aiwatar da umarnin Allah ne, kamar yadda Ya ce: {Ya kai Manzo! Ka isar da abin da aka saukar maka daga Ubangijinka}.

Koyi da Imam Husaini (A.S.) yana wajabta wa mutum ya kasance mai rahama a cikin gidansa da al'ummarsa, kuma ya nisanci tsanan
Koyi da Imam Husaini (A.S.) yana wajabta wa mutum ya kasance mai rahama a cikin gidansa da al'ummarsa, kuma ya nisanci tsanantawa da amfani da tashin hankali a cikin saɓanin da yake fuskanta na iyali da zamantakewa; ko a rikicin auratayya, ko saɓanin dangi, ko kuma bambance-bambancen ra'ayi. _Sheikh Hassan al-Saffar (H). https://t.me/Mahdisanda

Koyi da Imam Husaini (A.S.) yana wajabta wa mutum ya kasance mai rahama a cikin gidansa da al'ummarsa, kuma ya nisanci tsanan
Koyi da Imam Husaini (A.S.) yana wajabta wa mutum ya kasance mai rahama a cikin gidansa da al'ummarsa, kuma ya nisanci tsanantawa da amfani da tashin hankali a cikin saɓanin da yake fuskanta na iyali da zamantakewa; ko a rikicin auratayya, ko saɓanin dangi, ko kuma bambance-bambancen ra'ayi. _Sheikh Hassan al-Saffar (H).

"Ya Allah, Ka azurta mu da zuri'a saliha wadda za ta zarce mu a nagarta, shiriya da bautarka, ta zama mana sadaka jariya a duniya da lahira." _Mahdi Dahiru Sanda 29/6/2026

"Ya Allah, Ka azurta mu da zuri'a saliha wadda za ta zarce mu a cikin nagarta, shiriya da bautarka, ta zama mana sadaka jariya a duniya da lahira." _Mahdi Dahiru Sanda 29/6/2026

Kai ne abin ayiwa ta'aziyya Ya Sahibaz Zaman.💔🏴💕🖤💫

Muminai suna buƙatar nagartaccen Malami wanda zai kusantar da zukatansu ga juna, ba wanda zai rarraba su ko ya haifar da gaba
Muminai suna buƙatar nagartaccen Malami wanda zai kusantar da zukatansu ga juna, ba wanda zai rarraba su ko ya haifar da gaba a tsakaninsu ba. Suna buƙatar wanda harshensa ba ya gina ƙiyayya a zukatan wasu a kan wasu; wanda manufarsa ita ce gaskiya, ba son zuciya ko bin mutane ba; wanda burinsa shi ne neman yardar Allah, ba neman wani abin duniya ba. Rashin irin wannan mutum babban gibi ne a cikin al'umma Mumina. Wannan ne ya sa kullum muke jin kewar Babban Uba, Shaheed Sheikh Qasim (R), a tsakiyarmu. Ya tsaya wa Allah da cikakkiyar niyya, sai Allah Ya ɗaukaka ambatonsa, Ya ba shi ɗaukaka a duniya da lahira. _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda

Muminai suna buƙatar nagartaccen Malami wanda zai kusantar da zukatansu ga juna, ba wanda zai rarraba su ko ya haifar da gaba
Muminai suna buƙatar nagartaccen Malami wanda zai kusantar da zukatansu ga juna, ba wanda zai rarraba su ko ya haifar da gaba a tsakaninsu ba. Suna buƙatar wanda harshensa ba ya gina ƙiyayya a zukatan wasu a kan wasu; wanda manufarsa ita ce gaskiya, ba son zuciya ko bin mutane ba; wanda burinsa shi ne neman yardar Allah, ba neman wani abin duniya ba. Rashin irin wannan mutum babban gibi ne a cikin al'umma Mumina. Wannan ne ya sa kullum muke jin kewar Babban Uba, Shaheed Sheikh Qasim (R), a tsakiyarmu. Ya tsaya wa Allah da cikakkiyar niyya, sai Allah Ya ɗaukaka ambatonsa, Ya ba shi ɗaukaka a duniya da lahira. _Mahdi Dahiru Sanda

Masu sukarmu a kan raya lamarin Imam Husain (A.S), da sun ɗanɗane zaƙin walayar Ahlul Baiti (A.S), da ba za su zarge mu da ya
Masu sukarmu a kan raya lamarin Imam Husain (A.S), da sun ɗanɗane zaƙin walayar Ahlul Baiti (A.S), da ba za su zarge mu da yawan raya al'amarin Husain ba; sai dai su zarge mu da gazawa. Domin duk abin da muke yi, a haƙiƙa, bai kai kaɗan daga cikin haƙƙin da Husain (A.S) yake da shi a kanmu ba da sadaukarwarsa ba. _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda

Masu sukarmu a kan raya lamarin Imam Husain (A.S), da sun ɗanɗane zaƙin walayar Ahlul Baiti (A.S), da ba za su zarge mu da ya
Masu sukarmu a kan raya lamarin Imam Husain (A.S), da sun ɗanɗane zaƙin walayar Ahlul Baiti (A.S), da ba za su zarge mu da yawan raya al'amari Husain ba; sai dai su zarge mu da gazawa. Domin duk abin da muke yi, a haƙiƙa, bai kai kaɗan daga cikin haƙƙin da Husain (A.S) yake da shi a kanmu ba da sadaukarwarsa ba. _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda

Masu sukarmu a kan raya lamarin Imam Husain (A.S), da sun ɗanɗane zaƙin walayar Ahlul Baiti (A.S), da ba za su zarge mu da yawan raya al'amari Husain ba; sai dai su zarge mu da gazawa. Domin duk abin da muke yi, a haƙiƙa, bai kai kaɗan daga cikin haƙƙin da Husain (A.S) yake da shi a kanmu ba da sadaukarwarsa ba. _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda

Sirrin Tsayuwar Imamul Hussain (A.s). ✌🏻🏴🖤💕🌟

Al-Qasim Bn Hassan Al-Mujtaba (A.s). 🤌🏻🖤🏴🖤🏴💔🌟

Imam Hussain (A.s) a Ranar Goma Muharram. 💔🖤🏴🏴

إنّا لله وإنّا إلَيهِ رّاجِعُون اَعْظَمَ اللهُ اُجُوْرَنَا وَاُجُوْرَكُمْ بِمُصَابِنَا بِالْحُسَيْنِ عَلَيْهِ السَّلَامُ، وَجَعَلَنَا وَاِيَّاكُمْ مِنَ الطَّالِبِيْنَ بِثَارِهِ مَعَ وَلِيِّهِ الْاِمَامِ الْمَهْدِىِّ مِنْ اٰلِ مُحَمَّدٍ عَلَيْهِمُ السَّلَامُ۔💔 اَللّـهُمَّ الْعَنْ قَتَلَةَ الْحُسَيْنِ عَلَيْهِ السَّلامُ.

KA LURA DA RANAR ZABIN MAKOMA!!! Mutum yana roƙon Allah Ya haɗa masa Addini da Duniya, kuma wannan ba laifi ba ne. Amma akwai rana da za ta zo inda Addini da Duniya za su rabu, dole ne mutum ya zaɓi ɗaya daga cikinsu. A wannan lokaci, abin da zuciya ta fi ta'allakuwa da shi ne zai yi rinjaye. Wanda zuciyarsa ta fi zama manne da Addini, zai sadaukar da Duniya domin Addininsa. Wanda kuma zuciyarsa ta fi zama manne da Duniya, zai sadaukar da Addininsa domin Duniya. Babban misalin hakan shi ne Hur bn Yazid Ar-Riyahi (R) da Umar bn Sa'ad (L). Hur ya ga cewa tsakanin Aljanna da Wuta aka tsayar da shi, sai ya zaɓi Imam Husaini (A.S), domin Addini ne ya fi mamaye zuciyarsa. Umar bn Sa'ad kuwa ya ga mulkin Rayy da kusancinsa ga Yazidu sun fi muhimmanci a gare shi, sai ya zaɓi Duniya ya bar gaskiya. Karbala ta koya mana cewa ba kowa ne da ke faɗin “ina tare da gaskiya ba” yake kasancewa tare da ita ba lokacin jarabawa. Lokacin jarabawa ne yake tona abin da ke cikin zuciya. Hur ya zama abin koyi saboda ya zaɓi Addini akan Duniya, Umar bn Sa'ad kuma ya zama abin la'ana saboda ya zaɓi Duniya akan Addini. Saboda haka, dole ne mu riƙa gina zukatanmu tun yanzu kafin ranar zaɓi ta zo. Domin idan zuciya ta cika da son Duniya, za ta iya fifita ta akan Addini a lokacin gwaji. Amma idan ta cika da son Allah, Manzonsa, da Ahlul Baiti (A.S), za ta tsaya tare da gaskiya ko da kuwa hakan zai jawo asarar Duniya baki ɗaya. Karbala ba tarihin da ya shuɗe ba ne; Karbala tambaya ce da ake yi wa kowane mutum a kowace rana: Shin idan Addini da Duniya suka zo suna jan ka zuwa hanyoyi biyu mabambanta, wanne za ka zaɓa? _Mahdi Dahiru Sanda https://t.me/Mahdisanda