en
Feedback
ADDININ NASIHA

ADDININ NASIHA

Open in Telegram

ADDININ NASSIHA TAKU CE DOMIN TUNATARWA, NASSIHA, SAMUN KARATUTTUKAN MALAMAN SUNNAH IN SHA ALLAH ADMINS KADAI SUKE DA DAMA TURA SAKO CIKIN GROUPE MU DALIBAI NE BA MALAMAI BA MUNA ROQON ALLAH YA SA MANA IKHLASI KUMA YA HADAMU A CIKIN GIDAN AL-JANNAH.

Show more
The country is not specifiedReligion & Spirituality115 078
773
Subscribers
+124 hours
+227 days
+10330 days
Posts Archive
Khuɗubobin Juma'ahKhuɗubobin Juma`ah 01. 02 Talakan Nigeria Ya Shiga Uku. 02. Privatization A Wajen Gwamnatocin Afirka Da Kuma Matsayin Kishin Kasa. 03. Sako Zuwa Ga Zindiki Fu'ad Umar Mai Shafin Qibla Fm . 04. Baya Ta Haifu [Tsokaci Akan Khalifa Dan Ghana Mazaunin America]. 05. Hukunce Hukuncen Khudubah Da Haramcin Koyi Da Arna . 06. Zanga Zangar Daliban Makarantun Secondary Da Mutuwar Dr. Yusuf Alkhardawiy . 07. Matsayin Alkhardawiy Da Wasa'ilid Da'awah. 08. Abubuwan Da Aka Shigarwa Addinin Musulunci. Gabatarwar; Imam Dr.Idris Abdul'azeez Bauchi [Hafizahul-laa] follow us on; facebook; https://www.facebook.com/SGNnigeria/ Subscribe our You Tube Channel https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Twitter: https://twitter.com/SGNnigeria?t=vytGM6iYd3YDrUF8DXIYWw&s=09 Telegram; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel     WhatsApp Group ; https://chat.whatsapp.com/EF96RMxqVJ1ByjTiowcSKL       Telegram Group; https://t.me/+8lY3HniGbI5jMDM0 Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel for more info contact us on WhatsApp ; https://bit.ly/3pl20Vj

Hukuncin Kayan Dake Da Sunan Allah Jayo Hankulan Ƴan Kasuwa Akan Ire-iren Waɗannan Kayayyakin Jayo Hankulan Waɗanda Suka Samu Ire-iren Waɗannan Kayayyakin https://youtu.be/5zcacNaLrLg Daga; Ash-Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam Rahimahul-laah

Wanda Yabar Sallar La'asar Aikin Shi Ya Bace❗.mp35.18 MB

K. Muqaddimar Sharhus Sunnah .mp313.32 MB

 ☘ MUQADDIMAR SHARHUS-SUNNAH ☘ 📚 Muqaddimar Sharhus-Sunnah 📚 📚📖📓 K Gabatarwar; Ash-Sheikh Abu-Abdurrahman Muhammad Auwal Adam Albaniy Zaria [Rahimahul-laah] Date: Daren Juma'ah 19th Al-muharram 1435 A.H daidai da 21st November, 2013   Wuri: Daarul Hadeethis Salafiyyah, Zaria, Kaduna State, Nigeria   Daga cikin muhimman abubuwan da Malam ya tattauna; 1. Yadda Akai Malaman Ahlussunnah Suke Da Kyakkyawar Fahimta Ga Hadisan Annabi [SAW] . 2. Bambanci Tsakanin Sunnah Da Hadisi. 3. Shawara Ga Ɗaliban Ilimi Dangane Da Ƴan Shi'ah❗ 4. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Sahihul Bukhaariy Da Ƙimar Kowannen Su A Babukan Ilimi. 5. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Sahihul Muslim Da Ƙimar Kowannen Su A Babukan Ilimi. 6. Al-Imamun Nawawiy; Salafiy Ne Shi Ko Khalafiy ❓ 7. Aqidar Salaf Game Da AYOYIN SIFFOFIN ALLAH. 8. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Sunanu Abi Daawuud Da Ƙimar Kowannen Su A Babukan Ilimi. 9. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Sunanut Tirmizheey Da Ƙimar Kowannen Su A Babukan Ilimi. 10. Manufar Jami'atul Islamiyyah Ta Madinah. 11. Sheikh Zarban; tsohon Limamin Quba [Rahimahullah] 12. Addu'a Ta Musamman Ga Sarki Abdul'azeez Ɗan Abdurrahman Tare Da Ɗan Shi Sarki Fahad [Rahimahumullah] 13. Alama Ta Farko Da Za'a Gane Sarkin Musulmi Ko Gwamnan Sokoto Ahlussunnah Ne ❓ 14. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Sunanun Nasaa'iy Da Ƙimar Kowannen Su A Babukan Ilimi. 15. Mecece Aqidar Waɗanda Suka Rubuta Kutubus-Sittah❓ 16. Ƴan Salafiyyah Na Son Su Kafa Gwamnati, Amma Ta Hanyar Ilimi❗ 17. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Ibnu Majah Da Ƙimar Kowannen Su A Babukan Ilimi. 18. Malam Muntaqa Kumasi Da Sharhin Da Yayi Ma Ibnu Majah 19. Sharhin Littafin Bulughul Maraam 20. Sharhin Littafin Umdatul Ahkam. 21. Bayanai Kan Sharhohin Littafin Riyadussaliheen Da Ƙimar Su Ta Ilimi. 22. Sharhin Littafin Arba'una Hadeeth. 23. Asalin littafin "Nailul Awtar" Da Shaukaniy Yayi Ma Sharhi. 24. Wasu Littattafai Ne Ɗalibin Ilimi Ke Buƙata Dangane da Tattauna Saɓanin Mazhabobi Da Ra'ayoyin Malamai❓ 25. Imamu Malik Da Littafin Shi Na Muwaddah 26. Ko Muwaddah Ce Littafi Mafi Inganci Bayan Al-Qur'ani❓ 27. Sharhohin Muwaddah 28. Litattafan Sharhi. 29. Yaya Ɗaliban Ilimi Na Ahlussunnah Suke A Mataki Na Duniya A Yanzu❓ 30. Karantar Da Larabci A Daarul Hadeeth. 31. Cigaba Ba Haɓakar Larabci A Nigeria. 32. Professor Ali Abubakar mai Littafin "الثقافة العربية في نيجيريا" 33. Littafan Da Wasu Masana Suka Rubuta Da Suke Taimakawa Wajen Sanin Tarihin Nigeria. 34. Shawara Ga Ɗaliban Ilimi! Subscribe Our YouTube Channel; https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel

MAFIFICIN SALATIN ANNABI {S.A.W} ===================================== ALLAH {S.W.T} Yace: Haƙiƙa ALLAH da Mala'ikunsa suna yiwa Annabi salati, yaku waɗanda sukayi imani kuyi salati ga Annabi. Haƙiƙa salatai sunzo acikin hadisai mabanbanta daga Annabi {s.a.w} wanda sukazo da sigogi bakwai ingantattu kamar yadda tahiyar sallah tazo dasigogi bakwai. Amma mafificin salati acikin jerin salatansa mfi ƙololuwa, kuma mafi soyuwa a gurin ALLAH shine: Salatin da Bukhari da Muslim suka haɗu akansa domin kuwa bayan Alƙur'ani mafi sahihin littafi shine SAHIH BUKHARI sai kuma SAHIH MUSLIM. Dukkan maluman sunnah sun haɗu akan sahihancin waɗannan littattafai guda biyu wanda basa ɗauke da hadithi mai rauni acikinsu ko guda ɗaya, an tacesu an tabbatar da tsantsanin malaman da suka rawaito hadithan cikinsu. Salati mafi girma mafi ƙololuwa shine: اَللّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اَللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارِكْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ. Allahumma salli ala Muhammad, wa'ala ali Muhammad, kama sallaita ala Ibraheema wa ala ali ibraheema innaka Hameedun Majeed, Allahumma barik ala Muhammad, wa'ala ali Muhammad, kama barakta ala Ibraheema wa'ala ali Ibraheem, innaka Hameedun Majeed. Duk wani salati a bayan wannan salatin yake, domin wannan salatin ya fitone kai tsaye daga bakin Manzon ALLAH {s.a.w} kamar yadda kuma aka samu manyan malaman hadithi suka rawaitoshi acikin mafi sahihan litattafai wato Sahih Bukhari da Sahih Muslim. Salatin Annabi {s.a.w} yana da falala mai yawan gaske wanda babu wani abu da bawa zai faɗi ALLAH {S.W.T} ya ambace face sai salati ga Annabi {s.a.w}. Sannan idan kayi guda ɗaya ALLAH {S.W.T} zaiyi maka goma, salatin ALLAH ga bawa kuwa shine zai yabi bawan nasa, kuma zai ɗaga darajarsa zai kuma gafarta masa zunubansa. Sannan kuma mala'iku zasuyi maka salati, salatin mala'iku shine nema maka gafarar ALLAH {S.W.T}, Addu'ar Mala'iku kuwa karɓaɓɓace a gurin ALLAH. Sannan babu wani abu da zai sami bawa acikin rayuwarsa ko baƙin ciki ko rashi ko ƙunci ko wacce irin matsalace ta sami mutum, ya yawaita salati ga Annabi {s.a.w} face sai ALLAH {S.W.T} ya yaye masa dukkan damuwarsa. Yin salati ga Annabi {s.a.w} yanasa mutum ya sami ceto daga Manzon ALLAH {s.a.w} a ranar alƙiyama. Yin salati ga Annabi {s.a.w} yana sawa mutum ya tsallaka siraɗi cikin gaggawa ba tareda yasani ba. Babu wani alkhairi anan duniya da lahira face saika sameshi acikin salatin Annabi {s.a.w}. Saboda haka yaku musulmi masoya ALLAH da Manzon ALLAH {s.a.w} kuyi salati ga Manzon ALLAH {s.a.w}, ku yawaita salati agareshi kada ku gajiya, duk wanda ya yawaita salati agareshi tabbas zai dace da rahmar ALLAH {S.W.T}. ALLAH {S.W.T} ka bamu ikon yawaita salati ga Annabi {s.a.w} acikin dukkan rayuwarmu. ALLAH ka dawwamar damu acikin yiwa Annbi {s.a.w} salati. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

LITTAFIN UMDATUL AHKAM °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° LITTAFIN TSARKI °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° HADITHI NA [12] °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Daga Abu Ayubal Ansari (R.A) Yace: Manzon ALLAH {s.a.w} Yace: Idan kuka zo wajen yin kashi, to kada ku fuskanci alƙibla da yin kashin ko fitsari. Kada kuma kuma ku bada baya saidai ku kalli mahudar rana ko mafaɗarta. Shi kuwa Abu Ayuba Yace: Munzo ƙasar Sham sai muka sami irin banɗakunan nan an gigginasu a bakin hanyoyi suna fuskantar alƙibla, Mu kuma idan muka shiga saimu kaucewa alƙiblar sannan mu haɗa da yin istigfar, da neman ALLAH {S.W.T} ya gafarta mana. SHARHI: Wannan hadithi kai tsaye yana mana nuni da umarni da idan mutum ya shiga banɗaki domin uzurin kashi ko fitsari, to kada ya kalli alƙibla kuma kada ya bata baya, sai dai ya kalli ɓangaren da yake ba alƙibla bane. Idan kuwa angina banɗakin a yanayin da dole idan mutum zaiyi uzurin sai ya kalli alƙibla ko kuma sai ya bata baya, to sai mutum ya karkacewa daga kallon alƙiblar, kada ya zama dukkan jikinsa ya kalleta, Sannan kuma sai yayi istigfar a yayin daya fito daga banɗakin. HADITHI NA [13] °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Daga Abdullahi Ɗan Umar (R.A) Yace: Wata rana na hau kan rufin ɗakin 'ƴar uwata Hafsat (R.A) sai naga Manzon ALLAH {s.a.w} yana tsugune yana fuskantar ɓangaren ƙasar Sham (wato siriya) ya kuma bawa ɓangaren ka'aba baya. SHARHI: Wannan hadithin yana mana nuni da cewa Manzon ALLAH {s.a.w} ya shiga banɗaki domin yin uzuri kuma ya fuskanci alƙibla a yayin uzurinsa. Wannan yasa wasu daga cikin malamai ke hujja da wannan hadithin wajen cewa idan mutum yana cikin banɗaki ko yana da wani abu wanda yayi masa katanga da alƙibla, to babu komai don ya kallai alƙibla a yayin kashin sa ko fitsatin sa. Amma kuma wasu malaman su kace idan hadithai su kazo guda biyu kuma ingantattu, Sai aka sami ɗaya yazo da furucin umarni, ɗayan kuma yazo da aiki a aikace, to hadithin da yazo da umarni ta hanyar magana, yafi ƙarfi sama da wanda yazo da aiki a aikace. Kamar hadithin da yayi hani da shan abinsha a tsaye, sai kuma aka samu yasha abinsha a tsaye, anan ma wanda yazo da hani ta hanyar magana yafi ƙarfi, domin larura ce tasa yasha abinsha a tsaye, bawai ya sunnata yin hakan bane. Haka kuma hadithin da yazo da hani akan yin fitsari a tsaye, sai kuma aka samu yayi fitsari a tsaye, shima hadithin da yazo da hani yafi ƙarfi sama da wanda yazo da aikin a aikace, domin larurace tasa yayi fitsarin a tsaye bawai ya sunnanta hakan bane dadai sauransu. ALLAH shine mafi sani. ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayamu Ameen. Duk mai neman ƙarin bayani saiya tuntuɓemu ta private.

Repost from ADDININ NASIHA
TUNATARWA TUNATAR WA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN RABI'UL AWWAL 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akow
TUNATARWA TUNATAR WA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN RABI'UL AWWAL 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wata har zuwa Ramadhan yana dai dai da Azumin shekara guda"-(Muslim 1162). Hanya ce ta samin kusanci ga Allah da SOYAYYARSA. AZUMIN zai kasance daga gobe LAHADI 13 ga RABI'UL AWWAL Har zuwa TALATA 15 ga wata. N.B: RANEKUN ZAI KASANCE : LAHADI LITININ TALATA Allah Ta'ala ya bamu iko https://t.me/Addininassiha

Kuma kije ki yiwa mijin naki sihiri idan ALLAH yasa mai kula da sallah ne akan lokacinta wani da yayi alwala ma sai sihirin ya rage ƙarfi, da yayi sallah sihirin ya karye, haka dai zakita yawo kiyita bin bokaye, kinayi yana karyewa harsai kin mutu kina aikata shirka, kuma kije ki shiga wuta. ALLAH kabamu ikon aiki da abinda muka karanta. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

MATAN AURE DA 'ƳAN MATA """"""""""""""'''''''"""""""""""""""''''"""""""""""""""""" Da yawa matan aure na halaka, suna zama mushrikai ta hanyar bin malamai masu yi musu sihiri da manufar taimako. Matan aure suna zuwa gurin malamai domin neman mallake miji ko uwar miji da sauransu, sai dai kuma shi sihiri kafurci ne. Waɗannan da kuke ganinsu kamar malamai sun tara Alƙur'anai ga manyar carbi da yawansu bokaye ne. Da yawan 'ƴan mata suna rasa imaninsu, suna shirka ta dalilin zuwa gurin malamai da niyyar meman taimako akan wani saurayi daga ƙarshe saiki zama mushrika baki sani ba. Duk malamin da kikaje gurinsa dan neman taimako akan mijinki ko saurayinki yace miki za'ai miki aiki to boka ne, ki tashi ki bashi guri. Domin babu wani aiki da zai miki daya wuce ya baki rubutu ko wani garin magani ko laya ko yasa ayi yanka daga nan kuma sai a faɗa cikin halaka, dake dashi duk ku shiga wuta. Duk malamin da ki kaji yace miki za'ai miki addu'a amma da sharaɗi, za'ayi yanka, to boka ne, kitashi ki bashi guri, babu wata addu'a da take da sharaɗi sai anmata yanka ALLAH zai karɓa. Duk malamin da ki kaje gurinsa neman shawara akan mijinki yace to ki kawo kuɗi kaza ko zaki biya kuɗi kaza to ba malamin ALLAH bane ki tashi ki bashi guri, ɗan damfara ne. Malaman sunnah basa karɓar kuɗin kowa, saidai su ɗoraki akan hanyar da zakibi ki samo kan mijinki bisa hanyar koyarwar Manzon ALLAH {s.a.w}, ki sami lada kuma ki sami aljanah kuma ku zauna lafiya da mijinki. Babu wata addu'a da take da sharaɗin sai anyi yanka, shi yanka idan kinaso, bayan kin roƙi ALLAH da kanki akan wata buƙata taki ko akan mijin naki, koma wacce irin bukata ce, idan kinada halin da zaki iya yanka duk abinda ALLAH ya azurtaki dashi na halal sai ki yanka, Sannan ki dafa abinki kici a cikinki yaranki ma suci, ki aikawa maƙobta suma da niyyar ALLAH ya biya.miki dukkan buƙatunki, wannan kaɗai ya isar miki a gurin ALLAH {S.W.T}. Amma kada ki yarda wani malami yace ayi yanka kuma ki yarda, amma akan kanki ya halatta kiyi babu wanda ya saki ke kika ga dama kikayi a binki don ALLAH. Saboda haka ki dafa kowa yaci da mijiki da 'ƴa'ƴanki suci suyi farin ciki ALLAH zai biya miki buƙatarki saboda dalilin farin cikin da kika saka mijinki da yaranki. Manzon ALLAH {s.a.w} yace: Sadakar da tafi falala itace sadakar da aka bada ita ga ɗan uwa tana da lada biyu, ga ladan sadaka ga ladan zumunci. Sannan ki tashi cikin dare ki kyautata alwala, kiyi sallah raka'a biyu ki roƙi ALLAH dukkan matsalolinki acikin sujadarki ta sallah, sannan ki yanka duk abinda ALLAH ya hore miki, ki dafa kuci keda mijinki da 'ƴa'ƴanki da niyyar sadaka. Ko kuma ki sami alawa ki rabawa yara sadaka don neman yayewar dukkan damuwarki insha ALLAHU TA'ALAH zaki sami biyan buƙatarki daga ALLAH amma basai kinje wani malami yana cinye miki kuɗi kuma ya jefaki ga aikata shirka. Don haka yaku mata kuji tsoron ALLAH ku kiyayi bin malaman tsubbu, malaman-nan ba malamai bane bokaye ne, kawai neman kuɗi sukeyi da ayoyin ALLAH. Da yawansu sun kafurce, zasu iya aikata komai akan kuɗi, wasu daga cikinsu suna neman matan mutane suce sai ya kwanta dake sannan zaki sami biyan buƙata, ko kuma yayi rubutu a jikin azzakarinsa ya kwana dake wannan ai ba ƙaramin kafurci bane. Akwai matan da sunje gurin irinsu sun san komai, sun san yadda malaman suke, basu da kunya ko kaɗan, babu tsoron ALLAH a tattare dasu, ko mutum kikeso a kashe zai iya kashewa akan kuɗi. Akwai masu luwaɗi da maza, idan namiji yaje neman taimako sai suce sai anyi luwadi dashi sannan zai sami biyan buƙata. Ku rinƙa neman shawara gurin malaman sunnah su sanar daku hanyoyin da zakubi, ku sami mallakar mazajenku cikin sauƙi ta hanyar neman yardar ALLAH, kuma ba tareda kin kashe ko sisi ba. Ku sani da yawansu 'ƴan damfara ne, ku kula sosai, kada su damfare muku imaninku, su kuma damfare muku kuɗa-ɗenku.

LITTAFIN UMDATUL AHKAM °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° LITTAFIN TSARKI °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° HADITHI NA [11] °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° An karɓo dag Anas Ɗan Malik (R.A) cewa: Manzon ALLAH {s.a.w} Ya kasance idan zai shiga banɗaki yakanyi addu'a sai yace: بِسْمِ اللهِ اللّهُـمَّ إِنِّـي أَعُـوذُ بِـكَ مِـنَ الْخُـبْثِ BISMILLAH ALLAHUMMA INNEE A'UZU BIKA MINAL-KHUBTHI WAL-KABA-ITH. Ya ALLAH ina neman tsarinka daga sharrin Aljani namiji da Aljana Mace. SHARHI: Wannan hadithi yana mana nuni da yadda Manzon ALLAH {s.a.w} ya kasance yana neman tsarin ALLAH daga sharrin Aljanu maza da mata kafin ya shiga baɗaki. Sannan hadithin yana tabbatar mana samuwar wasu halittu wato Aljanu, domin akwai masu inkarin cewa babu Aljanu a duniya. Sannan hadithin yana tabbatar mana da banɗaki yana ɗaya daga cikin wajen zaman Aljanu. Sannan kuma hujjane akan cewa suma daga cikinsu akwai jinsin maza da mata, kuma ana neman tsarin ALLAH daga sharrinsu domin su masu sharri ne, suna iya cutar da ɗan Adam. Dadai sauransu. ALLAH shine mafi sani. ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu.

MU GYARA TAUHIDIN MU """""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""" DARASI NA [16] YADDA MAZA DA MATA KE AFKAWA SHIRKA °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Da yawan maza da mata na yiwa ALLAH shirka a dalilin neman arzuki, neman dukiya, neman duniya, neman kuɗi, neman abinci da neman mulki ko mallake miji ko dangin miji ko wanin haka. Zaka ga mutum yana aiki a wata ma'aikata, ko yana kasuwanci, ko yana sana'ar hannu, ko yana tuƙin mota daga gari zuwa gari, ko yana aikin police ko soja, da dai sauransu, Amma yana zuwa gurin malamai suna bashi rubutu yana sha, ko su bashi laya ya binne ko ya rinƙa yawo da ita, Ko su bashi wani ƙulli aje a binne a wani guri ko acikin shagonsa ko ma'aikatar da yake aiki. Ko suce a rinƙa yanka wata dabba duk sati ko wata ko wanin haka, saboda neman biyan buƙata, alhali malami nee yace a yanka dabbar, shi kuma umarnin aljani yabi. Ko su bashi wani sabulu ya rinƙa wanka dashi, wai sabulun sa'a ko kuma tsarin jiki. Ko su haɗa masa turare na sawa ajiki, wanda idan ka shafa ajikinka ko a hannunka ka shiga kasuwa zakayita cikiniki. Ko su bashi turaren wuta kamar ydda mata ke turarawa a ɗaki, wai kana amfani dashi da sunan tsarin jiki, wanda yake bana korar aljanu bane, kawai wannaan na tsafine aka baka. Ko abaka wani kwalli na mallaka ko wand a idan ka haɗa idon da mace ko wacce kakeso zata manne maka. Ko su bawa mutum wani hatimi ya rinƙa karantawa kafin ya fita daga gida izuwa aiki ko kasuwa, wai saboda tsarin jiki ko waninsa. Ko su bawa mutum wani abu ya ɓoye a wani lungu a shagonsa ko office ɗinsa dadai sauransu. Ko kuma kaga an rataya wani abu acikin ƙohon rago ko wanin sa, a soron gida wai na tsari ne, ko maganin ɓarawo. To duk wanda ya aikata ɗaya daga cikin waɗanan abubuwa haƙiƙa ya sani ya aikata shirka da ALLAH, idan ka mutu acikin wannan aiki, bai tuba ba, to ya mutu kafiri kuma zaka dawwama acikin jahannama. Haka kuma da yawan mata sukanyi shirka da ALLAH akan neman mallake saurayi ko miji, kaga buduruwa tana yawo gurin malamai tana neman wani abu wai saboda ta mallake saurayinta. Ko kaga matar aure tana yawo gurin malamai lungu da saƙo da cikin ƙauyuka tana neman abinda zata mallake mijinta, ta yadda duk abinda takeso zaiyi. Wasu matan kuma suna amfani da wani irin jan miski wanda yake da asirin mallaka acikinsa, idan ta shafa a jikinta ko a gabanta, idan mijinta ya kusanceta, kusanta ta aure, to shikenan sai ayi sati ana juyashi, sai yadda tayi dashi. Wasu kuma acikin abinci suke haɗa sihirin, harda masu yin tsarki su haɗawa namiji lemo da ruwan tsarki ko miya ko wanin haka duk saboda a mallake miji. Wasu kuma suyita binne-binne ko a aje a samo zuciyar wata dabbar a haɗa da laya a bawa kare ya cinye ko wanin haka. Wasu kuma 'ƴan kasuwa ne ko aikin gobnati amma komai nasu suna aiki da malamai suna musu tsubbu, ko tace a duba mata mezai faru da ita, ko a duba mata wane irin miji zata aura, ko kuma ta bada sunan saurayin wai ayi mata istikhara ko waninsa. To ku sani duk wacce take aikata irin wannan haƙiƙa ta aikata shirka da ALLAH, kuma idan ta mutu acikin wannan aiki bata tuba ba, to zata mutu kafira kuma zata dawwama acikin wuta. ALLAH ka nesantamu da yi maka shirka. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

1• Buɗe al'aura ga mace ko namiji acikin gida, kamar mace ta zauna tsirara zindir, ko ta sanya tufafi mai shara-shara marasa kauri kuma tazo ta tsaya gaban madubi, tana mamakin kyawun da take dashi, To adai-dai wannan yanayi idan akayi rashin sa'a Aljanin soyayya yana kusa, sai kawai yayi sha'awarta, kuma yaji ya kamu da sonta kawai sai ya shiga jikinta. 2• Haka kuma idan mace ko namiji suna kwantawa tsirara awaje, misali lokacin zafi kuma mutum ya kwanta bai ambaci sunan ALLAH ba, To adai-dai wannan yanayi namijin dare ko macen dare kanyi sha'awar mutum, kuma su shiga jikin mutum. 3• Idan mace ko namiji na shiga ban-ɗaki wajen wanka a tsirara ko shiga Ruwa kamar: • Kogi. • Gulbi. • Kududdufi. Don yin wanka a tsirara kuma mutum ya shiga basu ambaci sunan ALLAH ba. To adai-dai wannan yanayi namijin dare ko macen dare kan iya samun sauƙin shiga jikin mutum kuma ya aureta ko ta aureshi. 4• Idan mace tana bayyanar da adonta a titi ko a tsakan-kanin mutane,namijin dare na iya kai mata hari. 5• Idan Mutum namiji na saduwa da Iyalinsa ba tare da ya ambaci suannan ALLAH ba, shaiɗanin Aljani kan samu damar shiga jikinsa ko jikin Iyalin tasa. 6• Idan mutum ya sadu da Iyalinsa alhalin Iyalin nasa tana haila to namijin dare zai rigashi saduwa da ita. Idan ta samu ciki sai abinda aka samu ya zama ɗan Aljani, sai ku kasa gane kansa yayita wahalar daku. 7• Idan mace ko namiji na kwana shi kaɗai a ɗaki musamman mutum baya ambaton sunan ALLAH yayin kwanciya barci. To namijin dare ko macen dare na iya shiga jikin mutum. 8• Idan mutum na zama bakin ƙofar ɗaki ko zama gurin da yake rabin jikinsa a inuwa rabi a rana, to anan ma Aljani na iya shiga jikin mutum. Idan mutum yana yawan sauraron kaɗe-kaɗe ko zama cikin ɗaki da aka manna hituna ko ratayesu na mutum ko na wata dabba, to nan ma Aljani na iya shiga jikinsa. 9• Idan mace ya zama tana bayyanar da gashin kanta a waje, ko saka turare mai ƙarfi tana, to a dalilin wannan ma Aljani yana iya shiga jikinta. 10• Idan mutum ya zama yana zuwa wajen malaman tsubbu, ko malaman sauro masu bugun ƙasa da duba, ko boka, to Aljani yana iya shiga jikinsa. 11• Idan yamma tayi sosai, to an hana barin yara a waje, suna wasa, domin wannan lokaci ne da 'ƴa'ƴan Aljanu suke wasanninsu, to suna iya shiga jikin yaran mutane. 12• Idan yaro yana yawan wasa da ruwa sosai da sosai, musamman mace, to Aljani yana iya shiga jikinta, sai ta girma ya jefa mata Infection kuma ya ɗauke mata sha'awa gaba ɗaya ayita faman shan maganin sanyi amma yaƙi aiki. 13• Idan mutum yana kwanciya cikin haskeda daddare baya kashe fitila, kuma baya ambaton ALLAH, to Aljani na iya shiga jikinsa a wannan dre, Saboda sshaiɗanun Aljanu na yawo cikin dare, duk inda suka hango fitila sukan tafi gurin. ALLAH shine mafi sani. ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

HULƊA TSAKANIN ALJANU DA ƊAN ADAM ===================================== DARASI NA [2] DALILIN HULƊAR SU DA ƊAN ADAM °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Bayanan da suka gabata zasu iya gamsar damu cewar lallai akwai hulɗa tsakanin Aljanu da mutane. Masana al'adun Hausawa sun fitar da dalilai guda uku dake sa Aljanu mu'amula da mutane. Dalilan kuwa sune kamar haka: 1• QIYAYYA. 2• TSORO. 3• QAUNA /SOYAYYA. Bayanin ko wanne zaizo kamar haka: 1• Idan mutum ya aikata waɗannan abubuwa ga Aljanu kamar haka: • Cutar dasu. • Cutar da 'ƴa'ƴansu. • Cutar da Tsofaffinsu. • Kona Gidajensu. • Kwararawa Gidansu Ruwan zafi. Da dai sauransu. To Aljanu sukan ƙulla ƙiyayya da wannan mutum, kuma su ɗauki niyyar ramuwa a gareshi. Wannan zai kai ga Aljanu su shiga jikin mutum sannan su raunana masa lafiyar jiki. 2• Haka kuma a dalilin tsoro mai tsanani, irin wanda yake mantar da mutum tuna ALLAH ko ambaton ALLAH. To a dai-dai wannan lokacin Aljanu na samun daman shiga jikin mutum, musamman idan mutum baya yiwa ALLAH biyayya. Haƙiƙa rashin yiwa ALLAH biyayya yana ƙarawa mutum jin tsoro mai firgitarwa, kuma yana sanya shaiɗani ya ƙara jefa masa jin tsoronsa, sai tsoron yayi tasiri akansa, kamar faɗar ALLAH {S.W.T} Wancan shaiɗan ne kawai yake tsoratar da masoyansa, to kada kuji tsoronsa, kuji tsorona, idan kun kasance muminai. [Alƙur'ani sura 3: Ayata 175] 3• A dalilin soyayya ko ƙauna tsakanin Aljani da mutum. Idan Aljanu na sha,awar surar jikin mutum ko dabi'unsa da sauransu sai su nemi yin hulɗa dashi ko ƙulla alaƙa dashi. A wajen irin wannan hulɗar, shi Aljani yakan bayyana a cikin kamannin mutum kyakkyawa yadda bazai tsoratar da abokin hulɗar tasa ba, wani lokacin kuma yakan bayyana ne acikin surar mutumin da aka saba hulɗa dashi. HULAR TA KASU KASHI BIYU °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° 1• Hulɗa tsakanin jinsi daya. Wato kamar a samu hulɗa tsakanin namijin Aljani da namijin ɗan adam, ko hulɗa tsakanin macen 'ƴar adam da mace Aljana. 2• Akwai kuma hulɗar soyayya da ƙauna ta banbancin jinsi. Wato tsakanin namijin Aljani da mace 'ƴar adam, ko mace Aljana da namiji ɗan adam. Daga cikin irin wannan hulɗa ake samun namijin dare ko macen dare. MA'ANAR NAMIJIN DARE DA MACEN DARE °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Namijin dare ko macen dare wani nau'in Aljani ne daga cikin Aljanu wanda yake auren mace 'ƴar Adam yana saduwa da ita (jima'i). Ko kuma Aljana mace ta auri mutum ɗan Adam ta rinƙa saduwa dashi ta hanyar mafarki ko a farke, musamman cikin dare. Irin wannan saduwa takan haddasa cututtuka ga jiki ko zuciyar ɗan Adam. Malaman Ruƙya na kiran irin wannan iska da sunan Aljanin ko Aljanar soyayya. AURE TSAKANIN ALJANI DA MUTUM °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°′°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Malaman addinin muslinci, musamman waɗanda suka zurfafa acikin sha,anin Ruƙya da aikin asibiti, sun tofa albarkacin bakinsu dangane da wannan matsala ta aure tsakanin Aljani da ɗan Adam. Abinda ya tabbata ga malaman Ruƙya shine: Auren yana yiyuwa, amma bai halatta ba a shari'ah. Wato Namijin Aljani na iya saduwa da mace 'ƴar Adam, ko ɗan Adam ya sadu da mace Aljana, kuma su samu jin daɗi irin wanda akeji na saduwa amma shari'a ta ƙyamaci aikata hakan. Saboda an tambayi Imam Malik ɗan Anas (R.h) cewa: Wani Aljani yazo yana neman a bashi wata bazawara aure? Sai Imam Malik (R.h) yace: Banga illa ba ga hakan, sai dai ina ƙyamar idan macen tayi ciki idan an tambayeta, waye mijinki? tace wani Aljanine. To wannan zai haifar da ɓarna da fasadi a cikin muslinci. ALLAH {S.W.T} ya ƙara yi mana katangar ƙarfe dasu. DALILIN SHIGAR NAMIJIN DARE/MACEN DARE JIKIN MUTUM Daga cikin dalilan dake jawo shigar Namijin dare ga mace 'ƴar Adam sune kamar haka:

Duk waɗannan wuraren da Hausawa ne ke cewa mazaunin Aljanune, kuma mafi yawansu malaman Ruƙya da littattafan Muslinci sun tabbatar da hakan. Wannan tabbatarwar na daga cikin abubuwan da suka ƙara ƙaimin imanin Bahaushe da Aljanu kuma hakan ya ƙarfafa shi wajen cigaba da mu'amala dasu. Duk da samun wayewar kai na zamani da bunƙasar ilimin Addinin Muslinci. ALLAH shine mafi sani. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

HULƊA TSAKANIN ALJANU DA ƊAN ADAM DARASI NA [1] NAMIJIN DARE KO MACEN DARE Wato hulɗar soyayya dake gudana tsakanin mutum da aljan, Ma,ana: Tsakanin macen mutum da Aljani namiji ko tsakanin Aljana mace da mutum namiji. MATSAYIN ALJANI A WAJEN HAUSAWA Masana sl'adun Hausawa sunyi rubuce-rubuce da dama akan Aljanu da matsayinsu a rayuwar bahaushe. Sun kuma tabbatar da imanin Bahaushe akan samuwar aljanu, duk da yake baya ganinsu, amma yayi imani da samuwarsu da kuma kasancewarsu ɓoyayyu, masu kuma ban tsoro, masu ƙarfi akan mutane, kuma masu iya cutar dasu. Za,a iya fahimtar hakan tun daga sunayen da Bahaushe yake kiransu dashi. Bahaushe yana kiransu da waɗannan sunaye kamar haka: • ISKOKAI. Wannan suna ya samo asaline daga bahaushe saboda baya ganinsu kamar yadda baya ganin iskar da muke shaƙa. • MASU ABU. Shi kuma wannan sunan ya samo asaline saboda su aljanu suna nuna isa ga dukkanin abinda suke nufin aikatawa ko suke buƙata. • MUTANTANI. Wannan kuwa saboda sunyi tarayya da mutane ta ɓangaren jinsi da hali. Abin nufi shine: Suna da jinsin maza da mata, suna aure kuma suna haihuwa, kuma suna cin abinci da dai sauransu. Koda yake imanin Bahaushe a zamanin baya , ya yarda cewa , Aljanu basa mutuwa, amma yanzu malaman ruƙya, sun tabbatar da cewa aljanu suna mutuwa. Sai dai suna da tsawon rayuwa ba kamar mutane ba. Ta fuskar yadda Bahaushe ya fahimci Aljanu kuwa: 1• 'Ƴan bori suna ganin cewa akwai farare da baƙaƙe. • Fararen sune masu sauƙin mu'amala da mutane. • Baƙaƙeen kuwa sune masu mugunta da sharri. 2• Malaman da suke ruƙya sun kasasu kaso biyu dangane da mu'amala dasu. 1• Musulmai. 2• Kafirai. Bayan bayyanar muslinci a ƙasar Hausa, Bahaushe ya fara amfani da sunaye irin haka wajen kiran aljanu: • Aljani. • Ifritai. • Rafani. • Shaidani. Da dai sauransu. Dalili kuwa saboda waɗannan sunaye sunzo acikin nassin Al-ƙur'ani da Hadisin Manzon ALLAH {s.a.w} Saboda haka a yau, Bahaushe yafi amfani da waɗannan sunaye, saboda sunfi kusanci da addininsa na Muslunci. WURAREN ZAMAN ALJANU Kamar yadda yake kowane abu mai rai ko mara rai yake da mahalli-wajen zama, haka suma aljanu suke da nasu mahallin-wajen zaman. Bahaushe yayi imani da cewar aljanun dake rayuwa a ƙasar Hausa suna rayuwa a ko'ina a ƙasar Hausa. Suma sunan yare-yare, yadda mutane suke yare-yare suma haka suke yare-yare. Sannan kuma akan samesu a wurare sanannu kamar guda huɗu, sune kamar haka: 1• Wajen Gari. 2• Cikin Gari. 3• Cikin Gida. 4• Jikin mutum. Waɗannan wurare duk aljanu suna zama kamar yadda bayanai zasu zo akan hakan ɗaya bayan ɗaya. Wuraren zaman Aljanu a wajen Gari suna zama a wurare kamar haka:- 1* Kan Duwatsu. 2* Gindin Manyan Bishiyoyi/Itatuwa. kamar haka:- • Bishiyar Kuka. • Bishiyar Tsamiya. • Bishiyar Gawo. • Bishiyar Gamji. • Tumfafiya. Da dai sauransu. 3* Dokar Daji. 4* Cikin Ruwa/kogi. 5* Gidajen Tururuwa. 6* Fako/Tsan dauri. 7* Suri[Kunkuwa. 8* ]Tsohuwar Rijiya. Da dai sauransu. Dukkan waɗannan wuraren da Aljanu ke zama ne a wajen gari inda babu mutane. WURAREN ZAMAN ALJANU A CIKIN GARI Sune kamar haka:- 1• Mararrabar Hanya. 2• Kangon Gida. 3• Makabarta. 4• Juji ko Bola da wuraren zubar da shara. Da dai sauran su. Dukkan waɗannan wuraren da Aljanu ke zama ne acikin Gari tare da mutane. WURATEN ZAMAN ALJANU ACIKIN GIDA Sune kamar haka: 1• Ban ɗaki. 2• Tsakar Gida. 3• Ƙofar ɗaki. 4• Turakun Dawaki. Da dai sauransu. Duk waɗannan wuraren da Aljanu suke zama ne acikin Gidan da mutane ke rayuwa. WURAREN ZAMAN ALJANU A JIKIN MUTUM Shine: Suna zama a ko'ina ajikin mutum, amma inda sukafi zama shine acikin ƙwaƙwalwa. Wannan yana da dangantaka da kiransu da suna ƙwanƙwamai.

HATTARA MAZA DA MATA """""""""""""""""""""""""""""""""""'''''""''''''''''''''''' Akwai wata masifa dake faruwa a cikin ƙasashen duniya, wanda abin muma ya shigo mana ƙasarmu Nigeria. Masu sana'ar Comedy sai su sami musulma akan hanya wacce tayi shiga ta mutunci harda liqab, sai suyi mata sallama, bayan ta amsa, Sai wani yace zai bata kuɗi kamar 20k ko 50k ko sama da haka, amma yana so kawai ta cire pant nata anan take ta nuna masa saita ta maida abinta. Alhali kuma akwai mai Camera a laɓe, bata san ana ɗauka ba. Wato sunayin haka ne domin su nunawa duniya cewa musulmai mata da suke ƙunshe jikinsu cikkn hijab da liqab duk na ƙarya ne, da sunga kuɗi zasu iya bada kansu. Sai bayan ta cire ta bashi ya tabbatar ta cire ɗin, sai ya mayar mata da abinta, sannan sai ya bata kuɗin 20k ko 50 ko sama da haka, nan take. Videos ɗin suna-nan suna yawo a You Tube da sauransu. Ita wacce akace ta cire panta nata, lokacin da zata cire bazama ta sani ba, saboda yanayi na talauci da kuma buƙatu na yau da kullum da ake ciki, Amma kuma daga baya sai tayi nadamar da za taji dama batazo duniya ba, domin zasu yaɗa wannan video a duniya, su nuna da yadda kika cire pant naki akan hanya akan wasu 'ƴan kuɗaɗe. To wannan yayi nuni da cewa kenan idan a ɓoyene zaki iya bada kanki ga zina akan wasu 'ƴan kuɗaɗe saboda magance wata matsalarki tanan duniya, kuma ki rushe lahirar ki. Hattara mata, kuji tsoron ALLAH, kada siffarku ta bayyane ta banbanta da siffarku ta ɓoye. Kada ki bari kyan shigarki yafi kyan halinki, wannan yana jawo mummunan ƙarshe da kuma mummunar azaba a ranar alƙiyama. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

TAMBAYA AKAN GAƁƁAI A RANAR ALƘIYAMA :::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::: • Dukkan Ɗan Adam yana da gabɓai guda 360 a sassan jikinsa, kuma yana aiki dasu ga aikata alkhairi ko sharri. • Babu wata gaɓa a sassan jikin Ɗan Adam face sai ALLAH yayi masa tambaya akan abinda ya aikata da wannan gaɓa. • Duk abinda kayi tunani, ko ka ɓoye ko ka bayyana acikin zuciyarka, ko ka nufi aikatashi sai ka fasa saboda baka sami ikon aikatawa ba, to za'azo maka dashi gaba ɗayansa a ranar alƙiyama kuma sai anyi maka hukunci akansa. • Duk abinda zuciyarka ta umarci bakinka ya faɗi anan duniya alkhairi ne ko sharri, to za'azo maka dashi a ranar alƙiyama kuma sai anyi maka hukunci akan kowannensu. • Duk abinda idanuwanka suka kalla anan duniya alkhairi ko sharri suma za'azo maka dasu a ranar alƙiyama kuma za'ayi maka hukunci akan kowannensu ɗaya bayan ɗaya. • Duk abinda hannunka ya aikata harafi ɗaya ka rubuta ko waninsa, ko ya taɓa halal da haram ko ya ɗauki abin wani, to duk za'azo maka dasu a ranar alƙiyama kuma sai anyi maka hukunci akansu. • Duk abinda ka aikata da ƙafarka, rawa kayi ko tafiya kayi, gurin biki kikaje, ko yawan bin samari, ziyara kaje ko duba mara lafiya, masallaci kaje ko kallon ƙwallo koma me ka aikata dasu tabbas za'azo maka dasu gaba ɗayansu kuma za'ayi maka hukuncin akansu a ranar alƙiyama. • Duk abinda ka saurara da kunnenka karatu ne ko waƙace, zage-zage ne ko nasihohi, gulma ce ko kuma wa'azi ne, to suma za'azo maka dasu a ranar alƙiyama, kuma za'ayi maka hukunci akansu. • Duk irin baiwar da ALLAH yayi maka ajikinka, kyau yabaka sai kayi amfani dashi ka saɓa masa ko kayi girman kai, ko kayi yaudara da kyan naka, ko ilimi ya baka sai kayi amfani dashi wajen saɓawa ALLAH, to suma za'a tattarosu a kawosu gaban ALLAH kuma sai anyi maka hukunci akansu. • Duk abinda kaci ko kasha halal ne ko haram suma za'azo maka dasu a ranar alƙimaya kuma sai anyi maka hukunci akansu. • Duk abinda ka aikata da al'aurarka istimina'i (zinar hannu) ko zina kayi da mace ko maɗigo ko luwaɗi koma me kayi tabbas za'azo maka dasu a ranar alƙiyama kuma sai anyi maka hukunci akansu. • Duk abinda ka aikata na zunubi kona alkhairi tabbas zaka sami sakamakonsa a gaban ALLAH a ranar alkiyama, kuma za'a bawa kowa sakamakonsa gwargwadon abinda ya aikata anan duniya. • Don haka mu yawaita istigfar, mu nisanci manyan zunubai, sai ALLAH ya gafarta mana ƙananun zunubai ta hanyar kyautata alwala, ta hanyar murmushi ga musulmi, ta hanyar magana mai daɗi, ta hanyar kyautatawa matarka ko mijinki, ta hanyar sauke hakkin maƙobci, ta hanyar kyautatawa iyaye da sauransu. ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

Bayan gari ya waye sai suka gano basuyi sallah akan alƙibla ba, sai suka bawa Annabi {s.a.w} labari, sai yace laiial sallarku tayi, kuma baice su sake sallah ba. Saboda haka idan hadithi yazo ya warware wata matsala sai kuma aka sami maganar malamai taci karo da hadithin, to sai a ajiye maganar malamai a ɗauki hadithi muyi hukunci dashi, shi kuma malamin mu nema masa dacewar ALLAH. MALAM YACE: Dukkan mayarwa a cikin lokaci mustahabbine dukkan abinda ake mayarwa na daga sallah a cikin lokaci, to ba’a yarda sallah tserarriya da nafila. Ma'ana: Malam yana nufin idan sallah ta farillah ta wuce mutum, bai samu ya yita akan lokacin ta ba, a dalilin bacci ko mantuwa, to idan ya tunata, to ya ramata a daidai lokacin da lokacin daya tuna ta, wajibine akansa wannan. Idan kuwa bai tuna ba, sai bayan wucewar lokacinta, to wajibi ya ramata a wannan lokacin daya tuna ta. Idan kuma yaƙi ramata a lokacin daya tuna ta, yace sai lokacin wata sallar irinta ya zagayo sannan zai ramata, to wannan yana da zunubi mai girma, dole sai dai ya ramata a lokacin daya tuna ta. Sannan malam yace idan sallar nafila ta wuce mutum, baiyi ta a daidai lokacinta ba, to ba wajibi bane a ramata, amma ga wanda yaso saiya ramata. ALLAH shine mafi sani. Duk mai neman ƙarin bayani yayi mana magana ta private. ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.