en
Feedback
ADDININ NASIHA

ADDININ NASIHA

Open in Telegram

ADDININ NASSIHA TAKU CE DOMIN TUNATARWA, NASSIHA, SAMUN KARATUTTUKAN MALAMAN SUNNAH IN SHA ALLAH ADMINS KADAI SUKE DA DAMA TURA SAKO CIKIN GROUPE MU DALIBAI NE BA MALAMAI BA MUNA ROQON ALLAH YA SA MANA IKHLASI KUMA YA HADAMU A CIKIN GIDAN AL-JANNAH.

Show more
The country is not specifiedReligion & Spirituality115 078
773
Subscribers
+124 hours
+227 days
+10330 days
Posts Archive
Babbar Matsalar Mu Kai Yara Makarantun Kiristoci Ba Abunda Zai Canza Sai Mun Canza Taron Malaman Kiristocin Duniya Akan Al'ummar Musulmi Yadda Za'a Raba Musulmi Da Allah Halin Da Muke Ciki Ba Mala'iku Ne Zasu Su Gyara Mana Ba Yakar Abu A Zuciya; Kin Abu Na Gaskiya A Cikin Zuciya Duk Wadanda Kuke Cewa Maɓarnata Ne Ku Guje Su, Ku Daina Girmama Su A Tsarin Musulunci Ba Shugaba Kaɗai Za'a Zarga Ba Akan Zaluncin Mai Mulki Kwamitin EFCC Ba Mu'amala Ina Musuluncin Yake ❓ Dole Mu Bambanta Da Wadanda Ba Musulmi Ba Daga: Prof. Ibrahim Ahmad Aliyu https://youtu.be/7VLeQl00bjc

Hukuncin Ambaton Bismillahi Har A Wajen Aikin Banza.mp33.17 MB

04. Sharhus sunnah 4.mp313.48 MB

SHARHUS-SUNNAH ☘ 📚 Karatun Littafin Sharhus-Sunnah 📚 📚📖📓 04 Gabatarwar; Ash-Sheikh Abu-Abdurrahman Muhammad Auwal Adam Albaniy Zaria [Rahimahul-laah] Rana: Daren Laraba 24 ga watan Muharram, 1435 wanda ya yi dai dai da 26 ga watan November 2013.   Wuri: Daarul Hadeethis Salafiyyah Zaria, Kaduna State, Nigeria   Daga Cikin Muhimman Abubuwan Da Malam Ya Tattauna; 1. Muraji’an Karatun Baya, Tare Da Bayani Kan Zamunnan Da Baghawiy Ya Rayu Cikin Su. 2. Daskarewar Ƙwaƙwale Da Ustazai Ke Fama Da Ita! 3. Nasiha Ga Ma’aikatan Gwamnati. 4. Bayani Kan Mutuwar Ƙwaƙwale Da Ta Samu Ƴan Boko, Malamai, Matasa Da Sauran Su. 5. Tsokaci A Kan Ash-Sheikh Abdur-razaq Yahya Haifan Da Mutanen Yola. 6. Gwamnatin Mursi A Ƙasar Masar. 7. Yadda Ƙasar Malaysia Ta Cigaba. 8. Bayani A Kan Masallatan Arewacin Najeriya. 9. Yaƙin Salibiyyun [Christian Crusaders] . 10. Bayani Kan Gwamnatotin Ƴan Shi'ah; Buwaihawa Da Ƴan Badiniyyah. 11. Ƴan Bidi’a Su Shehu Dahiru Bauchi Da Sharu Saleh. 12. Wasu Bayanai Kan Daarul Hadethis Salafiyyah. 13. Bayani Kan Ƴan Fadimiyyah Da Kuma Kafurcin Su ❗ 14. Zaluntar Tarihi Da Aka Yi A Ɓangaren Aqeedah. 15. Shawarwari Kan Yadda Ake DA’AWA A ƘASASHEN DA AKE ZALUNCI. 16. Talauci Da Rashin Aikin Yi Ba Su Suka Kawo Boko Haram Ba! 17. Bayanai Kan Mai Yin Qasaru Da Kuma Mazaunin Gida. 18. Amsa Tambayoyi. Subscribe Our YouTube Channel; https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel

02. IN ANBIGI JAKI......mp36.01 KB

IN AN BIGI JAKI... ☘ 📚 In An Bigi Jaki... 📚 📚📖📓 02 Ash-Sheikh Albaniy Zaria Rahimahul-laah Rana; Daren Asabar 28 Ga Watan Rabi'ul Thaani, 1432 Dai Dai Da 1st Ga Watan April 2011. Wuri; Masallcin Aljaami'us-Salafiy [Masallacin Albaniy] Muciya, Sabon Garin Zaria, Kaduna St, Nigeria. Daga Cikin Muhimman Abubuwan Da Aka Tattauna: 1. Jayo Hankulan Mutane Akan Zaɓe. Subscribe Our YouTube Channel; https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel

01. IN ANBIGI JAKI......mp310.49 MB

IN AN BIGI JAKI... ☘ 📚 In An Bigi Jaki... 📚 📚📖📓 01 Ash-Sheikh Albaniy Zaria Rahimahul-laah Rana; Daren Asabar 28 Ga Watan Rabi'ul Thaani, 1432 Dai Dai Da 1st Ga Watan April 2011. Wuri; Masallcin Aljaami'us-Salafiy [Masallacin Albaniy] Muciya, Sabon Garin Zaria, Kaduna St, Nigeria. Daga Cikin Muhimman Abubuwan Da Aka Tattauna: 1. Gabatarwa. 2. Albaniy Ba Yaron Kowa Bane. 3. Amanar Da Allah [Swa] Ya Dankawa Duk Wanda Ya Ɗora Ga Shugabanci. 4. Gargadi Ga Duk Wanda Ke Kwadayin Shugabanci. 5. Yaya Titunan Nigeria Suke. 6. Halin Da Muka Samu Kan Mu A Nigeria. 7. Wutar NEPA. 8. Duk Wani Shuga Za'a Tambaye Shi Akan Talakawan Shi Har Akan Jaki. 9. Kula Da Tarbiyyar Yara. 10. Abubuwan Da Mace Zata Kiyaye Ta Samu Sassaucin Tambaya A Ranar Al-Qiyama. 11. Kafin A Kira Shugaba Adilin Shugaba. 12. A Musulunci Babu Secularism. 13. Kula Da Addinin Mutane. 14. Yan Siyasa Ba Ruwan Su Da Addini. 15. Jawabin Sir. Abubakar Tabawa Balewa. 16. Yan Siyasa Na Gaskiya Aiki Ne Yake Fassara Maganganun Su. 17. Babu Hukumar Da Take Tsarewa Mutane Mutuncin Addinin Musulunci. 18. Yaudarar Yan Siyasa Ga Malaman Islamiyyah. 19. Wanda Yafi Kowa Daraja. 20. Rikicewar Addini A Nigeria. 21. Martani Ga Yan Madakhila Akan Magana Akan Zaluncin Masu Mulki. 22. Babu Security A Nigeria. 23. Masu Mulki Nada Hannu A Wajen Hadurran Jiragen Sama. 24. Gidajen Yankan Kai A Nigeria. 25. Tsarewa Mutane Mutuncin Su. 26. Yunkurin Hana Sallar Juma'ar Da Muke Yi Karfe 9am Na Safe. 27. Bala'in Daya Faru A Lokacin Da Aka Fara Demokuradiyya. 28. Canji Muke Bukata. 29. Canjin Daya Faru A Kasar Tunisia. 30. Ina Ne Aka Dosa. 31. Ku Nuna Mana Ribar Demokuradiyyah. 32. Abunda Ya Karawa Yar Aduwa Hawan Jini. 33. Jama'ah Ku Staya Ku Kare Kuri'ar Ku. 34. Buhari Ba Zai Iya Gyara Kasar Nan Cikin Shekara 4 Ba. 35. Yadda Rayuwa Tayi Kunci A Kasar Gwana Da Gyaruwar Ta. 36. Ko Kun Zabi Buhari Zaku Haɗa Da Addu'a Ne. 37. Kasar Swizland A Karkashin Dukiyar Nigeria Suke Rayuwa . 38. Wadanda Ke Tare Da Buhari Corrupted Ne. 39. Jayo Hankulan Yan Bangan Siyasa. 40. Abunda Ya Faru A Tsakanin Yan Niger Delta Da Obasanjo. 41. Nigeria Babu Wani Mutum Ɗaya Da Zai Iya Gyara Ta. Subscribe Our YouTube Channel; https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel

Idan kuwa a cikin karatun fatiha ne ya ɓoye ko ya bayyana, to saiya sake wannan karatu, sannan kuma sai yayi sujjadah ba'adi daga ƙarshe. * Idan ya wuce da yin ruku’u, sai yayi sujjada dan barin bayyanawa sujjada ƙabali, yayi sujjada ba’adi dan barin ɓoyewa, idan ya kasance a cikin fatiha ne ko a cikin sura ita kaɗai. SHARHI: Idan kuma bai tuna da ya ɓoye karatu a gurin da ake bayyanawa ba, har ya riga yayi ruku'u, to bayan ya gama sallarsa, sai yayi sujjadah ƙabli, wato sujjuda guda biyu kafin sallama. Ida kuma bai tuna da ya bayyana karatu a gurin da ake ɓoyewa ba, har yayi ruku'u, to daga ƙarshe bayan ya gama sallarsa, sai yayi sujjadah ba'adi, wato sujjada guda biyu bayan sallama. * Wanda yayi dariya a cikin sallah, to sallarsa ta ɓaci, koda kuwa acikin manutuwane ko yana sane, ba mai yin dariya a cikin sallarsa sai gafalalle mai wasa. SHARHI: Idan mutum ya ƙyal-ƙyala dariya acikin sallah, da mantuwa ne ko kuma yana sane, to sallarsa ta ɓaci, amma murmushi baya ɓata sallah. * Shi kuwa mumini idan ya tashi yin sallah yana bijirar da zuciyarsa daga dukkanin wani abu sai ALLAH {S.W.T}. SHARHI: Mumini mai son rahmar ALLAH mai tsoron azabar ALLAH baya tunanin duniya acikin sallarsa sai dai ya rinƙa tunani akan wanda yake bautawa, wato ALLAH TA'ALAH. * Yana barin tunanin duniya da abinda ke cikinta har sai ya halartawa da zuciyarsa girman ALLAH {S.W.T}. SHARHI: Idan mumini yana sallah, yana haramtawa zuciyarsa tunanin duniya da duk wani abu da yake cikinta, baya tuna kowa sai ALLAH {S.W.T}. Tabbas abune mai wahala mutum yayi sallah baiyi tunanin wani abu na duniya ba, to amma abinda akeso, ya zama kada tunanin duniya yafi yawa acikin sallarka sama da tuna girman ALLAH, Bayan sanin sharaɗan sallah, abindake taimakawa sallar mutum ta karɓu, shine tunani akan girman ALLAH yafi tunani akan sha'anain duniy yawa. Duk sallar da tunanin duniya yafi yawa acikinta sama da tunani akan girman ALLAH da tsoron azabarsa da son rahmarsa, to wannan sallah bata zama abar karɓa. ALLAH shine mafi sani. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen. Duk mai neman ƙarin bayani yayi mana magana ta private.

MUSAN HUKUNCE-HUKUNCEN FIQHU [ 16 ] °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° BAYANIN RAFKANUWA A SALLAH NA UKU °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° * Wanda ya ƙara sura a raka’o’i biyu na ƙarshe babu sujjada a gareshi. SHARHI: Idan mutum ya ƙara sura acikin raka'a biyun ƙarshe wanda iya fatiha ake karantawa acikinsu kawai, kamar sallar azahar, ko la'asar ko magriba ko isha'i, to idan mutum ya manta, saiya ƙara wata sura bayan ya gama karanta fatiha, to babu komai akansa. * Wanda yaji an ambaci Annabi {s.a.w} yana cikin sallah sai yayi salati a gareshi, to babu komai a gareshi, koda ya kasance mai mantuwa ko kuma da gangan ko yana tsaye, ko yana zaune. SHARHI: Idan mutum yana sallah, sai yaji an ambaci Annabi {s.a.w} ko acikin karatun liman, ko daga wani guri yajiyo an ambaci Annabi {s.a.w} sai yayi masa salati acikin sallarsa, to babu komai akansa, koda a tsaye yake, ko a zaune, ko cikin ruku'u ko sujjada, to babu komai akansa, ma'ana ya halatta ayi hakan. * Wanda ya karanta surori guda biyu ko fiye da haka a cikin raka’a ɗaya, ko ya fita daga sura zuwa wata surar, ko yayi ruku’u kafin cikar sura to babu komai a gareshi acikin baki ɗayan waɗannan. SHARHI: Idan mutum yana sallah bayan ya gama karanta fatiha, saiya karanta sura sama da ɗaya, biyu ko uku ko sama da haka, to babu komai akansa, Ko kuma kuma yana cikin karatun surar kawai saiya katse karatun baije har ƙarshen surar ba, sai yayi ruku'u, to babu komai akansa. * Wanda yayi nuni da hannunsa ko kansa acikin sallarsa babu komai a gareshi. SHARHI: Idan mutum yana sallah, sai yaga wani yana neman wani abu baiga abinba, to idan kaida kake sallah kasan inda abin yake, ya halatta ka nuna masa babu komai, Ko kuma yayi maka tambaya alhali kana cikin sallah, ya halatta kaɗan motsa kanka domin nuni da na'am, misali: Idan yace najiraka mutafi unguwa tare, sai ka jijjaga kanka sama da ƙasa kana masa nuni da eh, ko kuma ka jijjiga kanka gefe da gefe kana masa nuni da a'a, to wannan babu laifi acikin sallah. * Wanda ya maimaita faitiha yana mai mantuwa yayi sujjada ba’adi, idan kuma da ganganne zance mafi ƙarfi sallarsa ta ɓaci. SHARHI: Idan mutum yana sallah, bayan ya gama karanta fatiha daidai, sai kuma ya sake maimaitata, amma bada nufin sura ta gaba ba, kawai yayine da mantuwa, to yayi sujjada ba'adi, wato sujjada guda biyu bayan ya gama karatun tahiya. Idan kuwa dagangan yayi yana sane, to malam yace sallarsa ta ɓaci, in kuma ya sake maimaita fatiha ne a matsayin sura mai zaman kanta, Misali: Bayan ya gama karanta fatiha, to a maimaikon ya ɗakko wata surar, sai kuma ya sake karanta fatiha a matsayin sura to babu komai akansa, musamman ga wanda bai iya karatun wata sura ba sai iya fatiha, amma idan ya iya wata surar to ya karanta wata surar shi yafi agareshi. * Wanda ya tuna sura bayan sunkuyawarsa zuwa ruku’u bazai dawo izuwa gareta ba. SHARHI: Idan mutum yana karantun sura a bayan ya gama karanta fatiha, sai kawai ya manta wata aya, ya kasa cigaba da karatun, har saida yayi ruku'u sai kuma ya tuna, to bazai ɗago ba, zai cigaba da sallarsa ne a haka, kuma babu komai akansa. * Wanda ya tuna ɓoyewa ko bayyanawa kafin ruku’u, to ya mayar da karatun, idan hakan ya kasance a cikin sura ne ita kaɗai ya sake ta babu sujjada a gareshi, idan kuma ya kasance a cikin fatiha ne ya sake yinta, yayi sujjadar ba’adi. SHARHI: Idan mutum yana karatu a cikin sallah, saiya ɓoye karatu alhali kuma gurin bayyanawa ne, sai bayan ya gama saiya tuna, to idan baiyi ruku'u ba, to ya sake karatunsa a bayyane. Idan kuma boƴewa akeyi a gurin, saiya bayyana, to daya tuna inhar baiyi ruku'u ba, to ya sake wannan karatun, saiya ɓoyeshi ayayin sakewarsa, amma idan ya kasance acikin karatun sura wannna matsalar ta faru, kuma babu wata sujjada da zaiyi a ƙarshe.

Hukuncin Ambaton Bisimillahi Har Wajen Aikin Banza Nasiha Zuwa Ga Masu Sabon Allah Tsokaci Akan Abunda Mawaka Da Yan Film Keyi Na Ambaton Sunan Allah Ba'a Cakuda Karya Da Gaskiya A Wajen Sabon Allah Ba'a Ambatar Sunan Allah Daga: Ash-Sheikh Dawud Azzahiriy Hafizahul-laah https://youtu.be/-yD2cEXvj60

Karancin Wutar Lantarki A Nigeria .mp34.79 MB

06. Bukhaariy.mp33.62 MB

SAHEEHUL BUKHAARIY ☘ 📚 Saheehul Bukhaariy 📚 [KITAAB; BAD`UL WAHYI] 📚📖📓 06 Gabatarwar; Ash-Sheikh Abu-Abdurrahman Muhammad Auwal Adam Albaniy Zaria [Rahimahul-laah] Date; Daren Lahadi 13 Jimadal-Ulaa 1429 A.H Daidai Da 17 May 2008 Wuri; Markazus Salafiyyah Zaria, Kaduna St, Nigeria. Daga Cikin Abubuwan Da Malam Ya Tattauna A Ciki Sun Haɗa Da; 1. Muraji'ar Darasin Baya. 2. Fara Wasika Da Sunan Allah. 3. Sunnah A Cikin Wasika. 4. Yadda Ake Yiwa Yahudawa Da Nasara Sallama Da Amsa Sallamar Su. 5. Kira Zuwa Ga Yan Boko Da Yan Siyasa Akan Interfaith. 6. Jayo Hankulan Sarakunan Kasar Hausa. 7. Addu'a Ta Musamman Ga Sarkin Musulmi Muhammadu Sada. 8. Hukuncin Daukar Al-Qur'ani Aba Wanda Ba Musulmi. 9. Shin Kiristocin Yau Da Yahudawan Yau Ahlul-Kitabi Ne Koba Ahlul-Kitabi Bane ❓. 10. Kiristoci Da Yahudawa Malaman Su Suna Yin Tsafi Da Duba 11. Kiristoci Yan Ta'adda Ne 12. Yahudawa Ba Suda GARI Subscribe Our YouTube Channel; https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel

Sahabbai Ƴan Gatan Allah.mp318.87 MB