ADDININ NASIHA
Open in Telegram
ADDININ NASSIHA TAKU CE DOMIN TUNATARWA, NASSIHA, SAMUN KARATUTTUKAN MALAMAN SUNNAH IN SHA ALLAH ADMINS KADAI SUKE DA DAMA TURA SAKO CIKIN GROUPE MU DALIBAI NE BA MALAMAI BA MUNA ROQON ALLAH YA SA MANA IKHLASI KUMA YA HADAMU A CIKIN GIDAN AL-JANNAH.
Show moreThe country is not specifiedReligion & Spirituality115 078
773
Subscribers
+124 hours
+227 days
+10330 days
Posts Archive
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
Idan ƴan Shi’a sun yarda da Alƙur’ani don me suke kafirta waɗanda ya yi wa shaida da imani, watau Sahabban Annabi(SAW)? Sai gogan naka ya yi turus! Allah ya tsarshe mu ɓata.
- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 1: "Aƙidar Ƴan Shi’a dangane da Alƙur’ani" - na Prof. Umar Labɗo
✍ AnnasihaTv
Call/WhatsApp: 08142286718
Twitter: https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
[DALILAN DA YASA ƳAN SHI’AH BA SA BUGA ƘUR’ANIN SU]
Wataƙila mai karatu ya yi tambaya: Don me ƴan Shi’a ba sa buga wannan tafkeken “Ƙur’ani” nasu, wanda ya ninka na Musulmi har sau uku, su sayar a kasuwa? Amsa ita ce, abinda yake hana su bayyana wannan littafi nasu shi ne taƙiya, watau munafunci da yaudara!! A haƙiƙa ƴan Shi’a ba Ƙur’aninsu kaɗai suke ɓoyewa ba; aƙidarsu ta taƙiya tana umarnin su da su ɓoye manyan littafan malamansu, waɗanda suka ƙunshi aƙidojinsu da manufofinsu, sai ga manyan mabiyansu waɗanda suka riga suka yi zurfi a cikin tafarkinsu.
Kaɗan daga cikin littafansu suke sayarwa a kasuwa, sauran sai dai a same su a manyan cibiyoyinsu da makarantunsu. Ƙur’aninsu kuwa, idan akwai shi cikakke, to babu shakka ba mai ganin sa sai manyan shaihinnansu, sai kuma almajirai amintattu.
Wannan ya sa ƴan Shi’a suke ƙalubalantar mutane da cewa, idan gaskiya ne suna da nasu Ƙur’ani dabam, kamar yadda ake dangana musu (ko da yake mai karatu yana iya ganin cewa ruwayoyinsu ne suka tabbatar da samuwarsa) to don me ba’a fito musu da shi su gan shi? Su kan yi tambaya: Ina Ƙur’anin nasu yake?
To wannan tambaya tasu malamansu sun amsa ta da kansu. Shaihinsu, Hussain Alkhurasani yana cewa, “Mu ƴan Shi’a muna ƙudure cewa akwai wani Alƙur’ani da Imam Ali ya rubuta da hannunsa mai albarka, bayan da ya ƙare yi wa Annabi sutura kuma ya zartar da wasiyyarsa. Littafin ya ci gaba da zama a hannun Imamai a matsayin amana daga Allah har ya iso ga Imam Mahadi wanda ya adana shi kuma zai fito da shi a yayin da zai bayyana.” [Duba Al’islam ala Dau’it Tashayyu’i na Hussain Alkhurasani, ba tarihi, shafi na 204].
Wannan ruwaya tana tabbatar da cewa Ƙur’anin ƴan Shi’a ya kasance akwai shi, kuma ya ci gaba da zama a hannun Imamai har na tsawon kimanin shekaru 250 daga zamanin Sayyidina Ali(RA) zuwa zamanin Mahadinsu (watau Imaminsu na 12) wanda aka haife shi a shekara ta 255 bayan Hijira. Wannan Imamin nasu shi ne ya tafi da littafin a lokacin babbar fakuwarsa, kuma zai komo da shi a lokacin da zai bayyana a ƙarshen duniya.
Ƴan Shi’a suna ƙudure cewa Imaminsu na 12, wanda suke kira Mahadi ya faku fakuwa biyu, babba da ƙarama. A lokacin ƙaramar fakuwa, wacce ta yi tsawon shekara 65, ya riƙa saduwa da manyan almajiransa waɗanda ya riƙa aiko su da saƙwanni zuwa ga mabiyansa. Kuma a shekara ta 259 bayan Hijira, ya shiga fakuwa babba, wacce yake kai har zuwa yau, kuma wacce a cikinta ba ya saduwa da kowa. Wannan babbar fakuwa za ta ƙare a ƙarshen duniya, sa’ad da Mahadin zai bayyana don ya ƙaddamar da wasu ayyuka masu ban tsoro da ban mamaki. [Domin bayanin wannan tatsuniya, duba A Critical Reɓision of Shi’ah na Imam Musa Musawi, bugun the Supreme Islamic Council, Columbia-Amurka, 1412/1992, shafi na 77-78.] Mai son ganin waɗan nan ayyuka, sai ya duba littafinmu mai taken Mugun Nufin ƴan Shi’a ga Al’umma.
Har yau, wani malamin nasu ya ba da bayani mai kama da wannan. Ya ce, “Bayan rasuwar Annabi, Sarkin Musulmi (yana nufin Ali) ya ɗauko Alƙur’ani a cikin mayafinsa, ya kawo wa Abubakar da Umar suna zaune a Masallaci su da wasu mutane. Ya ba su shi, amma sai suka ce: Ba ma bukatar Ƙur’aninka; muna da namu Ƙur’anin, ya ishe mu! Sai ya ce: Shi ke nan, ba za ku ƙara ganin sa ba daga yau, sai Mahadi ya bayyana!” [Duba Nur Al’anwar fi Sharhis Sahifatis Sajjadiyya na Ni’imatullahi Aljaza’iri, bugun Darul Mahajjatil Baida, Bairut, 1420, shafi na 175].
Waɗan nan bayanai daga malaman Shi’a, idan sun gaskata, suna tabbatar da cewa Ƙur’anin ƴan Shi’a ya kasance akwai shi a hannun Imamansu, kuma almajiran Imamai sun karanta shi har lokacin da Imami na 12 ya shiga das hi kogo inda ya faku fakuwarsa ta ƙarshe. Saboda haka sai su jira shi daga nan har sanda jaki ya tsuri ƙaho!
Akwai wani ɗan Shi’a wanda ya taɓa yin wata burga. Ya ɗauko Ƙur’ani cikakke na Musulmi, wanda aka buga a ƙasar Iran, ga tambarin Jumhuriyar Islama rangaɗau a bangon littafin. Sa’an nan ya ce, “Kun ce ƴan Shi’a ba su yarda da Ƙur’ani ba, ya aka yi suka buga wannan?” Sai aka ce masa, ai buga Ƙur’ani ba shi ne yarda da shi ba.
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
☘ SAHEEHUL BUKHAARIY ☘
📚 Saheehul Bukhaariy 📚
[KITAABUL IMAAN]
📚📖📓 08
Gabatarwar; Ash-Sheikh Abu-Abdurrahman Muhammad Auwal Adam Albaniy Zaria [Rahimahul-laah]
Date; Daren Litinin 21 Jimadal-Ulaa 1429 A.H Daidai Da 25 May 2008
Wuri; Markazus Salafiyyah Zaria, Kaduna St, Nigeria.
Daga Cikin Abubuwan Da Malam Ya Tattauna A Ciki Sun Haɗa Da;
1. Bayanai Akan Kalmar KITAAB, Al-BAAB, FASLU, MAS'ALATU, FAR'UN, KHASHIYA.
2. Ma'anar Imani.
3. Kuyi Karatu Karku Damu Da Certificate ❗.
4. Imani Na Rakuwa Yana Raguwa.
5. Yadda Imani Ya Ratsa Sahabban Manzon Allah [Saw].
6. Wadanda Ke Yin Ridda.
7. Wanda Ya Shiga Musulunci Da Gaske.
8. Ya Halatta Mutum Yace Shi Mumine, Fitinar Data Faru Tsakanin Hanafiya, Hanabila Da Shafi'iyyah.
9. Mas'alar Kafirta Musulmi.
10. Yada Da'awar Musulunci A Irin Hanyoyin Da Suka Dace Da Zamani.
11. Tattaunawa Akan Basmala.
12. Qa'idar Kawo Hadisi.
13. Imani Na Karuwa.
24. Idan Allah Yaso Bawa
Subscribe Our YouTube Channel;
https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A
Download More From;
https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
Wanda yake son ya ga waɗannan sauye-sauye filla-filla, to sai ya koma ga littafin Alshi’atu wal Ƙur’an na Ihsan Ilahi Zahir, Allah ya yi masa rahama, domin shi ya tsamo waɗan nan canje-canje waɗanda suka shafi surorin Alƙur’ani guda 114 baki ɗaya daga littafan ƴan Shi’a kuma ya jera su, ya rattaba su, tare da ruwayoyinsu.
- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 1: "Aƙidar Ƴan Shi’a dangane da Alƙur’ani" - na Prof. Umar Labɗo
✍ AnnasihaTv
Call/WhatsApp: 08142286718
Twitter: https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
[AL-ƘUR’ANIN ƳAN SHI’AH]
Ƴan Shi’a suna da nasu Alƙur’ani dabam, wanda suke kira Mushafu Faɗima, watau Kundin Faɗima. Dangane da wannan littafi, malaman Shi’a suna dangana ruwaya ga Imaminsu na shida, Imam Ja’afar Sadiƙ, cewa wai ya ce, “Faɗima ta bar wani kundi wanda ba Ƙur’ani ba ne, amma kuma kalmar Allah ce da ya yi wahayin ta zuwa gare ta. Shi kundin shiftar Annabi ne kuma rubutun hannun Ali.” [A duba Basa’irud Darajat na Alsaffar, shafi na 176]. A wata ruwayar kuma, ya ce: “Shi kundi ne da ya ninka Ƙur’ani uku kuma amma, na rantse da Allah, babu kalma ɗaya a cikinsa ta Ƙur’aninku.” [Duba Alkafi na Kulaini, mujalladi na 1, shafi na 171].
A ganinsu, Mushafu Faɗima shi ne Ƙur’ani na gaskiya wanda Imamansu suka gado shi daga Nana Faɗima ɗiyar Manzon Allah (SAW) da mijinta Ali binu Abi Ɗalib, Allah Ya ƙara musu yarda.
Muhammad binu Hassan Alsaffar, wanda ake lasafta shi daga cikin manyan malaman Shi’a magabata (ya rasu a shekara ta 290 B.H.), ya ruwaito a cikin littafinsa, Basairud Darajati, daga Imam Abu Ja’afar wai ya ce, “Babu wani da zai iya da’awar cewa ya tattare Alƙur’ani dukkaninsa, zahirinsa da baɗininsa, sai masu wasici,” yana nufin Imamai. Har yau, a cikin littafin ya ruwaito daga gare shi yana cewa, “Babu wani daga mutane wanda zai ce ya tattare Alƙur’ani dukkaninsa, kamar yadda Allah ya saukar da shi, sai maƙaryaci. Ba wanda ya tattare shi, ya haddace shi kamar yadda aka saukar da shi, sai Ali binu Abi Ɗalib da Imamai a bayansa.” [Duba Basa’irud Darajatil Kubra fi Fada’ili Aali Mahammad na Muhammad binul Hassan binu Farrukh Alsaffar, bugun Manshuratul A’alami, Teheran-Iran, 1362, shafi na 213].
Ƙur’anin ƴan Shi’a ya sha bamban da Alƙur’anin Musulmi ta fuskoki masu yawa.
Mun riga mun gabatar da bayanin bambancinsu ta wajen jimillar ayoyinsu, inda Ƙur’anin ƴan Shi’a yake da adadin ayoyi dubu goma sha bakwai (17,000) dai-dai wa daida, a yayin da namu yake da ayoyi dubu shida da ɗari biyu da talatin da shida (6,236) kacal.
Ta fuskar tsawon surori ma, littafan guda biyu sun sha bamban. Ga misali, ya zo a cikin Kitab Sulaim binu Ƙais, mashahurin littafin nan na Shi’a wanda saboda ingancinsa a wajensu suke masa laƙabi da A.B.C. Din Shi’a, cewa wai Suratul Ahazab wacce take da ayoyi 73 a Ƙur’aninmu, su a nasu Ƙur’anin adadin ayoyin Baƙara ne da ita, watau 286.
Suratun Nur kuwa, wacce take da ayoyi 64, su a wajensu ayoyi 160 ke gareta. Suratul Hujurati kuma, wacce a cikin Ƙur’anin da muka sani ayoyinta 18 ne kacal, su a nasu Ƙur’anin ayoyinta 90 ne dai-dai wa daida. [Duba Kitab Sulaim binu Ƙais na Sulaim binu Ƙais Alhilali Alkufi, bugun Mu’assasatul A’alami, Bairut, ba tarihi, shafi na 122].
Ta fuskar adadin surori ma, akwai ɗan bambanci saboda akwai wasu surori waɗanda ƴan Shi’a suke ƙudure cewa an ɗebe su daga cikin Alƙur’ani. Misali shi ne wata sura da suke kira Suratul Wilaya wacce suka ce wai a cikinta Allah ya yi umarni da a naɗa Ali binu Abi Ɗalib a matsayin Khalifa bayan rasuwar Annabi (SAW). Wannan sura ba mu san ta ba, babu ita a cikin Alƙur’aninmu, amma su ƴan Shi’a suna ƙudure cewa wai Sahabbai ne suka ɗebe ta don cin amana, a faɗinsu, domin su hana Ali binu Abi Ɗalib haƙƙinsa na gadar Annabi, suka naɗa Abubakar a makwafinsa. Wannan ita ce aƙidarsu. Wal iyazu billah!!
Dangane da kalmomi da lafuzza da ma’anoni, babu wata sura a cikin Alƙur’ani kamar yadda muka san shi face ƴan Shi’a sun zo da saɓanin kalmomi ko ayoyi a cikinta. Za mu ba da ƴan misalai kaɗan.
A ƙarshen Suratul Fatiha suna karanta: Ihdinas siraɗal mustaƙim. Siraɗa man an’amta al aihim, gairil magdubi alaihim wa gairid dalin.
A farkon Suratul Asri, suna karanta: Wal asr innal insana la fi khusr. Wa innahu fihi ila akhirid dahr. Illal lazina amanu wa amilus salihati, wa’ atamaru bit taƙwa, wa’atamaru bi s sabr. Suratul Fili kuma, watau Alam Tara Kaifa, suna fara ta kamar haka: Alam ya’atika kaifa fa’ala rabbuka bi ashabil fili.
Waɗan nan ƴan misalai ne kawai muka kawo domin mai karatu ya ganewa idanunsa.
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
MUNIN KISAN MALAMAI
Daga: Ash-Sheikh Albaniy Zaria Rahimahul-laah
https://youtu.be/z-vWM9P5g4k
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
❝ Babu Yadda Za'a Yi Ka Iya Yin Bauta, Bautar Ta Zamto Karbabbiya Abada Lada Akai Sai In Manzon Allah Ya Koyar Da Yadda Akeyin Bautar ❞
- Ash-Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam Rahimahul-laah
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 1: "Aƙidar Ƴan Shi’a dangane da Alƙur’ani" - na Prof. Umar Labɗo
✍ AnnasihaTv
Call/WhatsApp: 08142286718
Twitter: https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
AƘIDAR ƳAN SHI’A DANGANE DA ALƘUR’ANI
Ƴan Shi’a suna ƙudure cewa Alƙur’ani mai girma wanda yake a hannun Musulmi a yau ba cikakke ba ne; domin, a ganinsu, Sahabbai da suka tattara Alƙur’ani a zamanin Abubakar da Usman, Allah ya ƙara yarda a gare su, sun sauya abubuwa da dama a cikinsa ta hanyar yin ƙare-ƙare da rage-rage a cikin ayoyinsa.
Suka ce wai wannan Alƙur’ani da muke karanta wa a yau babu abinda yake cikinsa daga abinda aka saukar ga Annabi (SAW) sai ɗan kaɗan.
Ƴan Shi’a suna zargin Sahabbai da sauya Littafin Allah, da canja ayoyinsa. Suka ce wai Sahabban sun yi haka ne ta hanyar ɗebe ayoyi masu yawa da aka saukar waɗanda suke tona asirinsu da kuma ayoyi da suke nuna falalar Ali binu Abi Ɗalib(RA) da zuri’arsa. Abinda suke nufi da tona asirinsu, wai bayyana kafirci da munafuncin Sahabbai. Wal iyazu billahi!!
Saboda haka a wurin ƴan Shi’a, ayoyi da yawa dake cikin Alƙur’ani ba maganar Allah ba ce, wannan ya sa suke zaɓar abinda ya dace da son zukatansu a cikin Alƙur’ani, saura kuwa su yi burus da shi.
Wani babban malaminsu mai suna Hashim binu Sulaiman Albaharani yana faɗi a cikin wani littafi nasa da ya rubuta a kan Tafsiri, “Ka sani cewa a haƙiƙanin gaskiya wacce babu kokwanto a cikinta, gwargwadon ruwayoyi mutawatirai, wannan Alƙur’ani da yake hannunmu sauye-sauye sun faru a cikinsa bayan rasuwar Manzon Allah (SAW) kuma waɗanda suka tattara shi bayan Annabi sun ɗebe kalmomi da ayoyi masu yawa daga cikinsa.” [Duba Alburhan fi Tafsiril Ƙur’an na Hashim binu Sulaiman Albaharani, bugun Almadaba’atul Ilmiyya, Ƙum-Iran, 1393, shafi na 36].
A cikin littafin Alkafi, littafin da ya fi ko wanne inganci a wajen ƴan Shia, an yi bayanin gwargwadon abinda aka ɗebe daga cikin Alƙur’ani. Marubucin littafin, watau Muhammad binu Ya’aƙub Alkulaini, ya ce, “An ruwaito daga Abu Abdullahi (watau Imamin Shi’a na shida) cewa Alƙur’anin da Jibrilu ya zo da shi ga Muhammad (SAW) aya dubu goma sha bakwai (17,000) ne.” [A duba Alkafi na Muhammad binu Ya’aƙub Alkulaini, Darul Kutubil Islamiyya, Teheran-Iran, ba tarihi, mujalladi na 2, shafi na 634].
Wannan yana nufin ke nan cewa Kur’anin da yake hannunmu ɗan ragowa ne kawai; domin kuwa a bisa ga wannan ruwaya waɗanda suka tattara littafin a bayan rasuwar Annabi (SAW) sun ɗebe kimanin sulusi biyu na littafin.
Za mu tabbatar da haka idan muka lura da cewa Alƙur’anin da yake hannunmu, wanda Musulmi suka sani a yau, ayoyinsa dubu shida da ɗari biyu da talatin da shida ne (6,236) kawai, kamar yadda malaman Sunna suka tabbatar. [Duba Tafsiru Ibnu Kathir na Isma’il binu Kathir, bugun Maktabatus Safa, Alƙahira, 1423/2002, mujalladi na 1, shafi na 7].
Akwai ruwayoyi masu yawa a cikin littafan malaman Shi’a da suke izna da su, waɗanda suka tabbatar da wannan mugunyar aƙida tasu.
Wani malaminsu mai suna Ni’imatullahi Aljaza’iri da ya ƙididdige ruwayoyin ya tabbatar da cewa sun fi dubu biyu. [Duba Faslul Khidab na Hussain binu Muhammad Taƙiyyud Din Aldabarsi, ba tarihi, shafi na 248]. Saboda haka, ita aƙida ce wacce dukkan ƴan Shi’a, ciki har da na Nijeriya, suka yarda da ita. Kuma idan ka ji suna musun ta, to taƙiyya ce kawai suke yi, watau munafunci da yaudara!!
Wani ƙasurgumin malamin Shi’a, mai suna Hussain binu Muhammad Annuri Alɗabarsi, ya rubuta shirgegen littafi musamman don ya tabbatar da aƙidar ƴan Shi’a cewa Alƙur’anin nan da yake a hannunmu a yau ba cikakke ba ne, kuma akwai sauye-sauye, da ƙare-ƙare, da rage-rage, a cikinsa. Littafin wanda ya sa wa suna Faslul Khiɗab fi Ithbati Tahrifi Kitabi Rabbil Arbab, (watau Yankakkiyar Magana A Kan Tabbatar Da Sauya Littafin Mamallakin Mamallaka), ya ƙunshi dubunnan ruwayoyi daga Imaman Shi’a da malamansu waɗanda suke tabbatar da cewa wai waɗan nan sauye-sauye, da ƙare-ƙare, da rage-rage Sahabbai, waɗanda suka haɗa da Abubakar da Umar da Usman, Allah ya yarda da su baki ɗaya, su ne suka zartar da su. A cikin littafin har ila yau, an tabbatar da cewa malaman Shi’a kaf, magabatansu da na bayansu, sun haɗu a kan wannan aƙida. [Duba Faslul Khidab na Aldabarsi, shafi na 34].
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
☘ AT-TAQLID ☘
📚 Muhadara/Lecture 📚
Mai Taken; At-Taqlid
📚📖📓
Gabatarwar; Ash-Sheikh Albaniy Zaria Rahimahul-laah
follow us on;
Telegram;
https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel
facebook;
https://www.facebook.com/SGNnigeria/
Subscribe Our YouTube Channel;
https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A
Twitter; https://twitter.com/SGNnigeria?t=vytGM6iYd3YDrUF8DXIYWw&s=09
WhatsApp Group;
https://chat.whatsapp.com/EzDg9IAKCNwEjCJakQVwnj
Telegram Group;
https://t.me/sgnnigeria
Download More From;
https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel
for More Info contact us on;
WhatsApp;
https://bit.ly/3pl20Vj
Email; sgnnigeria@gmail.comRepost from ADDININ NASIHA
FALALAR SALATIN ANNABI MUHAMMAD SALLALAHU ALAYHI WASSALLAM
DAGA BAKIN MALAMIN MU
SHEIKH AHMAD B.U.K RAHIMAHULLAH
https://t.me/Addininassiha
Repost from Salafiyyah Global Network Nigeria
AƘIDAR ƳAN SHI’A DANGANE DA ALƘUR’ANI
Aikina na yaƙar bidi’ar Shi’a ya fara a garin Sakkwato, a wajejen shekarar 1993, bayan na kwashe kimanin shekaru biyar ina koyar da fannin Alfiraƙul Islamiyya (Ƙungiyoyin Bidi’a a Musulunci) a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Wannan aiki ya lafa bayan da na shiga gwagwarmayar kafa Shari’a a jihohin Sakkwato da Kebbi a ƙarshen shekarar 1999. Daga baya kuma aikin ya tsaya cik a lokacin da na tafi ƙasar Uganda domin koyarwa a Jami’ar Musulunci ta Uganda (IUIU) dake garin Mbale a Uganda.
Bayan komowa Nijeriya a farkon shekarar 2003, na sabunta nashaɗina na yaƙar Shi’a a Sakkwato, inda na fitar da littafin Ɓacin Tafarkin ƴan Shi’a da Aƙidojinsu a ƙarshen shekarar 2004.
Ayyukana na rubuce-rubuce da lakcoci sun ci gaba a tsawon zamana na shekaru huɗu a Katsina, yayin da na fitar da littafin Larabci mai suna Bayanu Fasadi Aƙa’idis Shi’a. Da na koma Kaduna a ƙarshen shekarar 2009, na ci gaba da nashaɗina, inda na buga littafai biyu: Dangantaka da Auratayya Tsakanin Ahalul Baiti da Sahabbai da Wa Ya Kashe Hussaini?
A duk tsawon wannan lokaci, na kasance ina mai amanna da muhimmancin karatu da rubutu a cikin ko wace al’umma. Wannan ya sa koda yake ina wa’azi da lakcoci, amma ban fiye damuwa da yaɗa su ta hanyar kasakasai ba. Wani lokaci ma na kan hana a ɗauki karatuna a rikoda, saboda ba na son mutane su dogara da sauraro maimakon karatu. A koda yaushe, na fi ƙarfafa guiwar mutane da su karanta littafai, maimakon su saurari kasset da radiyo.
A lokacin da na komo gida Kano, kuma na mai da hankali zuwa ƙauyuka da yankunan karkara (saboda ganin makircin Shi’a na shiga ƙauyuka), yaƙinina da muhimmancin karatu da rubutu ya ƙaru. To sai dai na fuskanci wata matsala guda: Yawancin mazauna ƙauyuka da yankunan karkara suna tsoron littafi idan yana da girma, wani lokaci kuma ya kan yi musu tsada. Ƙoƙarin warware wannan matsala shi ya kawo tunanin rubuta Jerin Littafan Shi’a.
A haƙiƙa ba mazauna ƙauyuka ne kawai suke tsoron karatu, ko suke ƙin sa ba. Yawancin al’ummarmu suna da ƙiwar karatu da ƙyamarsa; sun fi son su saurari radiyo ko rikoda. Sai dai abu ne da yake tabbas cewa, ba wata al’umma da za ta ci gaba matuƙar ba ta karatu. Yawancin malaman zamani sun biye wa Malam Bahaushe, suna ganin tunda mutanenmu ba sa son karatu, to sai a bar su da abinda suke so: kasset da rikoda. Amma ni ban yarda da wannan ra’ayi ba. Ina ganin ba dai-dai ba ne a biye wa mara lafiya da ya ƙi karɓar magani don yana zaton maganin yana da ɗaci. Maimakon haka, kamata ya yi a riƙa ba shi kaɗan-kaɗan, yana kurɓa sannu a hankali, har ya saba, kuma ya warke! Warakar al’umma na cikin karatu.
Wannan shi ne abinda na yi da ƙananan littafai na wannan jeri. Kuma abin ya yi nasar har na fara rubuta na Larabci da na Turanci.
Waɗan nan jerin littafai, daga na ɗaya zuwa na tara, sun ƙunshi duk abinda mai karatu yake bukata ya sani dangane da ƴan Shi’a da aƙidojinsu da hukunce-hukuncensu da ibadojinsu da halayensu da ɗabi’unsu da tarbiyyarsu da dangantakarsu da sauran Musulmi, musamman Ahalus Sunna. Kuma, kamar yadda mai karatu zai gani ƙarara, a cikin waɗan nan al’amura duka, ƴan Shi’a suna yin nesa da Musulunci da duk abinda ya ƙunsa na aƙidoji da hukunce-hukunce da ibadoji da halaye da ladubba da ɗabi’u da tarbiyya. A taƙaice, ƴan Shi’a suna yin nesa da koyarwar Alƙur’ani da Sunnar Annabi da tafarkin Sahabbai da Ahalul Baiti baki ɗaya.
Wani abu muhimmi da wannan jerin littafai suka yi fice da shi, shi ne dogaro kacokan wajen bayanin aƙidojin ƴan Shi’a da hukunce-hukuncensu da ibadojinsu da halayensu da dangantakrsu da sauran Musulmi a kan littafan malamansu da shaihunnansu waɗanda suka yarda da su, tare da lazimtar amana wajen naƙalto maganganunsu daga littafan nasu. Saboda haka, abinda mutum zai karanta a cikin waɗan nan littafai dangane da ƴan Shi’a kai-tsaye ne daga bakin mai ita. Duk abinda aka faɗi dangane da su daga littafansu aka ɗauko, ba daɗi, ba ragi. Wannan kuma domin a yi adalci ne gare su, kuma a lazimta musu hujja.
- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 1: "Aƙidar Ƴan Shi’a dangane da Alƙur’ani" - na Prof. Umar Labɗo
