en
Feedback
ADDININ NASIHA

ADDININ NASIHA

Open in Telegram

ADDININ NASSIHA TAKU CE DOMIN TUNATARWA, NASSIHA, SAMUN KARATUTTUKAN MALAMAN SUNNAH IN SHA ALLAH ADMINS KADAI SUKE DA DAMA TURA SAKO CIKIN GROUPE MU DALIBAI NE BA MALAMAI BA MUNA ROQON ALLAH YA SA MANA IKHLASI KUMA YA HADAMU A CIKIN GIDAN AL-JANNAH.

Show more
The country is not specifiedReligion & Spirituality115 078
773
Subscribers
+124 hours
+227 days
+10330 days
Posts Archive
Repost from ADDININ NASIHA
ADDU'AR BUDA BAKI 👇👇👇👇👇 ذَهَبَ الظَّمَأُ، وَابْتَلَّتِ العُرُوقِ، وَثَبَتَ اْلأَجْرُ إِنْ شَاءَ اللهُ. DAGA BAKIN MALAMIN MU SHEIKH MUHAMMAD ADAM ALBANIN GOMBE HAFIZAHULLAH https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
ADDU'AR BUDA BAKI 👇👇👇👇👇 ذَهَبَ الظَّمَأُ، وَابْتَلَّتِ العُرُوقِ، وَثَبَتَ اْلأَجْرُ إِنْ شَاءَ اللهُ. DAGA BAKIN MALAMIN MU SHEIKH MUHAMMAD SANI UMAR RIJIYAR LEMU HAFIZAHULLAH https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
TUNATARWA TUNATARWA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN SHA'ABAN 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wa
TUNATARWA TUNATARWA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN SHA'ABAN 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wata har zuwa Ramadhan yana dai dai da Azumin shekara guda"-(Muslim 1162). Hanya ce ta samin kusanci ga Allah da SOYAYYARSA. AZUMIN zai kasance daga gobe LAHADI 13 ga SHA'ABAN har zuwa ranar TALATA 15 ga wata. N.B: RANEKUN ZAI KASANCE : LAHADI LITININ TALATA Allah Ta'ala ya bamu iko https://t.me/Addininassiha

Zikirin safe da yamma duk maiyi ba zai tabe ba Sheikh Ibrahim Daurawa

Repost from ADDININ NASIHA
TUNATARWA TUNATARWA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN RAJAB 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wata
TUNATARWA TUNATARWA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN RAJAB 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wata har zuwa Ramadhan yana dai dai da Azumin shekara guda"-(Muslim 1162). Hanya ce ta samin kusanci ga Allah da SOYAYYARSA. AZUMIN zai kasance daga gobe ASABAR 13 ga RAJAB har zuwa ranar LITININ 15 ga wata. N.B: RANEKUN ZAI KASANCE : ASABAR LAHADI LITININ Allah Ta'ala ya bamu iko https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
ALBARKA DA FALALA DAKE CIKIN SALATIN MANZAN ALLAH TELEGRAM https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
FALALAR SALATIN ANNABI MUHAMMAD SALLALAHU ALAYHI WASSALLAM DAGA BAKIN MALAMIN MU SHEIKH AHMAD B.U.K RAHIMAHULLAH https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
YAWAITA SALATI GA MANZON ALLAH ﷺ Ibnul Jauziy (RA) Ya ce: "Ku sani babu wani bawa musulmi da zai yawaita yin salati ga Annabi Muhammad ﷺ fa ce: (1)Allah ya haskaka zuciyarsa, (2)Ya gafarta masa zunubansa, (3)Ya buda masa kirjinsa, (4)Ya saukaka masa lamurransa, Saboda haka ku yawaita salati ga Annabi ﷺ". ﺑﺴﺘﺎﻥ ﺍﻟﻮﺍﻋﻈﻴﻦ ﺹ ٢٩٧ Telegram https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
SIGOGIN SALATIN ANNABI ﷺ GUDA 7 DA SUKA INGANTA A SUNNAR MANZON ALLAH ﷺ 1-SIGA TA FARKO {اللـهم صَـلِّ عـلى مُحَـمَّدٍ وَعَـلَى آلِ مُحَـمَّدٍ كمـا صَـلَّيْتَ علـى إبراهـيم وَعَلَـى آلِ إبـراهيم إِنَّـكَ حَـمِيدٌ مَجِـيدٌ اللـهم بَـارِكْ عـلى مُحَـمَّدٍ وَعَلَـى آلِ مُحَـمَّدٍ كمـا بَارَكْـتَ علـى إبراهيـم وَعَـلَى آلِ إبـراهيم إِنَّـكَ حَمِـيدٌ مَجِـيدٌ}. @صـحيح البـخار رقـم〘3370〙 2-SIGA TA BIYU {اللـهمَّ، صـلِّ علـى محـمدٍ وعـلى آلِ محـمدٍ، كـما صـلَّيْتَ علـى آلِ إبراهـيمَ وبـارِكْ علـى مـحمدٍ وعـلى آلِ محـمدٍ، كـما بارَكْـتَ علـى آلِ إبـراهيمَ ، فـي العـالمين إنـك حمـيدٌ مجـيدٌ} @صحـيح مسـلم رقم : 405 3-SIGA TA UKKU {اللهـم صـل علـى مُحَمَّـدٍ النبـي الأمـي وَعَلَـى آلِ مُحَمَّـدٍ كمـا صَـلَّيْتَ علـى إبراهيـم وَآلِ إبراهيـم وَبَـارِكْ علـى مُحَـمَّدٍ النبـي الأمـي كمـا بَارَكْـتَ علـى إبراهيـم وَعَـلَى آلِ إبراهـيم انك حَمِـيدٌ مَجِيـدٌ} @حـسنه الألبـاني فـي صحيـح الجـامع رقم 670 4-SIGA TA HUDU {اللـهم صَـلِّ علـى مُحَـمَّدٍ وَأَزْوَاجِـهِ وَذُرِّيَّتِـهِ كمـا صَلَّـيْتَ عـلى آلِ إبراهيـم وَبَـارِكْ عـلى مُـحَمَّدٍ وَأَزْوَاجِـهِ وَذُرِّيَّتِـهِ كمـا بَـارَكْتَ عـلى آلِ إبـراهيم إِنَّـكَ حَـمِيدٌ مَـجِيدٌ}. @صحيح البخاري رقم 3189 صحيح مسلم رقم 407 5-SIGA TA BIYAR {اللـهم صَـلِّ عـلى مُحَـمَّدٍ عَبْـدِكَ وَرَسُـولِكَ كـما صَـلَّيْتَ علـى آلِ إبراهـيم وَبَـارِكْ علـى مُحَـمَّدٍ وَعَلَـى آلِ مُـحَمَّدٍ كـما بَارَكْـتَ علـى آلِ إبـراهيم}. @صحـيح البـخاري 4520 6-SIGA TA SHIDA {اللـهم صَـلِّ عـلى مُحَـمَّدٍ عَبْـدِكَ وَرَسُـولِكَ كـما صَلَّـيْتَ عـلى إبراهيـم وَبَـارِكْ عـلى مُحَـمَّدٍ وَعَلَـى آلِ مُـحَمَّدٍ كـما بَارَكْـتَ علـى إبراهيـم وَآلِ إبـراهيم}. @صـحيح البخـاري 5997〙 7-SIGA TA BAKWAI {اللَّهـمَّ صـلِّ عـلَى محـمَّدٍ النَّبـيِّ الأُمِّـيِّو عـلى آلِ مـحمَّدٍ} @حـسنه الألبـاني فـي صحـيح أبـي داود 981〙 Wadan nan sune suka tabbata a sunnar Manzon Allah ﷺ ya koyar da bakinsa,kuma shine wanda Allah yake bada lada. Allah ne mafi sani Telegram https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
FALALAR SALATIN ANNABI MUHAMMAD SALLALAHU ALAYHI WASSALLAM DAGA BAKIN MALAMIN MU SHEIKH AHMAD B.U.K RAHIMAHULLAH https://t.me/Addininassiha

Repost from ADDININ NASIHA
TUNATARWA TUNATARWA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN JUMADAL AKHIRA 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akow
TUNATARWA TUNATARWA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN JUMADAL AKHIRA 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wata har zuwa Ramadhan yana dai dai da Azumin shekara guda"-(Muslim 1162). Hanya ce ta samin kusanci ga Allah da SOYAYYARSA. AZUMIN zai kasance daga gobe JUMA'A 13 ga JUMADAL AKHIRA har zuwa ranar LAHADI 15 ga wata. N.B: RANEKUN ZAI KASANCE : JUMA'A ASABAR LAHADI Allah Ta'ala ya bamu iko https://t.me/Addininassiha

Insha ALLAHU duk abinda ke damun mutum zai rabudashi, idan kuma wannan hanyar tayi wahala, to sai mutum yabi hanya ta uku. 3• Hanya ta uku: Ita ɓangaren man shafawa sai asami: • Vaciline na habbbatu sauda. • Vaciline na zaitun. • Jibda. • Jan miski. Sai a sami ruwan zafi a saka kwalbar aciki man zasu narke, zasu tashi sai a haɗesu wuri ɗaya acikin wata kwalbar babba, sai a rinƙa shafawa sau uku a rana, amma kafin a shafa ayi karatun ruƙya acikinsu: • Ayatul kursiyu 1. • Qulhuwallahu 3. • Falaq 3. • Nass 3. Sai a tofa acikinsu, sai a rinƙa shafawa idan za'a kwanta bacci kaɗan amma ake shafawa, da kuma bayan anyi wanka bayan mutum ya shafa man daya saba shafawa, saiya dangwalo maganin ya shafa sama-sama, Sannan kuma sai da safema a shafa, ko kuma idan mutum zai shiga sha'anisa ya shafa a ƙalla sau uku dai a rana. Sannan mace zata iya rinƙa saka cokali ɗaya na garin Habbatus-sauda acikin miya tana girki dashi yara suci da kowa da kowa saboda kariya daga iska da sihiri. Sannan kuma mace zata iya rinƙa turarashi a ɗakinta kuma zata iya zubashi akan garwashi tayi tsuguno akansa. Insha ALLAH duk wacce ko wanda yake fama da matsalar aljanu ko sihiri ko maita ko kambun baka, to ya ɗauki ɗaya daga cikin hanyoyi ukun-nan damuka kawo ya jaraba, in ALLAH ya yarda zai sami lafiya. ALLAH duk wanda yake fama da larura ta rashin lafiya ALLAH ka yaye masa, ALLAH ka bawa kowa lafiya ingantacciya. ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen. Duk mai neman ƙarin bayani yayi mana magana ta private.

HULƊA TSAKANIN ALJANU DA ƊAN ADAM °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° DARASI NA [ 4 ] °°°°°°°°°°°°°°°°°°° HANYOYIN WARAKA DAGA CUTAR NAMIJIN DARE KO MACEN DARE KO SIHIRI DSSR Hanyoyin da akebi wajen warkar da cutar namijin dare ko macen dare sun kasu kashi biyu sune kamar haka: 1• Hanyar Girka. Hanyar Girka itace wacce 'ƴan bori suke bi wajen warkar da marar lafiya. 2• Hanyar Ruƙya. Hanyar Ruƙya itace wacca malaman Ruƙya kebi wajen warkar da marar lafiya. Girka wata hidima ce da 'ƴan bori ke gudanarwa ga marar lafiya wadda suke ganin ta iskokaice. Gudanar da aikin Girka ga marar lafiya na nufin kodai iskokai su fita daga jikinsa ya samu lafiya, ko kuma a girkesu a jikinsa, su zauna cikin aminci da salama, ba tare da suna cutar dashi ba, Amma tare da yadda da bin ƙa'idojin da zasu gindayawa shi mara lafiyar a rayuwarsa wanda ba ƙa'idar ALLAH da Manzon ALLAH {s.a.w} bace. Hanyoyin da malaman Ruƙya suke bi wajen warkar da cutar namijin dare ko macen dare suna da mataki guda uku, waɗannan matakan kuwa sune kamar haka: 1• Ƙoƙarin gano alamomin da akayi bayani na bayyanar namijin dare ko macen dare, su tabbatar da namijin daren ne ko kuwa wani nau'in aljani ne daban. Idan alamomin sun tabbata, sai malamai su gudanar da Ruƙya ga marar lafiya, kamar yadda sukanyi ga sauran cututtukan da suka shafi Aljanu. 2• Gabatar da wasu ayyuka da karance-karance ga maras lafiya. Dama kuma shi namijin dare, ko Aljanin soyayya da kuma aljanin da aka turawa mutum ta hanyar sihihi sune mafi haɗari da sharri daga cikin nau'o'in Aljanu, kuma shine mafi tsanani ga riƙe jikin ɗan Adam da wahalar fita ga naci. Saboda haka akwai hanyoyi guda uku masu sauƙi da zamu baku wanda mutum zaibi domin ya rabuda aljanun ko sihirin dake jikinsa ya karye ko tsafin ya karye. 1• Hanya ta farko: A nemo ganyen magarya guda bakwai ɗanye ko busasshe, Sannan a sami wani abu kamar bokiti ko wata roba babba wacce za'a ajiye ruwa mai kyau sosai acikinta, ruwan da zai iya kaishi tsahon sati ɗaya, kwana bakwai kenan yana amfani dashi, sai a murje wannan ganyen magaryar acikin wannan ruwan. Bayan an murjeshi acikin ruwan zai iya kasancewa aga ruwan yana wata kumfa-kumfa, to sai ayi karatu acikinsa kamar haka: 1• Suratul Baƙarah gaba ɗayanta. 2• Qulhuwallahu Ahad 3. 3• Falaq 3. 4• Nass 3. A sami wanda ya iya karatu sosai koshi mara lafiyar zai iya karantawa da kansa, zai zauna ne a kusa da ruwan a yayin da yake karatun numfashinsa yana shiga cikin wannan ruwan. Bayan angama karratun sai mara lafiya ya rinƙa ɗibar ruwa kofi ɗaya yanasha kullum, kofi ɗaya tak kullum. Sannan kuma sai ya sami wani tsumma ko tawul sai ya ɗebi ruwan a wani abu kaɗan daban sai ya rinƙa tsomashi aciki yana matsewa, sai ya rinƙa goggowa ajikinsa ko ina da ina, kamar dai wanka, amma ayi a guri mai tsarki koda acikin dakine. Ma'ana mutum ya shiga ɗaki shi kaɗai ya cire kayansa yabi dukkan jikinsa da wannan ruwa da yake matsowa da wannan tsumma mai kyau, ya tabbatar da ruwa ya taɓa dukkan jikinsa. Ko kuma ya sami kofi yana ɗibar ruwan yana kwararawa akansa da dukkan jikinsa yana zubowa ya wanke ko ina, amma idan zaiyi haka, sai dai yayi acikin wani ƙaton baho kuma a guri mai tsarki, ba'a banɗaki ba, ko kuma ya shimfiɗa tawul a ɗaki ruwan yana zuba akan tawul ɗin, idan ya gama saiya shanya tawul ɗin. Haka mutum zai rinƙayi harna tsahon sati ɗaya, ko kuma mutum yayi amfani da hanya ta biyu idan wannan zata wahalar dashi. 2• Hanya ta biyu: Mara lafiya ya samu: • Man zaitun. • Man Habbbatu sauda. • Man tafarnuwa. • Zuma ya sami kamar cikin robar yoghut ƙarama. Idan zai yiwu a sami na kamfanin HEMANI kowaninsu 60ml sai a haɗesu wuri ɗaya a rinƙa shan cokali biyu da safe, cokali biyu da Rana cokali biyu da yamma.

Repost from ADDININ NASIHA
TUNATARWA TUNATAR WA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN JUMADA ULAH 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowan
TUNATARWA TUNATAR WA AZUMIN FARAREN KWANAKI NA WATAN JUMADA ULAH 1444 A.H Manzon Allah (SAW) ya ce: " Azumin kwana uku akowane wata har zuwa Ramadhan yana dai dai da Azumin shekara guda"-(Muslim 1162). Hanya ce ta samin kusanci ga Allah da SOYAYYARSA. AZUMIN zai kasance daga gobe LARABA 13 ga RABI'UL AWWAL har zuwa ranar JUMA'A 15 ga wata. N.B: RANEKUN ZAI KASANCE : LARABA ALHAMIS JUMA'A Allah Ta'ala ya bamu iko https://t.me/Addininassiha

[KAFIRCIN AƘIDAR SHI’AH A TAƘAICE!!] Bayan mun gabatar da bayani a kan wannan aƙida kamar yadda take a cikin littafan ƴan Shi’a masu inganci a wajensu, muna ganin babu wani Musulmi da yake buƙatar wani ƙarin bayani dangane da abinda aƙidar ta tattare na kafirci da jahilci da ɓata. Amma saboda yankan hanzari ga masu kiran kansu ƴan Shi’a, bari mu yi bayanin kafircin wannan aƙida a taƙaice. Da farko dai aƙidar ta ƙaryata Alƙur’ani mai girma saboda a cikinsa Allah mai girma da ɗaukaka ya tabbatar da cewa ya tsare Littafinsa ta yadda ƙari ko ragi ba za su shige shi ba.  Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Lalle, mu ne muka saukar da Ambato (Alƙur’ani), kuma lalle mu, masu kiyayewa ne gare shi.” (Suratul Hijr: 9).  A wata ayar kuma, ya tabbatar da cewa ɓarna ba ta shiga wannan littafi ko ta halin ƙaƙa: “Waɗan nan da suka kafirta game da Alƙur’ani a lokacin da ya je musu, kuma lalle ne, haƙiƙa, littafi ne mabuwayi.  Ɓarna ba za ta je masa ba daga gaba gare shi, kuma ba za ta zo ba daga baya gare shi.   Saukarwa ce daga Mai Hikima, Godadde.” (Suratu Fussilat: 41 – 42).  Na biyu, wannan aƙida har ila yau, tana ƙaryata Alƙur’ani ta wata fuskar dabam; domin tana kafirta ko fasiƙantar da waɗanda Allah ya bayar da labari cewa ya yarda da su kuma ya yi musu gafara: su ne Sahabban Annabi (SAW), Allah ya ƙara musu yarda baki ɗaya. Aƙidar ta kafirta Sahabbai ta hanyar dangana musu sauya Alƙur’ani, da ɓoye abinda Allah ya saukar, da yin ƙari da ragi a cikinsa. Allah yana faɗi dangane da Sahabban Annabinsa: “Kuma magabata na farko daga Muhajirina da Ansar da waɗanda suka bi su da kyautatawa, Allah ya yarda daga gare su, su kuma sun yarda daga gare shi, kuma ya yi musu tattalin gidajen Aljanna:  ƙoramu suna gudana a ƙarƙashinsu, suna madauwama a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma.” (Suratut Tauba: 100).  Ɗan uwa mai karatu ka dubi abinda Allah Ya ce dangane da Sahabban Annabinsa, har ma da waɗanda suka bi su da kyautatawa, sa’an nan ka dubi abinda ƴan Shi’a suka jingina musu na sauya maganar Allah da cin amanar Manzonsa, za ka san cewa lalle ƴan Shi’a sun yi nisa daga barin shiriya.   Muna roƙon Allah Ya arzuta su da tuba kyakkyawa, da komawa ga tafarki madaidaici: tafarkin Sunnar Annabi(SAW). Mu kuma, ya nesantamu da irin wannan ɓata mabayyani.  - JERIN LITTAFAN SHI’A NA 1: "Aƙidar Ƴan Shi’a dangane da Alƙur’ani" - na Prof. Umar Labɗo ✍ AnnasihaTv Call/WhatsApp: 08142286718 Twitter: https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09

Kisan Albaniy Da Ja'afar Bamu Yafe Ba❗ Daga: Ash-Sheikh Dawud Azzahiriy Hafizahul-laah https://youtu.be/f_icrt-L-D8

Farin Sako 1.mp310.69 MB

FARIN SAQO ☘ 📚 Muhadara/Lecture 📚 Mai Taken; Farin Saqo 📚📖📓 01 Gabatarwar; Ash-Sheikh Albaniy Zaria Rahimahul-laah Ranar;  Daren Lahadi - 7th ga Watan Safar 1433 daidai da 31st ga Watan December, 2011 Wuri: Markazus Salafiyyah, Tudun Wada, Zaria, Kaduna State, Nigeria.   Daga Cikin Muhimman Abubuwan Da Malam Ya Tattauna;   1. Dalilin Yin Farin Sako. 2. Muhimmancin Haɗin-Kai Da Haƙuri Da Juna. 3. Ƙungiyar Izala. 4. Tsarkin Zuciyar Wadanda Suka Kafa Izala. 5. Addu'oi Na Musamman Ga Mazajen Jiya Na Gida Da Wajen Nigeria. 6. Ash-Sheikh Abubakar Mahmud Gumi. 7. Tarihin Sheikh Sama'ila Idrees. 8. Yadda Aka Sanya Sunan Ƙungiyar Izala. 9. Manufofin Ƙungiyar Izala. 10. Yadda Ake Shiga Ƙungiyar Izala. 11. Tsarin Shugabanci A Ƙungiyar Izala Da Tsarukan Wa'azi. 12. Masu Adawa Da Izala. 13. Kafa Masallacin Gwallaga A Bauchi. 14. Gwagwarmayar Izalah. 15. Makircin Ƴan Shi'a Ga Ƴan Izalah. 16. Jarrabawar Da Allah [Swa] Yama Izala. 17. Tarihin Rikicin Izalah. 18. Dr Jalo Jalingo. 19. Mas'alar Qabalu, Ahlul-Kitabi, Ɗan Gungun Da Sadalu❗️ 20. Sulhun Ƙungiyar Izala A Gaban Abubakar Gumi. 21. Shawarwari Kan Addini Ga Ƙungiyar Izala. 22. Shawarwari Kan Siyasar Ƙungiyar Ga Izalah. 23. Malam Sani Yahya Jingir Da Sheikh Bala Lau. 24. Farin Saqo Ga Ƙungiyar Izala Kan Haɗuwar-Kai. Subscribe Our YouTube Channel; https://youtube.com/channel/UC0ACx2Mm-1UOjEgws_v8n3A Download More From; https://t.me/Salafiyyahglobalnetworktvchannel

Munin Kisan Malamai .mp311.18 MB