3 279
Subscribers
+324 hours
+257 days
+1130 days
Posts Archive
Ga wanda yake bibiyar fina-finan Shi'a, zai ga cewa fitowar wasu a matsayin Annabawa, da har fuskarsu ma ana gani a fili, ba wani sabon abu ne. Amma a iya wanda na sani na kalla kuma, ba za ka taɓa ganin wani film da yake nuna limamansu ba. Har gwara Aliyu (RA) , sukan ɗan nuna shi, jefi-jefi.
Karka yi mamaki idan ka san cewa a tsakanin 2020 zuwa 2021 sun yi wani film da suke bada tarihin Faɗima (RA) bisa riwayar Shi'a, inda a ciki suka bayyana aƙidunsu game da Abubakar (RA) da Umar (RA) da Aisha (RA) da sauran sahabbai. Abu ma fi ban takaici, a wannan film ɗin har Annabi (SAW) an nuna a fili. Babu ƴar sakayar wannan da ake yi a wasu fina-finai, ka ga an nuno wani haske ko kuma aƙi nuno shima gaba ɗaya, saidai a saka wani sahabi yana isar da maganarsa ga mutane. Duk babu wannan. Hakanan an nuna Ali (RA), amma Faɗima (RA) ko tafin hannunta ba a nuna ba, haka nan ƴaƴanta Hasan (RA) da Husaini (RA). Wani kuma abin takaicin, ƴan film da suka fito a ciki duk arna ne, ko ƴan Shi'an ma babu a ciki!!
Wannan film ɗin ya tada ƙura a lokacin. Wasu ƙasashe sun hana haska shi bayan an gama tallata shi. Ina iya tuna cewa Kuwait tana daga cikin waɗanda suka hana, amma hakan bai sa an fasa haska shi ba, yanan kuma ana samunsa a yanzu haka.
Wannan shi zai nuna maka yadda matsayin Annabawa, ciki har da Annabi (SAW), da matsayin limamai 12 yake a wurin Shi'a. Idan ba ka iya karantawa a littfaansu ba, to a fina-finansu za ka gane. Su kan sahabbai ba ta su ake ba daman.
Don haka, don a satinnan a arewacin Nigeria an samu wasu ƴan Shi'a sun yi wani wasan kwaikwayo inda a ciki aka ayyana wani a matsyin shine Annabi (SAW), wasu sun ga abun banbarakwai. Ka da ku yi mamaki. Wannan da kuka gani da sauki, tinda shi aƙalla an rufe ma fuskarsa, domin iyayen gidansu, wanda suka fi su tumbatsa a Shi'ancin, tuni suka wuce wurin!!
Allah ya yi mana tsari.
Repost from قناة: محمد إلهامي
الذي ينبغي في ذكرى عاشوراء هو التركيز على قصة موسى عليه السلام ونجاته من فرعون، وهي قصة كثيفة العبر، بل عبرها لا تنتهي، وفي كل قراءة نرى فيها جديدا!
ومن هنا يمكنك مراجعة المنشور السابق!
ومع ذلك، فلا بد من إلقاء بعض الضوء على مقتل الحسين الشهيد، رضي الله عنه، ريحانة النبي وسيد شباب أهل الجنة، فالأمر يُثار بفعل الشبهات التى تلقى حول تاريخنا وحول أمتنا وحول نظامنا السياسي وحول الدولة الأموية العظيمة!
وقد زاد الشر في السنوات الأخيرة ببروز فرقة النواصب الجدد، الذين جددوا الفرقة الناصبية المنقرضة من بعد ما قد كانت طوتها صفحات التاريخ، وما ذلك إلا أنها رد فعل متطرف على الغلو الشيعي والمقاتل التي نزلت بأهل السنة لا سيما في العراق ولبنان واليمن.
وتوفيرا للجهد والطاقة وتتبع الأسئلة الواردة، فإني أحيل إلى حلقتيْن من سلسلة: مائة سؤال في التاريخ، عن عهدي معاوية بن أبي سفيان -رضي الله عنه- وولده: يزيد بن معاوية!
https://youtu.be/y__hsR9ro3I
https://youtu.be/inL92ncOk4Y
وإلى هذا المجلد الثالث من كتابي: خلاصة تاريخ الإسلام
https://t.me/kotob_elhamy/64
ففي ذلك خلاصة ما أرى وأعتقد.. والله الهادي إلى الصواب والموفق إلى سبيل الرشاد
Repost from Abdurrahman Muhd Sani Umar
Sakamakon ƙaratowar ranar Ashura ga wasu rubuce-rubuce da suka taɓa gabata game da wannan munasabar da take tunkararmu:
1-Mu muka fi cancanta da Musa (As) da Husain (RA)
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=5167162576714273&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
2- Ashura :Alaƙar Annabi (SAW) Da Musa (As):
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=5166357280128136&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
3-Abubuwa 6 Game Da Yazid Bin Mu'awiyah:
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=5177158035714727&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
4-Munfar Bukukuwan Ashura A Wurin Shi'a:
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=5160952677335263&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
5- Yaushe Aka fara bukukuwan Ashura?
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=5157995154297682&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
6-Tufka Da Warwara!!
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=5171823346248196&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
7-Daga Cikin Darussan Ashura:
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=6263896893707497&id=100002617460854&mibextid=Nif5oz
8- Karkatar Da Manufar Ashura:
https://www.facebook.com/share/p/si9svaseu55ELCwe/?mibextid=oFDknk
9- Darasi na Har Abada Game Da Ashura :
https://www.facebook.com/share/p/1AXnZY1eH8/
#Ashura
Repost from Abdurrahman Muhd Sani Umar
KARKATAR DA MANUFAR ASHURA!!
Kasancewar ƴan shi'a sun maida ranar Ashura zuwa ranar baƙin ciki, wanda suke fakewa da wannan suke zagin waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, a gefe guda kuma ƴan sunna sai suka shagaltu da yi musu martani, hakan sai ya haifar karkarta daga maƙasudin wannan rana da Annabi (SAW) ya ambata na farin ciki da kuɓutar Annabi Musa (As) zuwa wani abu daba, har aka wayi gari mutane da yawa da an ambaci Ashura babu abinda yake fara faɗowa a ransu face batutuwan shi'a da shi'anci !! Wanda kasantuwar hakan za a iya cewa ƴan shi'an sun ci nasara tinda aƙalla sun iya canza wa mutane da yawa tinani game da Ashura ya zamanto ba sa halarto komai face batutuwan shi'a ko da ba su yarda su ba !
Yana da kyau ga malamai da masu karantarwa da duk waɗanda alhakin tarbiyantarwa take hannunsu a karon farko su fi maida hankali wajen dasa wa al'umma abinda Annabi (SAW) ya nuni gare shi na yi farin ciki game da kuɓutar Annabi Musa (AS) da kuma koyar da su darussa da ma'anonin da wannan munasabar ta ƙunsa, tare da bayani akan batutuwan da ƴan shi'a suke tayarwa nan da can. Hakan zai sa ya zamanto maƙasudin da Annabi (SAW) ya tabbata a kuma gefe guda kuma ba a wofantar da martani akan batutuwan shi'a ba, domin hakanne zai ba wa mutane cikakkiyar garkuwa.
Allah ya datar da mu.
Azumin Tasu'a: Shaidar Cin Gashin Kan Musulunci
Azumin Tasu'a yana ɗauke da ma'ana mai girma ta sabawa waɗanda ba Musulmai ba, tare da ƙara fito da keɓantacciyar siffar Musulunci da bambancinsa da sauran addinai, akidu da ra'ayoyi. Haka kuma yana ƙara tabbatar da cewa Musulmi yana da cikakken tsarin rayuwa mai zaman kansa; ba a yarda ya gauraya da wasu ta yadda za a rasa bambanci tsakaninsa da su ba, balle ya narke cikinsu har a kasa gane asalinsa da ainihin martabarsa.
Wannan keɓantacciyar siffa tana farawa ne tun daga akida da ibada, har zuwa tsare-tsaren rayuwa, mahanga, da ma'aunan da Musulunci ya gina, waɗanda suka sha bamban da na sauran addinai da tsarin tunani. Wannan bambanci ne ma ya sa Musulunci ya kasance abin tsoro ga maƙiyansa fiye da sauran wasu addinai, domin yana kiyaye wa mabiyansa ainihinsu da cin gashin kansu na tunani da rayuwa.
Muna da matuƙar buƙatar tabbatar da wannan manufa musamman a wannan zamani, lokacin da jahiliyyar Yammacin duniya ta samu ƙarfi da tasiri a zukata da tunanin mutane da dama daga cikin Musulmai. Har an kai ga samun wasu masu kiran kansu Musulmai, amma tunaninsu, furucinsu, ma'aunansu, abubuwan da suka yi imani da su, da ma salon rayuwarsu gaba ɗaya sun kasance ƙarƙashin tasirin Yamma. Suna kallon komai ne ta mahangar da ba ta samo asali daga Musulunci ba, suna auna abubuwa da ma'aunan da ba na addininsu ba. Wannan shi ya kai ga wasu zuwa musunta tabbattun abubuwa a musulunci, ko karin tabbatar abubuwan da suka ci karo da shi, da bankara shi domin ya dace da waccan lalataciyyar jahiliyar da ta riga ta cinye su.
Wannan ita ce Falasafa da ma fi muhimmancin sako da ke cikin azumtar ranar Tasu'a.
*The Malicious Death of Nihal in Catholic School: A call for Justice and accountability*.
The death of Maimuna Sani at St. Louis Catholic secondary School does not the first time Kano is witnessing controversies involving schools and students.
In December 2021, five-year old Hanifa was kidnapped by her school teacher, Abdul Malik Tanko, WHO eventually poisoned her with Rat 🐀 killer after she recognised him which led to her death. More recently, in May 2026, a teacher at Al-Hadeed private school in Ungogo Kano was accused of Raping four underage sisters of the same parents.
On Saturday, 13 June late Nihal (A Muslim), little girl was reportedly slumped at the Catholic Christian School as a result of the alleged corporal punishment that she suffered under the Careless watch of the School management.
According to Nihal's mother, The doctor told her sister that the little girl was already dead when they brought her to hospital.
We have seen how the case of Abdulmalik Tanko sparked nationwide outrage, and in July 2022, he was sentenced to death by hanging. Conversely, "uncle Kamal" of Al-Hadeed private school was arraigned before a magistrate court in Kano and remanded in correctional custody pending the trial and the private school was shut off indefinitely.
To the Police, I strongly strongly emphasizes that no person, institution, or authority should be allowed to attempt to suppress evidence, conceal facts, intimidate witnesses, distort findings, shield perpetrators, or otherwise obstruct justice in the case of NIHAL. Any such conduct would constitute a further assault on the rule of law and public confidence in the administration of justice.
One important question that needs to be asked is why does the Kano State government refuse to shut down the St. Louis Catholic School immediately after the alleged murder of the innocent girl as we have seen in the case of Al-Hadeed private school ❓❓❓As a follow up question, is the Abba Kabir's led government trying to draw a clear dichotomy between Christian and Muslim Citizens, by treating the former as first Class Citizens and the latter as mere asylum seeker❓❓ ❓
The Malicious death of Nihal in Catholic School if confirm, would constitute a tragic violation of the right to life as enshrined in section 33 of the constitution of the federal Republic of Nigeria, human dignity under section 34, equality before the law, and the fundamental principles of justice and due process.
Based on the above, we can logically deduce that the tragic death of Nihal and the like may erode parental confidence in schools, and if not controlled many parents will begin to remove their wards, and we will end up with more dropouts, out-of- school children and street hawkers.
While reminding both the Kano State government and the Nigeria police Force, that the alleged Murder of Nihal is Grade "A" felony offence that should be treated with all sense of seriousness, we equally discourage the slow pace of the criminal justice process, where murder trials can span years or even decades.
As we await the quick response of the Kano State government, we say NO to unnecessary delayed police investigation in the case of the tragic death of Nihal.
The Kano State government should also recall that protection of human life is among the highest obligations imposed upon every Democratic government.
Justice for NIHAL, justice for her family, justice for the vulnerable children, justice for Muslims, and justice for society at large requires full accountability wherever the evidence may lead.The famous Latin maxim says "Fiat Justitia ruat caelum"
A stitch in time saves Nine!!!
Salim Usman
23-06-2026
*Karatun Littafin*
*نبي الرحمة سيرة ودروس وعبر*
Drs na 53
*Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar*
Daga Masallacin Markazul Imamul- Bukhari Rijiyar Zaki Kano.
23/06/2026 - 08/01/1448
- Me yasa Ƙuraishawa suka tsorata da Hijira?
- Wasu hikimomin kasancewar garin Madina shine garin Hijira.
- Tsokaci kan falalar garin Madina.
- Me yasa hijirar Manzon Allah (SAW) da Abubakar (RA) da Aliyu (RA) ta yi Jinkiri?
- Taƙaitaccen bayani game da azumin Tasu'a da Ashura
Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:*
Whatsapp:
(A)
https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv
(B)
https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc
Telegram:
https://t.me/Abm_Sani
Facebook:
https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL
YouTube:
https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm
A jiya an yi hira da shugaban ƙasar Syria, Ahmed al-Sharaa, inda ya bayyana cewa an sanya musu matsin lamba da nufin su tura sojojinsu zuwa Lebanon domin yaƙar Hezbullahi, amma gwamnatin Syria ba ta amince da hakan ba. Haka kuma ya ce, duk da abin da ya faru a baya tsakaninsu da Hizbullahi, a shirye yake ya zauna da su domin tattaunawa da warware sabani ta hanyar fahimtar juna.
Wannan magana ta zo ne bayan shugaban Hizbullahi, Naim Kasim, ya bayyana a satin da ya gabata cewa lallai Syria ta fuskanci matsin lamba domin ta shiga Lebanon ta yaƙi Hizbullahi. Ya kuma gode wa Allah da gwamnatin Syria ba ta amince da wannan matsin lamba ba. Bugu da ƙari, wasu rahotanni sun nuna cewa sabuwar gwamnatin Syria ta kan kawar da kai wajen yi wa Hizbullahi fasa kaurin makamai daga kasarta.
To, mene ne ma'anar wannan?
A cikin wannan ɗan taƙaitaccen bayani akwai saƙonni masu yawa ga 'yan Shi'a, da kuma wasu masu dangantuwa da Ahlus-Sunnah.
Ga 'yan Shi'a, wannan na iya zama hujja ta dubu da daya akan karerayin da wasu daga cikinsu suka dade suna yadawa cewa sabuwar gwamnatin Syria tana aiki ne a ƙarƙashin umarnin Isra'ila da Amurka. Domin da ace hakan gaskiya ne, da ba za ta yi jinkiri ko nuna wata-wata ba wajen shiga Lebanon domin taimakawa wajen yaƙar Hizbullahi musamman yadda suke da dalilai sama da dubu da za su iya yakarta ga kuma cikakken goyon bayan kasashen yamma da na larabawa da za su samu. Haka kuma wannan yana nuna wani irin dattako da hangen nesa daga gwamnatin Syria, domin ba ta bari tarihin rikici da raɗaɗin abin da ya gabata ya sa ta zama kayan aikin wasu ƙasashe wajen cimma manufofinsu ba. kamar yadda irin wancan kawancen na shi'anci ya yake su karkashin jiragen Amurka da Rasha, Duk da irin wahalhalun da ta sha a baya, ba ta amince ta ɗauki matakin da zai amfani Isra'ila ko Amurka a wannan yanayi ba.
Ga wasu masu dangantuwa da Ahlus-Sunnah kuwa, darasin da ke ciki shi ne cewa waɗanda suka fi kowa shan azaba a hannun Iran da ƙawayenta, ciki har da Hizbullahi da wasu ƙungiyoyin Shi'a, su ne mutanen Syria. Sun ga kisan kare dangi, tarwatsa garuruwa, da nau'o'in zalunci iri-iri. Amma duk da haka, ba su bari wannan tarihi ya sa su mayar da su ma'aikatan yahudawa da sauran kafiran duniya ba, ba su ce gwara Isra'ila akansu ba saboda da a farke suke sun san matsayin kowanne.
A nan akwai wani muhimmin darasi na siyasa da dabarun mu'amala: kamar yadda soyayya take da matakai, haka ma adawa da ƙiyayya suke da matakai. Ba kowane abokin gaba ne yake a matsayi ɗaya ba, kuma ba kowane lokaci ne ya dace a mayar da hankali kan kowane abokin gaba ba. Hikima ita ce a san yadda za a tantance matakan barazana da fifikon abubuwan da suka kamata a tunkara. Duk wanda ya kasa jera abokan adawarsa bisa matakan da suka dace, kuma ya kasa fahimtar bambancin matakan maslaha da mafsada, to akwai yiwuwar ya jefa kansa da al'ummarsa cikin matsalolin da ba za su haifar da da mai ido ba.
Game da Makarantun Ƴan Mission
Wasu ɗauka suke yaƙar Musulunci shi ne a kama Musulmai, a yi ta azabtar da su, ana kashe su, kamar yadda kafiran Makka suka yi. Don haka idan ba haka suka gani ba, to zaune ake kalau, babu wani yaƙi da ake yi wa Musulunci da Musulmai. Duk irin salo da za a yi ta amfani da shi iri-iri wajen yaƙar Musuluncin su, ba za su gamsu ba saboda a wurinsu salo ɗaya ake a yaƙi Musulunci, shi ne irin wancan salon da ya gabata!!
Salon amfani da ƙarfi da fitowa fili wajen yaƙar Musulunci, a da an samu ƙasashe da gwamnatoci da dama da suka bi wannan salo, kuma har yanzunma akwai masu bin ire-iren wannan salo. Saidai kasancewarsa bai cika bada irin sakamakon da su maƙiya Musulunci suke nema ba, shi yasa suka fi dogaro da salo na ruwan sanyi, salon da za a canza Musulmi tuanani, a tubesa daga Musuluncin ma ba tare da ya sani ba!!
A irin wannan salo, ba laifi za a iya barin Musulmi yayi sallah, ya yi azumi, ya yi umara da hajji, ya yi sadaka, amma za a nuna masa cewa iya nan ne Musuluncin. Idan ya yi haka to ya gama, sauran ɓangarorin rayuwarsa kuma ba ruwan Allah a ciki!!
A irin wannan salo za a ba shi dama ya yi karatun Alƙur'ani, yama hadda shi, kilama har makarantarsa a buɗe masa, a shirya masa musabaƙa. Amma za a yi ƙoƙari kada ya san haƙiƙan ma'anonin da saƙonnin da suke cikin Alƙur'ani, za kuma a jirkata masa fassararsu. Idan har ta kama sai ya san fassarar, sai ya zamanto abin da yake karantawa daban, fassarar da ake ba shi daban!!
Salon da za a da za bar mace ta saka hijabi a sallah ko a jimamin mutuwa, amma a makaranta ko wata sabgar rayuwar kuma a ƙi ba ta dama, tare da suranta mata cewa hijabin al'adace kawai, ba ba umaranin Allah bane.
Salone wanda za a dinga juyawa mutane tarihi, yayin da za a yi ƙoƙari a jahiltar da su na su tarihin. A gefe guda za a yi ƙoƙari a cusa musu tarihin wasu maƙiya Allah, 'yan ta'adda mashaya jini, a matsayin cewa su din gwaraza ne, ababen koyi ne.
A taƙaice, salone wanda zai zarewa Musulumi duk wani kishin addininsa, da dasa masa ƙyamar msulumai masu riƙo da addininsu, da kuma cire musu tsoron aikata saɓo, da kuma tsuke musu addinin a iya alaƙar bawa da ubangiji, da kuma bankara Musulunci domin yayi daidai da abin da suke kai.
Don haka masu kumfar baki akan St Louis da ƙoƙarin nuna cewa ai ana ba wa Musulmai dama, ya kamata su hankalta su san me suke yi. Kamar yadd ana faɗa a baya, ko iya saka sunan kaɗai ya nuna manufar ire-iren waɗannan makarantu, wanda ko a iya shigar ɗalibanta da kuma yadda wasu lalatattun Musulmai suke ƙoƙarin bata kariya za ka gane inda ake so a je. Kuma kamar yadda ya gabata shi wanda aka raɗa sunansa a makarantar shine madugun irin wannan salo na ƙoƙarin gurɓata wa musulmai addininsu bayan ya gagara cin nasara ta ƙarfi.
Allah yasa mu dace.
Game da yaƙin America, Isra'ila da Iran, duba da abin da aka ce yarjejeniya ce da tsagaita wuta, za ka iya cewa:
Wanda ya fi kowa samun riba a wannan yaƙin ita ce Iran, kasancewar ta shiga yaƙin ba ta da wasu abubuwa, ta kuma fita daga yaƙin da abubuwan da ita kanta ba ta yi tsammanin za ta same su nan kusa ba, ta kuma wannan hanya ba.
Wanda ya fi kowa tozarta kuma ita ce America, kasancewar ƙarfinta da ikonta da take takama da shi wajen mulkar duniya, har shugabanta ya ɗauki kansa tamkar wani ubangiji, sai ga shi ta zama kassasshiya, rauninta ya bayyana a gaba. Wata miskiniyar ƙasa da takunkumi ya gama galabaitar da ita sama da shekara 40, wanda a ƙarshe ta saka hannu a yarjejeniyar da take shelanta cewa ta ba da gari.
Wanda kuma ya fi kowa takaici kuma ita ce Isra'ila, domin ta samu wata dama wadda ba lallai ta sake maimaituwa nan kusa ba, na kifar da mafi hatsarin tsarin mulkin da yake mata barazana, da kuma tunkarar sauran ƙasashe, dama canza taswirar Gabas ta Tsakiya ta yadda za a wayi gari ita ce shugaba, sauran ƙasashe kuma bayinta. Duk waɗannan manufofin Isra'ilan da ta ga cewa tana dab da cimma musu, duk sun tashi a iska yanzu sakamakon wannan yarjejeniya, wanda hakan zai sa za ta ci gaba da matsawa da ƙoƙarin lalata wannan yarjejeniyar.
Mafi ƙaskanta da wulakanta kuma su ne ƙasashen Gulf. An shiga yaƙi ba da izininsu ko shawararsu ba, an mayar da ƙasashensu filin wasan wannan yaƙi ba tare da sun iya buɗe baki ba. Yanzu kuma an kallafa musu cewa su ne za su biya Iran diyyar barnar da aka mata a madadin waɗanda suka shigar da su yaƙin da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba, su kuma asarar da ƙasashen suka yi ko oho!
Mafi ban tausayi kuma su ne mutanen Gazza, domin kowa ya shiga cikin wannan yarjejeniya amma su ban da su. 'Yan uwansu ƙasashen Sunna ba sa sama zancensu, balle a zo kwancen Shi'a, wanda dama maslaha ce take ɗan haɗa su wani lokaci!
Wannan shi ne sakamakon wannan gwabzawa a yanzu. Sai dai, kamar yadda ya gabata, Isra'ila ba za ta yarda a tafi a haka ba. Kai, har ma masu kishin America, musamman waɗanda suke ma'aikatar tsaro da leƙen asiri, suma ba lalle su yarda a dore a haka ba. Hasalima, rahotannin da suke fitowa, tsaid a yaƙin an yi shi ne domin wasu dalilai wanda duk sanda suka kau za a dawo, za kuma a iya dawowar a kowane lokaci. Yaƙi ba zai zo ƙarshe ba sai an kassara ɓangare ɗaya, kassarawar da za ta sa ba zai sake miƙewa ba.
Waye "St Louis"?
Sarkin Faransa Louis na 9 ya zama sarki ne bayan rasuwar babansa Louis na 8 a shekara ta 1226. Saboda tsananin taƙawarsa da biyayyarsa ga addinin Kiristanci, Cocin Katolika ta ba shi mafi ƙololuwar matsayi a addininsu, wato matsayin Saint. Daga nan aka fara kiransa da “Saint Louis” ko “St. Louis”.
Ana bayar da labari cewa ya yi fama da wata rashin lafiya mai tsanani har ta kusa kashe shi. Sai malaman addininsa suka nemi ya yi bakance cewa idan ya warke, zai yaƙi “kafirai”, wato Musulmai kenan. Suka ce masa saboda yaƙi yaƙar musulman ne ma Allah ya jarabce shi da wannan rashin lafiya.
Bayan warkewarsa, sarki Louis ya jagoranci runduna daga Faransa zuwa Masar, da nufin idan ya ci nasara a kanta zai ci gaba zuwa birnin Ƙudus domin kuɓutar da shi daga hannun Musulmai. Wannan ya faru ne a shekara ta 1248.
A farkon yaƙin ya samu wasu nasarori, amma daga baya a 1250 (648H) aka gwabza Yaƙin Faraskur a garin Mansura, inda Musulmai suka yi nasara akansa suka kama shi. Daga baya ya biya fansa ya koma ƙasarsa, amma hakan bai hana shi ci gaba da shirye-shiryen yaƙi ba. A shekara ta 1270 ya sake jagorantar wata yaƙin zuwa Tunisiya, inda ya rasu sakamakon rashin lafiya.
Wannan sarki ana danganta masa wasu wasiyoyi da ra’ayoyi game da yadda za a yaƙi Musulmai, musamman ta hanyar yaƙin tunani cikin ruwan sanyi. Akan irin waɗannan ra’ayoyi ne ci- ranin addini (Orientalism) ya ginu.
Wannna shine baƙin tarihin wannan mutumi da ya ƙarar ds rayuwarsa wajen yaƙi da musulmai da muslunci, kuma har yau maƙiya musulunci suna kan amfana da shwarwarin da wasiyoyinsa wajen yaƙar musulmai.
a yau za ka ga makarantu da asibitoci da wurare da dama ana raɗa sunansa, abun takaicin kuma ka ga musulmai suna rige-rigen kai ƴaƴansu ire-iren waɗannan makarantu, wanda duba da tarihinsa kai kasan cewa mecece manufar duk wata makaranta ko gidauniya da za a buɗe da sunansa.
Abun takaicin kuma iyaye musu wannan aika-aikar ta halaka imani da addini da tarbiyar ƴaƴansu saboda da abun duniya, ji suke suna ba wa ƴaƴansu tarbiya saboda da su a wurinsu taribiya ita ce ka ba wa yaro ci da sha ka tufatar da shi ka saka shi a boko shikenan ba ruwansu da addininsa da ɗabi'arsa da halayensa, a hakane ake wayar gari a samar da al'ummar da alaƙarsu da musulunci ta sunane kawai, amma a komai sun yi hannun riga da shi.
Ba ka buƙatar kai ɗanka ko wani naka makarantun mission, don kawai ya iya turanci ko ya samu karatun boko, a yau akwai makarantun musulmai da yawa wanda sun wadatar ɗalibi zai samu iingataccen karatu sannan kuma ya samu tarbiyya irin ta musulunci.
*Karatun Littafin*
*الأربعون النووية*
Drs na 56
*Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar*
Daga Masallacin Imamu Musulim, Ɗanbare Unguwar katako, Kano
03/01/1448
18/06/2026
Hadisi na 19
* Tsokaci game da Hijira da watan Muharram
* Taƙaitaccen tarihin marawaicin hadisin.
*Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:*
Whatsapp:
(A)
https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv?mode=wwt
(B)
https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc
Telegram:
https://t.me/Abm_Sani
Facebook:
https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL
YouTube:
https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm
*Karatun Littafin*
*نبي الرحمة سيرة ودروس وعبر*
Drs na 52
*Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar*
Daga Masallacin Markazul Imamul- Bukhari Rijiyar Zaki Kano.
16/06/2026 - 01/01/1448
- Buƙatuwa zuwa ga mazaje masu manufa.
- Abinda zai saka maka jin girman ni'imar musulunci.
- Wasu hikimomi na rashin wajbta Jihadi a Makka.
- Shimfiɗa game da Hijira.
Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:*
Whatsapp:
(A)
https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv
(B)
https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc
Telegram:
https://t.me/Abm_Sani
Facebook:
https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL
YouTube:
https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm
Wasu Munanan Halaye da Wasu Sassan Al'umma Suka Fi Faɗawa Cikinsu
Daga cikin munanan halayen da suka yawaita a wasu sassan al'umma akwai mara wa azzalumai da zalunci baya da kuma daɓi'antar da shi wato "Normalization".
Wannan mugun hali ya fi bayyana a tsakanin wasu 'yan siyasa da magoya bayansu, da kuma waɗanda suka mayar da kansu tamkar wata haja a kasuwa; duk wanda ya biya farashin da suke so, a shirye suke su mara masa baya komai irin laifinsa. Haka kuma, ana samun wannan hali a wurin wasu masu dangantaka da ilimin addini da wa'azi.
Wasu suna faɗawa cikin wannan mummunan hali ne saboda sun yarda cewa abin da ake yi daidai ne, yayin da wasu kuma tsabar kwaɗayi da son abin duniya ke sa su amince su ci amanar al'ummarsu. Mafi muni daga cikin su kuwa su ne waɗanda suke fakewa da addini wajen kare azzalumai da kuma ƙoƙarin shar'anta zalunci.
Hali na biyu shi ne daɓi'antar da ayyukan alfasha da saɓo. Wannan kuwa ya fi yawaita a tsakanin gama-garin mutane, inda ake ba wa ayyukan alfasha da fasaƙanci kariya ko uzuri, musamman idan asirin wani ɗan duniya ya tonu. Sau da yawa za ka ji ana cewa: "Ai kowa ma haka yake" ko "Babu wanda ba zai iya aikatawa ba", da nufin rage girman laifin ko kare mai aikata shi.
Ya kamata a sani cewa haɗarin kare laifi ya fi haɗarin aikata laifin kansa. Mai yiwuwa Allah Ya gafarta wa mai laifi saboda tuba ko wasu dalilai, amma Ya ƙi gafarta wa wanda ya tsaya yana kare laifin da kuma ƙoƙarin nuna cewa ba laifi ba ne. Domin aikinsa yana kama da shar'anta laifi da kuma ƙarfafa mutane su ci gaba da aikata shi.
Haka kuma, idan uƙubar Allah ta sauko saboda yaɗuwar laifi da rashin hana shi, ba za ta taƙaita ga masu aikata laifin kawai ba; har waɗanda, suke ba su kariya ko suka yi shiru duk da suna da ikon yin magana, za su shiga cikin wannan uƙuba. Ƙissar matar Annabi Luɗ (AS) da kuma mutanen da aka hana kamun kifi ranar Asabar manyan misalai ne.
Saboda haka, idan mutum ba zai iya yin Allah-wadai da laifi da saɓo ba, to abinda ya fi masa alheri ya yi shiru akan ya fito yana kare masu laifi ko ayyukansu. Domin hakan wani nau'i ne na taimakawa yaɗuwar ɓarna da kuma nuna rashin ƙyamar abin da Allah Ya haramta, da fito na fito da Allah.
Mafi girman ɓarna kuma shi ne a shar'anta ɓarna, a mayar da ita wata hanya ko tafarki na rayuwa, ko a riƙa tallata ta a matsayin abin da ya dace. A irin wannan yanayi ne al'umma ke fuskantar mafi girman haɗari, kuma a irin wannan yanayi ne uƙubar Allah take fi kusantowa idan ba a tuba ba kuma ba a yi gyara ba.
Available now! Telegram Research 2025 — the year's key insights 
