ru
Feedback
Abdurrahman Muhd Sani Umar

Abdurrahman Muhd Sani Umar

Открыть в Telegram
3 470
Подписчики
+124 часа
+1247 дней
+18830 день
Архив постов
Arba'una 59.m4a10.96 MB

*Karatun Littafin* *الأربعون النووية* Drs na 59 *Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar* Daga Masallacin Imamu Musulim, Ɗanbare Unguwar katako, Kano 08/02/1448 23/07/2026 Hadisi na 19 * Kasan Allah cikin yalawa zai san da kai lokacin tsanani * Nasara tana tare da haƙuri. * ƙunci da musiba suna tare da sauƙi da yaye musiba. *Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:* Whatsapp: (A) https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv?mode=wwt (B) https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc Telegram: https://t.me/Abm_Sani Facebook: https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL YouTube: https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm

*Karatun Littafin* *نبي الرحمة سيرة ودروس وعبر* Drs na 56 *Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar* Daga Masallacin Markazul Imamul- Bukhari Rijiyar Zaki Kano. 21/07/2026 - 06/02/1448 * Fitowar Annabi (SAW) da nufarsa garin Madina. - Haɗuwar Suraqah bin Malik da Annabi (SAW) da abinda ya gudana tsakaninsu. Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:* Whatsapp: (A) https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv (B) https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc Telegram: https://t.me/Abm_Sani Facebook: https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL YouTube: https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm

A yau aka cika shekara goma cif da yunƙurin juyin mulkin da aka yi a Turkiyya, wanda za a iya cewa shi ne ya shata layi tsakanin Turkiyar jiya da Turkiyar yau, a matakin cikin gida da kuma a idon duniya baki ɗaya. Akwai dimbin darussa ga musulmi a cikin wannan lamari, amma watakila mafi girman darasin shi ne muhimmancin jagora da kuma turjiya. Da ba a samu jagora ba — wanda shi ne shugaban ƙasar a wancan lokaci — tare da kyakkyawan jagoranci, da tuni wannan yunƙuri ya yi nasara a kan ƙasar da ma al’ummar musulmi. Haka kuma, da ba a tsaya tsayin daka wajen turjewa wannan guguwa da maƙiyan Allah suka shirya ba, da Allah kaɗai Ya san irin halin da ake ciki a yau. Saboda haka, samun jagora nagari tare da kyakkyawan jagoranci, sannan kuma haƙuri da turjiya, su ne manyan muƙullan duk wata nasara da ka sani a tarihi. Al’ummarmu kuwa cike take da masu kishi, da waɗanda suke shirye su sadaukar da komai domin abin da suka yi imani da shi. Sai dai rashin samun jagora da kyakkyawan jagoranci ne yake hana su cin moriyar damammakin da suke da su, domin ba sa iya sarrafa su yadda ya kamata. Babu yadda za a samu cikakkiyar nasara idan aka rasa waɗannan abubuwa, duk tsananin kishin da mutane suke da shi ko yadda suke shirye su sadaukar da komai. Muddin ba su da jagora nagari da kyakkyawan jagoranci, to da wuya su kai ga nasarar da ake buri. Wannan ita ce sunnar Allah wadda ba ta taba canzawa.

photo content

Lendsey Graham fitaccen ɗan majalisar dattijai ta America tsawon shekara 23, kuma ɗan majalisar wakilai kafin nan daga 1995 zuwa 2003, sannan ɗan majalisar jiha kafin nan daga 1992 zuwa 1994. Mutum ne wanda ya yi kaurin suna wajen ba wa ya%hudawa da ta'addancinsu cikakken goyon baya; wani lokaci ma yakan fi su yahuda%nci ma. Haka nan ya shahara da ƙin Musulunci da musulmi. A ƙarshe-ƙarshe ma sai dai ya kira ga Isra'ila da ta daina tsayawa, bata lokacinta kawai ta yi amfani da makamin kare dangi "Nuclear", ta shafe Gazza daga doron ƙasa! Haka nan shi ɗin ana zarginsa da kasancewa mai aikata aikin mutanen Annabi Lud. A taƙaice, za ka iya cewa duk wata ƙazanta da sharri na duniya na zahiri da na ɓoye sun tattara a tare da shi. Bai daɗe da faɗin cewa shi ba zai taɓa mutuwa ba har sai ya tabbatar da mugayen manufofinsa, sai ga shi lokaci guda cikin wata gajeriyar rashin lafiya Allah ya ɗauki ransa, ya zama tarihi kamar babu shi! Ya mutu ya bar duniya ba tare da waɗanda yake karewa ba sun iya masa komai ba; haka nan bayan ya ba da gagarumar gudummawa wajen cutar da miliyoyin mutane, musamman musulmai, wanda suna can suna jiransa a gaban Allah. Mutuwar Lendsy da ire-irensa suna ƙara tunatar da mu ni'imar samuwar ita kanta mutuwa, da kuma ni'imar ranar Alƙiyama da hisabi da sakamako. Haka nan kuma tana ƙara nuna mana cewa duk wani jabbari ɗan ta'adda, to ƙarshensa yana nan zuwa, kuma haka zai ƙare ya tafi ya bar Musulunci da musulmi kamar yadda magabatansa suka yi. Haka nan mutuwar wannan mugun bawa tana ƙara haska mana munafukan wannan al'umma, yayin da ake jin murnarsu da shewarsu tare da mummunar addu'a duk sanda wani fitaccen malami ko mujahidi, ko wani mai ba wa addinin Allah gudummawa ya rasu ko wani ibtila'i ya same shi, sai ga shi a kan wannan sun yi tsit, ba a jin ko tarin su. Da yawansu ma ba lalle sun sani ba, domin ba ta shi suke ba; kasancewar maƙiyinsu da maƙiyansa duk ɗaya ne, wato musulmai. Shi yana ƙiyayyarsu da sunan Kiristanci da kare Yahudanci, su kuma suna yi da sunan tafarkin magabata! Allah muke roƙo da Ya nuna ƙarshen duk wani azzalumi ɗan ta'adda.

photo content

Yau ba mu samar karatun Nabiyur Rahma ba sai wani satin idan Allah ya kaimu

*Karatun Littafin* *الأربعون النووية* Drs na 58 *Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar* Daga Masallacin Imamu Musulim, Ɗanbare Unguwar katako, Kano 24/01/1448 09/07/2026 Hadisi na 19 * Ma'anar neman Taimakon Allah. * Kashe-kashen neman taimako. * Dalilin dake nuna cewa Allah shine ma fi cancanta da bauta. * Imani da kaddara da tasiransa a rayuwar dan adam. *Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:* Whatsapp: (A) https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv?mode=wwt (B) https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc Telegram: https://t.me/Abm_Sani Facebook: https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL YouTube: https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm

Duba da hare-haren jiya, da kuma jawaban Trump (duk da cewa ba kasafai ake dogaro da jawabansa ba), za a iya cewa yaƙi zai iya dawowa ɗanye a ko wane lokaci, wanda daman tsagaitawar da aka yi, an yi ne ba don tattaunawa domin kawo ƙarshen yaƙin ba, saidai don ko wane ɓangare ya ƙara shiri. Ba kuma mamaki a shiga jerin gwanon yi wa Iran kisan gilla, musamman jiga-jigan da suka bayyana a taron bikin mutuwar Khamina'i, da kuma fuskokin da aka sune ake tattaunawa da su, irin su Abbas Araghchi, Muhammad Baƙir Ghalibaf da shugaban ƙasar. Wannan yaƙi dai, kamar yadda muka sha faɗi, ba zai ƙare ba sai ɗayan ɓangare ya karya ɗaya, domin zamantowa duka ɓangarorin, a yadda suke yanzu, barazane ne ga juna.

*Karatun Littafin* *نبي الرحمة سيرة ودروس وعبر* Drs na 55 *Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar* Daga Masallacin Markazul Imamul- Bukhari Rijiyar Zaki Kano. 07/07/2026 - 22/01/1448 - Yadda Manzon Allah (SAW) ya fara shirin hijira. - wasu darussa daga shirin Manzon Allah (SAW) Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:* Whatsapp: (A) https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv (B) https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc Telegram: https://t.me/Abm_Sani Facebook: https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL YouTube: https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm

Dukkanin ƙungiyoyin Musulmi (in ban da Shi'a Imamiyya), sun yi ittifaki cewa Alƙur'ani cikakke ne, kuma Allah Ya kiyaye shi daga duk wani ƙari ko ragi. Malamai da dama sun naƙalto wannan ijma'i. Ɗaya daga cikin wuraren da ake iya ganin hakan shi ne a cikin littattafan tafsiri, musamman wajen bayanin ayoyin da suka shafi kiyaye Alƙur'ani. Misalan da wasu ke ƙoƙarin kawowa domin kada a ga baƙin Shi'a a kai, kamar batun Annasikh da Almansukh, ba hujja ba ce a wannan mas'ala. Duk wani ɗalibin ilimi ya san cewa wannan ba yana nufin an yi ƙari ko ragi a cikin Alƙur'ani. Haka kuma, Shi'a ma suna yarda da samuwar naskhi. Masu tabbatar da cewa an sauya Alƙur'ani a cikin Shi'a suna nassanta cewa an samu ƙari ne da ragi a cikinsa. Har ma su kan ambaci wasu ayoyi kosurori harma da wasu sunaye da suke ganin cewa an cire su, kuma da gangan aka cire su saboda ƙiyayya da ake yi wa Ahlul Baiti da ƙokarin yiwa munafukai rufa-rufa !!! Kuma idan Mahadi ya bayyana zai fito da na asalin!! Don haka, a wannan bigire ba sa kawo batun naskhi, kwata-kwata. Wanda ya san Shi'anci da kuma abubuwan da ya ginu a kai, zai ga cewa mafi dacewa da mazhabar shi ne ra'ayin jirkita Alƙur'ani da sauya shi. Kasancewar tafarkin Shi'anci ya ginu a kan Imama, wanda hasalima yake suranta cewa kusan abin da Allah Ya turo Annabi (SAW) domin shi kenan. Kuma shi wannan muhimmin rukuni babu abin da ke tabbatar da shi a Alƙur'ani ƙarara kamar sauran rukunan addini; sai dai a yi ta kame-kame. Bayanan Sahabbai kuma ba su da kyakkyawan matsayi a Shi'anci, inda ake nuna su a matsayin kafirai, munafukai, maciya amana, mayaudara, da duk wata mummunar siffa da ka sani. Bayan duk wannan kuma, a ce su ne suka tattara Alƙur'ani, suka rubuce shi, suka naƙalto shi. Don haka, za a samu tufka da warwara idan suka yarda da Alƙur'anin da ya biyo ta hannunsu. Don haka, a hankalce, dole Shi'anci ya ƙi yarda da wannan Alƙur'anin, duba da waɗanda suka yi masa hidima, da kuma rashin ƙunsarsa ga babban ginshiƙinsu, tare da yabon manyan maƙiyansu. Sai dai kuma tabbatar da wannan yana da hatsarin gaske. Shi ya sa wasu daga cikin malamansu suka zaɓi zama cikin tufka da warwara, domin gujewa abin da ya fi hakan muni. Za ka iya kamanta irin wannan saɓanin da saɓanin da ke tsakanin Ikhbariyyun da Usuluyyun a cikin Shi'a. Ikhbariyyun sun fi gaskiya, sai dai idan aka bi tasu, akidar za ta mutu. Usuluyyun kuma sun fi wayo, amma a fakaice sun saɓa wa tushen Shi'anci, wato Imama.

photo content

Yayin da ake jana'izar Khamina'i, wasu suna cewa Alƙur'anin da suka ji ana karantawa a wurin jana'izar shi ne Alƙur'anin da Musulmi suka sani, saɓanin ikirarin da ake yi cewa Shi'a suna da wani Alƙur'ani daban. Amma abin da ya kamata a sani shi ne, malaman Shi'a Imamiyya sun samu saɓani a tsakaninsu game da inganci da cikar Alƙur'anin da yake hannun Musulmi. Wasu daga cikinsu sun yi iƙirarin cewa Alƙur'anin da yake hannun Musulmi ya samu ragi ko sauye-sauye. Daga cikin masu wannan ra'ayi akwai Al-Kulaini ( Bisa saɓani tsakaninsu) , Al-Majlisi, Ni'imatullahi Al-Jaza'iri, Nuri Aɗɗabrasi, da sauransu. A gefe guda kuma, akwai wadanda da suka tabbatar cewa Alƙur'anin da yake hannun Musulmi shi ne cikakken Alƙur'anin da Allah Ya saukar, ba a yi masa ƙari, ragi ko canji ba suna ma kafirta mai fadin akasin haka. Daga cikin waɗannan akwai Ibn Babawaih al-ƙummi, Asshariful Murtada, Aɗɗusi, Al-Khu'i, da sauransu. Masu ra'ayin farko kuwa, waɗanda suke ganin an samu ragi ko sauyi a Alƙur'ani, suna cewa a yi aiki da Alƙur'anin da yake hannu a halin yanzu har zuwa lokacin bayyanar Mahadi, wanda, a cewarsu, shi zai fito da cikakken Alƙur'anin na asali. Saboda haka, masu cewa: "A fito mana da Alƙur'anin Shi'a," ya kamata su fahimci cewa, idan manufarsu ita ce wai Shi'a suna da wani Alƙur'ani daban da suke ɓoye wa, to ba haka bane. A aikace, Shi'a Imamiyya suna karantawa kuma suna amfani da Alƙur'anin da yake hannun sauran Musulmi. Haka kuma, bai dace a jingina wa dukkan Shi'a Imamiyya aƙidar cewa an canza Alƙur'ani ba, domin wannan lamari ne da malamansu suka yi saɓani a kai, kuma mafi yawan manyan malamansu na wannan zamani suna musanta cewa an samu ƙari ko ragi a Alƙur'ani. Allah ya sa mu dace.

photo content

*Karatun Littafin* *الأربعون النووية* Drs na 56 *Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar* Daga Masallacin Imamu Musulim, Ɗanbare Unguwar katako, Kano 03/01/1448 18/06/2026 Hadisi na 19 * Tsokaci game da Hijira da watan Muharram * Taƙaitaccen tarihin marawaicin hadisin. *Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:* Whatsapp: (A) https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv?mode=wwt (B) https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc Telegram: https://t.me/Abm_Sani Facebook: https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL YouTube: https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm

Sheikh Muhammad bin Abdulwahab da Sarki Muhammad bin Su'ud sun kafa Daular Saudiyya ta Farko a shekarar 1744. Sheikh Muhammad
Sheikh Muhammad bin Abdulwahab da Sarki Muhammad bin Su'ud sun kafa Daular Saudiyya ta Farko a shekarar 1744. Sheikh Muhammad bin Abdulwahab ya rasu a 1792, yayin da Daular Saudiyya ta Farko ta rushe a 1818. A gefe guda kuma, Sharif Husain, wanda ya kasance jagoran Makka a ƙarƙashin Daular Usmaniyya, an haife shi ne a 1854 ya kuma haɗa kai da Ingila a 1915, sannan ya shelanta tawaye ga Daular Usmaniyya a 1916 yayin da ake tsaka da yakin duniya na 1. Haka kuma, Sharif Husain ba bawahabiye ba ne, sai dai yana daga cikin mabiya tafarkin Sufanci. Yana da kyau mutane su tsaya su yi bincike kafin su fadi wani abu, ka da son bata wa wasu ko farantawa wasu yasa idonsu ya rufe domin za su bayyana jahilcinsu su kuma mayar da kansu abun dariya !!

*Karatun Littafin* *نبي الرحمة سيرة ودروس وعبر* Drs na 54 *Mal. Abdurrahman Muhd Sani Umar* Daga Masallacin Markazul Imamul- Bukhari Rijiyar Zaki Kano. 30/06/2026 - 15/01/1448 - Salon da ƙuraishawa suka ɗauka domin daƙile hijira zuwa Madina. - Taron Darun Nadaw da mataki mai hatsari da aka cimma. Domin samun karatukan malam ku bibiyi waɗannan shafuka:* Whatsapp: (A) https://chat.whatsapp.com/EYip4EPotboLSTwqiPKkfv (B) https://chat.whatsapp.com/LvMW02BVKegCbubI7E3ZbS?mode=wwc Telegram: https://t.me/Abm_Sani Facebook: https://www.facebook.com/am.sani3?mibextid=ZbWKwL YouTube: https://youtube.com/@abdurrahmanmuhammadsani7823?si=SqgPVhLHWJTTBRIm

Ga wanda yake bibiyar fina-finan Shi'a, zai ga cewa fitowar wasu a matsayin Annabawa, da har fuskarsu ma ana gani a fili, ba wani sabon abu ne. Amma a iya wanda na sani na kalla kuma, ba za ka taɓa ganin wani film da yake nuna limamansu ba. Har gwara Aliyu (RA) , sukan ɗan nuna shi, jefi-jefi. Karka yi mamaki idan ka san cewa a tsakanin 2020 zuwa 2021 sun yi wani film da suke bada tarihin Faɗima (RA) bisa riwayar Shi'a, inda a ciki suka bayyana aƙidunsu game da Abubakar (RA) da Umar (RA) da Aisha (RA) da sauran sahabbai. Abu ma fi ban takaici, a wannan film ɗin har Annabi (SAW) an nuna a fili. Babu ƴar sakayar wannan da ake yi a wasu fina-finai, ka ga an nuno wani haske ko kuma aƙi nuno shima gaba ɗaya, saidai a saka wani sahabi yana isar da maganarsa ga mutane. Duk babu wannan. Hakanan an nuna Ali (RA), amma Faɗima (RA) ko tafin hannunta ba a nuna ba, haka nan ƴaƴanta Hasan (RA) da Husaini (RA). Wani kuma abin takaicin, ƴan film da suka fito a ciki duk arna ne, ko ƴan Shi'an ma babu a ciki!! Wannan film ɗin ya tada ƙura a lokacin. Wasu ƙasashe sun hana haska shi bayan an gama tallata shi. Ina iya tuna cewa Kuwait tana daga cikin waɗanda suka hana, amma hakan bai sa an fasa haska shi ba, yanan kuma ana samunsa a yanzu haka. Wannan shi zai nuna maka yadda matsayin Annabawa, ciki har da Annabi (SAW), da matsayin limamai 12 yake a wurin Shi'a. Idan ba ka iya karantawa a littfaansu ba, to a fina-finansu za ka gane. Su kan sahabbai ba ta su ake ba daman. Don haka, don a satinnan a arewacin Nigeria an samu wasu ƴan Shi'a sun yi wani wasan kwaikwayo inda a ciki aka ayyana wani a matsyin shine Annabi (SAW), wasu sun ga abun banbarakwai. Ka da ku yi mamaki. Wannan da kuka gani da sauki, tinda shi aƙalla an rufe ma fuskarsa, domin iyayen gidansu, wanda suka fi su tumbatsa a Shi'ancin, tuni suka wuce wurin!! Allah ya yi mana tsari.

photo content