uz
Feedback
تربية الأولاد لشيخة رقية

تربية الأولاد لشيخة رقية

Kanalga Telegram’da o‘tish

Mun bude wannan channel din ne don ilimantarwa,fadakarwa, tunasarwa,da kuma yada Karatuttukan malaman sunnah.

Ko'proq ko'rsatish
1 591
Obunachilar
-224 soatlar
+47 kun
+1830 kun
Postlar arxiv
Ovozli xabar00:31

*FADAKARWA TA (198)* = *DAGA ZAUREN* = *تربية الأولاد لشيخة رقية* *What'sApp* *08149629880* *07045498743*  *24/02/1444* *21/09/2022* *¤¤بسم الله الرحمن الرحيم ¤¤* = *FALALAN SALLAN ASUBA DA LA'A'SAR:* *1️⃣ KIYAYE SALLAN ASUBA DA LA'A'SAR SUNA TABBATAR WA  MUTUM SHIGA AL'JANNA:*      An karbo daga abi Musal Ash'a'ry lallai Manzon ALLAH ﷺ Ya ce: *(( Duk wanda ya yi sallaci lukota biyu, "asuba da la'a'sar" ya shiga al'janna))* _Imamu Bukhari (574)Imamu Muslim (635)_ *2️⃣ KIYAYE SALLAN ASUBA DA LA'A'SAR ZASU HARAMTA MAKA SHIGA WUTA.*           An karbo daga Jundab bin Abdullahi ALLAH ya qara masa yarda ya ce, manzon ALLAH ﷺ ya ce: *((Duk wanda ya  yi sallah asuba  yana cikin alqawalin ALLAH,"Allah zai kula da shi"kada kasake ALLAH ya nemiku acikin alqawalinsa na da'a wani abu amma  sai ya sameku/riska baku yiba,sai ya kiffar da shi acikin wuta. "Allah ka tsaremu"* _Imamu (657)_ *3️⃣ SALLAN ASUBA TANA SANYA MUTUM CIKIN ALQAWALIN/KARIYA ALLAH DA KIYAYEWAR SA DA KULAWANSA.*           An karbo daga abu Malik Ashshaji'iy ALLAH ya qara yarda da shi ya ce, Manzon ALLAH ﷺ ya ce: *((Duk wanda ya sallaci sallan asuba yana cikin alqawalin/kiyayiwa ALLAH kuma sauran aiyukan sa/kididdigan  aiyukan sa suna wajan Allah.))* _Imamu Dabarani acikin AUSAD (4147) Albany ya inganta shi acikin Sahihul TARGIB WATTARHIB(458)_        *4️⃣DUK WANDA YA SALLACI SALLAN LA'A'SAR ACIKIN JAM'I YANA DA LADA GUDA BIYU "RODI BIYU".*            An karbo daga Abu Basratal Gifari ALLAH ya qara masa yarda ya ce munyi sallah tare da manzon ALLAH ﷺ sallan la'a'sar a wani waje da ake kira "MUGAMMAS"sai Manzon ALLAH ﷺ ya ce *(( lallai wannan sallah ta la'a'sar anbijiro da ita ga wadanda suka gabaceku sai suka tuzartata,"ku al'umma ta "duk wanda ya kiyaye ta yana da lada guda biyu/"ru6i biyu" babu wata sallah bayanta" ta la'a'sar "har sai mai hallatuwa ya mullu, shi ne tauraro))* _Imamu Muslim(830)_ *5️⃣KADA KACUTAR DA WANDA YAYI SALLAH ASUBA ACIKIN JAMA'A DOMIN ALLAH YANA TUNKUDE HARIN DA KAKE KAI MASA*          An karbo daga Abubakar Siddiq ALLAH ya qara masa yarda ya ce, Manzon ALLAH ﷺ ya ce: *((Duk wanda ya sallaci sallah asuba yana cikin alqawalin ALLAH kada ku warware alqawalin Allah acikin alqawalin sa,duk wanda ya yaki /nufaci  cutarwa ga wanda yayi sallah asuba a jam'i ALLAH zai nemushi da kansa a farfajiyan alqiyama" wanda ya yaqeshi din nan", har sai ALLAH ya kiffar da fuskan sa a wuta.))* _Ibn majah (421)Albany ya inganta shi_ An karbo daga Salim dan Abdullahi dan Umar  ALLAH ya qara masu yarda ya ce: Baba na ya bani labari, lallai yaji daga Manzon ALLAH ﷺ yana cewa *((Duk wanda yayi sallah asuba zai kasanci cikin makwabtakan ALLAH a wannan yinin"))* _Imamu Dabarani acikin Kabira(12990)Albany ya ingantashi acikin Sahihul TARGIB (459)._ _ALLAH kabamu ikon kiyaye wa._ _Domin karin bayani a duba cikin littafin_ 👇👇👇👇👇👇👇👇 *DARIQUL SALIHIN ILA RABBIL ALAMIN(page=41/43)*             _NA_ *SHEIKH WAHID BIN ABDULSALAM BALIY*        = = ✍🏾 _Yar uwarku dalibar ku_ *RUQAYYA AUWAL MUHAMMAD* ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ. Domin samun shafinmu na telegram 👇👇👇👇👇👇 https://t.me/Ilimantardaalumma

MATSALOLIN MU A FILI SUKE. (1.) Muna Aure ba tare da Soyyayya ba. (2.) Muna haihuwa ba tare da yin tarbiyya ba. (3.) Muna sallah ba tare da tsaron Allah ba. (4.) Muna koyan ilmi ba tare da aiki ba. 5.) Muna Magana ba tare da gaskiya ba. (6.) Muna ɗaukan alƙawari ba tare da cikawa ba. (7.) Muna karɓar amana ba tare da kulawa ba. (8.) Muna son kuɗi ba tare da Sana'a ba. (9.) Muna son Annabi (SAW) ba tare da bin koyarwar sa ba. (10.) Muna son Aljannah ba tare da aiki ba. (11.) Muna son a amsa mana addu'ah ba tare da cin halal ba. (12.) Gamu da bala'in son duniya da ƙin Mutuwa. Mafita kawai mu tuba mu gyara, muce Allah mun tuba, ka yafe mu. _ Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

*عقيدة الأطفال في توحيد المتعال*📚 *👨‍👧‍👧👩‍👧TAUHIDI AQIDAR YARA BISA KADAITA ALLAH MADAUKAKIN SARKI👨‍👨‍👧👨‍👧* *Wallafar Abu* Musal'ash'ari Isa Bin Umar Bin Abdullah *DAGA ZAURAN* *تربية الأولاد لشيخة رقية* *WHATS'APP* 08149629880 07045498743 *27/05/1441* *22/01/2020* *DARASI NA (3)*   *بسم الله الرحمن الرحيم* *س/هل يرى الله في الدنيا؟* *Tambaya*/ _Shin ana ganin Allah a duniya?_ *ج/الله لا يرى في الدنيا* . *Amsa* / _Ba'a ganin Allah a duniya_ . *س/هل المؤمنون يرون الله يوم القيامة ؟* *Tambaya*/ _Shin muminai zasu ga Allah ranar alqiyama ?_ *ج/نعم:المؤمنون يرون الله يوم القيامة.* *Amsa*/ _Eh:Muminai zasu ga Allah ranar alqiyama._ *س/من نبيك؟* *Tambaya _* /Wanene Annabinka?_  *ج/نبيي محمد صلى الله عليه وسلم* *Amsa*/ _Annabina shi ne  Annabi Muhammad sallallahu alaihi wa sallama._ *س/هل النبي صلى الله عليه وسلم نور؟* *Tambaya* / _Shin Annabi sallallahu alaihi wasallama haskine?_ *ج/لا هو بشر،ولكن يوحى إليه* *Amsa* / _A'a  shi mutum ne, sai dai ammasa wahayi._ *س/ هل هو حي أو ميت؟* *Tambaya* / _shin yana rayi ku ya bako/rasu ?_ *ج/ هو ميت ودينه باق إلى يوم القيامة.* *Amsa*/ _Ya rasu kuma addininsa yana nan yana wanzuwa har ranar alqiyama._ *=Fa'ida* Wannan karatu yana gaya mana cewa ba'a ganin Allah a nan gidan duniya, kuma muminai zasu ga Allah ranar alqiyama ido da ido, kamar yadda muke ganin wata anan duniya. Kuma Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama shi ba haski bane, shi mutum ne,sai dai shi ammasa wahayi kuma shi yana da karamumi da yawa, kuma ya rasu amma addinin sa yana nan har izuwa ranar alqiyama. ALLAH ka nuna mana gaskiya ka bamu ikon binta ka nuna mana karya ka bamu ikon kauce mata. zamu da kata anan sai a futuwa ta hudu da yardar ALLAH. ✍🏾 DALIBARKU *RUQAYYA AWWAL MUHAMMAD* ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ. Subhanakallahumma wabi hamdika nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka  wanatubu ilaika. Domin samun shafinmu na telegram 👇👇👇👇👇👇👇 https://t.me/Ilimantardaalumma

أَعُوذُ بِكَلِمَاتِ اللَّهِ التَّامَّاتِ، الَّتِي لَا يُجَاوِزُهُنَّ بَرٌّ وَلَا فَاجِرٌ، مِنْ شَرِّ مَا خَلَقَ وَذَرَأَ وَبَرَأَ، وَمِنْ شَرِّ مَا يَنْزِلُ مِنَ السَّمَاءِ، وَمِنْ شَرِّ مَا يَعْرُجُ فِيهَا، وَمِنْ شَرِّ مَا ذَرَأَ فِي الْأَرْضِ، وَمِنْ شَرِّ مَا يَخْرُجُ مِنْهَا، وَمِنْ فِتَنِ اللَّيْلِ وَالنَّهَارِ، وَمِنْ شَرِّ كُلِّ طَارِقٍ، إِلَّا طَارِقًا يَطْرُقُ بِخَيْرٍ، يَا رَحْمَٰنُ. Mu hadda ce kuma mu koyama yaranmu suna karantawa safe da yamma ƙafa ɗaya ɗaya 19/3/1448 1/9/2026

*📚KARATUN LITTAFIN 📚* *متن عمدة المرأء* _{مائة حديث منتقاة من أحاديث المرأة}_ *MADOGARAN MACE* _Hadisai dari"100" da suka ke banci  mata_ *تأليف* _Mawallafi_  *د. عادل حسن يوسف الحمد * Dr Adil bin Hassan Yusuf Hamdi. *🏘️DAGA ZAURAN 🏘️* *تربية الأولاد لشيخة رقية* 🟢🟢♣️🟠🟠♣️🟢🟢♣️🟠🟠    🪀🪀🪀  🪀🪀 🪀 *07045498743* *08149629880* *21/11/1442* *28/06/2021* *DARASI NA (21)*           *(HADISI= 21/100)* ۝≽➖➖➖❃﷽❃➖➖➖≼۝ ٢١=- {أنت عورة فاستري نفسك لا يتلاعب بك الشيطان} ٢١=- عن عبدالله بن مسعود رضي الله عنه ،عن النبي ﷺ قال :(( المرأة عورة فإذا خرجت استشرفها الشيطان)) أخرجه الترمذي 21=- {KI AL'AURACI MAI DARAJA DA AKE SUTURTA KI,KI RUFE/SUTURTA KANKI, KADA KIBAR SHAIDAN YAYI WASA DA HANKALINKI} 21=- An karbo daga Abdullahi dan mas'ud Allah ya qara masa yarda, daga Manzon Allah ﷺ yace: ((Ita mace al'aurace a duk lokacin da ta sa kafa zata fita daga gidanta, shaidan yana qawata ta/ darajjata ta.)) Imamu Turmizi FA'IDA=- 1⃣  Shaidan yana farin ciki yaga mace ta fita zuwa ga gamagarin mutane ta yadda yake qara qawata ta. 2⃣Fitan mace lokacin da ta yi ado tana baiyyana jikinta,wannan shaidan abin yana qayatar dashi. 3⃣Fitan mace ba laifi bani indai ta kiyaye dukokin da shari'a muslinci ta samata wajan rufe jikin ta. Anan muka kawu karshen karatun mu na yau sai a fitowa ta ashirin da biyu da yardar Allah mai kuwa mai Komai. _Abin da na fada na rubuta daidai ALLAH ya taramu a ladan wanda nayi tuntuban rubutu Allah ya gafartamin da ni da ku bakiya daya. DALIBARKU 📝 *_RUQAYYA  AUWAL MUHAMMAD_* *ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.* Domin samun shafinmu na telegram 👇👇👇👇 https://t.me/Ilimantardaalumma

*🌸 KI TSARE MUTUNCINKI – 002 🌸* *Kada ki nemi ƙima daga wanda bai san kimarki ba. 💔* *Ya ke 'yar'uwa!*  Kar ki rage darajarki don neman ƙaunar wanda bai san kimarki ba. Idan mutum baya ganin ƙimar ki, ki tuna Allah yana ganin ta. *Mutuncinki daraja ce – kar ki sayar da ita akan farashin kulawa mara kyau.* *Allah (SWT) yana cewa..* ﴿وَلَقَدْ كَرَّمْنَا بَنِي آدَمَ﴾ *_"Lalle Mun girmama ɗan Adam."_* – [Al-Isra: 70] *Ya ke 'yar'uwa!*  Wani zai iya wulakanta ki, ya raina ki, ko ya ki ganin ƙimarki. Amma Allah ya riga ya ɗaukaka ki. Kada ki bari mutumin da bai san Allah ba ya wulaƙanta ki. *Sheikh Ibn Qayyim (RH) ya ce:*  > *Wanda ya gane ƙimarsa, ba zai taba yarda ya rage matsayin kansa don halayyar wani ba.* - Idan ba'a girmama ki – ki bar wajen.  - Idan ba'a ƙaunace ki bisa gaskiya – ki kau.  - Ki nemi Allah, ba mutane ba.  - Allah zai kawo wanda zai san kimarki cikin tsarkin zuciya. *Ya Allah!* Ka tabbatar mana da mutuncinmu, Ka hana mu neman ƙauna a wuraren da ba zaka yarda da su ba. Ka kawo mana wanda zai ƙaunace mu saboda Allah. *الله تعالى أعلم*

*عقيدة الأطفال في توحيد المتعال*📚 *👨‍👧‍👧👩‍👧TAUHIDI AQIDAR YARA BISA KADAITA ALLAH MADAUKAKIN SARKI👨‍👨‍👧👨‍👧* *Wallafar Abu=-* Musal'ash'ari Isa Bin Umar Bin Abdullah *DAGA ZAURAN* *تربية الأولاد لشيخة رقية* *Whasapp* 08149629880 07045498743 *26/05/1441* *21/01/2020* *DARASI NA (2)* *بسم الله الرحمن الرحيم* *س* / *من خلقك؟* *Tambaya* =-  _Wanene yahalicce ka?_ *ج* / *الله هو الذي خلقني, وخلق كل شيء.* *Amsa* _=- Allah shi ne wanda ya halicce ne, ya halicce dukkan komai._ *س* / *لماذا خلقك الله ؟* *Tambaya* _=-saboda me Allah ya halicce ka?_ *ج* / *خلقني لعبادته* . *Amsa* _=-ya halicceni ne damin  na bauta masa._ *س* / *كيف تعبد الله ؟* *Tambaya* =- _Tayaya kake bautawa Allah?_ *ج* / *أعبده كماأمر  الله ،وكما أمر رسوله.* *Amsa* =- _Ina bauta ma Allah kamar yadda ya ummarcemu,kuma kamar yadda Manzon Allah(SAW)  ya ummarcemu._ *س* */ما معنى لا إله إلا الله ؟* *Tambaya* =- _Menene ma'anar La'ilaha illallahu?_ *ج* */معناها لا معبود بحق إلا الله .* *Amsa* =- _Ma'anar ta Babu abin bautawa da cancanta da gaskiya sai Allah._ *س* / *إينا الله ؟* *Tambaya* =- _A ina Allah yake?_ *ج* / *الله في السماء مستويا على العرش.* *Amsa* =- _Allah yana sama ya dai dai ta akan al'arshi_ = *Fa'ida:*     Wannan karatu da mukayi yana da kyau iyaye su sanar da ya'yan su wannan tambayoyi tare da amsa, ta yadda tun suna qanana zasu san Allah daya ne ba shi kuma da abokin tarayya, kuma su san a inda Allah yake, su san ma'anar kalmar shahada. = = _Zamu dakata anan sai a darasi na gaba in sha Allah_ ✍🏾Yar Uwarku a musulunci *RUQAYYA AWWAL MUHAMMAD* ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ. Subhanakallahumma wabi hamdika nash hadu anla ila ha illah anta nastagfiruka  wanatubu ilaika. Domin samun shafinmu na telegram 👇👇👇👇👇👇👇 https://t.me/Ilimantardaalumma

MADOGARAR MACE 09.mp36.23 MB

*Karatun Littafin:* *متن عمدةالمرأة* *(Madogarar Mace)* *Wallafar: Dr. Adil Hassan Yusuf Alhamd* *Darasi na 9* Tare da: Mal. Ismail Saidu Bulama AYI SAURARO LAFIYA 📢📢📢📢📢📢📢

003.*SIFFOFIN MASU JIN TSORAN ALLAH*        *BASA  CIN HARAMUN* *_masu jin tsoron Allah_* _sune wadanda basa cin haramun domin – cin haramun da tara haramun yana jawo fushin Allah Madaukakin Sarki akan bawa, saboda  Allah mai tsarki ne, ba ya karbar aiki kuwa sai mai tsarki, don haka duk wanda ya tara haramun, ya zama shi ne cin sa da shan sa, to ya sani babu shi ba Allah, yayi nisa da Allah Madaukakin Sarki._ *_musu jin tsoran Allah_* _Basa cin haramun domin dukiyar haram tana hana karbar addu’a ta sa Allah Ya rufe wa mutum kofofin sama._ Manzon Allah ﷺ ya ambaci wani mutum wanda yake cin haramun yana addu'a yana cewa *Ya Ubangiji! Ya Ubangiji!! (Alhali) abincinsa haramun ne, abin shansa haramun ne, kuma tufafinsa haramun ne, kuma an ciyar da shi da haramu, to ta yaya za a amsa masa.”?* *_masu jin tsoran Allah_* _Basa cin haramun domin  manzon Allah ﷺ yace: *Ina rantsuwa da Wanda raina ke hannunsa, haqiqa da wani zai sanya loma daya ta haram a cikinsa, Allah ba zai karba masa addu’o’insa ba na tsawon kwana arba’in. Kuma duk mutumin da namansa ya ginu da haram ko riba, to wuta ce ta fi cancanta da shi.”*_ *_masu jin tsoran Allah_* _Basa cin haramun domin manzon Allah ﷺ  yace: *“Wanda ya san ya zalunci wani ya yi kokarin mayar masa kafin a karba masa daga kyawawan ayyukansa, idan kuma ba ya da kyawawan ayyuka sai a kwaso miyagun ayyukan wancan a jibga masa a jefa shi a wuta.*” Buhari ya ruwaito._ *_Yaku bayin Allah_* _Jabir bin Abdullahi (RA)_ yana cewa “Lallai Manzon Allah ﷺ yace: *“Duk tsokar da ta ginu da haram ba za ta shiga Aljanna ba.”* *_Yaku bayin Allah_* Dukiyar haram hanya ce abar kyama mai cike da hadari da ke jefa ma’abucinta a cikin wuta! _Ku ji tsoron Allah, Ya  ku bayin Allah! Ku mayar da amanoni ga masu su, ku tuba zuwa ga Allah kowa yayi duba zuwa ga abinda ya gabatar a rayuwarsa kafin ya kowa zuwa ga Allah._ Ina roqon Allah dacewa da shiriya zuwa kowane alheri, ga kaina da ku, lallai shi Allah  mai iko ne a bisa kowane abu. Allah ya albarkace ni tare da ku da abin da muka ji na Alqur’ani ya gafarta mana zunubbanmu, lalle shi mai yawan gafara ne mai jin qai *الله تعالى أعلم*

*📚KARATUN LITTAFIN 📚* *متن عمدة المرأء* _{مائة حديث منتقاة من أحاديث المرأة}_ *MADOGARAN MACE* _Hadisai dari"100" da suka kebanci  mata_ *تأليف* _Mawallafi_  *د. عادل حسن يوسف الحمد * Dr Adil bin Hassan Yusuf Hamdi. *🏘️DAGA ZAURAN 🏘️* *تربية الأولاد لشيخة رقية* 🟢🟢♣️🟠🟠♣️🟢🟢♣️🟠🟠    🪀🪀🪀  🪀🪀 🪀 *07045498743* *08149629880* *20/11/1442* *27/06/2021* *DARASI NA (20)*           *(HADISI= 20/100)* ۝≽➖➖➖❃﷽❃➖➖➖≼۝ ٢٠=- {مشيك وسط الطريق العام دليل على ضعف الستر في نفسك} ٢٠=- عن أبي أسيد الأنصاري رضي الله عنه أنه سمع رسول الله ﷺ يقول وهو خارج من المسجد فاختلط الرجل مع النساء في الطرق فقال رسول الله ﷺ للنساء : ((استأخره فإنه ليس لكن أن تحققن الطريق،عليكن بحافات الطرق)). فكنت المرأة تلتصق بالجدار حتى إن ثوبها ليتعلق بالجدار من لصوقها به. أخرجه أبو داود 20=- {TAFIYAR DA KIKE YA KE YAR'UWA MUSULMA A TSAKIYAR HANYA DA MUTANE SUKE HUCEWA ,WANNAN HUJJA NE/YANA NUNI AKWAI RAUNIN SHAMAKI  A ZUCIYAR KI} 20=- An karbo daga Abi Usaidul al'ansari Allah ya qara masa yarda, na ji Manzon ALLAH ﷺ Yana cewa. Lokacin da ya fito daga masallaci sai yaga  maza suna cakuduwa da mata a hanya, sai Manzon ALLAH ﷺ yace da mata : ((Kuja da baya ku mata,domin bakune kuka cancanci bin "tsakiyar" hanya ba, ina huranku da bin gefan hanya))Mata sun kasance suna mannuwa da garu, har sai kayansu yana leqewa da bango,saboda tsananin leqewansu abango. Imamu Abu Dawud FA'IDA=- 1⃣Wannan hadisin yana tsare rayuwar society,ta yadda yake gaya mana mata su na bin gefan hanya shi yafi dacewa da su. 2⃣Tsare qa'ida na tafiya a hanya, ta yadda maza subi tsakiyar hanya, amma ita mace tabi gefan hanya nan ne yafi. 3⃣Manzon ALLAH ﷺ ya hana cakuduwar maza da mata. 4⃣Nuna biyyaya da mata sahabbai sukai wa Manzon ALLAH ﷺ. Anan muka kawu karshen karatun mu na yau sai a fitowa ta ashirin da daya da yardar Allah mai kuwa mai Komai. _Abin da na fada na rubuta daidai ALLAH ya taramu a ladan wanda nayi tuntuban rubutu Allah ya gafartamin da ni da ku bakiya daya. DALIBARKU 📝 *_RUQAYYA  AUWAL MUHAMMAD_* *ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.* Domin samun shafinmu na telegram 👇👇👇👇 https://t.me/Ilimantardaalumma

🍃Yin karatun Alqur'ani akai-akai yana ƙarfafa masu karatu ba tare da sun sani ba, yana ƙara musu imani, yana kawo kwanciyar hankali ga zukatansu, yana sa su gamsu da rayuwarsu da abincinsu da Allah Ya ba su, yana ƙara musu iya magana cikin mutane, yana cire kalmomin da ba su dace ba daga maganganunsu, kuma yana sa su bar tarurruka marasa amfani da sauran ayyukan da suka saba yi, domin zuciyarsu ta haskaka da haske, kuma harshen su ya jiƙu da magana mai dadi da girma. 🍃Allah Ka Sa Mu Cikin Ma'abota Wannan Littafin. Amin