Dr. Muhammad sani umar rijiyar lemu
Open in Telegram
2 355
Subscribers
No data24 hours
-17 days
-1130 days
Posts Archive
*[Tafsirin Surah Âl-
Imrân:]*
Darasi Na 84
[Surah Âl-Imrân: 118]
{ یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تَتَّخِذُوا۟ بِطَانَةࣰ مِّن دُونِكُمۡ لَا یَأۡلُونَكُمۡ خَبَالࣰا وَدُّوا۟ مَا عَنِتُّمۡ قَدۡ بَدَتِ ٱلۡبَغۡضَاۤءُ مِنۡ أَفۡوَ ٰهِهِمۡ وَمَا تُخۡفِی صُدُورُهُمۡ أَكۡبَرُۚ قَدۡ بَیَّنَّا لَكُمُ ٱلۡـَٔایَـٰتِۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ }
[Surah Āli-ʿImrān: 118]
*Prof. Muhammad Sani Umar R/Lemo OON (Hafizahullah)*
25-11-1446
23-05-2025
1. Makomar ayyukan kafiri wanda ya yi ikhlasi a cikinsu bayan ya musulunta.
2. Yarjejeniyar da Annabi (SAW) ya kulla da kabilun Yahudawa da yadda suka warware yarjeniyoyin.
3. Dalili da hikimar da ta sa Allah yake kiran muminai da sunan imani.
4. Ma'anar kalmar "Biɗana".
5. Ma'anar kalmar "Khabal".
6. Halin da al'ummar suka shiga sakamakon yin biris da irin wannan umarnin na Allah.
7. Me ya sa aka ce, "In kun kasance masu hankalta". Ba a ce, "In kun kasance masu ilimi", ba?
👇👇👇*[Tafsirin Surah Âl-
Imrân:]*
*Darasi Na 83*
[Surah Âl-Imrân: 117]
{ مَثَلُ مَا یُنفِقُونَ فِی هَـٰذِهِ ٱلۡحَیَوٰةِ ٱلدُّنۡیَا كَمَثَلِ رِیحࣲ فِیهَا صِرٌّ أَصَابَتۡ حَرۡثَ قَوۡمࣲ ظَلَمُوۤا۟ أَنفُسَهُمۡ فَأَهۡلَكَتۡهُۚ وَمَا ظَلَمَهُمُ ٱللَّهُ وَلَـٰكِنۡ أَنفُسَهُمۡ یَظۡلِمُونَ }
*Prof. Muhammad Sani Umar R/Lemo OON (Hafizahullah)*
18-11-1446
16-05-2025
1. Iskar da ake kira da "As-sirru.
2. Dalilin da ya sa musibu suke samun al'umma.
3. Shin kafirai za su ci gajiyar ayyukan jin kan da suka yi a lahira?
4. Nau'ukan ayyukan kafiri, wadanda yake iya cin gajiyarsu da wadanda ba zai ci gajiyarsu ba.
5. Nau'ukan arziki da Allah Ta'ala yake ba wa bayinsa.
6. Cikar adalcin Allah Ta'ala.
7. Yadda ake saka wa kafirin da Musulmi ya ci hakkinsa.
8. Yadda za a sakawa Musulmi a lahira idan kafiri ya zalunce shi.
👇👇👇Khudubar Juma’a mai taken: Hukunche Hukunchen Aikin Hajji
Prof Muhammad Sani Umar R Lemo OON
Daga Masallacin Juma’a na Dorayi Karama Kano
11/11/1446 09/05/2025
👇👇👇
*[Tafsirin Surah Âl-
Imrân:]*
*Darasi Na 82*
[Surah Âl-Imrân: 113]
{ ۞ لَیۡسُوا۟ سَوَاۤءࣰۗ مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَـٰبِ أُمَّةࣱ قَاۤىِٕمَةࣱ یَتۡلُونَ ءَایَـٰتِ ٱللَّهِ ءَانَاۤءَ ٱلَّیۡلِ وَهُمۡ یَسۡجُدُونَ }
*Prof. Muhammad Sani Umar R/Lemo OON (Hafizahullah)*
11-11-1446
09-05-2025
1. Matsayin mataki salaha.
2. Wasu daga cikin kyawawan halayen Ahlulkitabi.
3. Me ake nufi da karanta Alkur'ani hakikanin karanta shi?
4. Wajahin lafazin "wa ma yaf'alu" da na "wa ma taf'alu" da ya zo a kira'ar jumhur.
5. Muhimmancin yin takawa a ayyuka.
6. Me ya sa Allah ya kebance iliminsa da masu takawa tare da cewa, iliminsa ya kewaye dukkan komai?
7. Dalilin kebance dukiya da 'ya'ya da ambato daga cikin abin da ba zai amfani kafiri ba.
8. A lahira kowa ta-kansa yake!
👇👇👇MUHADARA 1446/2025
MAHADAR MAI TAKEN DUKIYA TA HALAL A HANNU NAGARI
Wuri:- _Agege A Jahar Legos._
Tare: Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo OON.
👇👇👇
23 RAMADAN TAFSIR 1446/2025.
[Surah An-Nūr: 3]
{ ٱلزَّانِی لَا یَنكِحُ إِلَّا زَانِیَةً أَوۡ مُشۡرِكَةࣰ وَٱلزَّانِیَةُ لَا یَنكِحُهَاۤ إِلَّا زَانٍ أَوۡ مُشۡرِكࣱۚ وَحُرِّمَ ذَ ٰلِكَ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِینَ }
Daga: Masallacin Jumma'a Na Gwallaga Bauchi State.
Tare: Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo OON.
Da Alaramma
Abubakar Rariya
23/9/1446.
23/03/2025
👇👇👇👇
Ramadaniyyat: 1446 [22]
Alƙur'ani Zalla ko Bijire wa Manzon Allah
4.0. Taƙaitaccen Tarihin Masu Ƙaryata Hadisai
Ci gaba…
4.6. Fitinar Ƙaryata Hadisai a ƙasashen Larabawa:
Duk waɗand suka nazari na ilimi a kan wannan fitina ta ƙaryata hadisan Annabi (SAW) a ƙasashen larabawa sun tabbatar da cewa, yawancin waɗanda suka yi ƙaurin suna a cikin waɗannan lamari ba malaman addini ne ba, domin a cikinsu daga wanda ya karanci ilimin likitanci sai wanda ya karanci Adabin Larabci sai kuma mai ɗauke da shaidar lauya, wani kuma ɗanjarida ne, amma masu karatun ilimin addini a cikinsu kaɗan ne ƙwarai.
Ga wasu kaɗan daga cikinsu:
1. Muhammad Taufiƙ Sidƙi (Likita):
Wannan mutum ɗan ƙasar Masar ne kuma likita ne, amma ƙarfi da yaji ya cusa kansa cikin al'amuran ilimin addini, har ta kai wani lokaci ya rubuta wasu maƙaloli biyu a wata shahararriyar Mujalla mai sun "al-Manar" wadda Sheikh Muhammad Rashi Ridha yake bugawa.
A cikin waɗannan maƙaloli biyu waɗanda ya yi musu matashiya kamar haka: (Musulunci shi ne Alƙur'ani Kaɗai), ya yi da'awar cewa:
• Da Alƙur'ani ne kaɗai Musulmi za su dogara wajen tabbatar da hukunce-hukuncen shari'a ban da hadisan Manzon Allah (SAW).
• Ya kuma yi iƙrari da cewa, sunna ba ta samu kulawa yadda ya kamata ba, domin Annabi (SAW) bai so a isar da wani soƙo daga gare shi ba sai Alƙur'ani ba kawai.
• Sannan ya ƙara da cewa, Alƙur'ani ne kawai ake da tabbas a kansa, amma hadisai ba a da tabbas a kansu.
• Kuma ya bayyana cewa, wai an shigar da ƙarerayi masu yawa a cikin hadisan Annabi (SAW), don haka bai kamata a gina addini a kan abin da ba a tantance ƙarya da gaskiya a cikinsa ba.
• Sannan ya ƙara da cewa, aiki da hadisi ya taƙaita ne kawai a kan sahabbai wanda suka yi zamani da Manzon Allah (SAW), amma shi Alƙur'ani ya shafi kowa da kowa.
• Ya sake yin wata banzar hujja ta cewa, shi hadisi ai zato ne ba yaƙini ba, Allah kuwa bai yarda da zato ba.
• Ya kai ga cewa, littattafan hadisai suna kama da littattafan Ahlulkitabi waɗanda aka riƙa ruwaito su daga ƙwaƙwalwa ba daga wani rubutaccen abu ba, saboda haka yana ganin yin haka ya ba da wata babbar dama da kurakurai suka riƙa shiga cikinsu. Sannan kuma ya fake da cewa, wasu masu ruwaito hadisan ba mutanen kirki ba ne, amma suka riƙa wayancewa har aka riƙa ɗaukan su a mutanen kirki, suka ruɗi mutane har suka amince da ƙarerayinsu a matsayin hadisan Annabi, don haka Sidƙi yake ɗaukar littattafan hadisai kamar littattafan Ahlulkitabi ne.
To da ire-iren waɗannan shubuhohi ne ya dogara wajen ƙaryat a duk hadisan Annabi (SAW).
Amma kuma malamai da dama sun rubuta masa martani a kan waɗannan shubuhohi nasa, wanda ya sa shi daga ƙarshe ya janye wasu daga cikin miyagun ra'ayoyinsa a kan sunna, amma kuma ya kafe a kan wasu ra'ayoyin nasa munana, bai sauka daga kansu ba har zuwa rasuwarsa a shekara ta 1920.
Za mu ci gaba in sha Allah….
22 RAMADAN TAFSIR 1446/2025.
[Surah An-Nūr: 2]
{ ٱلزَّانِیَةُ وَٱلزَّانِی فَٱجۡلِدُوا۟ كُلَّ وَ ٰحِدࣲ مِّنۡهُمَا مِا۟ئَةَ جَلۡدَةࣲۖ وَلَا تَأۡخُذۡكُم بِهِمَا رَأۡفَةࣱ فِی دِینِ ٱللَّهِ إِن كُنتُمۡ تُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡیَوۡمِ ٱلۡـَٔاخِرِۖ وَلۡیَشۡهَدۡ عَذَابَهُمَا طَاۤىِٕفَةࣱ مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِینَ }
Daga: Masallacin Jumma'a Na Gwallaga Bauchi State.
Tare: Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo OON.
Da Alaramma
Abubakar Rariya
22/9/1446.
22/03/2025
👇👇👇
Ramadaniyyat: 1446 [21]
Alƙur'ani Zalla ko Bijire wa Manzon Allah
4.0. Taƙaitaccen Tarihin Masu Ƙaryata Hadisai
4.5. Wasu Daga Cikin Jagororin Wannan Fitina: (6)
Ci gaba…
Ghulam Ahmed Perwez yana da ilimi mai zurfi a kan aƙidun turawa, don haka yake ganin ya kamata a sanya wa waɗannan aƙidu rigar Musulunci. Sannan yana ganin duk abin da ya zo a cikin ilimin boko, to lalle wannan abu gaskiya ne babu tababa a kansa, soboda haka dole ne fassarar Alƙur'ani ta dace da shi. Ya yi matuƙar ƙwarewa wajen karkata ayoyin Alƙur'ani domin su tafi daidai da ra'ayinsa.
Perwez ya fara bayyana ra'ayoyinsa na ƙaryata hadisan Manzon Allah (SAW) tun lokacin da gwamnatin ta naɗa shi limanci a masallacin Sakatariyar Delhe. Ya fara da yi wa hadisan Manzon Allah (SAW) mummunan tawili, sannan daga bisani ya shiga ƙaryata su.
Wannan mummunar ƙadiar tasa ce ta sa wata rana wani ma'aikacin shara da ke wannan Sakatariya ya kasa haƙuri, ya miƙe tsaye ya ciwo kwalar rigar Perwez yana tsaka da huɗuba ya dakatar da shi. Wannan shi ne musabbabin barin sa limanci a wannan masallaci.
Kada mai karatu ya manta cewa Perwez ya jima da haɗuwa da malaminsa Alhafiz Aslam Jirajburi, ya kuma kwankwaɗi ra'ayoyin ƙaryata sunnar Annabi (SAW) a wurinsa, to amma saboda yanayin garin Delhe na yawan malamai, ga kuma rakita-rikitar siyasa da Musulmi suke fama da ita, duka wannan ya hana masa samun sukunin yaɗa aƙidarsa a cikin Musulmi, sai bayan da Musulmi suka samu ƙasarsu ta kansu watau Pakistan, sannan Perwez ya yi hijira zuwa Karachi, a nan ne ya kafa cibiyarsa ta wucin gadi, domin yaɗa mummunar aƙidarsa.
Ghulam Ahmed Perwez ya kasance yana girmama magabatansa masu aƙidar ƙaryata hadisan Annabi (SAW), kamar Sir Ahmad Khan da Abudullahi al-Jakralawi, yana kuma yaba wa aƙidunsu da manufofinsu, duk kuwa da cewa, ya saɓa musu kaɗan a wasu ɓangarori, amma dai yana tare da su a cikin manyan-manyan rukunan aƙidar ƙaryata hadisai da taƙaita a kan Alƙur'ani bisa fahimtarsu su kaɗai.
Perwez ya yi rubuce-ruɓucen littattafai fiye da talatin, domin kana iya cewa cikin malaman 'Alƙur'ani zalla' babu wani wanda ya yi rubuce-rubuce kamarsa.
Birnin Lahore tun a shekarar 1959 ya zama cibiyar addini ga 'yan ƙungiyar ' Ɗulu'ul ƙur'ani'. Abul-A'la al-Maudidi shi ma ya mayar da wannan gari cibiyar ƙungiyarsa ta al-Jama'atul Islamiyya. Ya kuma tunkari ƙungiyar Perwez da kakkausan suka tare da gargaɗin Musulmi a kan su gujewa aukawa cikin komarsu.
A shekara 1961 manyan shugabannin makaratun Arabiyya da na Islamiya na Karachi suka ƙaddamar da neman fatawa a gurin malamai game 'yan ƙungiyar Perwez, suna tambayar cewa, shin duk mai ɗauke da ra'ayoyin Perwez zai yiwu a ci gaba da ɗaukar sa a matsayin Musulmi? Ko kuwa dai ya yi ban kwana da Musulunci?
Sama da malamai dubu daga ƙasashen Pakistan da Indiya da Sham da Makka da Madina suka ba da fatawa cewa, wannan mutum ya kafirta ya bar Musulunci. Sai dai wannan bai kawo ƙarshen da'awar Perwez a ƙasar Pakistan ba, ya ci gaba da yaɗa gubarsa har zuwa lokacin mutuwarsa.
Ghulam Ahmad Perwez ya rasu a ranar 24 Fabrairu, 1985 yana da kimanin shekaru 81 a duniya.
21 RAMADAN TAFSIR 1446/2025.
[Surah An-Nūr: 2]
{ ٱلزَّانِیَةُ وَٱلزَّانِی فَٱجۡلِدُوا۟ كُلَّ وَ ٰحِدࣲ مِّنۡهُمَا مِا۟ئَةَ جَلۡدَةࣲۖ وَلَا تَأۡخُذۡكُم بِهِمَا رَأۡفَةࣱ فِی دِینِ ٱللَّهِ إِن كُنتُمۡ تُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡیَوۡمِ ٱلۡـَٔاخِرِۖ وَلۡیَشۡهَدۡ عَذَابَهُمَا طَاۤىِٕفَةࣱ مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِینَ }
Daga: Masallacin Jumma'a Na Gwallaga Bauchi State.
Tare: Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo OON.
Da Alaramma
Abubakar Rariya
21/9/1446.
21/03/2025
👇👇👇
Ramadaniyyat: 1446 [20]
Alƙur'ani Zalla ko Bijire wa Manzon Allah
4.0. Taƙaitaccen Tarihin Masu Ƙaryata Hadisai
4.5. Wasu Daga Cikin Jagororin Wannan Fitina: (5)
Ci gaba…
5. Gulam Ahmad Bawiz: An haife shi a garin Batala da ke yankin Punjab na ƙasar Indiya a shekarar 1903.
Ya taso a gidan ilimi, ya kuma fara karatunsa a hannun kakansa. Kakansa babban malami ne mai yawan ilimin addinin Musulunci, kuma mai bin ɗariƙar al-Jistiyya al-Nizamiyya. Don haka ya cika ƙwaƙwalwar jikansa da asraru irin na sufaye, amma daga baya sai Barwiz ya yi musu tawaye, ya zama mai nuna ƙiyayya a gare su.
Barwiz bai wuce makarantar sakandare a karatunsa ba. Yana gama Sakadandare sai ya tsunduma cikin aikin gwamnati, inda ya fara aiki da wata ma'aikatar gwamnati ta buge-bugen littattafai, har ya kai matakin babban manaja a wannan ma'aikata.
A shekara ta 1938 Barwiz da wani abokinsa suka yi haɗin gwiwa suka kafa wata mujalla mai suna " Ɗulu'ul Islam" wadda ta ɗauki shekaru ta ɗauki shekaru tana yaɗa wa Musulumi ilimomin addinin Musulunci, wanda haka ne ya jawo mata farin jini mai yawa a tsakanin Musulmi, musamman lokacin da ta zama mujalla mai rajin kare haƙƙoƙin Musulmi da fafutukar ganin Musulmi sun kafa ƙasarsu mai cin gashin kanta ƙarƙashin jagorancin ɗangwagwarmaya Muhammad Ali Janah.
Bayan Musulmi sun sami 'yancin kafa ƙasar Pakistan, sai Barwiz ya yi hijira daga Indiya ya koma can da zama, ya kuma ci gaba da buga mujallarsa 'Ɗulu'ul Islam'.
Bayan Barwiz ya samu wurin zama a Karachi babban birnin ƙasar Pakistan, sai ya shiga harkokin yaɗa da'awarsa gadan-gadan ba ji ba gani, domin yanzu inda yake da zama ba ya da wasu abokan hamayya, sannan kuma ga taimakon gwamnati da yake samu akai-akai, don haka sai ya samu cikakkiyar dama ta ɗora da'awarsa a kan harsashi mai ƙarfi, ya kuma kafa dandali-dandali da sunan "Dandalin Ɗulu'ul Islam", ya kuma buɗe ofisoshi a ko'ina a faɗin ƙasar Pakistan. Cikin 'yan shekaru kaɗan sai labarinsa ya bazu ko'ina a faɗin ƙasar Pakistan har ma da ƙasashen ƙetare, watau ƙasashen Larabawa da Turai da ƙasashen Amruka. Mutane suka riƙa tururuwa suna shiga ƙungiyarsa.
Ta ɓangare guda kuma kafafen watsa larabi na hukuma suka riƙa koɗa shi, suna ta yabon sa, wannan ya jawo da dama daga cikin 'yan boko da lauyoyi da alƙalai da malaman jami'o'i da injiniyoyi da ɗalibai suka riƙa rungumar da'awarsa ido rufe.
Tun daga shekarar 1956 ya fara shirya wa mabiyansa tarurruka, don tattauna al'amuran da suka shafi da'awarsa da nemo hayoyin yaɗa ra'ayoyinsa ko'ina a duniya.
A dai wannan shekarar ne aka samu juyin mulki a ƙasar Pakistan, ƙarƙashin jagoranci Janaral Ayyub Khan wanda ya rusa duk wasu jam'iyyun siyasa da ƙungoyin addini na ƙasar Pakistan, amma abin bai shafi ƙungiyar "Ɗulu'ul Islam" ba, saboda manufofinta suna tafiya daidai da kowace irin gwamnati da za a samu, saboda sun ba wa kansu cikakken ikon su hallata ko su haramta abin da suka dama. Wannan kuma shi ne abin da duk wani mai mulkin kama karya yake da buƙata. A sanadiyyar haka ne ma aka soke dokokin Masulunci masu alaƙa da hukunce-hukuncen aure da iyali.
Za mu ci gaba in sha Allah…
