en
Feedback
BINTUS-SUNNAH

BINTUS-SUNNAH

Open in Telegram

Domin Faɗakarwa da Tunatarwa Zuwa Ga Al'ummah Ta Fannoni Daban-Daban. TELEGRAM: https://t.me/BINTUSSUNNAH FACEBOOK: http://www.Facebook.com//Bintusunnah/ YouTube: https://youtube.com/channe WHATSAPP: http://api.whatsapp.com/send?phone=+2349030947171

Show more
3 719
Subscribers
-424 hours
-97 days
-6730 days
Posts Archive
TASKAR HIKIMA //37 ❝Duk da cewa rana tana fitowa kullum, Amma ba kowa yake ganin alfarmarta ba.❞ ✍️ Yunus Abdullahi.
TASKAR HIKIMA //37 ❝Duk da cewa rana tana fitowa kullum, Amma ba kowa yake ganin alfarmarta ba.❞ ✍️ Yunus Abdullahi.

#DailyHadith
#DailyHadith

25/RABI'UL AWWAL/1448 07/SEPTEMBER/2026 ADDU’AR YAU LITININ: Ya ALLAH ka jiƙan Mamatanmu ka haskaka makwancinsu, ka bawa mara
25/RABI'UL AWWAL/1448 07/SEPTEMBER/2026 ADDU’AR YAU LITININ: Ya ALLAH ka jiƙan Mamatanmu ka haskaka makwancinsu, ka bawa maras lafiyar cikinmu lafiya Ingantacciya. HADISIN YAU LITININ: Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce:  “Idan ku kaje wajen maras lafiya ko gawa toh ku faɗi alheri, domin mala'iku suna aminta da abin da kuke faɗi ne.” [Muslim Ya ruwaito shi] Telegram https://t.me/BINTUSSUNNAH Facebook http://www.Facebook.com//Bintusunnah/ YouTube https://youtube.com/channel/UCG_W7_7gQdibxDgvhQdIEyQ

sticker.webp0.52 KB

sticker.webp0.29 KB

Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Ku isar da saƙona koda da aya ɗaya ne.” [Bukhari]
Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Ku isar da saƙona koda da aya ɗaya ne.” [Bukhari]

Sheikh Muhammad Basheer Al-Ibrahimiy (Rahimahullah) yana cewa dalibansa: “Kada karancin rabonku cikin ilmi ya dame ku matuƙar
Sheikh Muhammad Basheer Al-Ibrahimiy (Rahimahullah) yana cewa dalibansa: “Kada karancin rabonku cikin ilmi ya dame ku matuƙar kun samu rabo mai yawa na kyawawan halaye. Domin Al'ummarku tafi tsananin buƙatar kyawawan halaye sama da yadda take buƙatar ilmi, saboda wannan ƙasƙanci da wannan Al'umma take cikinsa a yanzu ta same shi ne saboda ƙarancin kyawawan halaye ba wai dan ƙarancin ilmi ba” [عيون البصائر ٢٩٦]

Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “Mafi alkhairin zukata sune tatattu masu taushi, domin ta hakane mutum zai kalli gaskiya a
Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “Mafi alkhairin zukata sune tatattu masu taushi, domin ta hakane mutum zai kalli gaskiya a yadda take, ya karɓeta cikin tausasawa, ya kiyayeta domin kar ta gurɓace.” [Badda'iuttafseer: 316]

Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “Ayoyin Alƙur'ani suna raya zukata kamar yadda ƙasa take samun rayuwa da zubar ruwa.” Mift
Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “Ayoyin Alƙur'ani suna raya zukata kamar yadda ƙasa take samun rayuwa da zubar ruwa.” Miftahu Daar Assa'adah]

Ibnu Rajab (Rahimahullah) Ya ce : “Tattaki zuwa masallaci wani nau'i ne jihadi domin yana daga tafarkin ALLAH, kuma kaffara n
Ibnu Rajab (Rahimahullah) Ya ce : “Tattaki zuwa masallaci wani nau'i ne jihadi domin yana daga tafarkin ALLAH, kuma kaffara ne na zunubai.” [Majmu'urrasaa'il: 4/35]

24/RABI'UL AWWAL/1448 06/SEPTEMBER/2026 ADDU’AR YAU LAHADI: Ya ALLAH ka sanya mu masu gode maka kuma masu godewa mutane. HADI
24/RABI'UL AWWAL/1448 06/SEPTEMBER/2026 ADDU’AR YAU LAHADI: Ya ALLAH ka sanya mu masu gode maka kuma masu godewa mutane. HADISIN YAU LAHADI: An Karɓo daga Abu-Hurayrah (RA) Yace Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Ba ya godema ALLAH wanda ba ya godema mutane.” [Ahmad ya ruwaito shi] Telegram https://t.me/BINTUSSUNNAH Facebook http://www.Facebook.com//Bintusunnah/ YouTube https://youtube.com/channel/UCG_W7_7gQdibxDgvhQdIEyQ

sticker.webp0.38 KB

sticker.webp0.29 KB

TSORON ALLAH. - “Duk mutumin da tsoron Allah ya yi yawa a cikin zuciyarsa, to saɓon Allah zai taƙaita a cikin zuciyarsa. Domi
TSORON ALLAH. - “Duk mutumin da tsoron Allah ya yi yawa a cikin zuciyarsa, to saɓon Allah zai taƙaita a cikin zuciyarsa. Domin, haƙiƙa, tsoron Allah yana hana bawa yawan saɓa wa Allah.” - © Islamic Graphics Designers

TASKAR HIKIMA //36 ❝Jurewa shine mafi ƙarfin jarumtaka.❞ ✍️ Yunus Abdullahi.
TASKAR HIKIMA //36 ❝Jurewa shine mafi ƙarfin jarumtaka.❞ ✍️ Yunus Abdullahi.

WATAƘILA ABINDA YA GIRGIZA KA, BA DON YA KARYA KA BANE… Wataƙila ALLAH ne yake ƙoƙarin Ya tashe ka daga barcin gafala. A cikin Alƙur'ani Maigirma ALLAH (ﷻ) Ya ce: ﴿وَمَا نُرْسِلُ بِالْآيَاتِ إِلَّا تَخْوِيفًا﴾ Ma'ana: “Ba Ma kuwa aiko da ayoyi sai don tsoratarwa.” [Isra'i: 59] ALLAH (ﷻ) Ya bayyana cewa, yana aiko da ayoyi ne kawai domin tsoratarwa, ba domin tursasawa ba. Kuma yana tsoratar da mutane da duk wata aya da Ya so, domin ko za su ɗau darasi, ko kuma suyi tunani, ko kuma su koma zuwa (gare Shi). A rayuwa, akwai abubuwan da suke faruwa su sa mutum ya tsaya cak. Wata jarabawa ta zo. Wata ƙofa ta rufe. Wani abu da ka dogara da shi ya gushe. Wata addu’a ta ɗauki lokaci kafin ka ga amsarta. Wani lokaci ma sai ka tambayi kanka: “Me ya sa wannan ya faru da ni?” Amma ba koyaushe muke gane hikimar abinda ALLAH Ya ƙaddara mana a lokacin da yake faruwa ba. Wani lokaci, ALLAH yana girgiza rayuwarka ne domin ya farkar da zuciyarka. ● Wataƙila abin da ka ƙira matsala shi ne ya hana ka ci gaba da tafiya a hanyar da za ta cutar da kai. ● Wataƙila ƙofar da ta rufe a gabanka ita ce wadda ALLAH Ya rufe domin kada ka shiga abinda ba shi da alheri gare ka. ● Wataƙila jinkirin da kake ƙorafi a kansa shi ne lokacin da ALLAH Ya zaɓa domin Ya shirya maka abin da ya fi wanda kake nema. ● Wataƙila abin da ya sa ka zubar da hawaye shi ne zai sa ka yi sujjada da zuciyar da ba za ta manta da ALLAH ba. Saboda haka, idan rayuwa ta tsoratar da kai, kada ka gudu daga ALLAH. Gudun zuwa gare Shi ne ya kamata ka yi. Idan ka yi zunubi, Ka tuba, Idan ka yi nisa, ka dawo, Idan ka gaji, ka yi addu’a. Idan ka kasa fahimtar abinda yake faruwa, ka amince da hikimar ALLAH. Kada ka bari Shaiɗan ya mayar da gargadin ALLAH zuwa yanke ƘAUNA a gareka. ALLAH yana tsoratar da bawansa domin ya dawo, ba domin ya ce masa babu sauran mafita ba. Ka tuna cewa: ● ALLAHn da Ya nuna maka kuskurenka, shi ne ALLAH ɗin da Ya buɗe maka ƙofar tuba. ● ALLAHn da Ya sa ka gane cewa ka yi nisa, shi ne ALLAH ɗin da yake son ka dawo kusa. ● ALLAHn da Ya sa ka ji tsoron sakamakon zunubinka, shi ne ALLAH ɗin da Ya sanar da kai cewa rahamarsa ta fi girman zunubinka. Don haka kada ka ce: “Na yi wa ALLAH laifi, ALLAH ba zai gafarta mini ba.” A’A Ka ce: “Na yi Laifi mai yawa, amma Ubangijina Mai gafara ne. Zan dawo gare Shi.” Kada ka ce: “Komai ya lalace.” Ka ce: “Matuƙar ina da rai, ina da damar gyarawa.” Kada ka ce: “Na rasa komai.” Ka ce: “Ban rasa ALLAH ba.” Domin idan Allah yana tare da kai, akwai abin da har yanzu ya rage maka a matsayin bege. Kuma wani lokacin, abin da muke ƙira ƙarshen labari, ALLAH yana kiransa farkon sabon babi. Don haka idan yau akwai wani abu da yake tsoratar da zuciyarka, ka ɗaga hannuwanka zuwa sama ka ce: “Ya ALLAH, idan wannan gargaɗi ne daga gare Ka, Ka sa ya zama sanadin komawata gare Ka. Idan jarrabawa ce, Ka ba ni haƙurin da zan tsallake ta. Idan kuskurena ne, Ka gafarta mini. Idan kuma akwai alheri da ban gani ba, Ka sa zuciyata ta yarda da ƙaddararka.” Kada ka ji tsoron gargadin Allah har ka manta da rahamarSa. Wataƙila abin da yake karya zuciyarka yau… shi ne yake gyara maka hanyar zuwa ga ALLAH. ALLAH Ya sa mu zama daga cikin waɗanda suke fahimtar gargadinsa kafin lokaci ya ƙure, su tuba kafin mutuwa ta zo, su gyara tsakaninsu da Shi kafin su haɗu da Shi. Aameen ✍🏼 Faridah Bintu Salis (Bintus-sunnah)

photo content

#DailyHadith
#DailyHadith

23/RABI'UL AWWAL/1448 05/SEPTEMBER/2026 ADDU’AR YAU ASABAR: Ya ALLAH ka taimake mu wajen kyautata ibadarka, ka sanya mana nut
23/RABI'UL AWWAL/1448 05/SEPTEMBER/2026 ADDU’AR YAU ASABAR: Ya ALLAH ka taimake mu wajen kyautata ibadarka, ka sanya mana nutsuwa a cikin Sallolinmu. HADISIN YAU ASABAR: Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “Idan a ka tada sallah, kada ku zo mata kuna masu gaggawa, ku zo mata kuna masu tafiya, na horeku da yin nutsuwa, duk abin da kuka riska na sallah, To ku sallace shi, abin da kuma ya tsere muku, To sai ku ciko shi.” [Bukhari Da Muslim suka ruwaito shi] . Telegram https://t.me/BINTUSSUNNAH Facebook http://www.Facebook.com//Bintusunnah/ YouTube https://youtube.com/channel/UCG_W7_7gQdibxDgvhQdIEyQ

sticker.webp0.34 KB