cookie

We use cookies to improve your browsing experience. By clicking «Accept all», you agree to the use of cookies.

avatar

SCHOLAR DHSN

Dr Kabir Abubakar Asgar

Show more
Advertising posts
8 490
Subscribers
+1024 hours
+667 days
+36530 days

Data loading in progress...

Subscriber growth rate

Data loading in progress...

صلاة_وخطبتي_عيد_الأضحى_المبارك_من_بيت_الله_الحرام.mp339.67 MB
صلاة_وخطبتي_عيد_الأضحى_المبارك_من_المسجد_النبوي_الشريف.mp329.61 MB
DAGA CIKIN FALALAR YININ ARAFAT (V) Hadisin Abu Qatadah (RA) wanda ke cikin Saheehu Muslim ya zo da falalar azumin Ranar Arafat ga mazauna gida. Manzon Allah (SAW) ya ce: "Azumin ranar Arafat ina fatan duk wanda ya yi shi Allah (SWT) ya gafarta masa zunubin shekarar da ta wuce da shekara mai zuwa.
Show all...
DAGA CIKIN FALALAR YININ ARAFAT (IV) Al-Imam Muslim ya ruwaito hadisi daga Nana A'isha (RA) cewa: Manzon Allah (SAW) ya ce: Babu wata rana da Allah yake gafara ga bayinsa da ƴanta su daga wuta kamar ranar Arafa. A wannan rana Allah yana kusantowa ga bayinsa sannan ya yi wa mala'iku alfahari da bayinsa mahajjata. A wata riwaya ta Imam Ahmad: "A yammacin Arafat, Allah yana yi wa mala'ikunsa alfahari da mahajjata. Sai ya ce musu: ku kalli yadda bayina suka taho gare ni daga wurare masu nisa cikin wahalar tafiya"
Show all...
DAGA CIKIN FALALAR YININ ARAFAT (III) Al-Imam Ahmad ya ruwaito daga Ibnu Abbas (RA) cewa: Manzon Allah (SAW) ya ce: Lallai Allah (SWT) ya yi alƙawari da dukkan zuriyar Adam (AS) a Arafa; Allah ya shafa gadon bayan Adam (AS) sai zuriyar bil adama suka bayyana gaba ki dayansu, a nan Allah ya tabbatar musu da alqawarin cewa za su bauta masa ba za su yi shirka ba. Kamar yadda ya zo a Suratul A'araf (172-173)
Show all...
DAGA CIKIN FALALAR YININ ARAFAT (II) Wabi ba.ya.hu.de ya ce da Umar Ɗan Khattab (RA), "Akwai wata aya a cikin littafinku, in da a ce mu aka saukar wa ita, da mun yi riƙo da ranar saukanta a matsayin idi". Sai Umar ya ce masa wace aya ce: sai ya karanta masa faɗin Allah (SWT) (اليوم أكملت لكم دينكم وأتممت عليكم نعمتي ورضيت لكم الإسلام دينا). Sai Umar Ɗan Khattab ya ce masa: "Ka ga mu kuwa mun san inda ta sauka da sanda ta sauka; ta sauka sauka ne a yammacin ranar juma'a, a lokacin Manzon Allah (SAW) yana tsaye a Arafa.
Show all...
DAGA CIKIN FALALAR YININ ARAFAT (I) Allah Ubangiji ya rantse da ranar Arafa a cikin faɗinsa: (والشفع والوتر) da kuma cikin faɗinsa (وشاهد ومشهود). Hadisai sun tabbata cewa (الوتر) ma cikin Suratul Fajr ana nufin ranar Arafa ne. Haka nan ma (اليوم المشهود) shine ranar Arafat.
Show all...
03:25
Video unavailableShow in Telegram
61.30 MB
خطبة عرفة 1445.m4a8.33 MB
VID-20240615-WA0046.mp43.64 MB