3 386
订阅者
无数据24 小时
-67 天
+2030 天
帖子存档
3 386
“Mtsw! Ayodele fita! Fita na ce !” Dr ya yi min wata muguwar tsawa.
Tako ɗaya na yi na tsaya,cikin fushi ya kuma cewa “kenan ba za ki fita ɗin ba?”
Murya a raunane na ce “ba ka ga ta riƙe min hannu ba ne?”
Duk ido suka waro Dr har da ɗora hannu a kai ya ce “wai Ayodele haukata ni kike son yi? Ku kun ga ta riƙe ta?” ya tambayi nurse suka girgiza kai.
Da mamaki nake kallonsu bisanin na mayar da dubana ga Emeka wacce ta riƙe ni gam ta na girgiza kai idonta na shatatar da hawaye.
“Ke kaɗai ke jin abin da nake cewa da kuma ganin abin da nake don Allah kar ki biye su” cewar Emeka .
Cikin jin haushi Dr ya fizgo hannuna da niyyar fitar da ni da ƙarfin tsiya sai dai sam ya kasa sakamakon ɗayan hannun da ke riƙe da Emeka .
“Dr ni fa na fara jin tsoro! Ina ga fa gaskiya ne! Dubi yadda hannunta ke jone kamar a rinƙe shi ɗin kuma ....kuma gadon kamar ya na motsa wa” nurse ta faɗa.
Dr ya sake min hannu,ya ce “ba zan yi mamaki ba don Abeno cike take da ƴaƴan matsafa da Mayu....” bai rufe bakinsa ba Emeka ta fara shaƙuwa,da sauri duk suka nufeta tare da saita na'urar aiki a kanta.
Ni kuwa ganin numfashinta ya dawo kawai sai na sulale na koma can ɓangaren mu.Kasa bacci na yi sai zaune da na yi na rabka uban tagumi ina tunanin abin da ya faru.Gadon bayana ne ya fara yin ƙaiƙayi,tare kuma da wata irin tsira wa tamkar ana nitsa wasu abubuwa gefe da gefen kafaɗuna.
Dishi-dishi idona ya fara,ban san ya aka yi ba na tsinci kaina a wata duniya wacce na fi kyautata zaton ta mafarki ce.
Wani ƙaton gida mai ɗauke da ɗakuna kashi-kashi,ruhina ya sallama.Babu wanda ya amsa min haka ba wanda ya ɗago ya dube ni sai tsohuwa wacce tun farkon shigowata na ji yaran gidan na ambaton sunanta da “Yaba”
Mugun kallon nan mai cike da hassada,ƙyashi haɗi da baƙin ciki ta jefo min bisanin ta miƙe tsaye ta zo gare ni.“Mi kike so kuma yanzu?”
“Abin da kika ɓoye!” na bata amsa.
“Maganar ahali ce wannan bai shafe ki ba,kin dai yi naki ikon don haka ki....” ban bari ta dire ba na tari numfashinta da “ki bani cikin lumana ko kuma na ƙwata ta ƙarfin tsiya! Yin haka kuma babba asara ce gare ki domin duk abin da kika ɓoye zan fito da su ne”
Tsoro ne na gani shimfiɗe ƙarara a fuskar Yaba,bisanin ta yi gaba ni kuma na take mata baya har cikin ɗakinta na laka wanda aka yi ma rufin kara.
Ƙarƙashin gado ta duƙa ta fito da wani asusun ƙarfe tare da miƙo min shi,ban ɗauki lokaci ba wurin buɗe shi.Baƙin hayaƙi ya fito kamar fitar iska ya tashi sama,guntun ƙyallen atamfa na gani sai na ɗauke shi bisanin na aje asusun na fito.
Daidai nan kuma na farka daga baccina,na dafe gefen goshina da yake sara min bisanin na buɗe idona taram .Da sauri na tashi ganin Emeka a tsaye ta na min murmushi.
“Na gode sosai Ayodele,kin ceci rayuwata!” ta faɗa tare da ƙoƙarin karɓa wani abu daga hannuna da nake jin na jimƙe ba tare da na san mine ne ba sai da na kai dubana sai na ga ƙiren atamfar da na yi mafarki ne.
Emeka ta ci gaba da cewa “wannan zanen ankon bikina ce,Inna Yaba ta yi amfani da shi don kashe ni saboda kawai zan auri bare wanda ba cikin danginmu ba.Na gode!” ta na gama faɗar haka ta fice ta bar ni sake da baki ina tunanin kar dai ace mafarkin da na yi gaskiya ne? ??????
MRS SADAUKI ce🌬️
[31/10 à 11:05] MRS SADAUKI 💫: *MUTUWARE ...*🧟♀️
GIDAN GAWA🧞♀️🌬️
Love
and
Anan zan dakata duk mai son cigaban labarin kuma cikakken labarin Sai ya latsa shudin rubutun Dake nan kasa ko kuma hoton da ke kasa zai kaishi shafinmu inda zai downloading littafin zuwa kan wayarshi
https://taskarnovels.com.ng/novel/mutuware-gidan-gawa
Note: ku tabbataa kuna da asalin data ba wai na facebook ba in ba haka ba zaiyi ba, duk wanda ya gagara karantawa ko downloading yai min magana a a comment section.
Yadda ake downloading na littafin: idan kuka shiga link dana ajjiye dinnan zai kaiku zuwa ga shafinmu na inda zaku ga hoton littafin da wasu details da suka shafi littafin, to sai kuyi kasa sosai. Zaku tarar sa wani shudin maballi wato BUTTON an rubuta DOWNLOAD a jikinsa sai ku tabashi.
3 386
MUTUWARE GIDAN GAWA
Littafin Mrs Sadauki
https://taskarnovels.com.ng/novel/mutuware-gidan-gawa
[31/10 à 11:05] MRS SADAUKI 💫: *MUTUWARE ...*🧟♀️
GIDAN GAWA🧞♀️🌬️
Love
and
Horror story
`MRS SADAUKI💫✍🏻```
Dedicted to Ameera Adam
FCWA ☀️
_____
Ƙirƙiraren labari ne,ban yi shi don cin mutumci kowa ba.Duk wanda ya zo daidai da rayuwarsa to akasi aka samu.
1
#ƘASAR COTE D'IVOIRE
#Babbar asibitin Abengourou
A tsorace nake ƙara tushe kunnuwana ko zan samu sa'ar toshe ma'adanar sautina da ke zuƙo min wata murya mai cike da tashin hankali.Sai dai yaudarar kaina nake,domin kuwa toshe kunnen da na yi hakan bai canza zane ba .Na kai hannu da niyyar ɗaukar pilow ko shi Allah zai sa na dace,hasken ɗakin ne ya ɗauke ɗif wanda ya yi sanadiyar tsayawar na'urar da ke kore zafi.
Ƙaiƙayi na fara ji yayin da sauro da zafi suka ce salama alaikum,shegiyar muryar nan mai shegen naci sai ƙara ƙaimi take wurin roƙon abin da ban san mi take so ba “ku cece ni ! Ku cece ni don Allah babu kowa ne?”
Na ja tsuki bisanin na lalubo wayata na kunna fitila,duk abokan aikina baccinsu kawai suke a gajiye.Na miƙe tare da nufar ƙofa,na murɗa handle na fito ,ga mamakina ko ina na asibitin akwai hasken wuta sai ɗakinmu da kuma wani ɗakin da ke can gabashi wanda akwai ƴar tazara tsakani.
Haka kawai na ji zuciyata na tunzura ni kan na je na duba tako ɗaya ,biyu,ina daɗa matsawa ina kuma daɗa jin sautin muryar nan mai neman taimako har na isa bakin ƙofar daidai nan hasken ɗakin ya dawo.Na kutsa kai,sai na tarar da nurse biyu da wani Dr a tsaye kan wata matashiyar budurwa ,gefe kuma wata jemamiyar tsohuwa ce zaune ta na kaɗa ƙafa.
Duk kallonsu ya dawo kaina,ni ma su nake kallo ɗin.
“Ayodele mi kike yi a nan? Babu aiki ne ɓangaren ku?” Dr ya tambaye ni,na buɗa baki da niyyar yin magana na tsinkayo wata murya kuma na ce min “Ayodele please ki taimaka min ban mutu ba!”
Inda sautin ya fito na duba,sai yanzu na lura da idon budurwar rufe suke ruf kamar mai yin bacci.Da mamaki nake tambayar kaina ‘dama mai bacci ya na iya yin magana?’
“Ta rasu ne! Ƙoƙarin cire duk abubuwan da ke jikinta ne muke amma sun ƙi fita” Dr ya katse min tunani.
“Amma yanzun nan fa ta min magana akan na taimaketa ba ta mutu ba” na faɗa .
Duk kallon mamaki suka bi ni da shi,hakan yasa na ci gaba da cewa “tun ɗazu fa ita ta hana ni bacci kururuwar ta ce ta tashe ni”
“Ayodeleee?” Dr ya kira ni da wani sauti,bisanin ya tambayi nurse ɗin “ku tun ɗazu da muke nan kun ji kururuwar ne?” duk kai suka girgiza alamun a'a.
Sai ya maido kallonsa gare ni “to kin ji ta yiyu kunnuwanki ne ba su jiye miki daidai ba”
“Mi sunanta?” ita ce tambayar da na yi,“Emeka” ɗaya daga cikin nurse ɗin ta ban amsa.
A hankali na fara taka ƙafata sai dai kafin na isa ga Emekar tsohuwar nan ta taso tare da tsaya wa a gabana “ina za ki je? Mi za ki yi?” ta jero min tambayoyi haɗi da jifata da wani mugun kallo mai ratsa ɓargo da tsoka don sam bai da daɗi.
Dakyar na fizgo numfashi tare da jarumtar kallonta cikin tsakiyar ido ,kawai sai na ga mugun razani a nata idon tare kuma da saurin ja ta bani wuri ba tare da na san dalilin yin haka ba.
Kai ga Emeka na yi tsaye bisanin na kai hannu kan fuskarta na ce “Emeka ?”
“Ayodele ta fa mutu,ya kike yi wa matatta magana kamar zautatta?” Dr ya tari numfashina.Ba tare da na dube shi ba na ce “ba ta mutu ba Dr ! Doguwar suma aka sa ta”
“Wa ya sa ta doguwar suma? Nan fa asibiti ce kuma mun san aikinmu ”
“Dr ita wacce ta saka ta suman ta san kan ta! Ina iyayenta suke?” na tambaya.
“Daga ita sai Kakarta suka zo,kuma ga ta can ta fita” cewar nurse.
Na ɗago kaina sai na ga tuni tsohuwar nan ba ta nan,wato abin da na fahimta ita ce Kakar Emeka.
“Ayodele ki taimaka ki damƙa ni ga iyayena Kakata ba ta sona shi ne take son kashe ni,ta ɓoye ruhina cikin asusun ƙarfe ta lashi takobi ba za ta fiddo shi ba har abada” shiru na yi ina sauraren esprit ɗin Emeka da ke yi min magana ba tare da ni kaina na san shi ne ba.
“Dr yanzu ma ba ga shi ta na yin magana ba?”3 386
NASANMA Hausa Novel Document By Ruqayya Isa Aliyu (Oum Misbahu) https://taskarnovels.com.ng/novel/nasanma
3 386
DESTINY LOVE Hausa Novel Document By Oum Yasmeen https://taskarnovels.com.ng/novel/destiny-love
3 386
ME KAMAR SARKI Book 1 Hausa Novel Document By Yusrah Musa Abubakar https://taskarnovels.com.ng/novel/me-kamar-sarki-book-1
3 386
K'ADDARAR SO Hausa Novel Document By Fatima Rabiu (Zarah Royal Star) https://taskarnovels.com.ng/novel/k-039-addarar-so
3 386
MURADINA Book 1 Hausa Novel Document By Fateey Zaarah https://taskarnovels.com.ng/novel/muradina-book-1
3 386
SUNE SILAR ƘADDARA TA Hausa Novel Document By Fateey Zaarah https://taskarnovels.com.ng/novel/sune-silar-kaddara-ta
3 386
.
Hankalin taufidatu ne ya tashi ta tuna da mugun mafarkin datayi yau amma da shike tayi imani da cewa duk wani abun da zai samu mutum toh daga Allah yake kuma ba'a taba gujewa Kaddara
Tayi murmushi ta dubeshi sannan tace Allah ya dawo dakai lafiya
.
Bayan yarima juraish da dakaru kusan dari sun fita daga birnin yemen basu nausa ko'ina ba sai cikin daji, inda suka runga tafiya amma cikin ikon Allah basu hadu da Dabba ko daya ba sai tsuntsaye kawai , suma tsuntayen ko da sun harbesu da kibau basa samunsu sai de kibau din subi ta gefensu, a haka sukayita kutsa kai cikin daji batare da tunanin cewa gari ya fara duhu ba,
.
Kwatsam ba zato ba tsammani sai gani sukayi wani abu ya wuce su da gudu, kamar wucewar walkiya,
Su kansu basu da hakikanin sanin ko menene wannan ya gilmasu, nan take yarima juraish ya zaburi dokinsa da gudu , ya nufi wannan abu daya wuce, suma sauran dakarun koda ganin yarima ya zaburi dokinsa dukkansu sai suka rufa masa baya suna masu wani irin azababben gudu,
.
Bayan kaman wani lokaci sai gashi yarima juraish ya kusa cimma wannan abu, koda ya matso kusa da wannan dabba sai yaga ashe ma wata katuwar barewace keta tikar gudu, yarima juraish na ganin haka sai ya zaro kibau din dake bayansa ya zaro kifiya daga cikin kwarinsa sannan ya dameta a cikin bakarsa, sai da ya tabe iyaa karfinsa sannan ya saki, ai kuwa yana saki sai wannan kifiyar yaje ya caku a kafar dama na wannan barewar,
.
Barewar ta yi kara sakamakon zafin data ji Amma duk da haka bata daina falfala gudun datake ba, sai gashi an kasa tsere tsakaninta da yarima juraish, ya kasance ita ta kasa guduwa masa shi kuwa ya kasa cimmata,
Ahaka suka kasance suna wannan tsere har tsawon sa'a daya,
Kwatsam ba Zato ba tsammani sai yarima juraish yaga wannan barewar ta fada cikin wani wawakeken rami dake gabansa, cikin matukar sauri ya kama linzamin dokinsa yaja don ya tsaida shi, Amma yadda kasan ma alokacinne yake karama dokin Gudu, yayi ya tsaida dokin Amma dokin taki tsayuwa,
Har dokin ta iso gaban katon ramin sannan ta fada ciki tare da yarima juraish a bayanta
.
Anan na kawo karshen littafi na daya
SHIN YARIMA JURAISH ZAI RAYU
.
INA LABARIN SARKI AYYUB DA MATANSA
.
Domin jin wayannan amsoshin sai ku tareni a littafin SADAUKI UBAN SADAUKAI na biyu 2
......
Yo anan zan tsaya sai wani jikon
Marubuci Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Hakkin mallak (m) keffians News Teller (K N T)
Tare da hadin guiwan hausaebooks page
3 386
.
Zarishatu ta sallami aljani maljanu
Tafiyarsa keda wuya sai zulaikha da shamlika suka farfado daga dogon suman da suka yi nan take zarishatu ta zayyane masu duk yadda sukayi ita da Aljani Maljanu
.
Allah mai girma hakika Allah yayi gaskiya dayace "iza qadha amran fa inna ma yakunu lahu kun fa ya kun"
.
Bayan kwana bakwai sai taufidatu ta kamu da cikin sarki Ayyub bayan wata tara ta haifi santalelen yaronta , kyakkyawa na gaban kwatance, alokacin da aka haifeshi ma mutane sun zata aljani ne saboda tsabar kyawunsa, mutane daga wasu garuruwan da kauyukan sassan nahiyar suna ta zuwa ganin wannan yari
.
Farin ciki kuwa agun sarki Ayyub bata faduwa,
Do min kuwa saboda farin ciki yana ta raba dukiyarsa ne yana baiwa jama'a
Mutanen birnin yemen baza su taba mancewa da wannan ranar ba, saboda kuwa wannan rana, talakawa,marasa galihu da attajirai sunga yadda ake barin dukiya
.
Su kuwa sauran kishiyoyin taufidatu wannan rana sai ta kasance tamkar ranar bakin ciki ce a garesu, amma zarishatu ita abun bai dameta ba don kuwa tasan mahaifinta ma yafi sarki ayyub dukiya da wasu abun hakan yasa ta saki ranta a ka runga sha'ani da ita
.
Zulaikha da shamlika kuwa hankulansu ba karamin tashi yayi ba a wannan rana saboda sun san cewa izan sarki ya fadi ya mutu toh babu wani abun kirki da zasu samu daga cikin dukiyarsa
.
Sai da aka kwana arba'in ana shagali a birnin yemen sannan dukkanin gidajen garin saida aka yi musu sabbin fenti, Attajirai, yayan sarakuna da sarakai kuwa suka runga halartar garin yemen,
Har takai cewa babu wani isasshen masauki na saukar bako wannan yasa sauran bakin suka sauka a wajen gari suka kafa tantunansu
.
Facaka akayi tayi da abinci da abunsha tamkar ba a san darajarsu ba, ko wanne mutum na garin yemen ranar yasan anyi walima tunda kuwa har cikin gidanka dakaru zasu shigo ma da katuwar tukunyar abinci wanda ko mutane dari ba zasu iya cinyewa ba su girke ita a wajen sannan su baka dukiya mai dumbin yawa, suyi gaba
.
Al'ummar birnin yemen gaba dayansu sun nuna farin cikinsu da wannan yaro , na sarki Ayyub wanda yaci sunan JURAISH
.
Kwanaki suka rinka zuwa suna wucewa har yarima juraish ya cika shekara biyar da haihuwa, alokacin yarima juraish ya taso da ababen Al'ajabi, da mamaki domin kuwa yana dan shekara biyar dinnan yake fita farauta sannan ya farauto manyan namun daji danginsu damisa zaki da sauransu
.
Wata rana yarima juraish yaji yana sha'awar tafiya farauta sai ya nufi fada domin ya sanar wa Abbansa sarki Ayyub, koda ya kariso fada sai sarki ya ayyub ya rungumeshi ya na mai murmushi, ya dubi yarima juraish yace yakai dana farin ciki na shin meke damun kane naga yau kana cikin walwala,
.
Yayin da juraish yaji haka sai yace ya abbana zuwa nayi ka bani izni don ina son fita farauta yau dinnan , koda jin wannan batu sai ran sarki ayyub ya dugunzuma ainun domin kuwa shi ba a son ransa ne ba juraish yake fita farauta saboda kankantar shekarunsa, cikin sanyin jiki yace yakai dana kayi sani cewa sam sam bana kaunar wannan farauta da kake tafiya amma kuma saboda na faranta maka rai yau zan barka ka tafi amma da sharadi guda daya
.
Yarima juraish ya dubi mahaifinsa yace ya abbana shin mene ne wannan sharadi, sarki ayyub ya yi murmushi yace sharadin itace daga yau baza ka sake fita farauta ba har sai shekarunka sun kai ashirin , shin ka yarda da wannan sharadi nawa,
.
Hankalin yarima juraish ya dugunzuma ainun amma da shike yasan mahaifina nasa yana fadane kawai sai yayi murmushi yace na amince
Sarki ayyub ya dubi sarkin yaki yace mai ya hada dakaru dari biyu suyi ma yarima rakiya
.
Cikin kankanin lokaci har wayannan dakaru sn gama shiryawa, yarima juraish kawai suke jira su dau hanya
.
Shi kuwa yarima koda ya baro fada bai zame ko'ina ba sai turakar mahaifiyarsa, da shigarsa cikin turakar sai yazo gaban taufidatu ya russuna yace ya ummina hakika yau naji ina sha'awan zuwa farauta shine nazo na sanar dake don na riga dana fadawa abba koh
3 386
Kwatsam sai wani murgujejen Aljani ya bayyana ya durkusa yace " Umarce ni yake shugabata koda akisa taga wannan aljani saita kadu ainun sannan ta juya da gudu da nufin ta fice daga dakin
.
Wannan aljanin yace da ita "bazan cutar dake ba ya shugabata hakika ni bawan kine akisa najin haka sai ta juyo ta dubi aljanin a tsorace tace "yakai wannan aljani shin ya akayi ka zama bawana"
$
Koda aljanin yaji wannan batu sai ya dago kai yace ni bawan wannan zoben dake sanye a hannunki ne, hakika duk wanda ya sanyashi kuwa toh zan kasance bawanshi"
Koda jin wannan batu sai akisa ta cika da matukar mamaki, tayi shiru sannan tace "toh nidai bana da bukatanka don haka kar ka sake bayyana mani"
.
Aljanin yayi murmushi yace "ya shugabata ai kece ki kayi kirana "
Ta yaya na kiraka akisa ta bukata,
Aljanin yace ai duk lokacin da kika shafa zoben nan dake hannunki toh ni kuwa zan bayyana maki ako wani lokaci" aljanin na gama fadin hakan ya bace bat tamkar bai taba wanzuwa ba
.
Cikin hanzari akisa ta cire wannan zoben daga hannunta ta bude wani jaka ta jefa zoben ciki
Bayan shekaru goma sha bakwai lokacin akisa ta kwanta ciwon ajali , toh alokacinne kuma yarsu zarishatu ta cika cikakkiyar mace sai allah yai mata baiwar kyau da farin jini
Don kuwa a wannan lokaci yayan attajirai da sarakuna nata zuwa neman aurenta wajen mahafinta sirrinaddalib
.
Itako zarishatu taki amincewa da gaba dayansu wannan daliline yasa har ta cika shekaru goma sha bakwai batayi aure ba,
Alokacin da akisa taga cutar dake jiiknta bana tashi bane sai ta kira zarishatu tace da ita yake yata hakika wannan cutar dake jikina bana tashi bane, wannan yasa na kiraki don nai maki nasiha na karke.
Bayan akisa tayiwa zarishatu nasiha mai tsuma zuciya sai ta mika mata wannan zoben sannan ta fadi mata amfaninsa, kuma ta sanar da ita labarin wannan zoben
**
Toh kunji labarin zarishatu yar Attajiri sirrinaddalib matan sarki Ayyub ta uku
*
Koda sauran matan sarki sukaga zarishatu tayi shiru sai babbarsu zulaikha tace "yake zarishatu shin me kike takama da shi da har kika dauki wannan al'amari karamin abu"
Koda zarishatu taji wannan batu sai tayi murmushi sannan ta fiddo da wani zoben azurfa sai kyalli yake, ta ajjiyeta akan teburin dake gabansu, kowannensu yakai dubansa kan wannan zoben sannan shamlika tace "tambayarki ake kin wani fiddo zobe maimakon ki bada amsa
.
Murmushi mugunta zarishatu tayi sannan tace "yaku yan uwana kuyi sani cewa wannan zobe itace amsar tambayanku"
Nan take ta fede masu biri har wutsiya game da al'amarin wannan zoben
.
Koda suka saurari labarin wannan zoben sai dukkansu suka kamu da matukar mamaki nan take zarishatu ta dauki wannan zoben ta sanyashi cikin dan yatsanta
.
Aiko tana sanyawa sai shamlika tace da ita "na rokeki zarishatu kada ki kira mana wannan aljani"
Babbarsu zulakiha kuwa sai ta tashi tsaye ta nufi kofan dakin da nufin fita,
Cikin sauri zarishatu ta shafi gefen zoben
Wani murgujejen aljani mara kyan gani ya bayyana koda bayyanar wannan aljani sai shamlika da zulaikha suka suma alokaci guda saboda raazana da sukayi da ganinsa
.
Aljanin ya russuna da guiwowinsa sannan yace "ya shugabata gani na amsa kiranki, ki umarceni ni kuma na aikata"
Zarishatu ta dan sauke ajiyar zuciya sannan tace "kasani yakai MALJANU hakika labari ya iso mani cewa daya daga cikinmu zata samu haihuwa da sarki shin wacece wannan , abunda nake bukata dakai shine kayi bincike ka gano min ko wacece a cikinmu"
.
Aljani maljanu yace "ya shugabata ki sani wannan aikin da kika bani ba sai naje nayi bincike ba, domin na dade da sanin hakan"
Koda zarishatu taji wannan batu sai ta dka masa tsawa tace "gaggauta sanar dani wacce zata haihu da sarki a cikinmu
"
Cikin kyarma aljani maljanu yace " ya shugabata ki gafarceni hakika wacce bakwason nan toh itace zata haihu da sarki, amma nayi bincike na gano cewa bayan ta haihu toh dan da suka haifa zai bace bat daga wannan nahiyar tamu nayi nayi in gano inda zai tafi amma abun yaci tura"
3 386
.
Wata rana mun fito fatauci ni da mahaifina da kuma sauran hadimansa su goma muka durfafi wannan birni naku don munji jama'a suna labarinsa ,
Asalin tafiyarma nice na takura wa mahaifina nace sai munzo sabida irin labarin birnin da nake ji daga bakin jama'a
.
Akan hanyarmu ta zuwa wannan birni naku ne a cikin wani jeji mai yawan dogayen bishiyu muka hadu da yan fashi,
Nan take wayannan yan fashin suka kashe gaba dayan mutaninmu ya rage daga ni sai mahaifina,
.
Shugaban yan fashin ya fashe da dariya sannan yace "yaku wayannan fatake lallai kuyi sani kunyi babban kuskure da har kuka biyo wannan hanya, "ya nuna mahaifna da yatsa yace "kayi sani yakai wannan tsoho lallai yanzu a take zan yi maka kisan gilla, sannan na maida wannan kyakkyawar budurwa dake gefenka ta zamto karuwata ,
.
Yana gama fadin hakan sai ya daga Addansa sama ya lumata a ruwan cikin mahaifina n
Mahaifina ya sulale daga kan dokinsa ya fadi kasa nan na kwala ihu sannan na na sauko daga kan dokina na durkusa na tallafo wuyan mahaifina, a sannan ne ya dubeni yace "yake yata hakika banso wannan abu ya faru garemu ba, nan ya saka hannu cikin aljihunsa ya dauko wata zobe ya bani sannan ya umarceni dana sanyata na mika hannu na karbi zoben na ciri zoben zan sanya a hannuna sai naga kan mahaifina ya langwabe,koda naga haka sai rungume gawan mahaifina ina mai rusa kuka shugaban yan fashin ya iso inda nake rungume da gawan mahaifina,
.
Kawai sai ya saka hannunsa ya tallafo wuyana sannan yace yake wannan kyakkyawa shin ba gani ba meye na kuka don wannan lalataccen tsohon ya mutu....."
Yana gama fadin haka shida yaransa suka fashe da dariya, inata fisge fisge don na kwaci kaina daga hannunsa amma na kasa
Nan idanuwana su ka kai kugunsa naga wata yar karamar wuka ,
Banyi wata wata ba na zaro wukar daga kubenta sannan na soka ma wannan dan fashin a cikin tumbinsa, take ya kwallara waata irrin kara sannan ya fadi matacce, koda sauran yan fashin sukaga abunda naiwa shugabansu, sai suka yun kuro kaina take na falfala da gudu na nausa cikin daji
.
Aduk lokacin dana waiga bayana sai naga sun kusa cimmini, hakance tasa na zage na dunga wannan gudu iya karfina, ba zato babu tsammani na jini na lume cikin kasa anan na suma
.
Dana farfado na tsinci kaina cikin wani wawakeken rami nafara kiciniyar fitowa daga wannan kwari dakyar na fito
.
Ina fitowane mukayi arangama da wannan zakin da kuka ceci rayuwata daga gareshi "
Koda akisa tazo nan a labarinta sai ta kara fashewa da kuka
.
Attajiri sirrinaddalib ya jinjina kai sannan ya dubi akisa yace "lallai na tausaya maki abisa rashin mahaifinki da kikayi, Allah ya jikansa,'
Ya sauke gwauron numfashi yace ........
Me kuma zaice
......
Yo anan zan tsaya sai wani jikon
Marubuci Shuraih Usman
Typing:- Shuraih Usman
Hakkin mallak (m) keffians News Teller (K N T)
Tare da hadin guiwan hausaebooks page
SADAUKI UBAN SADAUKAI
Littafi na daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih 99%
Part C
.
.
Attajiri sirrinaddalib ya jinjina kai sannan ya dubi akisa yace "lallai na tausaya maki abisa rashin mahaifinki da kikayi, Allah ya jikansa,'
Ya sauke gwauron numfashi yace "yake akisa kiyi sani a farkon lokacin dana ganki take naji ina matukar kaunarki kuma naji bazan iya jure boye sonki a cikin zuciyata ba hakance tasa na sanar dake kudirina da fatan zaki karbeni hannu bibbiyu,
.
****
Bayan andaura auren akisa da attajiri sirrinaddalib da watanni uku sai akisa ta samu juna biyu bayan wasu watanni ta haifi yarta kyakkyawa ,son kowa kin wanda ya rasa, a sannan ne wata rana da daare tana gyara kayanta acikin wani jakan fata, ba zato ba tsammani sai taga wani abu na walkiya koda ta lura da kyau sai taga she zoben nan ne da mahaifinta ya baTa lokacin dayake gargarin mutuwa
.
Murmushi tayi sannan ta dauki zoben ta sanya a hannunta tadan shafi zoben da gefen hannunta
3 386
" Yanzu akan wannan dan abin ne muke ta wani damun kawunanmu, sannan tayi shiru na dan lokaci kankani
.
Ita dai zarishatu bakaramar hatsabibiya bace don kuwa mahaifinta wani babban Attajirine wanda duk kasar yemen babu mai arzikinsa, ko sarki ayyub bazai nuna masa arziki ba sunansa Sirrinaddalib
.
Alokacin da sirrinaddalib ya cika shekaru ashirin da biyu a duniya sai ya kasance wata rana da daddare yana barci yayi mafarki acikin mafarkin nasa yaga wata kyakkyawar budurwa sai gudu take a cikin dokar daji kafafunta babu takalmi sai sossokewa take da kayoyi koda yai duba izuwa bayan wannan budurwa sai yaga wani murtukeken naman jejine yake biye da ita, koda wannan dabbar ya kusan cimma kyakkyawar budurwan sai sirrinaddalib yasha gabansa take wannan dabbar yayi tsalle da zummar ya fadawa sirrinaddalib
.
Firgigit ya farka daga wannan mafarki washe gari kuwa da sirrinaddalib yayi shiri ya fita farauta don kuwa halaiyarsa ce duk wata ranar alhamis toh wajibine agareshi sai yaje farauta shida hadimansa da dakarunsa kimanin su dari,
Ayayin da suka tsinci kansu acikin dokar daji sun
.
Sai ya kasance cewa sun zagaye wannnan jeji kaf amma ko bera basu kama ba, nan take sirrinaddalib ya harzuka yaba wa hadimansa umarni cewa acigaba da tafiya koda kuwa za'a kwana ne ana wannan farauta ba zamu koma da baya zuwa gari batare da mun kama wani dabba ba,
.
Suna cikin wannan zance ne sukaji alamun motsi a cikin ciyawa take kowannensu yayi shirin fada dakarunsa suka zare takubbansu masu kibbau suka dameta,
Wata kyakkyawar budurwace mai matsakaicin tsayi da matsakaicin jiki ta fito daga cikin wannan ciyayin tana mai falfala masifaffen gudu,
A bayanta kuwa wata murgujejiyar zakanya ce ke biye da ita ,
Koda sirrinaddalib yaga haka sai ya tuna da mafarkinsa nan take yabada umarnin a sakar ma wannan zakin ruwan kibbau
Dakiku kadan sai ga wannan zakanyar ta fadi rikica aa kasa gaba dayan jikinta kibiyoyine
.
Bayan kuran ta lafane attajiri sirranaddalib ya iso gaban kyakkyawan budurwannan sannan yayi mata nuni data hau kan dokinsa , batare da gardama ba kuwa ta hau,
Koda Sirrinaddalib da tawargarsa suka cikin gari sai ya nufi gidansa wacce aka kawata ainun har tafi gidan sarauta kawatuwa,
.
Yana isa gidansa ya sa kuyangi suka shiga da kyakkyawar budurwannan wacce har yanzu bai san sunanta ba, wani shashe na wannan gida
.
Sannan ya umarcesu da su gyarata suka wo mai ita falonsa,
Sirrinaddalib ne zaune bisa luntsuma luntsuman kujerun dake makare a wannan falo, sallama yaji sannan wata kuyangarsa tazo ta russuna akusa da shi tace ranka shi dade ga wannan bakuwar nan isowa
.
Murmushi kawai yayi sirrinaddalib ba karamin kyau yake da ba, don ba kowacce budurwace zata hada idanu dashi bata kamu da sonsa ba, shidai attajiri sirrinaddalib tunda ya hada idanu da fuskar kyakkyawan budurwar yaji taake ya kamu da matsanancin kaunarta
.
Takun sahu yaji alamun wani yana shigowa , juyawar da zaiyine yayi arba da abunda ya zauta mai kwakkwalwa, tunaninsa ya dushe, suciyarsa bugawa take da karfi tamkar zata faso kirjinsa,
.
Tana sanyene da kayan sarauta ayayin da wannan kaya ya kasance na zallar alharini ce, a kasan doguwar rigar wasu duwatsu ne masu maatukar daukar idanu, sa'adda wannan budurwa ta iso gaban sirrinaddalib sai ta zauna bisa kilishin da daben wajen rufi,
.
Attajiri sirrinaddalib yayi murmushi sannan yai mata inkiya da hannu kan cewa ta tashi ta zauna bisa luntsumemen kujeran dake gefenta, ba musu ta mike ta zauna bisa kan wannan kujera, zamanta keda wuya sai Attajiri sirrinadalib ya dubeta ido cikin ido sannan yace da ita"yake wannan kyakkyawar budurwa shin wacece ke , sannan daga ina kike mekike a cikin wannan daji mai hatsarin gaske,"
.
Koda budurwannan taji wannan batu sai ta fashe da kukan bakin ciki mai tsuma zuciyan dukkan mai sauraro, sai da tayi mai isarta sannan tayi shiru ta bude baki tace "yakai wannan attajiri mai jin kai da tausayi lallai kayi sani cewa suna na Akisa mahaifina falkene, yakan yawata manyan kasashe fatauci, tun ina yar shekara biyar mahaifina ke futa yawon fatauci dani,
3 386
Koda wannan kara yayi kamar dakiku ashirin sai ya dauke dif tamkar bai taba wanzuwa ba
Wazirine ya dubi sarki ayyub sai yaga ko gezau ba yayi ba, sannan fuskarsa yana duban gaban fada kai daga ni kasan yayi nisa acikin tunani
.
"Ranka shi dade " waziri yace
Firgigit sarki yayi sannan ya mike tsaye a matukar razane koda ganin hakan sai kowa dake wannan fadar ya mike tsaye
.
Sarki ya dubi jama'ansa a matukar tsorace yace da su
"Yaku Al'ummar birnin yemen shin idanuwanku basu gane muku abin dana gani bane, "
Koda jin haka sai dakaru ,hadimai da yan majalisa duk suka hada baki suka ce
"Ba muga komai ba ranka shi dade"
Nan take sarki ayyub ya dubesu yace da su
"Yaku mutanina kuyi sani cewa dazu da wannan kara mai amo mara dadin sauraro ta bayyana a wannan fada, to kusani a sa'ilin ne wani haske ya bayyana a gabana take wannan hasken ya rikide ya koma izuwa wani kyakkyawan saurayi wanda ko atarihi ban taba jin labarin sa ba
.
Saurayin ya dubeni yace dani "yakai wannan sarki mai tarin iko ina mai yi maka albishir da abubuwa guda biyu, na farko ina mai sanar dakai nan da kwana bakwai daya daga cikin matayenka zata sami cikinka,
Koda naji ya ambata cewa zan sami haihuwa sai na kamu da tsananin farincik, ai bansan lokacin dana tari numfashin wannan kyakkyawan saurayi nace da shi
"Ya kai wannan kyakkyawan saurayi gaggauta sanar dani shin waye kai?" Nan take wannan saurayi yayi murmushi sannan yace " sanin ko waye ni ba shine mai muhimmanci ba, n manzo ne kuma zan isar da sakon da aka aikoni da shi,
Abu na biyu dazan sanar dakai shine
.
Yaron da zaka haifaa zaizo da ababen mamaki da al'ajabi, sannan kuma zai shuhura agaba dayan wannan duniya har sai takai cewa kowa dake fadin wannan duniya ya sansa, kuma ya san sunansa, ammafa zai shiga cikin muggun yanayi don kuwa zaiga masifu da bala'u kala daban daban, akarshe sai ya yada addinin musulunci a gaba dayan wannan duniya"
.$
Koda kyakyawan saurayinnan yazo nan a zancensa sai yayi mani murmushi wanda sai da hakoransa suka fito take wani siririn haske ya daga cikin tsakiyan hakwaransa tun wannan hasken na fitowa kadan kadan har wannan hasken ya cika mani idanuwa har takai bana iyaganin wannan saurayi,
Lokaci guda sai wannan hasken ya bace bat , na nemi saurayin kasa ko sama ban ganshi ba, hakan ya tabbatar mani da cewa ba mutum bane
.
Sarki ayyub ya tada gwauron numfashi sannan ya dubi dukkan yan majalisarsa wayanda suke a matukar tsorace game da jin wannan labari da sarki ayyub ya basu, yace dasu
"Kunji al'amarin daya kasance dani a yayin da wannan karar mai amo da sauti ya bayyana"
.
Koda yan majalisa da sauran fadawa suka saurari wannan zance mai kama da al'mara daga bakin sarkinsu sai wasu daga cikinsu suka kamu da matukar farincikin jin cewa burin adalin sarkinsu zai cika, a sannan ne wasu kuma suka kamu da tsananin bakin ciki
.
****
Babban turaka ne wanda aka kawata shi ainun da ababen kawa
Zaune bisa kujeru na alfarma yan mata ne kyawawa su uku, dukkansu sunci ado ainun
Wayannan yan mata ba wasu bane face matayen sarki ayyub kishiyoyin Taufidatu
Dukkansu suna zzazaune a bisa kujeru na alfarma a yayin da suka yi zagaye da junansu yadda zasu fuskanci juna
.
Babbarsu mai suna zulaikha ta mike tsaye tace "yaku yan uwana, hakika kunsan cewa an sanar da mai martaba cewa daya daga cikin matansa nan da kwanaki bakwai zata samu ciki, shin idan cikin ya kasance ya bayyana ga abokiyar hamayyarmu fa, mene ne mafita
.
Ta biyun wacce ta kasance sunanta shamlika , ta mike tsaye ta fara bayani "hakika zulaikha kinzo da magana mai muhimmanci, ni kuma nan take zan warware wannan matsalar"
Zulaikha ta dubeta tace " tayaya kenan "
Murmushin mugunta shamlika tayi sannan tace "ta hanyar hana sarki ayyub kusantar taufidatu, ta hanyar kissa da kisisina "
.
Ta ukunsu wacce tunda aka fara wannan tadin bata ce uffan ba , sunan ta zarishatu ta dubesu sannan ta kyalkyale da dariya sai da tayi mai isarta sannan tace
3 386
.
Narkul ya dumfari imran gadan gadan shi kuwa imran sai zulliya da gociya ya runga yiwa narkul take mutane suka ringa kiran sunan narkul, koda narkul yaga imran na neman ya bata mai lokaci sai yayi kukan kura ya falfalo da gudu don yayiwa imran kwab daya ya fiddashi daga filin ,
.
Alokacinda imran yaga narkul ya falfalo da wannan azababben gudun sai dai hankalinsa yayi matukar tashi, dai dai ya rage baifi saura taku goma b ba narkul ya riski imran sai imran shima falfalo da gudu yana dumfarar narkul, ai nan jama'a suka zuba idanu don suga waye zaa kayar
.
Koda ya rage baifi saura zira'I daya ba su hadu sai imran ya tsuguna akan guiwowinsa cikin wani irin salo na ban mamaki ya bi ta tsakanin kafafuwan narkul ya wuce, shi kuwa narkul saboda karfin gudunsa yama kasa tsaida kanshi don kuwa yayi turjiyar amma sai da ya karisa wajen jen kyallen nan har ya ballata
.
Ai koda da ganin hakan sai jama'a suka dauki shewa kowa yana ma imran jinjina
Toh kunji yadda imran yayi gwagwarmaya akan mahaifiyar Taufidatu,
.
Basufi shekara biyu ba Allah ya arzucesu da kyakkyawar yarinya inda suka saka mata suna taufidatu, tun taufidati tana karama take da matukar kyawu don kuwa saboda kyawunta ne ma masunci imran ya hanata fitowa koda bakin kofar gidanne ahaka har ta girma
.
Wata rana ta tafi icce a jeji ta saba takan rufe fuskarta da mayani ta tafi yin iccenta kuma izan ta tafi tunda safe bata dawowa sai dare hakan yasa take daukar abincinta da abinshata ta tafi dasu wannan jeji,
.
Wata rana ta fita icce kawai sai taga wata barewa tana gudu dakyar a kafar barewan na dama akwai wani kifiya take tausayin wannan barewa ya darsu a zuciyanta
Barewar ta zube kasa sakamakon raunin dake kafarta,
.
Taufidatu ta karisa wajen barewar sannan ta zare wannan kibiya daya ke kafar barewar, har hawaye na zuba a fuskarta ta cire mayanin data rufe fuskarta ta daure daidai wajenda yake zubar dai jinin, motsi taji abayanta ta cikin surkukin daji
.
Hakan yasa ta waiga don taga wanene nan tayi arba da sarki Ayyub koda sarki Ayyub yaganta sai ya dimauce nan danan ya ce " tsarki ya tabbata ga Allah daya halicci wannan kyakkyawa"
.
Sarki ayyub yaji ya kamu da tsananin son taufidatu ya tambayeta gidan da suke da zama ta bashi amsa , ko takan barewar daya biyo bai bi ba yana komawa fada ya shirya yanufi gidan don neman auren taufidatu, babu wata gardama masicni imran yaba shi aurenta
.
Ranar auren anyi shagali kala kala, don kuwa duk cikin matan sarki ayuub babu wacce yake matukar kauna tamkar Taufidatu
.
Wannan ce ta sanya hassada hade da kishi suka darsu a zuciyoyin wayannan kishiyoyin nata
.
Sarki ayyub baya da wata matsala sannan talakawa najin dadin mulkinsa ayayin da attajirai da masu hannu da shuni ke matukar bakin ciki
.
Kunsan ance kowane dan adam adunua bazai rasa wata matsala ba toh hakan take ga sarki ayyub, don dhi matsalar saya ce
Matsalar saiki ayyub itace rashin samun haihuwa
Yakan tara manyan malaman kasar yasanya su roka masa Allaj yabashi haihuwa a bangarensa kuwa baya samun isasshen barci sakamakon raba dare dayake yana rokon Allah akan yasa mu magaji
.
Izan kuwa ya zauna a waje guda kuwa babu abinda yake face tunanin irin duk arzikinan daya mallaka da kuma shuhurar dayayi a fadin nahiyar nan yasan cewa yana mutuwa shi kenan za'a dibi arzikinsa wanda shi bai masan yawansu ba , a raba wa matansa saura kuma asaka a baitulmali, daga nan shikenan an manta da shi kenan
.
Wata rana a fada ana ta fadanci sarki ayyun ya kacire bisa wata kujera ta alfarma wacce aka sana'antata da zallar jauhari sannan aka mata cinbaki da duwatsun yakutu a gefensa kuwa waziri ne sannan sai galadima a gefen hauninsa
.
A sannan ne wata mummunan kara mai kama da sautin jaki ta bayyana koda jin wannan kara sai hadimmai da dakaru suka fara zarya a cikin wannan suna neman daga inda karar yake fitowa,
3 386
SADAUKI UBAN SADAUKAI
Littafi na daya 1
Marubuci:- Shuraih Usman
Typing:- Shuraih 99%
Part A and B
.
.
Kimanin shekaru dubu daya da suka gabata a nahiyar sudan anyi wata birnin mai suna yemen birnin yemen babban birni ne don duk nahiyar babu wata birni data kaita girma, tattalin arziki da yawan dakarun yaki,
.
Birnin yemen na karkashin mulkin wani adalin sarkine ma'abocin addinin musulunci, sannan daukkan jama'an wannan birni Addini daya suke bi, itace kuwa Addinin Islama
.
Sarki ayyub ya kasance yana da matan aure hudu sannan kuma yana da ilmin Addini daidai gwargwardo kuma ya kasance yana kamanta adalci a tsakanin matayensa bil haqqi
.
Wayannan matayen nasa kyawawane na gaban kwatance dukkansu sun fito ne daga manyan gida in ka dauke amaryarsa mai suna Taufidatu, itace kawai ta kasance ya ga wani talakan masinci
.
Mahaifinta sunansa Imran kuma talaka ne don kuwa tun yana karami ya ke bin mahaifinsa a rafi, kuma da wannan sana'ar suke ci sannan susha har takai ga ma sun biya wasu bukatunsu
.
Ahaka imran ya taso har mahaifinsa ya rasu shi kuma ya riqi wannan sana'a da kima ya kuma jajirce ba'a dade ba ya auri wata kyakkywar mace wacce saboda saban kyawunta sai da akayi gasa kafin ya samu aureta
.
Al'adar wannan garine a duk lokacin da aka samu wasu suna son mace daya toh gasa akeyi don a fidda gwani, wannan gasar bata komi bane face gasar jarumta, shi dai imran da farko ba jarumi bane amma saboda tsananin kaunarsa ga Halimatu hakan yasa ya dage lallai sai ya shiga wannan gasa
.
Da ranar gasa tayi, mutane da yawa sun taru don kashe kwarkwatar idanuwansu, yayin da aka zagaye filin da wani yanki na jan kyalle, a dokar wannan gasa duk wanda ya fita daga cikin filin ko ya kama jan kyallen nan, ko kuma ya bari ta taba jikinsa toh ya fadi take zai fito daga cikin filin
.
Yadda akeyin gasar dai shine dukkanku za'ataru ku a cikin wannan fili duk wanda ya samu nasarar fitar da dan uwansa daga filin har ya rage babu kowa a filin sai shi kadai toh shine zakara
.
Zaratan Jarumai ne da sadaukai masu kirar sadaukan taka sannan sai kirba kirban katti sun kai su hamsin sai kuma masunci Imran wanda duk cikinsu shine san karami kuma baya da kirar jarumtaka a jikinsa,
.
Hakanne yasa mutane sukai tai masa dariya , koda aka buga gangar fara gasa sai filin ya haustine karajin mazaje ya yawaita kura ta turnuke, don kuwa sai dai kaga kato ya daka kato sama ya yi jifa dashi wajen filin , take wannan da'akayi jifa dashin zai karkade jikinsa yaje gefe don kuwa ya riga daya fadi
.
Shi kuwa imran cikin ikon Allah sai ba'a samu wani wanda ya dumfare shi ba, har dai jaruman da suke filin suka rage basufi su goma ba, can sai wani jarumi ya dumfari imran, take sai imran ya fara addu'a tun kafin jarumin kariso
.
Ai koda jarumin ya kariso sai ya kaiwa imran sura nan kuwa yayi nasarar kama mai wuya ya daga shi sama ya rungi tafiya da shi har yazo daidai wajen jan kyallen nan, shi kuwa imran sai wutsil wutsil yake da nufin ya kwace kansa amma katon yafi karfinsa , abisa dole yayi lamo tamkar ya suma
.
Koda katon yaga ya sumar da imran sai ya sake shi ya fadi a kasa sannan ya daga kafa da nufin ya taka shi ya fice daga filin , cikin shammata sai imran ya farka sannan ya matsa wa kafar wannan jarumi ai koda kafar wannan jarumi tabi iska sai yayi tangal tangal saakamakon rinjayi yarshi da kafartayi, shi kuwa imran koda yaga haka sai yazo ya bangeje wannan jarumi da kafarsa take jarumin yafadi ajikin wannan jan kyalle daya zagaye filin ai nan take jama'a suka dau shewa
Cikin jin kunya wannan jarumin ya fice daga filin
.
Haka aka cigaba da wannan gasa har ya rage saura imran da wani narkeken kato kadai a cikin filin, shi dai wannan kato ana kiransa da suna Narkul kuma duk cikin birnin yemen babu wanda yakaishi girman jiki, asalinsa ma zuwa yayi daga wata kasar,
.
Narkul ya dubi imran ya kece da dariyar farinciki don kuwa shi yariga da ya aiyana akan ya gama cinye wannan gasa don har ya fara hango amaryarsa a cikin dakin shi,
3 386
Mutane daddaiku ne sukayi saura a cikin masallacin har barci ya fara dibana sai naji ana tashi na na dago da kai domin naga waye wannan
"Malam tashi koh zamu rufe masallacin ne "
Su biyune suna sanye da manyan kaya
Kallo daya nai masu na ayyana araina kodai limaman masallacin ko kuma wasu malamai na daban
na tashi cikin rashin jindadi na fita daga masallacin na samu wani dan kewaye a jikin masallacin na kwanta,
Bayan sun kulle masallacin ne zasu tafi sai naji dayan yace "malam ladan kaga wannan yaro ya koma can ya kwanta kuma, da alama matafiyine don ga shi dauke da Jaka"
Wanda aka kira da ladan yace"malam liman kenan ai wannan yaro daka ke gani kasurgumin barawo ne, sau uku ana kamashi a kasuwar kwari, yanzuma daka ganshi anan inaga koh ya lababo ne ya sace mana mita,ko kuma mic"
Liman najin haka sai ya rike baki yace "assha "
Sai ya daga murya da alama wasu yakewa magana yace "kai samari kuzo ku jibgi wannan mara kunyar barawon, tun kafin ya kassaramu"
.
Ina jin haka ban san lokacin dana zabura a guje ba na tsallake, dan karamin katangar daya katange gewayin dana ke kwance na ranta ana kare, inajin ihu da kururwan mutane suna cewa atare barawone atare haka na ringa cin uban gudu har na fice daga angwar gaba daya, ina shawarar na tsaya kenan sai naji wani Abu mai nauyi ya bugi kaina daga nan kuma sai ji nayi na kife akan wani ruwa ruwa mai wari, daga jin wannan wari na gane warin giyane ko na aman giya,
Idanuna dishi dishi suke gani, wani katon mutum nagani ya tsaya akaina yana rike da wata katako 2 by 2, mutumin ya sunkuyo da kansa daidai kunne na yace
"Umar dan wasa daga yau wasanka ya kare , dun kuwa yanzu zan aika ka kiyama, dama sakamakon irinku kenan masu taurin kan tsiya"
Ya daga wannan katakon sama da nufin ya buga mini aka.........
.
Masu karatu anan muka kawo karshen littafin TARAR ARADU na daya 1
Kaman yadda kamin mufara wannan littafi na fada maku cewa 1 and 3 kadai nake da su bani da 2, dun haka gobe zan fara post na TARAR ARADU littafi na uku 3 Allah ya kaimu da rai da lafiya
$
TARAR ARADU
(m) Umar Lawan Abdul
Littafi na daya 1
Typing Shuraih Usman
.
.
Domin download na wannan littafi dama wasu sauran littatafan sai ku shiga shafinmu anan kuyi like
Like:- www.facebook.com/hausaebooksI
In kuna son cigaban sai ku sanar
3 386
Tamike tsaye akuma loakci guda da tazauna akan hannun
kujerata ta dubeni fuska da fuska
"Da ka gujeni umar da mutuwa zanyi, bazan iya rayuwa
babu kai ba "
Na girgiza kai
"Bazan gujekiba farida har abada koda kuwa za'rika
yankan naman jikina
(Kaji soyayyar gaskiay kenan
Its shuraih 99%)
* *** **Tarar Aradu
Littafi na daya 1
Umar lawan Abdul
Typing Shuraih Usman
Page 14
.
.
Toh jama'a sakamakon rashin sauran fallayen littafin hakan yasa, dole da kaina zan karasa maku wannan labari sai ayi hakuri da kura kuran da za'ai arangama da su
.
Ahalin yanzu nida tsuntsun da'ake kiwonsa akeji duk
daya
muke ,
Domin kuwa bana fita ko'ina daga shago sai shago,
Sai idan angama abinci a miko min ta kofa mai shiga
cikin
gida ,izan kaga na fita to da daddarene ko da asubah
idan
zamuje sallah nida yayana
.
Wata rana da asubah na fita sallar asubah nida yayana toh dama ni idan na fita salla nida yayana bama dawowa gida sai safiya domin kuwa tsayawa muke a masallacin muita karatu har sai gari ya waye, kaman kullum yau hakan ta faru,
Mun fito muka nufi gida ina zuwa kofan gidan gabana ya buga sakamakon ganin kfan dakina danayi a bude,alhalin kafin na tafi masallaci sai dana sanya dan makulli na kulle dakin gaba daya
.
Na dai daure na doshi dakin ina bude dakin na saki wani salati sakamakon abunda nagani acikin dakin,
Wata mata daga ita sai shimi iya cibiya da wani dingilallen wando iya cinya tana kwance kan katifar barcina,
Ina bude dakin matar ta tashi tayi mika, sannan tadan mummustsuka idanuwanta ta dubeni tace yauwa malam kai nake jira dama tun dazu nake son na tafi,
.
Na dubeta baki bude cikin mamaki nace mata wacece ke sannan meya kawoki cikin dakina,
Tayi tsaki tace kaji rainin hankali kadauko ni kuma kana tambayata ko waye ni lallaima, malam ka bani kudina yanzu ina son zan tafi
.
Ke dan ubanki wani kudin zan baki, yi maza ki fice daga cikin daki yar iskan karya, na fada cikin fusata,
Ai nan matannan tai tsalle ta cakumemin gaban riga muka fito daga waje tana cewa wallahi sai ka biyani kudin kwana na, tayaya za'a yi ka dauko ni ka kwana dani sannan kace baza kaa biya ba ai wallahi sai ka biya,
.
Ba'a bata wani lokaci ba har matannan ta tara min jama'a nan raina ya baci na tsinka mata mari ai ba shiri ta sakeni, na cigaba da jibgarta da kyar mutanen angwa suka kwaceta a hannuna amma duk da haka matannan sai ihu take ita sai na biyata kudinta, a haka yayana yazo ya samemu
.
Yayi bakinciki sosai kuka ne kawai baiyi ba ya tambayeta nawane kudin bakunya bare tsoron Allah matannan tace dari uku ne, cikin kunan rai yayana ya ciro kudin ya bata, matar ta wuce dakina ta kwashe kayanta tazo wucewa ta dubeni tace Assha, ai wallahi daga yau baka dauko ni dakinka, sai de mu ringayi acan yadda muka saba,tunda kai kace tsiyane aranka,, ko kallonta banyiba donni abun har mamamki nake ni daban taba ganinta ba,
.
Na dafa yayana nace wallahi yaya....ya katseni ta hanyar daga mani hannu yace umar da na zata abun naka zai tsaya kan sace sace ne toh tunda takai ga sai ka bata bin suna ka kawo karuwa cikin gidana toh ka kwashe naka ya naka ka kara gaba kasan inda dare ya maka daga yau kabar gidannan kenan
.
Iya tashin hankali yau na gani, kuka ne kawai banyi ba,
Cikin kankanin lokaci na shiga shagona na dauki wata tsohuwar jakar kayana, na dauki hanya wacce bansan ina na nufa ba
Tafiya kawai nake zuciyata sai radadi take yimin A lokacin da hotunan abubuwan da suka faru dani suke yawo a kwalkwata tamkar a majigi,
Duk da ya kasance wunin ranan bansa ka komai a cikina ba, amma hakan bai sa naji yunwa ba
Na isa wata angwa na samu gindin wani waje na zauna na kifa kaina a cikin guiwowina, ayayin da tunani iri iri keta zarya a kwakkwana, ji nake tamkar na kashe kaina na huta
.
**
Na tashi na nufi wani masallaci domin yin sallar Isha'I domin kuwa yanzu na tabbata mutane ko sun gani ba zasu shaidani ba, bayan na gama sallar ne sai kwanta a masallacin da nufin na kwana a masallacin in yaso gobe da safe sai in wuce kauyenmu wajen iyayena,
