3 386
订阅者
无数据24 小时
-67 天
+2030 天
帖子存档
3 386
mutane.
"Wayyo Allah umar kacuceni kaci mutuncina"
Muryar yayanace lokacin daya iso yana kuka, ya nufo
kaina da gudu yansanda suka rirrikeshi.
"Ku kyaleni na kasheshi tunda bashi da sauran amfani"
Da kyar yansanda suka janyeshi baya
"To shikenan daga yau umar na sallameka kar ka kara
fitowa indai akwai mutumin da bama shiri dashi bai wuce
barawo ba"
Alhaji kenan loakci na farko dayayi magana tun bayan
isowar mu.
Ya sallami yansanda, da sunso abarsu su tafi dani alhaji
ya hana 'aka barni anan .
Har saida jama'a suka watse sannan na. Tashi, aranar
unguwarmu sai da daddare nashiga........
AYYA JIKI MAGAYI
DAMA DUK WANDA YACE ZAI TARI ARADU DAKA TO
LALLAI SHIMA YASAN SAKAMAKON
(Maudu'I)
Izan da kaine umar zaka cigaba da soyayya da farida ko
ko zakayi hankali
Waitin for sharhi
Zanci gaba
Its shuraih 99%
TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 13
aranar unguwarmu sai da daddare nashiga........
*** ** ****
Ahalin yanzu nida tsuntsun da'ake kiwonsa akeji duk daya
muke ,
Domin kuwa bana fita ko'ina daga shago sai shago,
Sai idan angama abinci a miko min ta kofa mai shiga cikin
gida ,izan kaga na fita to da daddarene ko da asubah idan
zamuje sallah nida yayana.
Shi kansa rashin jituwa mai karfi ta shiga tsakaninmu.
Abisa abunda yakira cimasa mutunci.
Nayi masa rantsuwa da Allah akan duk abubuwanbani da
hannu aciki yaki yarda.
Sai yanzu na fuskanci ashe irin wasan da mutuminnan
yake nufi kenan.
Hakikanin gaskiya wasan nasa bantaba ganin wanda
yakaishi muni ba, sai dai duk wannan bana zaton zan bar
farida,domin kuwa kaunarta ta rigaya tabi jikina.
Yau iatace rana ta farko dana shirya zanje wajenta tun
bayan da'aka yimin sharri.
Bakomaine yasa na daga kafa illa tsabar bakin cikin dake
damuna.
Ahalin yanzu kuka awajena babu wuya domin kuwa da
zarar na tuna bana control na kaina abinci ma kadan
nake ci.
Na isa goron dutse da kimanin karfe tara na dare .
Badon komai ysa nayi dare hakaba sai don gudun kada
wani wanda yake kasuwar kwari yaganni ya tona min
asiri.
Tuni su farida rufe gida, nasani abune mai wuya ace wai
bacci take kasancewarta mai matukar kwazo, na
kwankwasa kofa.
Bada jimawaba naji takun kafa
"Waye"
Aka tambaya muryar farida ce
"Umar ne"
Na bada amsa tuni ta gama shaida muryata nan da nan ta
zare sakata takuma bude kofa kawai naga ta fashe da
kuka.
Nayi mamakin abinda yasa haka , kodai dun na dade
banzo bane?
Muka dunguma cikin gida kukantane yafoto da hajiya yau
maimakon gaisuwa kuramin ido kawai tayi,ta kuma rike
baki
"Ashe zaka sake dawowa gidanmu umar, na dauka bazaka
kara takowa ba"
"Me zai hanani zuwa mummy?"
Itama sai naga tafara kwalla
"Kai kuma umar hanyar da za'abi da kai kenen"
Sai nagane ashe labarin abin dayafaru tuni ya iso
garesu.banyi mamaki ba domin kuwa goron dutse
unguwace data kushi yan kwari da dama.
Nida farida muka zarce daki alokacin datake ta faman cin
kuka.
"Umar nafadamaka muddin kana tare dani bazaka sami
kwanciyar hankali ba amma ka ke keshe kasa kaki yarda
to yanzu daka gani da idonka ai ka hakura"
Tacigaba da kuka
"Dakata farida"
Nace da ita
"Shin wai kin daina kaunatane ko yaya"
Ta tsuguna agabana
"Umar bazan daina kaunar kaba har abada"
Nayi murmushi
"To indai hakane farida banga wani abin dazai sani in
janye ba,kisani na dora tubalin soyayyarmune akan gini
biyu,imma dai nasami cikar burina imma a kirgani a
mutum na hudu daya rasa ransa, kisani ahalin yanzu
cigaba da kaunarki ya fiyemin sauki,domin kuwa mutuwa
afagen dagar neman aurenki yafiyemin mutuwa
asakamakon hauhawar jini"
Na sunkuyo gareta
"Farida izan narasaki bazankai labaraiba"
Kuramin ido kawai tayi tana kallona , unkai tsawon minti
daya mun zurawa juna idanu, daga bisani fuskarta ta
yaye izuwa murmushi.
"Oh! Umar Allah yabar mu tare har abada"
Na mayar da murmushinta sa'arda bakina yake motsawa
a kokari na lalubo kalmar amin .
3 386
kunsa.
"Ku zauna "
Yace damu lokacin daya ke nuna mana benci.muka zauna
daura da juna
"Bawani abune yasa na kirakuba illa wani abu daya afku
wanda banji dadin saba.ya nunani nida jamilu jiya ku na
aika cikin motata , to amma dana isa gida sai natarar da
abin da baiyimin dadi ba, wanda banga amfanin abar min
kes ba alhali an dauke agogon.
Wand yin hakan babbar rainin hankaline da bazan juraba
.
Abin dana keso nasani shin jamilu kaine ka zare agogon
ka kai kedin kawai ko kuma umar kaine ka dauki agogon.
Kuna iya bani amsa anan izan bahaka ba kuwa kuna iya
shaida ma yansan da"
Uka kalli juna nida jamilu akuma lokaci guda muka fara
rantsuwa ,wallahi mu bamu dauka ba.
Alhaji yayi murmushi
"To shikenan kuzauna anan "
Yazare sailula bisa ga dukkan alamu yana ma yansanda
wayane. Bada jimawaba sai gasu sun iso su hudu
"Gasunan ku tafi dasu gida jensu ku bincikomin agogona
"
Aka tasamu agaba .
Nidai babban abin daya dameni aga nazo da yansanda
gida a matsayin ana zargina da sata.to amma badan
hakaba to da ina iyayin komai ma
Musamman tunda nasan bandauki agogoba.
"Ku hau nan"
Yansandan sukace damu lokacin da muka iso gindin
motarsu.
Bayan mun zauna kan bencinne aka fara tambayar inda
za'a nufa .
"Ana iya zuwa ko'ina ma "
Nabada amsa cikin halin yarda da kaina .
"Wanene umar"
Daya daga cikin yansandan ya tambaya.
Na dora yatsana a kirji lokacin da nake nuna kaina
"Gidan ku za'anufa"
Dansandan yacigaba da fada.
"Dama kana da kyasa kyasan sata harbiyu abaya"
Nazare idanu sakamakon jin kazafin da bazai yiwu na
musa shi ba.aka sanar da direban inda za shi.
Bai gushe yana tuki ba saida muka iso kofar gida.
Bakom al'amarin ya sanya tulin yara taruwa, cikin
kyarma nasa kuba na bude dakin , tare da yansanda
muka shiga.
Suka shiga laluben kowanne lyngu da kowanne kusurwa.
Badon bakin cikin daya ke cina ba da babu abinda zai
hanani dariya.
Sakamakon dagewar da yansandan sukayi neman agogo.
Wanda hakan tamkar leka tundin kulline domin gano
rakuminka daya bata.
Tuni sun gama birkita ko'ina amma haryanzu ba'a ga
agogo ba.
"Muje a duba cikin gida"
Daya daga yansandan yafada.
"Dakata tukunna"
Inji wani dayake kokarin daga katifata.kyalkyalin daya
bayyana a karkashin katifar shi yasanar dani akwai wata
ajiyar da bansan da'ita ba,
Ba komai bane illa kyakkyawan agogo yana walkiya,
daukewar numfashina yazo daidai da lokacin dawani
radadi ya ratsa kuncina.
Sakamakon wani bahagon mari da daya daga cikin
yansandan ya kwadamin.
"Kace bakai kasata ba"
Nan danan bakina yafara fadin abin dani kaina nasan
baza a yarda da shi ba.
"Wallahi yallabai sharri akayimin"
"Barawon banza barawon wofi dama tun sa'arda kazo
kake yimana sace sace kaboye kudin alhaji, kaci sailula ,
yau luma gashi ka saci agogo"
Jamilu kenan ya hauni da bambami sa'arda muka fito
waje!
"Barawo! Barawo!! Mai kasata? Agogo ya sunan ka? Umar"
Wata kwarya kwaryan waka kenan da yara suka kirkirota
bayan da'aka watsani mota akafara tafiya.
Aguje sukabi motan suna raira waka , basu rabu da muba
saida muka hau titi.
Nasha zagi kala kala da kuma mari dabam dabam kafin
mu karasa.
Ahaka muka iso har kasuwar kwari daya da ga yansandan
na cumuimiye da kuquna . Ya kwadamin mari sa'arda
yake kokarin dankwafar dani agaban alhaji
"Alhaji yaron tsinannen barawone daya kamata a
ladabtar dashi"
Yamika ma alhaji agogon kafin kace meye tuni mutani
sun cika wajen.
Kama daga kwastomomi zuwa masu kanti.
"Allah wadaranka"
"Allah tsinema"
"Allah watsa ka"
Sune mabambantan lafuzzan dake fita daga bakin
mutane.
Wadansu har basa samun daman ganina sabida
cunkosan mutane.
Zazzafan radadi yarinka bin jikina, ba radadine na zafin
duka ba 'a'A radadine na mamakin sharrin da'aka yimin
da babu daman na musa shi, babban abinda yafi damuna
shine sunana daya riga yabaci akasuwa da
unguwarmu,toni yanzu da wacce fuskar zan ringa kallon
3 386
"Kadan kenan daga hikimarsa"
Alhaji ma ya waiwaya wajen domin yagane ma idanunsa ,
Jamilu kuwa yace sai ya daukoshi.
Adai dai lokacin haske yagama kantin sakamakon
generator da'aka tayar,
To amma kwaron ya shige cikin kaya wutar kawai ake
gani.
Dana kura ido sanaga ashe ma rigata ya shiga.
Jamilu ya laluba ,sai naga ya hada. Gami da fadin "kai"
Ya kuma ja dabaya
"Menene?"
Ibrahim ya tambaya
"Ba kwaro bace ashe sailulace"
"Wace irin sailula"
kuma na tambaya fuska a yakune
"Sailula nawa kasani"
Jamil yafada loakcin dayake dauko rigar,
Akazo da ita gabanmu aka sanya hannu aikuwa sailular
alhajice, wai ashe kyallin danjar sabis muke hangowa
Alhaji yai gauron numafashi ya mika hannu ya karba ,
nikuwa alokacin nawa numfashi ya dauke (nima nawa ya
kusan daukewa da kyar na seta hanaklina ,lol Shuraih
99%)
Akwai kallon yaya haka ?
Da fuskokin mutanen ke dauke dashi bayan kallona na
tsayin lokaci da alahaji yayi sai kawai yakada kai ya fita .
* ** ***
Ahalin yanzu duk wani amincin dake tsakanina da jama'a
akasuwa yakau .
Hakan bakaramin kuntata min yakeba
Alhaji dai yadena aikena ko'ina izan kuwa nazauna kusa
da mutum ko carbi ya fitar sai ya mayar da abinsa aljihu.
Wai gudun kar na faki idonsa na dauke.
Duk inda na nufa kuwa kaga ana C.I.D na hatta da randa
izan zan sha ruwa sai atsareni da ido wai duk karna faki
ido na tura modar aljihu
(hahaha sai ni masoyi shuraih 99%)
Kai abubuwan takaici dabam-dabam
Ahaka na cigaba da zama cikin zullumi da bakin ciki .
Izan kaga na saki raina to tabbata muna tare da farida
don gudun karta gane halin dana keciki.
Inanan rakube a cikin kanti sai gwani alhaji ya shigo .
Da ganinsa kaga babban mutum akwai wani mutum biye
dashi alhaji ya mike tsaye suka gaisa
Sannan ya sami waje ya zauna
"Alahi agogonne na kawomaka"
Yafada lokacin dayake duban mai gidan mu
"Yauwa! Ansamo"
Alhajinmu ya tambaya
"Kwarai kuwa"
inji wacan mutumin
Lokacin dayake karbar wani dan akwati daga hannun
mutumin da suka zo tare,
Da bude akwatin sai ga wani walwali, agogone na danyen
gold mai matukar tsari ,
Alhaji ya jinjina kai
"To shikenan sai mun hadu"
Mutumin ya mike
"To sai na ganka"
Suka yi sallama yatafi alhaji yaba ma jamilu akwatin
"Ungo wannan kaimin motata, ka bude aljihy(glove
compartment) ka sanya min aciki"
Ya karba yatafi ba'a jima ba ya maido wa alhaji makullin
"Nakai"
Aka cigaba da harkoki anahaka har loakcin sallar la'asar
yayi , nida Alhaji muka fara tafiya masallaci da muka
dawo sai jamilu da ibrahim suka tafi,
Ana haka ne akayo wa alhaji waya ya dauka suka fara
tattaunawa,
Wani mutunne yakeso abashi cikakken addreshin wani
kamfani a ingila
Alhaji ya dubeni loakcin daya ke mikomin makulli
"Don Allah kaduba kan seat din baya akwai wani karamin
littafi kadauko minshi kayo sauri"
Na karba na tafi aguje ba'adadeba na dawo da littafin
.Alhaji yabashi adreshin sannan yabani na mayar ,
akacigaba da sabga .har lokacin tashi yayi akabani kudin
mota kamar yanda aka saba nakama hanyar gida.
** ** *****
Nayi mamakin irin wannan sammako da alhaji ya bugo a
yau mu dukkaninmu ya rigamu zuwa.
Hatta ibrahim wanda shi yake tafiya da makullai.........
YAU KUMA WATA KALUBALECE
KE KALUBALAN TAN UMAR
Don't trouble troubles
Till troubles trouble you
Shuraih 99%
Zan cigaba
TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 12
Nayi mamakin irin wannan sammako da alhaji ya bugo a
yau mu dukkaninmu ya rigamu zuwa.
Hatta ibrahim wanda shi yake tafiya da makullai.........
Naga saukar ibrahim daga mota kafin mu karaso to
menene ya fito dashi?
Kodai irin abinnane domin yakama mai kin fitowa da
wuri.
Na durkusa na gaidashi jamilu ne kawai bai iso ba.
Ba 'afi minti biyar ba shima ya'iso akafara hada hada
"Kuzo inji alhaji"
Ibrahim yafada yana raba mana idanu
Muka nufi wajensa cikin rashin sanin abin da kiran ya
3 386
Nayi tafiya mai dan nisa .
Kawai sainaji anyayimeni nayi sama bansan
komaeneneba.
Saidai na jini acan gefe guda nayi kokarin namike amma
ina juwa ta daukeni dole nakoma na zauna .
Sai bayan yan dakiku nayi kiliya .saboda haka na lalubi
jakata
Amma babu ita kuma babu dalilinta .
Tashin hankali shin wai meyafaru danine
Bandai san takamaiman abinda ya yayimeniba.
Kuma gashi babu mutane a eriyar wajan
Na duba jikina babu inda naji ko da kwarzane toni yanzu
yazan saka kaina zuwa zanyi wajen alhaji ko kuwa
karasawa zanyi inda aka aikeni?
Duk biyun dai kusan ma'anarsu daya kusan duk inda naje
dai bani da abin fada.
Wannan yasa na share waje kawai na zauna (da yafimaka
umar lolx shuraih 99%)
Ina wajen la'asar tayi.nahada kai da gwuiwa na rasa me
yake min dadi.
Kawai sanaji ana tabani.
Dana daga kai sainaga ashe jamil ne.
"Lafiya kazo nan kazauna"
Na maida kaina batare dana bashi amasa ba
"To kazo alhaji yana kira"
Da kamar bazani ba sai wata zuciyarta ce jeka.
Na bishi muka rankay zuwa kasuwa.
Alahaji ya dubeni
"Ya akayine umar nayi waya ance baka kai kudinba"
Na sunkuyar da kaina kasa cikin rashin sanin abinda
yakamata nafada
"Ina kudin suke"
Sai naji bakina suna fadin
"Sun bata"
"Kamar yaya sun bata?"
Yatambaya cikin mamaki.
Ni kaina nasan bakina yayi gidadanci daya bada wannan
amsar.
Na bayyana masa duk abinda nasani.
Ya dade yana kallona daga bisani ya mike tsaye game da
faidn
"Allah ya kyauta"
* ** ****
Nacigaba da zama akasuwa cikin rashin jin dadi
dominkuwa ina fuskantar wani irin kallo daga abokan
aikina .
Alhaji ma kuma ya canza taku .
Ahalin yanzu baya aikena nakai kudi ko kuma na karbo
,nasan bakomai bane ya jawo hakan ba illa bacewar jakar
kudi.
Wannan yasanya akullum takaicin duniya na damuna .
To amma yana iya abin sai hakuri .
Bayan dana karya kumallo sai najawo wata bakar jaketna
na dora sakamakon sanyi da akatashi da shi.
Sai kawai na nufi kasuwa muka ci gaba da hulda kamar
yadda muka saba ........
WATA AZAL DIN KUMA
Keep following
Its shuraih 99%
Zan ci gabaTARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 11
Bayan dana karya kumallo sai najawo wata bakar jaketna
na dora sakamakon sanyi da akatashi da shi.
Sai kawai na nufi kasuwa muka ci gaba da hulda kamar
yadda muka saba ........
Da rana ta raba sai kuma zafi ya kori sanyi,
Wannan yasanya kowa cire rigar daya kara .
Muka rarrataye.
Da alamun yau alhaji agajiye yake ,domin kuwa tunda
yazo ya dare kujera yake ta gyangyadi abinsa.
Sailularsa kashe alarm din yayi domin kar adameshi.
Kawai ya dorata ahannun kujera .
Bai farkaba sai bayan la'asar shima sai da muka yo sallah
sannan na tasheshi
Yayi mika da hamma sannan yafara lalube-lalube ba
musan kome yake nema ba sai bayan daya rasa sannan
ya dubemu
"Wai ina sailulata take?"
"Ina kuka sanya min sailulata"
Duk muka yi shiru,kawai sai muka fara rantse-rantse
kowa yana fadin bai gantaba.alhaji yafara salati
"Da batan sailular nan gwara batan kudin da'aka
sayeta,manya manyan abokan mu'amalata ta taurai suna
tuntubatane ta wannan layin,akwai kuma nombobi da
dama wanda a sailular kawai na shigar dasu,ciki kuwa
harda wani mutumin danakeso na tuntuba in anjima don
Allah duk wanda yasan inda take yafada zan bashi dubu
hamsin"
Babu wanda yayi magana acikinmu.
Ahaka alahaji yafita akaba da cigiyar sailular duk
kasuwa.amma shiru kakeji.
Duk yanda akayi de wanine ya lababo ya saceta.
Bayan alhaji yadawo daga sallah sai ya zauna akan
kucjera.
Ko magana ma bayayi saboda tsabar takaici yananan
zaune har kusan sallar magriba.
Dif nepa suka dauke wuta ba'aganin komai agurin sai dai
in ka kura ido sosai zaka hango irin kwaronnan
"makyallu"
Koriyar wuta nata fita daga bindinsa
Yayi kememe abinsa ajikin bango.
Jamilu ya tabo ibrahim "dubi hikimar Allah"
Wai duk wannan haske daga bindin kwaro yake
Ya jinjina kai
3 386
Aciki na hango wani mutum yana tafe ana faduwa ana
gaisheshi.
Farine dogo mai dan kauri.
Badomin nasan mai martaba sarkin kano ba to da sai
nace shine wannan .
To ammma ko babu komai wannan bai kai mai martaba
sarkin kano farin jini ba.
Amma shima yana dade daidai nasa.
Sai naga yana matsowa garemu
"Ga shinan"
Yayana yafada sai muka mike tsaye domin karramashi.
Daya iso sai nayi kamar yadda naga yayana yayi wato
muka durkusa har kasa muka gaidashi,
"Yaya sunanka dana"
Alhaji ya tambaya , na sunkuyar dakaina yayin danake
cewa
"sunana umar"
"Allah sarki"
Yace dani
"Sunan naka da dadi"
Ya hadani dana cikin kantinan yace sununamin abinda
zanyi.
Aranar wuni nayi ina mimmiko kayayyaki.
Da akatashi aka bani dari biyu na hau mota sallama kuma
akace sai sati sati.
** ** ****
Ahankali kwanaki suka cigaba da zukewa irin zukar da
takarda ke yiwa ruwan biro.
TO FA ABI YAFARA KYAU GA UMAR
KUTAYASHI MURNA SAIDAI BANSAN
KO NAN GABA BA
@mr shuraih 99%
.zan ci gabaTARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 10
** ** ****
Ahankali kwanaki suka cigaba da zukewa irin zukar da
takarda ke yiwa ruwan biro.
Ahaka nafara kirga makonni
Ko kusa bazaka hada samuna na kasuwa dana makaranta
ba.$
Bada dadewaba nafara haskaka kantin.
Sakamakon iya mu'amala da jama'a da kuma ilimina
hatta kantinan makota idan akayi bakon bature ni suke
zuwa su kira.
Wannan si yasa akafara yimin lakabi da bakin bature.
Na shiga ran alhaji matuka sai yafara aikena wurare
dabam dabam sai ya zamto kullum da alhaji yafito toni
nagama zama .
Jeka nan tafi can kai wannan karbo wancan, kai dade
sauransu.
Amma duk samunnan danake yi dinki daya kawai nayi.
Sauran kudadena kuwa nakan kashesune aharakan hada
lefena.
Wannan yasanya watarana daya daga cikin abokan aikina
yake tambayata
"Wai kai umar mai kake da kudine?'Ullum kana samu
amma ba'agani jikinka"
Nayi dariya
"Jamil kenan kowanne mutum kasan yanada manufa,
abin dayasa kake ganin halka bawai kwalliya kuka fini son
yiba.
Bukatun kudi danakedasu shiyasa kukaga ina tattalawa"
Yarike baki
"Kai kuwa wani irin bukatune wayannan dahar sai ka
takura kanaka zaka biya?
Nagafa ko aure baka dashi"
Nakalleshi
"To mai aurene kawai yake da manyan bukatu?ka tsaya
idan lokaci yayi zaka gni"
Dai dai wannan lokaci alhaji yashigo ,wata kyakkaywar
sailulace ahannunsa.
Ni dai tunda nake bantaba ganin kan waya mai kyawun
na Alhaji ba.
Wannan yasanya akullum alhaji yana waya nakan bishoi
da ido har yagane yanda nake nuna sha'awata da kan
wayar wannan yasanya shi yimin karin bayani akan
muhimmancin kan wayar.
Ya kuma shaidamin naira dubu dari biyu yasiya nayi
matukar mamaki da jin haka .
Dubu dari biyu ai kudin kyakkyawar motane .
Da alhaji yazo ya tsaya akusa damu
Sai naji ashe suna tattaunawa ne da wani mutum mai
harkar setlit.zance da akeyima zai kawo setlit ne guda
biyar.
Kuma duk za a sanyasune a sabon gidan da alhaji yake
ginawa.
Ni alahaji har mamaki yake bani komai nasa sai ya
burgeka.to amma mai zaiyi da wannan sabon gidan alhali
ko haihuwa bai taba yiba.
Hirar tasu takare akan cewa za'a aikomasa da kudin gobe
da rana.
(Umar harka fara bani tausayi)
Shuraih 99%
** *** **
Ina cikin cin abin ci alhaji yakirani sai yamiko min key din
motarsa
"Je ka kabude but akwai wata jaka kadaukomin"
Nakarfa na tafi da gaggawa
Ina dauko jakan saina gane kudine aciki babu tantama sai
na baiwa alhaji zan tafi ya tsaidani
Ada nayi zaton zasukai miliyan daya ashe dubu dari da
hamsinne bako maine yajawo hakan ba sai kasancewarsu
yan wazobiya
Ya dubeni
"Kaga kudinnan kakai wa malam abba mai dishi su"
Anan IBB malam abba yake amma naira dari biyu
akabani kudin mashin.
Nafito na tsaya abakin titi shiru babu wani dan acaba
mara fasinja .
Wannan yasa na yanke shawarar nafara tattakawa akafa
har zuwa loakcin da zansamu dan acaba.
3 386
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 9
Saida nashafe wata guda cur harda kwana shida amma
kullum naje sai yace ba'azo an tayaba dana lura sai naga
nima in naje har nadawo ko kuda ban taba gani ya sauka
akai ba .
Wannan ya sanyani yake shawarar na bari sai sati-sati
narika zuwa.
Ina nan ahaka atsakiyar sati nabiyu wanda har nafara cin
bashi saiga wani yaro har gida
"Wai kazo anzo sayen baburrinka"
Nan danan na zari takalma .
Don tsabar sauri kamar na tsahi sama.
Duk da cewa yaron da gudu ya koma amma duk kusan
tare muka isa.
Wani dattijone rigarsa duk dauda yayi furtutu dashi.
Da gani sana'arsa bazata wuce saida harawar dabbobi ba
na sunkuya na gaidashi
"Kaine me wannan babur din"
" Nine baba "
Na amsa masa
"To nasaya naira dubu uku"
Kaina yasara jin kudin tamakar za'asiyi mataccen keke
"Haba baba kadai fadi gaskiyar abinda kasaya"
Ya kalleni
"Kai yaro dattijo kamata baya ciniki da tayi inka sayar to
inbaka sayar ba nakara gaba"
"Kadai kara baba"
Nasake cewa dashi, sai kawai yakada kai yatafi hakika ba
zai kara ba.
Na tuna da dadewar baburdin awajen kotayawa ba'ayi
ba.
Kuma lallai innabari dattijonnan yatafi balallaine asiyaba,
sai kawai nabishi dagudu ina cewa
"Dakata baba"
Baiko saurareni ba ganinhaka yasanyani shan gabansa
"Ansiyar maka baba"
Ya kalleni fuska a turbune yacoi gaba da tafiyarsa,
Nan nashiga hadashi Allah da annabi da kyar na samu
yadawo yabiya .
Na baiwa mai gyaran dari uku yaron daya kirani kuwa
naira hamsin.
Sauran kudin nayi aniyar in na biya bashi sai in ajiye in
rika gutsura ahankali.
* ** **
Nayi tagumi sakamakon wannan tsaka mai wuya dana
shiga al'amarine da banga alamun karewarsaba
"Salamu alaikum"
Akafada daga kofar shagon muryar yaya nane.
Na amsa gami da kokarin mikewa ,sai gashi yashigo.
Nayi masa sannu dazuwa da kuma barka da yamma .
Yasami kujera yazauna
"Umar nasamo maka aiki awajen wani mutum
akasuwarmu"
Sai naji tamkar natsahi narungumeshi tsabar farin ciki,
nafara jero godiya kala da bam da bam
"Ya'isa ya'isa"
Yace dani sa'arda yake dagamin hannu
"Tsaya kaji yadda al'amarin yake"
"To yaya"
Nafada sa'arda na kara matsowa .
"Kasaida hankalinka sosai ayaransa na yanzu babu wani
cikakken mai ilmi.
Shi kuma burinsa akullum yasamu wanda zai
taimakamasa wajen harkar oda.
To ammam shiru kakeji, duk wanda yasamo daya fara sai
cin amana ya biyo baya.
Saboda haka inhar kai gaskiya ka gama warkewa"
Bakina har kunne saboda tsabar farin ciki
Na cigaba da godiya shi kuma yatashi yafita.
Na daka wani tsalle nafada kan katifa.
Waini umar nine zan zama dan kasuwar kwari.
Dama gani dason birni.
Kawai sai nafara mafarkin zaune
Wai ganinan nasha boyel zan hau mota kawai sai sailulata
tayi kara.
$dana fiddo sai naji ashe farida ce kecewa
"Mai gida kayo sauri kazo muatafi yawon shakatawar"
Sai nace
"To ganinan zuwa "
Kawai sai nabude motata na shiga kai naitayin shirme
kala kala tun kafinma naje naga kasuwar.
Da dare banyi wani barcin kirki ba saboda tsabar doki.
Sau uku ina murda hannun agogona ina kara awa guda
guda wai don saboda gari yayi maza ya waye.
Sai na tuna ashe saurin ba'a agogo bane.
Ahaka na hakura saidai naita duba loakci.
Akalla dai naduba sau saba'in ahaka akayi assalatu da
mukaje masallaci muka dawo sai kawai nashiga wanka .
Alhali yayan nawa sai karfe goma yake fita
Akalla dai jiran awa hudu nayi
Da lokaci yayai muka fita .
Rumfar da mukaje katotuwace dabana zaton tana dana
biyu.
Rumfar kawai dazata fita sai dai na Alhaji saminu da
umar lawan yabada labarinta acikin littafinsa "SAURA
KIRIS"
Mutum biyune aciki kuma duk matasa ne kamarni
yayana ya tambayesu Alhaji sukace karfe uku yake fitowa
Wannan yasanya ni faduwar gaba
"Ai munyi dashi nazo dashi da safe"
Yayana yace daso
"Ok kudanyi jiransa"
Wani acikin yaran yafada
Anan muka samu benci muka zauna
Nayi taraba idanu ina kallon masu wucewa.
3 386
" zanje nagabatar dawani uzurine"
"To adawo lafiya"
Ya maido amsa naci gaba da turawa , saida nayi nisa da
ginin makarantar sannan na tasheshi.
Nahau zuciyata na mai matukar tafarfasa saboda wannan
al'amari ahaka na karasa gida cikin rashin kuzari.
*** ** ****
Nan fa aiyuka suka yimin yawa kullum inafama da
matsaloli guda biyu
Neman aiki da kuma zaman banza.
Aduk sanda nake zaune nakan debe kewa da littatafan
hausa na(umar lawan)
Kamar su LINZAMiN DAN ADAM'
BABBAR MADAFA
SaURA KiRIS
Kai dama wasu masu dama.
Kwanaki suka cigaba da karfa karfa.
Akalla ko wacce ta maimaita sau takwas.
Wato wata biyu kenan.
Amma har yanzu banga wata alama dazata bani karfin
guiwa akan samun aiki ba.
Na ziyarci kanfaninuwa da ma'aikatu amma shiru kake ji
Kai kace wani arnen dajine yaje neman aiki da takaradan
tsire .
Tuni yan kudaden dake hannuna sun tafi karaye.
Wannan ya tilasta min canja salo.
Idan wajen dazanje ba mummuman nisane dashi ba
nakan daba sayyada.
Badon kamai ba sai don tsadar man fetur .
Wanda kudin rabin galan sun isheni sati uku ina gwaguya.
Da lamari yakai yakawo sai nadaina zuwa ko'ina,
Daga gida sai gidansu farida.
Ahalin yanzu ina gindin babur dina ba ko'ina zani ba sai
gidansu farida.
Na tashi babur din bayan dana sha fama.
Nahau na nufi goron dutse.
Bada jimawaba na'isa gidan
Tun kafin na sauka farida tafito domin tarata.
Muka rankaya cikin gida .
Muka gaisa da babarmu wadda ayanzu sai ka rantse ni ta
haifa ba farida ba.
Muka zarce falon shakatawa na zabi kujera daya na
zauna.
Farida ta zauna akan hannun kujerar idanuwanta kyar
akaina .
Kullum nazo haka take taraiyarayata takasa tsaye takasa
zaune.
Itace ta zauna ahaguna,
Ta dawo dama ta tsaya akaina , ta zauna agabana kaidai
abubuwa da bam- da bam nikaina nasan farida tana
kaunata irin kaunar da bantaba zaton zata yiminba ta
dubeni bayan data ajiye min tataccen lemo
"Umar dan Allah ina roko agareka"
Na kalleta bayan dana zuki ruwan lemon
"Inajinki"
Taci gaba
"Kaje ka kawo sadaki sai adaura mana aure izan ma baka
da kudi bari na baka"
Na kalleta a firgice
"Farida bari ma wannan zance ni da yanzu bana aiki yaya
za'ai nayi maganar aure? Dame zan rikeki farida"
Tayi dariya
"Kaji ka da wani zance to menene amfanin albashina?
Albashina ya ishemu
Wajan zama kuwa dama basai nafada ba, mummy ta
koma sama sai ta barmana nan kasa idan kuma bakason
zama da'ita sai nakama mana haya.$
To me kuma yarage? Ballantana kasan mummy ba'irin
sauran mata bane.
Kaima kagani dakanka "
Nagirgiza kai
"Duk naji jawabinki amma ban karbi rokonkiba.
Ki kuma tuna nayi miki alkawarin akwati biyar kuma
bazan saba ba "
Ta dakatar dani
"Bari wannan zancen umar aicewa kayi idan kana da hali.
Kuma baka dashi yanzu kaga ba saba alkawri kayiba"
Nayi dariya
"Ai halin danake nufi farida shine rai da lafiya , ahalin
yanzu ban rasa ko dayaba"
Ta daure fuska
" Nidai inhar nizakayiwa to banaso, mummy ma kuma
bazata karbaba "
Nayi dariya
"To mummy din taki ce ke kadai"
Ta kalleni
"Naji batawabace nikadai ba kuma bari ganin kafini gata
agunta dakayi magana sai tace haka za'ayi bama ta
sauraron zancena, to wallahi akan wannan bazata
goyama bayaba.
Kawai saita goyi bayanka akan abin dzaka takura? To akan
wannan kam gakucan da mummy arana"
Na mike tsaye
"To zaki gani nasan yadda zanyi na shawo kanta"
Itama ta tashi
"Barima zato bazata taba yarda ba"
** ** *
Zama yayi zama tuni kudaden hannuna sun gama karewa
.
Wannan ya tilastamin saida akwalar baburdina.
Na turashi inda akeyimin gyara nace asanyamasa ganye.
Haka kuwa akayi.
To ashe aiki aka samamin bansani ba
Saida nashafe wata guda cur harda kwana shida amma
kullum naje sai yace ba'azo an tayaba dana lura sai naga
nima in naje har nadawo ko kuda ban taba gani ya sauka
akai ba .
TOFA GA BABUR INA MAI SAYA
SAIYA TUNTUBENI
@mr:- shuraih 99%TARAR ARADU
3 386
Domin kaucewa wasu kananun maganganu, kisani yanzu
duniya ta zuba ido akanki , idan muka yi aure babu lefe ,
maganar daza ta yi ta yawo shine neman kai ake daka
shiyasa ko lefe ban yimiki ba.
Ni kuma inaso innuna ma duniya cewa kaunar ki nake
jini da tsoka don babbar abinda natsana bai wuci ace ba
auren soyayya mukayi ba"
Ta bata rai
"Tokai ina ruwanka afadi duka abinda za'afadi magana
zata warwaremana aurene"
"Jini farida na rantse da Allah indai ina da iko sai nayi miki
akwati biyar"
Ta mike tsaye
"Kasan kuwa abin da kake fada? Ni yar gidan wata
shugaban kasace daza'a yimin akwati biyar"
Nayi murmushi
"Kinfi yargidan ko wane shugaban kasa a wurina babu
kamar ki aduniya.
Farida ki shaida ina yimiki kaunar dazan iya bada sadaki
da raina"
Ta girgiza kai
"Gaskiya umar banyadda kayimin akwati biyar ba"
Na mike tsaye
"Bakin Alkalami yabushe farida "
* * ***
Na zage rubutu da cak , yaran anaji shida sun nutsu,
Inajin dadin yadda yara ke bani hankalinsu izan ina bada
assignment.
Najuyo na dubesu adaidai lokacin dana kare rubutu.
Ian shirin fara bayaninewani yaro ya durkusa agabana.
"Sir principle yana magana"
Nayio mamakoin abinda zai sa principle kirana awannan
lokaci.
Hakika yakan kiarani fiye da kowani malami wani loakcin
kira mai ma'ana wani lokacin kuma hayaniya kawai.
Na ratsa yara kai tsaye kuma na nufi kofa .
"Gani yallabai"
Nafada aloakcin danake kokarrinn zama akan kujera
hannuna furtutu da garin cak.
Yadago daga barin rubutun dayake ,ina iya hango
idanunsa kadan kadan ta cikin bakin gilashin daya
makala.
Fuskarsa kuma ta nunamincewa yana so ya gabatar da
wani bayani dayake dauke dashi muhimmi
" Wato umar nakirakane saboda wata matsala data dade
tana faruwa nasha ji da kunnena kuma andade ana kawo
min kara, wani irin turancine kake koyar dayara abin ko
ka'ida babu?
Ya zakarinka koyar dayara turanci broka , ko anfada
maka nan kasuwar sabon garice?
Gaskiya bazai yiwu mu tafi dakaiba mai cigaba muke
nema bawai mai kawo ci baya ba.
Saboda haka daga yanzu.........."
Yayi shiru baiyi magana ba na cika da mamaki wainine
nake koyarda turanci broka .
Wannan zacene mara tushe shi kansa pricinple din
baikaini iya yturanci ba.
Nakan fitar da kalma bayan kalma yadda kasan baturen
gaske
Wanda hakan yasa ake min lakabi da toni blayer.
Amma duk gashi ana kokarin kiransa a matsayin broka.
Na dubi principle
"Yallabai wayanda suka kawo maka koken sun gabatar
maka da shidace"
Yadaka min tsawa
" Wata shaida tunda nima naji da kunnena"
Ya watsomin takardu
"Tuni mun rika mun mika matalarka a ma'aikatan ilimi
kuma sun bamu madadinka, kana iya hangowa ta
window gashi can atsaye"
Nawai waya domin ganin wanda ake kira madadina wani
mutum ne mai yawan suma da gashin baki.
Najuwo ga principle fuskata cike da alamun karaya.........
...
TOFA UMAR YaFARA SHIGA
@mr:- Shuraih 99%
To be con.........
Keep followin.....
TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 8
Fuskata cike da alamun karaya
"Don Allah yallabai ka taimakeni"
"To wane tai mako kuma zanyi ma?
Kai dana fadamak maganar har taje ma'aikatar ilmi.
Katashi kawai kabani waje kaine kajawo wakanka"
Nayi tsawon minti biyu awajen banko motsa ba.
Daga bisani sai na tattara takarduna na dube shi
"To shikenan yallabai Allah ya taimaka"
Bai amasa maganar tawaba na fito daga ofis din cike da
mamakin wannan lamari.
$hakika zancene mara tushe ballantana makama.
Kuma lallai anzalunceni ayanda aiki yake wuya.
Ballantana kuma a wannan lokaci danake kokarin
mallakar masoyiyata farida.
Hawaye yazubo min daga idona lokacin danake kokarin
barin ginin ofis din.
Ahaka nanufi wajen babur dina saidai na yanke shawarar
na tura shi waje tukuna.
Domin tashinsa anan ciki zai iya juyo da hankalin kowa
nikuma banaso aga tafiyata.
Nafara turawa ahankali
"Mallam umar ina zuwa hakane"
Tambayar mai gadi lokacin danake kokarin fita"
3 386
"Karabu da farida tun kafin karasa ranka,karabu da ita
tun kafin ta zamto maka cowon ajali"
Na gwale ido saboda tsoro , akuma lokaciguda dana fara
tambayarsa cikin rawar murya .
"Saboda me"
Yadaka min tsawa , duk da awayane saida cikina tai kuka
"Karabu da ita muddin kai kanason rayuwarka ,inkuma
duniya ta isheka sai kafada
"Wai me isa"
Nakara tambayarsa
"Farida bazatayi aure ba har abada"
Lafazinnasa yabata min rai bansan sa'an danace
"Kar ya kake ba"
Ya barke da dariya wadda saida na kauda kan wayar yaci
gaba.
"Dan samari da karambani kake inakai ina karyata abin
da'aka ba ka labarinsa"
"Karya kake"
Nasake fadi
"Farida zatayio aure kuma ni zata aura"
" Shikenan babu mamaki amma dai ba'awannan duniyar
ba"
Na fusata
"Kai makaryaci awannan duniyar kuwa"
Yasake dakamin tsawa
"To shikenan tun da zaka iya TARAR ARADU DAKA .naga
kai mai musune, zamuyi wasa dakai yanda akeyi da dan
biri,sannan a karramaka kamar yadda ake karrama kudi"
Kafin nasake magana ya ajiye kan wayar.
Na dawo shago duk jikina a mace .
Babu mutumin nanne da farida tabani labari.
Inkuwa hakane hakika ina kan hadari.
Sai na kudure azuciyata bazan bawa farida labari ba.
Domin hakan zai iya tashin hankalinta harta fara hangen
kin yiwuwar aurenmu.
Ni kuwa bazanso hakaba. Sannan kuma na kudiri aniyar
bazan shaidawa yayana ba.
Domin kuwa shaidamasa kamar cinna ma takardar
alkawarinmu aurenmu da farida wutane,
Domin babu makawa zai rabani da'ita
Nikuwa ahalin yuanzu duka biyun sakamako daya zasu
bayar, tamkar shida atara da uku ne,da kuma uku atara
dashida,kowanne tara kenan
To hakama in har kaunar farida zata jamin mutuwa to
hakama barinta zaijamin.
Domin ahalin yanzu inna rasata ma zuciyata na iya
bugawa to kaga da wuya ya kasheka gara dadi ya kasheka
to waima da yake cewa zai yi wasa dani.....
@mr:-Shuraih 99%
Zan cigabaTARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 7
Domin ahalin yanzu inna rasata ma zuciyata na iya
bugawa to kaga da wuya ya kasheka gara dadi ya kasheka
to waima da yake cewa zai yi wasa dani kamar dani biri
yana gani mutane zasu bari a dauramin igiyya a kuguna
arinka ja a kasuwa ne?
Ashe makenan dubunsa ta cika .
$sai najini ina mai murna da wannan matakin dayace zai
dauka ,
To amma karramani dayace zai yifa yadda ake karrama
kudi.
Nadade ina tunani daga bisani nagane babu wani karamci
da kudi suke samu fiye da kashe su,
To kasheni za'ayi kenan kwarai kuwa babu tantama
kasheni zaiyi kamar yadda ya kashe uku abaya,
To amma wannan bai dameni ba dukwanda ya mutu
kwanansa ne ya kare.
*** ** **
Na dubi farida bayan dana lume acikin kujera
"Allah yakaimu ranara daza mukasance kamar haka
acikin daki daya a matsayin miji da mata"
Tayi murmushi
" Amin umar Allah yakarbi addu'arka har yanzu banji
kana maganar daurin aureba"
Nakai idona gareta
"Akwai dalili farida shiyasa kikaga banyi magana ba"
Ta maido hankalinta gareni
"Wane dalili"
"So nake nagama hada lefe"
Tarike baki
"Wani irin lefe kuma umar"
Nakalleta lefe kala nawa kika sani?
Aiduk inda kikaji ance lefe akasar hausa ana nufin kayan
da mai nemar aure zai kaiwa wadda yake nema"
Ta karkada yatsa
" Sam karma ka soma don kokayima bana so mummy
ma bazata karbaba.
Sadaki kawai zaka kawao shima bamai yawa ba"
Nayi dariya
"Farida arayuwar da akeyi irin na yau duk masoyi yakan
nuna kaunar dayake yine ta hanyoyi irinsu lefe.
Bawai ina nufin wajibi bane kokuma abin dayake makale
da shari'a
A'a saidai inda hali akwai bukatar kayi lefe mai yawa
domin toshe bakin masu kushewa. Saboda an riga anbata
lamarin aure
" Tayi tsaki
"To kai ina ruwanka da masu kushe kabi hadisi mana
daya kecewa mafi albarkacin mace mafi karancin
sadakinta"
Najin jina kai
"Babu shakka farida hakane ni kaina na kanki abubuwa
na bidi'a
To amma tunda wannan baisabawa shari'a ba nayi aniyar
yi miki lefe na ban mamaki.
3 386
da baka ta fadamin
Duk samarin farinda dasuka shede bataga wabda suka
dace da juna kamar niba.
Allah yabar ku tare har abada naji dadin maganar.
Yau ranace ta lahadi da kuma muka shirya zuwa yawon
bude ido dabi da masoyiyata.
Sabbabin jacket nasiyo musamman don tafiyar ta kara
armashi
Nahadu iya haduwa. Ga wanda bai sanniba zai dauka dan
wani ne daga yayan jiga jigan garinnan nan kuwa ba haka
lamarin yakeba.
Na iso gidan su farida da misalin karfe hudu, ahalin yanzu
nazama dan gidan salllama kawai nayinashiga,
Na tarar da mahaifiyarta tana karanta wat mujallar Africa
banyi mamaki ba
Sakamakon cewa na dade da sanin cewa tan jin har shen
nasara sakamakon zama a kasar ingla na tsuguna na
gaisheta ta amasa da fara'a bisa dukkanin alamu shigar
tawa ta burgeta.
Ta nuna min dakin farida......
@mr shuraih 99%
Tobe con....TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 6
Ta nuna min dakin farida.
"Tana nan inaga shiryawa takeyi"
Ba'ajimaba ta leko
"Umar shigo mana"
Na karasa ,bayau na fara shiga dakinba yanada tasari
matukar tsari.
Akalla yalunka nawa ko uku ko hudu.
Na cusa kaina bayan nacire takalmi.
Tuni tagama shiryawa tana daure gashin kanta ne da
ribbon.
Na kalli dressing din nata na doguwar riga mai hade da
wandonta,da kuma gyaran mayafi. Hakika sun yimata
kyauw
Ni kaina sai na tabbatar da cewa farida tafi karfina.
Sai kuma na sami zuciyata tana mai rayamin cewa afasa
tafiyar kar naje wani ya ganta ya kwacemin ita.
Maganarta ta katsemin tunanina
"Muje ko umar"
Nafito yayin data biyoni.
Mahaifiyarta ta kallemu ta jinjina kai gami da cewa
"You match each other"
Cikin wani harshen dabashi da banbanci dana turawa ,
nida farida muka kalli juna gami da musayar murmushi.
Bisa gaskiya .
Gasikaya ne abinda tafada ta dubemu
"Kuna da camara ko"
Na girgiza kai
"Bamu da camara"
"Tafiyar taku bata cika ba, a london duk duk inda zamuje
da Alhaji da camera muke tafiya haka kuma zaka rinka
gani ga duk saurayii da budurwa"
Ta mike tsaye
"Bari dauko muku tawa"
Ta shiga daki bada jimawa ba ta fito.
Yar karamar camara ce mai ban sha'awa, ta bude kwalin
film ta loda, sannan ta dubemu
"Kuzo nafarayi muku kala daya"
Muka jeru nida farida muna jiran muga ta dauka,
maimakon haka sai ta kama dariya, tafara magana
"Karfa nace muku kauyawa, ahaka za'ayi hoton? To
ma'anar me yabayar? Kubari kuga yanda za'ayi"
Ta nuna mana wata fulawa dake tsakiyar gidan
"Ku koma can, kusa fulawar a tsakiya"
Muka kamar yadda tafada.
Sannan tace
"To kai umar tsinki fure ka mika mata ke kuma miko
hannu ki karba, ku kumayiwa juna murmushi"
Mukayi kamar yadda tafada , sannan hoton,
Kyamarar taja film automatically.
Ta mikomin kyamarar
"To kunga yadda ake hoton soyayya , idan anyi aure
kuma akwai wani salon daban,dasannu zan nuna muku
shi duk randa aka daura maku aure"
Nayi dariya
"Mungode mummy"
Surukartawa tana burgeni, yadda take bidani ta hanyoyi
na musamman babu abin da yadameta tamkar ba suruka
ba.
"To zamu tafi mummy"
Farida tace daita
"To adawo lafya"
Gab da zamu shiga soro tafara magana
" Ina kara tunatar dakufa"
Muka waiwayo domin jin abidna zata fada , tayi
murmushi
" Kun dace da juna "
Muka kalli juna nida farida mukayi musayan murmushi.
Sannan muka juya gareta gaba daya.
Akuma lokaci guda muka hada baki
" Thank you mummy"
** ** **
Na bude shagona bayan dana dawo daga koyarwa .
Bayan na ajiye takardu sainafara tunanin yin wanka.
Na dubi ruwan wankan wanda ni kawai yake jira na
watsashi, adai dai lokacinne aka turo kofar cikin gidar
"Umar ana waya"
Inji matar yayana na dubeta
"Wanene yake waya? Ko baba ne?"
Ta juya hannu
" Ba baba bane yadaice kai yake son yagani"
Na jawop kofar shagopn na bita ciki, ina zuwa na dauka
na kara akunne
"Hello! Wake magana?"
"Ina ruwanka koma waye? Kadai kasa kunne da kyau kaji
abinda za'afada"
"Ina jinka"
Nace dashi yacigaba
3 386
fara soyayya da wani matashi habib , dan kasuwar kwari
ina mutuwar sonsa ana kokarin samana rana .
Watarana yazo tsallakawa titi dominisa wajen motarsa
wani mai mota yazo ya bankeshi.ko shurawa baiyiba .
Mai motar kuma yagudu"
Sai naga hawaye nazuba daga idonta .
Tacigaba
"Naci kuka har na gode Allah bayan komai yalafa sai
muka kulla da wani ma'aikacin savannah bank mai suna
isma'il soyayyar dayake nuna min hartamantar dani na
habib.
Asheshima ba rabonane ba.
Babbar motace tabi takan motarsa starlet.
Da kyar akaringa banbaro namarsa gashi kuma cikin
darene abin ya afku.
Ba'asan inda mai motar yayiba.
Hankalina yayi mugun tashi yanda kasan nayi hauka
sabida yanda nakeson isma'I'll banso habib ba,
nakasance cikin damuwa yanda samarina ke mutuwa
haka , sai natina zancen mutuminnan shkekaru biyu dasu
ka gabata.
Babu shakka shirinsane anan na shidawa mahaifiyata.
Tace saidai Addu'a tunda ba'asan inda yake ba .kuma ni
kaina tundaga ranar bansake jin duriyarasa ba.
Aifa wannan abubuwa dasuka faru suka sanya akafara
yimin son rakumin yara.
Sai dai mutum yabar kaunar dayakeyimin azuciyarsa
amma babu damar ya baiyana.
Na nesa kuwa ko mutum yafara zuwa sai naga ya janye
narasa dalili.
San dade ana haka sai wani dan'uwana yace yaji yagani
babu wani mamaci sai wanda kwanakinsa suka kare.
Saboda haka yace mahaukaci yahau kura
Sabida haka muka cigaba da soyayya abin gwanin
birgewa har ya mantar dani duk nabaya aka samana
rana.
Sai da abin yarage sati daya kawai akka tsinci gawarsa a
tsakiyar titi.
Aifa daganan sai zamto mujiya ma tafini farinjini.
Babu wani saurayi da yake fuskan tata"
Saita fashe da kuka har nayi zaton bazatayi shiruba.
Nima saida kwalla tazubo min don tausayawa taci gaba
"Wannan shine dalilin dayasa kaga naki amasa maka,
domin kuwa duk wanda ya kulla alakar soyayya dani
sunansa matacce, nikuma banso wani abu ya sameka.
Na dauki kaddara akan cewa Allah bai yi zanyi aure ba.
Domin kuwa har sai na sami wani ya dan kaunace ni
sannan zan ji sarai. Wanda ahalin yanzu abune mara
yiwuwa"
Nadaga mata hannu
"Dakata farida ni ina kaunarki"
Ta girgiza kai
"Bazai yiwuba umar banaso ka mutu sabida kaunar
danakeyi maka"
Na dubeta
"Don Allah farida da gaskene kina kaunata?"
Ta gyada kai
"Wallahi umar inayi maka kaunar da bantabayi ma wani
kamar taba"
Na mike tsaye
"To in hakane farida na daura damarar neman aurenki
koda zan mutu"
Na sun kuyo kusa da fuskarta.
"Wallahi farida babu wata wuya dazatasa na dakata"
Ta girgiza kai kuma alokacin data kirawo sunana ahankali
"Umar ,zaifi kyau kaje kasami. Wata domin samawa
kanka kwanciyar hankali"
Na bata fuska
"To ba kya kunata kenan"
Ta girgiza kai
"Bahaka bane"
"To kice kina kaunata da aure"
Tayi shiru kawai tana dubana
"To shikenan farida barinatafi tunda bakya klaunata"
Najuya cikin hanzari ,ta tare kofar na kalleta babu alamar
fara'a a fuskata
"Way or reply"
Nace da ita , murmushine yafara sauka akan lebenta
,sannan tafara fadin wasu kalmomimasu tsada
"Ina kaunarka da aure umar"
Sai wani farinciki ya mamayeni, kaunarta ya kara shiga
raina murmushi ya kubuce min.
Akuma lokaci guda dana sula le akan kujera.
Ban kula da hadarin dana ke akai ba.
"Za kiga abinda ake kira tsantsar kauna farida"
Shine abinda bakina yafara fada.
* ** **
Tun daga ranar danaje gidan su farida sai ya zamo a
kowane lokaci in ina tafiya akan babur nakantafine cikin
taka tsantsan.
Kai kace mai keken daya doro ciyawa gaba da baya kuma
ya debi garke tumaki,badon komaiba kuwa saidon samun
garkuwa daga mutumin da farida tace min shine
sanadiyyar mutuwar masi neman arenta har mutum uku
Na kirga adadin makwanni cikin tafi daya.
Amma har yanzu banga abinda ya sameni ba nida farida.
Munyi matukar shiga ran juna.
Soyayya agida sannan wani salon dabn a makaranta.
Mahaifiyarta tayi matukar faribciki da soyayyarmu, baka
3 386
gilashin na kofar direba ta fara janyewa ahankali, yana
gama janyewa sai naga ashe wani matashine jibgege
bakikkirin mai jajayen idanu.
Koda acikin dodanni na tabbata baza akirashi mai
kyawuba
Ya yaye fuskarsa yazuwa abinda yake murmushine,
nikuma aganina abinda yayi yafi kama da hammar jaki
"Yan mata shigo na rage miki hanya mana"
Yafada awta muryarsa mai kama da kukan balamar
tunkiya, na kau dakai daga kallonsa domin tsoratani yake
Akuma lokaci guda nakecew
@mr:- Shuraih 99%
"Jeka abinka na gode"
Sai ya leko da kansa waje wanda ke tsugune akan
wuyansa mai guru guru
Kamar gurun diro.yaci gaba da dubana da idanunsa
wanda suke zurma zurma kamar ramin tanda ,wayanda
suka sa war ga jejen hancinsa atsakiya.
Yaci gaba da magana da bakinsa irin na kada .
"Don Allah 'yan mata kishigo mana"
Nafara matsawa
"Nagode nace dakai"
Ya biyoni yaci gaba da nacinsa. Ana hakane mota tazo
natare na shiga.
Mummunar mutumin yabini da kallo.har muka bace
masa bai motsaba , akayi tafiya har akazo inda zan sauka
nabiya kudi dana fioto.
Nakama hanya zuwa gida bayan na tako kofat gidanmu
sai naji horn din mota.
Ina waiwayawa sai naga katon mutuminnanne
"Zan dawo da daddare"
Yafada cikin daga murya kamar kwamandan sojan daya
ke bada umarni.
Bancemasa komai ba nashige gida,
Banma sake yin tinaninshi ba da daddare kuwa sai gashi
an aiko.
"Wai farida tazo inji wanda sukayi alkawari"
Na dade ina kokarin tuno waye wannan bantuna ba sai
daga baya mutuminnan yafado min a rai.
Babu shakka shine nayi tsaki na dubi dan aiken
"Kace mata waidon Allah yayi hakurin anyimata miji"
Yayi ta maido dan aiken nace masa kar ya sake shigowa.
Nama tsahi nasa sakata akofar gidanmu ganin haka sai
yatafi yayi ta zuwa gidanmu jefi jefi na ki fita har watrana
mahaifiyata tace min ya wajaba na fita banda zabi dole
hakan akayi.
Yayi ta suratansa bance masa komaiba
Sai da yagama hayaniyarsa. Wadda take bayani akancewa
wai yana kaunata ni kuwwa banga abin da zaisa na'auri
mutumin wanda yafi kama da naman daji koda kuwa
maza sun kare.
Wannan yasanya ni cewa dashi
"A gaskiya karatu nake kuma bana zaton zanyi aure sai
sama da shekaru goma"
"Indon wannanne zanyi jiranki"
Raina yabaci yanda mutumin ke kokarin likemin tamkar
kaska
"Kai kaga kaje kawai kanemi wata "
"Kece kikayi min"
Yaci gaba dafada nayi tsaki sannan nayi tahowata gida.
Washe gari yasake dawowa naki fita.
Wata washe garin sai yatareni an taso daga makaranta
yafara yimin shirme.
Nikuma kiyayyar danakeyimasa takai intaha.
Wannan yasa na kalleshi afusace
"Mallam bari infada ma gaskiyama ni dai bana kaunarka
bakuma zan kaunaceka ba , zai fima sauki kaje kanemi
daidai da kai"
Ya fashe dawata irin dariya wadda take bada amo tamkar
ana tuttule ruwa daga jarka.
Yadade yanayi har ya tsoratani ,tamkar kuma dauke
wutan nepa sai yayi shiru gaba daya.
Nan danan fuskarsa takara muni sakamakon bata rai
dayayi.
"Yarinya kinyi shirme kintafka babban kuskuren
dayakamata aganar dake"
Ya nunani da dan yatsansa mai kama da busasshen itace,
Yayi kasa kasa da murya.
"Babu duka babu zagi saidai zaki mutu babu miji"
Raina ta baci na watsa masa kasa
"Aniyarka tabika saidai kai kamutu babu mata "
Yayimin wani kallo sannan yahau motarsa yatafi.
Da ganan muka rabu da mummunan mutumin.
Baisake zuwa gidanmu bako kuma ya tareni.
Ni kuwa gani da farinjini.
Aka rinka zuwa wajena naki fita don saboda ina ganin
hanani karatu za'ayi. Don babu abinda irin da daddare
narinka nazari , ahankali na.
@mr:-shuraih 99%
Tobe conti.......
Tobe cont......
@mr:- Shuraih 99%TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 5
Ni kuwa gani da farinjini.
Aka rinka zuwa wajena naki fita don saboda ina ganin
hanani karatu za'ayi. Don babu abinda irin da daddare
narinka nazari , ahankali na kammala digirina akan
mathematics .
Nakuma yi bautar kasa, sai maganar aure . Nan muka
3 386
Nidai nasan ba'ace dan tasami kudiba.
Banyi aune ba sai na ganni atsakiyar gidan aifa sai na ne mi kidimewa saboda tsabon tsari da kayatarwa.
Ta nufi wani daki dani tasa hannu ta tura kyauren na gilashi,
Ta tura kai ciki sa'arda ta kecemin shigo,
Nasa kafata nayi mamaki danaji sanyi ya dokoni alhali lokacin zafine, sai na tuna A.C babu shakka itace aka kunna ,
Na ratsa ta wani kilishi daya mamaye ilahirin dakin da a gidan nake to da babu ruwana da katifa kansa kawai zan rinka zuwa ina yin baccina.
Na dubi wasu maka makan kujerun dasuka mamaye dakin tai min nuni da daya
"Zauna umar"
Na juya nazauna sai naji nayi kasa zan nutse ,nan nafra zargin farida da laifin zaunar dani a bulalliyar kujera -kome yasa tayi min haka?
Kawai sai naji nadakata nan nagane ahe ba bulewa tayiba duk laushin soso ne.
Na jinjina kai lallai masu mura suke da tari.
Ta nufi kofa loakcin da takecewa
"Ina zuwa"
Bata dadeba ta dawo rike da farantin silverm
@mr:-shuraih 99%
Ta ajiyeshi akan wani karamin table sai naga kofa tabude wata matace ta leko.
Ita da farida tamkar an tsaga kara.
Sai nagane mahaifiyartane na sauka har kasa na gaidata tayimin kyakkywan maraba, sannan tafita na dubi farida
"Mai yasa baki kirani naje nagaishta acan ba sai ki wahalar da'ita kisa tazo nan"
Ta waiwayo gareni cike da murmushi
"Lallai bakasan momi ba umar, wani irin haline da'ita da kayi wahala dominta gwara ita ta wahalar da kanta yanzuma babu yadda banyiba akan tabari zamuzo ku gaisa tace a'a zan wahalar dakai"
Nayi murumushi gami da fadin
"Allah sarki"
Na gane mahaifyar farida irin mutanenane masu saukin kai,ta zauna akan kujerar dake kusa da tawa bayan ta gama bude tan garayen,
Dan kalin turawane wanda akahadashi da kwai aka soya sai kuma wani hadadden kosan doya.
Ta tsiya ya ruwan tatacciyar abarba akofuna sannan ta dubeni sa'arda ta ajiyemini cokali mai yatsu.
"Bismillah umar"
Muka fara gabatarwa harzuwa lokacin danaga ya kamata na dakata sannan na kora ruwar abarbar nayiwa Allah godiya.
Ta kawar da kayan gefe sannan ta fuskanceni
"To umar naga kana nema kadamu akan rashin baka amsar tambayarka ,to dayardar Allah ayanzunnan zan warwaremaka zare da abawa"
Tacigaba
"Ni da ka ganni yar wani hamashakin mai ar zikice mai suna. Alh Hashim.jigon dan kasuwane maiyin harkokinsa akasashen turai,kuma nan dakake gani dayane daga jerin gidajensa guda goma,kuma shine mafi kankanta dakuma muni"
Nakame baki jin abinda take fada
"Kwarai kuwa"
Ta tabbatar mini
"Yana da gidaje a Kaduna ,legas,Abuja kai harma da birnin london"
Zan cigaba
@mr:-shuraih 99%
TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 4
Na Jin jina kai taci gaba
"To kuma matarsa biyu hajiya halima uwargidan da
kuma hajiya safiyya wato mahaifiyata, kuma ita
uwargidan yayanta hudu uku maza daya mace.
Mazan kuma sune manya kuma abokanan harkar
mahifinmu wato masu taimaksa,ni kuma ni kadiace
awajen mahaifiyata.
Ina da shekara biyu Allah ya karbi abinsa kuma yayyen
namu sune suka san kudaden mahaifinmu na banki
hakanan kadarorinsa.
Wannan yabasu damar yin rubda ciki akan
kudin,hakazalika kadarorin, gidajenma cewa sukayi uku
kawai yabari duk sauran ya sayar dasu yabiya bashin
kamfaninnuwa.
Sai suka bamu wannan gida dakuma naira miliyan daya"
Nakar kada harshe game da jijjiga kai
Taci gaba 'yanuwan mahaifiyata sunta bata shawara akan
takai kara amma tace sam wanda yatara dinma yau ina
yake? Saboda haka ta hakura
Arzikin dake tsakanin suma na 'ya ai ya isa tayi ta renona
ta sanyani a nursery kai har zuwa lokacin dana sami shiga
jami'a nai ta fama da takardu daga samari.
An kuma sha tareni fuska da fuska.
To amma ban kula ba domin alokacin burina nayi digri
na kuma sami damar tallafawa kaina da mahaifiyata.
Kamar kullum na tsaya abakin titi don samun mota
akokarina na dawowa daga makaranata.
Wata honda hala tayi fakin agabana, ahankali bakin
3 386
yabada sa'a"
Ta kwantar da kai
"To Allah ya taimaka "
"Amin"
Nafito nabarta .
Raina yabaci yayinda na iso soro,baodn komaiba sai don
bata min lokacin da mashin zaiyi.
Na turashi har muka zo waje.
Nakafeshi nafara bugawa nayi tayi amma ina ko amsawa
bayayi kamar wanda na cika tankinsa da ruwa .
Yara kuwa sukazo suka yanyameni,kullum haka sukemin
in har nazo fita da yamma ,sukanyi ta dariya sa'arda nake
bugawa.
Wani lokaci nakanji kaman nasa duka amma sai na daure
na rabu dasu.
Har ina shirin hakura sai naji yafara amsawa.
Wannan yasa nacigaba banfi bugu ashirin ba kuwa
yatashi.
Yara suka kaure da shewa ye !yatashi yatashi!
Nan fa suka da baya yayinda suka ga dare,badon komai
ba saidon sun san in yayi wata zabura zai iya bi takan
yaro.
Raina yakara baci dana tuna yadda zanyi fama da giya
,amma cikin ikon Allah murdawata sau uku sai fada, na
murza totur sai tafiya ahaka na ringa tuki cikin hkima da
dabara.wai ance inkana da abin hawa dolene kazama
makaryaci saboda takurawar yan aro mai zuwa yau
dabam mai zuwa gobe dabam.
To nidai nakaryata domin kuwa babur dina saudaya wani
abokin aikina yataba aronsa da uzurin gaggawa ya
kamashi,daga ranar shima bai kara araba.
CABDI WANNAN BABUR KO WAHALA DA RAI
Zamu cigaba anjima
By @mr:- Shuraih 99%TARAR ARADU
Littafina daya (1)
Written:- shuraih 99%
Page 3
Adai dai junnction din bariki yellow fifi ya tsaida mu.
Raina yabaci domin kuwa shine abin dana tsana sakamakon rashin wadataccen burki,nayi iya yina domin ya tsaya amma ina ,har nakaiwa yellow fifan sura .yayi tsalle gefe guda .
Da kyar babur din ya tsaya bayan daya tungudi ginin express, na juyo domin bawa yallaban hakuri, sai naga ashe bai dauka da zafiba ,daomin ma dan unguwar ne.
Ba'ajima ba akabamu hannu nafara kokarin sa giya ina takawa da kafa da kyar na samu ta shiga,
Wata rana ma kin shiga takeyi sai nagaji da shan zagi da horn daga masu ababen hawa .
Kai har akwai kwandastan daya taba rankwashina wai tare musu hanya .
Haka naci gaba da taifya rakakai raka kai kamar wanda yake tafiya akan jaki, sauda yawa mai keke yakan wuceni tinma ba idan na hadu da sabon jini ba.
Aje ba'ajeba sai gani a goron dutse na dudduba hakika farida tayi mantuwa wajen kwatantamin gidansu.
Domin kuwa gidan daya kamata yazama nasun sam banasu bane ba.
Saboda yadda naga tsarin gidan ko yar wanke wankensu tafi karfun tayi koyarwa amakaranta.
Sai nafara tunanin yadda ya amata nayi daga karshe na yanke shawarar in sami yaro na tambayeshi.
Haka kuwa akayi ,
Nayafito wani yaro
"Dan Allah zo mana kanina"
"Gani"
Yafada okacin daya iso gareni
"Don Allah kasan wata farida malamar makaranta"
Ya gyada kai lokacin daya ke nuna min
kerarren gidan
@mr:-shuraih 99%
"Ga gidan sunan"
Nacika da mamaki badon ita tace nazo ba da juyawa zanyi domin kuwa nakaraya lallai farida tafi karfina .
Wata kila tayimin hakanne domin innaga gidansu sai in hankalta.
Har zan juya sai natuna yakamata tasan nazo don kartakamni da laifin saba Alkawari.
Na dubi yaron
"Don Allah jeka ka kirawomin ita"
Ya zura min ido kamar maisan yafada min wani abu, da na dauka bazashi ba
Sai naga ya kada kai yace
"Amma dai"
Sai yatafi nabi yaron da kallo shin me hakan yake nufine?
Kokuwa shima yagane cika kainane?
Bai jima ba sai gashi yafito tana biye dashi tana biye dashi abaya fuskarta cike da murmushi.
Ta tsaya abakin kofa , naga ashe farida kyawunta ya wuce yadda nake gani amakaranta, yaron yazo wucewa kusa dani
"Mallam Allah yaji kanka"
Yafada yakuma zura aguje bansa abinda yake nufiba .
Na kafe babur dina na kuma nufi wajenta
"Sannu da zuwa umar"
Tace dani idanunta akaina na amsa da
"Yauwa"
"Bismillah"
Tafada sa'arda take juyawa na bita abaya ta cikin soron wanda aka shimfideshi da tayil mai kayatarwa ,
Araina ina ta sake saken abin daysa farida koyarwa.
Shin sha'awar koyarwar take ko kuma me ?.
3 386
Tra amsa cikin daddar muryarta
To be conti......
Via:- mr:- Shuraih 99%
TARAR ARADU
Littafi na daya 1
Na Umar Lawan
Page 2
Typing and posted by Shuraih 99%
.
.
"Yau narigaki zuwa "
Nace da ita tadan kwatar da kanta
"Nadan ragewa mummy aikine saboda batajin dadi"
Ashsha Allah ya sauwake"
Nadan gyara tsayuwata "don Allah farida idan an tashi
tara ina son magana dake'
Ta kalleni da fararen idanunta sa'ar da take cewa
"Lafya dai ko umar"
Na kauda kaina domin bana jurewa kuramata ido saboda
wani kwarjini da take dashi.
"Lafya kalau akan dai maganar nan ne"
Ta sun kuyuyar da kanta kas daga bisani ta dago
"To Allah ya kaimu"
Muka juya muka tafi.
@mr:-Shuraih 99%
Tunda farida tafara aiki amakarantarnan Allah yasanya
min tsabar kaunarta , nayi kokari in yakice amma ina.
Abin yaki yiwuwa .
Wannan yasa nafara yi mata isharori amma tayi biris
kmar bta gane ba , ga misali nasha sai mata sabulai da
mayuka .
Amma sai dai tayi godiya ta kuma bini da Addu'ar Allah
yabar mutunci.
Wannan yasa nafito fili na shai da mata amma sai tace na
saurara zata tun tubeni .
Kuma shiru kakeji haryanzu taki tuntubata .
Dana tina mata saita kama noke-noke shine yau nayi
kunar bakin wake domin nasan wacce akeciki.
Ana tashi tara na nemi karkashin wata bishiya na hakimce
can jimawa sai ga farida tana isowa
"Mai yafaru ne umar?"
Ta tambayeni bayan data zauna ,nakara jingina sosai
ajikin kujerar danake kai.
Sannan na dubeta na fara dacewa
"Wai dan Allah farida mai yasa har yanzu kika ki bani
cikakkiyar amsa ?
Nidai idan kina ganin babu dama gwanda ki gayamun
insan yanda nayi.mai makon ki kyaleni kullum ina
azabtuwa da tsabar sonki, kuma ina hada ki da Allah ki
shaudamin hakikanin gaskiya "
Na dade ina sauraronta taki tace uffan .sai kawai ta
tokare habarta da hannu,
Babu tsammani kuma sai naga tafara kwalla .
Hakan ya rikitani ,cikin rudewa na fara cewa
"Maganata rai ya bata miki"
Don Allah kiyi hhakuri"
Batace komai ba taci gba da kukanta kawai
"Don Allah farida kiyi hakuri bazan sake tambayarkiba"
Ta girgiza kai lokacin da take share hawaye "umar ba
tambayr kabane ta bata min rai illa iyala wani al'amari
dabam , zan amsamaka tambayarka umar,amma saidai
in antashi kasameni agida "
Nadubeta
"Inane gidanku
Tadanyi jim sannan tacigaba 'goron dutse bayan gidan
isiyaka rabi'u gida mai kallon kudu, na biyu ahannun
dama"
* * *
Dayin sallar la'asar na shiga wankka , nadade ina shekawa
domin kuwa awa guda na karar cur, nakarar da ruwa ya
kai jarka uku, ba'a batun sabulu wanda nakarar da fakiti
guda badon komaiba sai don na kara haske.
Aranan sabon man shafawa nasiyo saboda ji nayi nawa
nada yana wari, alhalin kuma dukranda nashafashi har
tambata ake wannan wane maine?.
Saoda tsabar kamshi, na bude kwaba nayi ta zaro kaya
ina ajiyewa gefe guda ,har nazo kan na cin yewar
,dukranda na sanyasu ka tabbatar zani muhimmiyar
ungwa ko kayataccen fati.
Nan da nan nafara jikasu da tirarena.
Na makala farin gilkashi.
Ban nufi ko'inaba sai gindin dressin mirror don duba
haduwar tawa,
Hakika nafito kamar yadda nayi tsammani, nakalli
takalmana cali-cali wayanda tuni na baiwa shushaina ya
wankeminsu harda karin kudi nayimasa domin yayi mani
wanki na musamman nan danan na zura kafata nafara
takawa cikin takama ,
Kai kace wani dokin dan sarki,
@mr Shuraih 99%
Na kulle shagon nanufi cikin gida anan na sami matar
yayana tana kokarin dora girki.
"Kai umar ina zakne haka kaci kwalliya ?"
Nagoge fuskata da hankici
"Wallahi zani unguwne ,yaya kika ganni,nafito?"
Ta kalleni daga sama har kasa
"Wallahi ka fito"
Kaga yanda kake kyalli kamar sabon kwabo"
Wata dariya ta kwacemin .
"Toh madalla dama haka nakesopn ji"
"Zanyi miki karin kudin cefane tunda kin yaba "
Tayi shewa .
"To mai gida, godiya nake,ince dai ba kishiya zakayiminba
ko?"
Na duba agogona
"Ke dai wallahi kin cika tsoron kishiya kimin Addu'a Allah
3 386
TARAR ARADU DAKA
Littafi na daya 1
Na Umar Lawan
Typing:- Shuraih Usman
.
DANDANO daga cikin littafin
••••••••••••••••••••••••••••••••
Umar ya shiga gararin rayuwa
Inda ya rasa kwanciyar hankali
Sakamakon soyayya da
Yarinya mai suna Farida.
Wacce akan tane mutane uku
Suka rasa rayukansu,
Akokarin neman aurenta.kuma
Shima an gargadeshi
Amma yace yaji yagani
Kuma YATARI ARADU DA KA
Saboda fadin kai
Koya zata kasance kubiyoni acikin wannan littafi mai suna
TARAR ARADU
KunasooooTARAR. ARADU
Littafina daya 1
Na Umar Lawan
Page 1
Typing & posted by Shuraih 99%
.
Na yayi mo takarduna bayan na cika tumbina da
waina.nan da nan nafara angizo babur dina Vespa
zabuwa .zuciyata na mai dari darin dadewar da zan yi ina
bugu kafin ta tashi.
Bayan dana hada waya sakamakon gidan makullin
(ignition)da ya dade da lalacewa.
Abin mamaki yau bugu shabiyar kawai nayi ta tashi .anan
da nan wata kara ta cika wajan kamar an kunna injin
markade sabon washi, saudadama idan ina sabis acikin
gida in har na tasheta yara kanyi sallama ."Ga markade".
Ni kaina duk sanda ta tashi nakan toshe kunnena .
Lokacin kwanciyar zafi yan unguwar mu har basa so nayo
dare .
Darana kuwa matan aure basa son wuce wata wai nakan
tayar masu rigimammun 'yayansu daga barci,kuma na
kan hansu bin sallar jam'I.
Dama gababur babu gudu,kuma nakara kasheshi da kaya
.
Domin kuwa idan nabudema wajen adana kayayyakinsa ,
babu komai illa tulin fulogi wanda nikain nasan suna
ragemin gudu.
Amma inkaduba body ,mai motama sai yayi zaton zan iya
wuceshi har yagaza kamoni.
Nan da nan na dare sama mukafara kokoyi da giya na
dade ina shammatarta kafin tafada .
Aifa shigar giyar kedawuya na murdashi sai tyafiya ,kar
kaso kaga yanda nake doro ina kwambarewa .
Kullum nahau haka nake fankama naketakama kamar
sarki akan doki.
Idan na raina majalisama ko sallama banayi ahaka naita
wuta har makarantar dangiwa commercial secondry
school.
Inda anan nake koyarwa amatsayin malamin English.
Da malam sule mai gadi muka fara gaisawa "har an fito"
"Allah yayi"
Nabashi amsa .
Nakafe babur dina a inda aka tanada domin yin fakin.
@mr:-Shuraih 99%
Na nufi ofishin principle. Ko ba'a fada maka sunansa ba
zaka iya ganewa da kanka.
Domin kuwa yafi dacewa da malam Abba .akwai kwazon
aiki akwai kuma mugun son kudi na gaisheshi muka
kuma taba yar hira wadda zolaya acikinta tafi yawa .
Da fitowata na nufi wani abokin aikina kabir sabi'u. Muka
caccake na dubeshi "naga sai kyalli kake kodai kanasan ka
angoncene ban saniba?"
Yayi dariya" kaifa tsiyarka kenan baka kyale mutum haka"
Muka zauna na shiga dube dube wani lokacin har nakan
mike tsaye "wai kai me kake dubawane"
Na dawo na zauna bayan na gaza hango abin danake
nema "don Allah bakaga shigowar farida ba ?"
Na tambayeshi . Ya tintsire da dariya . "Kai mallam tunda
farida tafara aiki anan naga sai wani kankajeri Kake kana
kara kwalliya ,kodai da watane akasa?"Nace babu komai ,
don mutum ya tambayi abokin aikinsasai yazama laifi"
Ya girgiza kai
"To me isa baka tambayar su hafiz?
Kosu ba abokan aikin kabane"?
Na gyara takarduna sa'arda nake cewa
"Kaga mungama hirar ne ban tambayekasuba"
"To shikenan tunda boye-boye kake ,amma indai kuka
shirya kanku kayi sa'ar mata UMAR"
Bancemasa komaiba ,duk dacewa maganar tasa ta
kayatar dani . Bada jimawa ba na hangota tana shigowa
tana rungume da jakar takardunta .
Mace ce mai matukar tsari da kyau tana da yawan kuya
da kulawa da Addini,kai ni tunda nakke ban taba ganin
kamartaba .
Na mike tsaye kabir yabini da kallo
"To mallam ka hangota zaka gujeni ko?"
Na harareshi
"Ai kaine kake yimin wulakanci,ba gara na tafi inda inda
za'a karramani ba " ban tsaya wata wata ba nanufi inda
take da ganina ta fara murmushi ,
Murmushin da kullum in tayimin sai nadan rikice .
Na dubeta cikin sarkewar murya
"Ina kwana hajiya farida "
"Lafiya lau umar"
3 386
is"
Kakabi ya shigayi yina tafa hannu
"Amadu ina nan bansan sun fita ba Ni maganar da Abu take jawo mun ya isheni kamar ba gimbiya ba! ɗaiɗaikun matan ƙauye nan ne batayi fada dasu ba wohohoo"
***
Gidan Sarkin Musulunci Aminu ɗan isiyaku,Ƙauyen iyanbu (Ƙirƙirarren ƙauye a Kano Nigeria)
Gidane babban gidan sarauta Ginin tubali an masa kwalliya da hannun magini ,mai ɗauke da zauruka takwas ,da fankacecen tsakargida,da sasuna uku,na waje wajen shine sashen mai martaba sai cikon biyu na matan sarki,.
Inna ABU wacce ta kasance uwargida mai yara biyar duk mata. Babbansu saude tayi aure a Lagos sai saratu a Kaduna ,suwaiba a Cikin garin kano sai cikon biyun Wasila da Rafa'atu sune ƴan mata
Sai kuma Iya Talatu wato amarya mai yara biyu Nuratu da ɗan autan sarki Nuraddeni.
Akwai kyakkyawar zaman lafiya tsakanin zuriar wannan gidan ,ba kishi lafiyar Allah,kullum tare ake cin abinci sannan kowa yana kaunar dan uwansa
Nuratu wanda suke saanni da Rafa'atu gaba-daya ta dade da zama ƴar ɗakin Inna Abu ,kayan sallanta yina dakin Inna Abu tare suke zuwa don haka ɗaiɗaikun sirrin Inna Abu ne bata sani ba ,ta ɗauke ta tamkar aminiya
8pm
Lokacine da sarki yake tara rankatakaf iyalansa ya masu karatun addini In an gama mai tambaya yayi
Yau ma haka ta kasance kowa ya haɗu a baranda da littatafansa harda Iya Talatu Inna Abu ne kaɗai babu ita .
Falfalfal sarki ya fara fallo littafin gabansa ,kafin ya soma shafa gemu yana hamdala
"YAWWA ina Abu?" Nuratune tayi karaf tace "Tana ɗaki taje sallar ishai"
"Maza kirawota wannan darasin da ita ya dace"
Saida abu ta gama laƙaiƙaitan ta ta fito don ta tsani karatun nan na dare.
"Yawwa zauna nan gefene kisa kunni da kyau kowa ma yasa kunne" akace "To"
"Wasallalahu Alal nabiyyil Kareem Amma ba'a da yau BABUN ISTIGIFARI...Babi akan neman gafaran Ubangiji!"
"Shidai tuba yana tabbata ne bisa sharaɗi _Annadamu Ala ma fata_ yin nadama akan abinda ya wuce ,dakuma niyyar bazaka sake aikatawa ba daganan in ka cutar da wani da bakinka ko aikinka sai ka rokeshi ya yafe maka ,sannan kayi ISTIGIFARI Ubangiji ya yafe maka ,kinajina ko abu?"
"Kai mai martaba na gaji wai karatu kake koyawa ko ci mun mutunci kake son yi ? Kai koyarwanka mana ka daina sa sunana"
"Aah nidai bance ga tijaran da kikayiwa Ahmadu a hanya ba,kuma bance kin fita kinje kinci mutuncin mijin Suwaiba ba tareda izinina ba kawai karatu mukeyi"
Ras gabanta ya fadi sai kuma ta fuske tana muzurai haka ya dinga zuba karatu itakuwa sai raba ido takeyi tana tunanin hanyar neman kudi sam bata jinsa ma
Saida akwa kwashi kusan awa biyu kafafun kowa yayi tsami wasu ma sun fara barci duk an gaji an daina fahimta kana,ya ɗago ya kallesu a tsaya anan ko a cigaba?"
Kowa bazai iya cewa ya gaji ba don haka sukace a cigaba
Zabura inna ABU tayi "Kwarankwatsa na gaji a tsaya haka nan ,ke Nuratu zo muje ki kiramun Madam Kareema a waya na kar dare yayi ban sameta ba ,yau sai naci mutuncin Ahmadu da Abu-jafar sai na nuna masu ba sune sa'oina ba uwarsu ce daidai dani "
Taja hannun Nuratu fiii suka shige ɗaki
Kwance zani tayi ta ciro wayarta a lalita "karɓi nan Latso mun karima Madam"
Da sauri ta karba tana murna za'a tuzarta su Ahmed dama taji haushinsa wai bai kulata ba
Sallaman BABA ZULAI Ne ya karaɗa gidan
"Sallamanku dai masu gaida Aminiya kina ina?"
Washe baki inna Abu tayi ta buɗe murya "Maraba lale marhabin SARKIN NOMA da kanki(ta kirata da sunan mijinta) shigo mana"
Tafawa sukayi nan suka sarƙe da hira
"Ke ban baki labari ba ,tafiya Habuja danayi Allah ya hadani da taƙadiran ƴaƴansu ,kinsan me sukayi mun ? Wai na gansu sunata tsalle wai kamfanin MTN tana bada kyautan kudi ,jikina na ɓari na miƙa wayata nace a sa mun lambobin suma su zuba mun ....kinsan Allah suna sa numbobin sai ga ɗari biyar saaaa
Nan na mike na fara rawa ,abun mamaki sai suka fara dariya wai ai bashi suka bani,nan murna ta koma ciki ,ABU kinsan dai yanda na tsani bashin mtn ɗin nan ,don haka da sauri na kwaɗa ma kamfanin kira ,watanan jairar matar ta ɗauka,nan na
3 386
ahira kin siyar kinba miji wallahi bazai yuwu ba ko kinaso ko kina ƙi sai na ƙwatar maki ƴancinki gaba zaki gode mun ko ƙasa ya rufe mun ido,kuma zuwa gidan nan bazan fasa zuwa ba har sai abu-jafar yayi zuciya ya nemi sana'a .
Inyaso in nazo ki gaggaɓe kafafuwana!"
Sunkuyar da kai tayi batace komai ba "Kiyi magana mana ,Allazi miji,Indai namijine kasheki zaiyi ki gode ma Allah da ya baki tsayyayiyar uwa irina!.....Ni wuce muje a bani kajin nawa in wuce dashi don da ɗan taxi nike a waje ,in ma da ɗan agade (plantain) ki zubo mun a leda mu sama na kalacin gobe (Break fast) "
Cije baki tayi ,ta kalli Nuratu "ƙanwata a zubo abincine?"
"Aah saidai ki zuba mun a leda anjima zanci"
"Ku komai a zuba muku a leda sai kace baƙin Mayu?! Kowa sai yasan daga kauye kuke?"
"Allah sarki Suwaiba haihuwa tayi gardama Ni kike zagi ko? Lallai kinyi aure a burni...Nuratu tashi mu sa kai" ta ja hannunta fuuuu suka fita da gudu ta bi bayanta tana kira amma bata tsaya ba
Suna zuwa suka faɗa taxi dinsu yayi reverse zasu tafi ,Gararaf taxi ɗin ya buga ma gaban wata shimfidediyar baƙar mota sai sheƙi takeyi .
Take ya fasa masa madubin gaba
Cak yaja ya tsaya
Daga baya Inna ABU ta fara dannawa mai wancan motan zagi "Shegu ƴaƴan ɓarayi Allah ya isan mu kudin talakawa huhum da ikon Allah yanda ka dakar masa mota sai kayi rani saboda talauci....Ɗan nan wuce muje"
"Aah Baba Ni ne fa mai laifi ki tsaya in basa hakuri karki ja mun ɗauri"
"Kaji lusari ku kukeja ana wulakanta mu ka wuce nace"
A zuciye Ahmed ya fito daga Mercedes GLK ɗin saye yake cikin cream ɗin filtex mai sharara yayi askin funck gashinsa sai walƙiya yake a hasken rana ,fuskarsa manne da shade baƙa kalar takalmin sa da agogonsa masu azaban tsada.
"Hello Mr Idiot bazaka iya fitowa bane shashasha?"
"Kaima shashasha ɗan akuya ƴaƴan ɓarayi wooooo macuta wooooo masu shan jinin talaka"
Damtse mata baki Nuratu tayi "Ya Ahmed ne fa"
Daidai ya fincike hannun taxi ɗin ya buɗe
Cikin borin kunya ta soma bige bakinta "Subhanallh dara taci gida ,ɗan nan i_Haƙuri ban gane ka bane " murmushi yayi fuskarsa ta washe daga ɓacin ran da yake ciki
"Inna ABU laluwa bala'i gida za'a koma da tsakar ranar nan?"
"Eh wallahi maraba na da ganinku baƙin turai,ka ganmu a mota ƙarfe ƙarfeee,Ko muzo ka kaimu a waccan zazzafan motanne irin na ministoci?"
Dariya yayi "Ai dole na kumuje in kaiku Amma zan fara kai Madam gidan Yaya "
Fitowa sukayi suka koma motan ya yi ma mai taxi ɗin ihsani mai taxi ɗin nata basa haƙuri
A mota baya suka ɗuru sai zuba ƙauyanci sukeyi a haka suka gaisa da Fauza mata mai fara'a dason mutane "My love ga Nuratu ,besty ta da nake baki labari na wannan village din da nayi bautar ƙasa ,yarinyar Sarkin garin,itakuma wannan step mom ɗin ta ce kuma ƙawar mamanmu ce tun na yaranta surukuwar Ya abu-jafar"
Washe baki tayi "wow nice meeting you sannunku ,Love yana bani labarinku" caɓe baki Inna Abu tayi "ki saki jiki kiyi Hausa zalla ƴan ƙauye ne nan ,ki bar lanƙwashe murya sake shi ras"
Dariya suka fashe da shi a maimakon suji haushi sun maidata kamar cartoon
"Inna bala'inki na nan?"
"Allah ya rabani da bala'i gaskiya ne dole In faɗi hali zanen dutse ba abinda ya sauya mun sai wanda ya daɗu"
Haka suka isa har ƙauyen su Nuratu
A ƙarƙashin rungujejen bishiyar durumi dake ƙofar gidan suka riski sarki da mutanensa an shimfida manyan taburmi da dardumai ana ta fadanci ya tokare akan kujera kai yasha rawani.
Inna Abu itada da Nuratu da suka fita sarki bai sani ba ta ƙofar baya suka wuce siriri suka shige gida ,shikuma ya tsaya da Anty Fauza suka gaisa ya turota cikin gida suka gaisa da mutanen gida
Da zasu tafi ne ya ɗan kebe da sarki ya ciro kudi mai kauri ya masa ihsani sannan ne ya ɗaura da roƙonsa "Ranku ya daɗe a ƙara kula mana da Iyayenmu don Allah kar kuna nan aje ai masu duka a hanya!"
"Me yafaru malam Amadu?"
Nan ya zayyane masa duk irin tujaran da Inna Abu taso yin masa ya daura da cewa "inda Ni ba dan gida bane me kake gani? Tuni na aikata caji of
3 386
omai...Tushen labarin)
Kitumirmira akwai ƙatoton lauje cikin naɗi ,labarin nan dai ba'a soma komai ba ,gashi wannan shine page din kusa da ƙarshe ,ki biya kuɗin ki ta daya daga cikin wannan hanyoyin
7782217014
Mohammed Hassana
Fcmb
Ko katin MTN ta wannan Number 09065990265
Ƴan Niger katin Artel ta wannan Number na sama.
[11/30, 15:20] أم افنان✍️💞: *🫧SUGAR MUMMIES🫧*
Na
Hassana Bamalli
Oum Aphnan
🔟
_Crazy In_Law😄⛹️♀️_
#Fun🥳
#Apathy
#Village Islamic kingdom👑
NASSARAWA GRA
Tamfatsetsen Gidan sama ne mai kyawun gaske ,amma tsabagen bala'i har gilasan windinan gidan girgiza sukeyi
Arc. Abu-jafar cikin bala'i ya kalli matarsa Suwaiba yana nuna ta da yatsa
Shekara ta ɗai..ɗai..ɗai takwas ina biyan kuɗin hayan gidan nan da kaina ,ba wanda ya taɓa ji sai don yau kin cika mun dubu Ashirin ...Only twenty thousand kinje kin fada ma uwarki ,kalan gori da cin mutumci ya..."
Ɗaɗɗaga masa hannu ta ringayi alamar yayi shiru kar taji saboda daga dinning area ɗin da suke ta hango shigowar Inna Abu gidan riƙe da hannun ƴar ɗakinta Nuratu ,ta glasses ɗin windown kicin dake facing tsakar gida
Haba tsiya ya rufe ma Abu_Jafar Ido ko kallon matar bai yi sai da yaji an doka masa tsawa
"To mugu ! mai zaisa bazata faɗa mun ba.? Nice nan uwarta dole ta faɗa mun mashiga da mafitar dukiyarta kodon halin rayuwa da mutuwa. don tanada uwa da uba da yara ko da ta mutu kwabo ! baka samu gadonta!"
Kauda kai Suwaiba tayi tana fifita hannu cikin tarin jin kunya
Abu_Jafar sunkuyar dakai yayi ya ɗauki cinyar kazan dake kan abincinsa ya soka a baki zai gutsura
"Dallah jibeka mai mataccen zuciya ji yanda ka luma wani gabza gabzan haƙoranka a cikin kaza ko kunya babu anacin cefanen mata!,haba gaskiya kullum kake mulla ƙiba ɗiyata ke rama!"
Suwaiba miƙewa tayi kamar zata fasa ihu "Haba Inna surukinki ne fa ,kuma bani nayi cefanen ba ma ƙaninsa na Japan yazo ya kawo mana kajin ƙwara hamsin da miliyon guda muyi cefane ga kajin ashirin can ma Abu_Jafar ɗin ya ware a mota za'a kawo maku gida"
Ba kunya ta washe baki "Allah sarki Amadidi,na daɗe rabon da in gansa tun bayan da yayi bautar ƙasa a ƙauyen mu ,Nuratu Abokinkine ya kawo mana kaji ,kice zamuja dabge ,Yina ina Amadun?" Ɗaga mata kai Nuratu tayi tana murza yatsun hannunta,tana washe baki itama tayi kewar Ahmed
Ɗaure fuska Suwaiba tayi bata amsa mata tambayarta ba ,sai Abu_Jafar ne ya haɗiye naman bakinsa da ƙyar yace "Kina nan zakiga ya shigo yaje kai amaryarsa wankin gashine can plazan ƙasan mu"
Washe baki tayi "Allah srki kaji sha'anin su na Attajirai ,Abu jafar gwara dai kayi zuciya tunda an koreka aikin ba komawa zakayi ka maƙale a wuyar mace ba ,kaima dai ka nemi ko sana'ar ƙarfine in na gwamnatin ya kasa samuwa ,ga gidajen bulo nan ko dubu biyu suka baka a rana dame ka manta?"
Ƙwallane yaji ya kawo masa ido
Jan kujera yayi ya mike "To Inna ki neman mun in kinsamo zanyi" Yana gama magana ya juya ya shige ɗakin dake kusa da su .
Waigawa tayi ta kalli Suwaiba ,tana ƙasa da murya kamar munafuka
"Da gaske yike zai iya aikin gidan bulo?"
"Haba Inna aikin fini sani ,ya za'ayi babban mutum kamar abu-jafar kice yayi leburanci ,wannan cin fuskane yana fa raga makine Albarkacin keɗin surukansa ne"
Tafa hannu ta shigayi tana salati "Suwaiba ?! To don Allah kisa abu-jafar yayi ƙuli ƙulin kubura dani ,in yaso akai gawata gida ,kinga mun shahararriya! Nine kike wulaƙantawa akan miji? Aah lallai kin riƙa ,Ni ina kokarin kwatar maki ƴancinki sai ki barbaɗa mun ƙasa a ido?"
"Wannan shine ƙwatan ƴancin Inna? Kullum kina lilo a unguwarnan ko gate ɗin gidan nan ya shaida kalar bugun ƙofarki ,wallahi inna bai dacewa ,ni yanzu ma ya akayi Abu-jafar yasan na fada maki na ranta masa dubu ashirin ya cika ya biya haya?"
"Mai martaba na fada ma wa ,gwara ayi ma tufka hanci kafin ya tatike ki da bashi ki kasa ƙulla abun arziki ,ga Ƴan uwankinan duk da gwalagwalansu na aure ke ga faƙara'u Alal lalurati ,fataralle Sarkin fawan l
3 386
n gani a asibiti yau,bari ma kaga hujja ta "Nan take ta daburce tana kokarin dakko masa wayarta ta nuna masa wani abun da zai zama madogaranta na fita.
Ransa ne yaji ya sosu ,shidai yinaso ya zama man with authority a cikin gidansa, yana son matarsa ta zama cikakkiyar matar gida wacce zai fita aiki ya dawo yana da tabbacin zai tarar da ita a gida. amma ina bazai yuwu masa da Fauza ba,she too like money!
"Aaaah shikenan shikenan na yarda, duk saboda kudine ko Allah ya tsare _I've to be on my way_ Ni na tafi"
Tuntsirewa da dariya tayi " _Try to provocate me this morning_ "
"I'll 😃" ya Bata amsa yina dariya yayi hanyar ƙofa
"Kayi kyau sosai yau mijina"
Juyowa yayi ya buɗe mata hannuwarsa "Ke kikasa hakan ,jiya da daddare kin bani kulan da ya dace "
"😄😄😄 I do"
Ficewa yayi ya barta tana mika .ta janye tray din abincin ta ajiye a gefe zata fito a cikin bargo sai gashi ya turo ƙofa ya sake dawowa
Marvelously ta tambayesa "Forgot something ? Ehem ka yi mantuwa ne?"
Waskewa yayi ya fara sosa ƙeya "eh ,Aah dama...dama ina tunani ne ,Madam Plz me zai hana mu rage ma Nuratu aikin gidan da takeyi, in yaso sai a samo wata me aikin?"
Caɓe baki tayi "Love wai ka manta Nuratu me aiki ce ? To in batayi aikin nan ba wa zaiyi ? "
"Aah wallahi na sani kawai dai ina duba halin da take ciki ne kinga tanada ciki,banason tana stressing kanta da aikin gida saboda inason ɗanmu yafito lafiyayyen kyakyawa"
"Hello durling,ban taba jin inda akace mai ciki bazatayi aiki ba saboda hakan zai taba girma da wellness din ɗan cikinta ba .
so, _Nuratu must do all her domestic chores_ Kaje aikinka kaji mijina bye ,have a nice day"
Ba yanda ransa ya so ba yaje ya bata feck a saman leɓɓanta💋 ya fice gwuiwa a sanyaye jiki ba laka!.
Nuratu kusan duk abunda suke tattaunawa a kunnenta yake itadai abinda takeso ta samu su fice ta gudu ,don haka tana maƙale ta window har Ahmed ya fice a gidan.
Tana ganin ya fita itama ta sulale ta sunkuci kayanta ta fice a gidan
Zuwanta airport ba daɗewa aka samar mata jirgin da zai tashi da safen nan ,saboda kudin da ta ninnika yasa batayi jiran kwanaki ba kafin visa dinta ya fita ba , tunda nata yayi expire tuntuni
Dukda jirgin ba direct zai wuce Nigeria ba sai ya biya China ya kwashi kaya ya wuce Thailand ya ajiye passenger sannnan zai wuto Africa sai ya sauke tsirarun pasinjojin Nigeria a Lagos ciki kuwa harda Nuratun hakan ya mata daɗi ,ko banza indai taje Lagos ta fara jiyo ƙamshin Kano gida daɗi!.
•°•°°•°•°°•°•°°•°
Ba wanda yasan Nuratu ta bar gidan har sai da suka dawo daga wajen aiki ,nan fa Fauza ta soma ƙorafi an bar mata gida gaja gaja ita bazata juri ƙazanta ba ,waye waye
Ɗakin Nuratun ta shiga nan takaga ko'ina a bubbude sannan ba akwatinta a sama ,ƙwalla mata kira tayi ta nufi toilet tana taban ƙofan ya buɗe ba kowa a ciki ,da sauri ta fito tana kwarara ma Ahmed ɗin kira
A furgice ya nufo dakin nuratu "menene Fauza ? Atimes You scared me"
"Noor ta gudu!"
Ɗif ya ɗauke wuta na ƴan sekonni kafin ya shige ɗakin da sauri da gaske da babu ita
Dafe kai yayi kawai sai ga ƙwalla "Me yasa zakiyi mun haka Nuratu?!"
Haushine ya kawo ma Fauza wuya "And so fucking what in ta tafi ,dama karuwancin tafi so tayi sai taje tayi me ye na kuka akan karuwa..." Wata bahaguwar mari ya sakin mata a kunci
"Karki sake ce mata karuwa in ma ita karuwace to nine kwarton ,kuma ke ce kika janyo ,kuma dole zan bita don tsira da martabar gidan mu da Ni kaina!!!"
Dukda zafin mari da alaajabin yau ita Ahmed ya mara bai kai mata abun mamaki ba yatankacin kalmomin da suke fitowa daga bakin Ahmed
"Ahmed Ni ka mara akan fasiƙar ƴar aikina ? Ahmed kasan ko me kake faɗi? Rashin haihuwa haukane da har zaka ringa magana kamar taɓaɓɓe?"
"Kece taɓaɓɓiya Ni a hayyacina nike ,wallahi bazai yuwu inga samu inga rashiba dole sai nabi Nuratu yau yau dinnan kafin ai mun flushing din yarona yabi rariya don sarai nasan halin annobar Kishiyar uwarta INNA ABU!....."
FLASH BACK✨
(Mafarin k
