ar
Feedback
TASKAR NOVELS

TASKAR NOVELS

الذهاب إلى القناة على Telegram

Download all kind of hausa novels,musics videos and movies

إظهار المزيد
3 386
المشتركون
لا توجد بيانات24 ساعات
-67 أيام
+2030 أيام
أرشيف المشاركات
a tace min bazata aure ni ba na makara shine abun ya 'kona min na tare ta a ranar na mata fayd'e ba da niyyar kasheta na mata haka ba wallahi da nasan zaka mutu bazan yi mata ba kawai ganin ta gane ni yasa na kasa barinta dan karta tona min asiri har saida naji bata motsi ku gafarce n..................... Bai karasa ba Habu ya d'auke shi da mari yana hankad'a shi ya mi'ke ransa a 'bace ya goge hawayen fuskarsa yana kallon Sabi'u yace "wallahi tallahi bazamu yarda ba yaya sai munkai 'kararsu gaban hukuma dole ne a yanke musu hukuncin daya dace dasu". Kai Sabi'u ya jinjina yana cewa "muje" fita sukai daga gidan yayin da Mudi ya tashi a guje yana zuwa gurin Tanko dake kwance yana numfashi ya d'ago shi yana mikar dashi tsaye yace "sannu abokina gaskiya habu ya cika 'kasurgumin mugu kaga yadda duk ya sauya ma kamanni Allah ne yai da sauran kwanan ka a gaba da yanzu ya kashe ka" shidai Tanko shiru yai ya kasa magana cikin azaba da'kyar yake jan kafa suka fita daga gidan. Bayan fitar su Habu kai tsaye gida suka nufa a kofar gidan suka samu Baffah zaune yayi ba'ki dan haka basuyi masa magana bayan sun gaisa suka wuce zuwa ciki suna jiransa ba'a dad'e ba shima ya shigo tare da zama kan wani 'karamin dutsi dake kafe a wajen kofar d'akinsa yana kallon yadda yanayin ya sauya yasan ba kalau ba akwai matsala. "Sabi'u Habubakar me ya faru nagan ku haka ko kun samu wani bayani ne". Kai Sabi'u ya d'aga "eh Baffah samu ma na ha'ki'ka Habu ya baka labari". Maida kallon kan Habu Baffah yai yana cewa "Habubakar meya faru ne na ganku cikin fushi musamman ma kai"?. Zazzafan numfashi Habu ya sauke yana cewa "wallahi Baffah baza mu yarda ba sai munje kotu wai tsabar zalunci ashe wannan tsinannan ne Tanko ya mata fayd'en bamu sani ba gashi yanzu da yaji wahala ya fad'a da bakinsa harda dan kada takai labari yasa bai 'kyale taba saida ta daina motsi". Runtse ido Baffah yai jin abinda Habu ke cewa basu ankara ba sai ganin hawaye sukai sharr yana zuba a idanun Baffah tabdijan tashin hankali wanda ba'a sa masa rana hawaye fa suke ganin a idanun Baffah a zabure cikin tsananin fushi habu ya mi'ke yana cewa "wallahi bazan kyale Tanko ba Baffah saina kashe shi tunda yai silar zubar hawaye a idonka abunda ban ta'ba gani tare dakai ba a rayuwa ta sai yau" juyawa yai zai fita muryar Baffah da alamun kuka yace. "Habubakar dawo kada ka koma gurin su na barwa Allah shine ya halicce mu sannan shike da iko damu zai sakawa Lami bazai kyale shiba Tanko ya cuce bazan ta'ba yafe masa ba har ranar komawa ta ga ubangiji" ya karasa maganar kukan nasa na sake fitowa. 'Durkusawa gaban sa Habu yai yana kifa kanshi a jikin Baffah kawai shima ya fara kuka wanda Sabi'u da sauri ya rungume su shima yana zubda hawaye suna wannan hali sukaji sallama yaro. "Wai Baffah yana nan yazo inji Isubu me gari yana nemansa". 'Dagowa Baffah yayi yana kallon yaron cikin ajiyar zuciya yace "kace masa gani nan ina zuwa" yaro na fita Baffah ya mi'ke yana daukar buta ya wanke fuskarsa. Ran Habu a 'bace yace "wato 'kara suka kai gurin me gari? Aiko yau saina tabbatar basuyi kwanan gida ba wallahi saina d'ebo musu hukuma muje Baffah. Baffah bai iya magana ba kawai yayi gaba ne suka bishi a baya har gaban me gari suka samu guri dam ya cika da jama'a ma'kil ana ta hayaniya sallama Baffah yai yana zama cikin mutunci suka gaisa da kowa. Kallon sa me gari yai "Baffah kasan dalilin kiranka?. Kai Baffah ya girgiza "a'a ina fata lafiya"?. Cigaba me gari yai "eh lafiya ba lafiya malam Balah ne ya kawo 'kararka cewa Habu da Sabi'u sun daki d'ansa Tanko harda rauni sukayi masa ga sun zubar masa da ha'kora guda biyu haka ne"?. Kallon su Sabi'u Baffah yai ganin basu musa ba yace "gasu nan me gari ka tambaye su ni ban sani ba". Kafin me gari yai magana Balah yace "a 'kwarai ka turo suwa adamu dukan mutuwa sannan kace wai baka san komai ba wallahi bazan yarda ba sai munyi shari'a dakai" gun me gari ya juya yana cigaba "me gari nifa ba cewa nai a tambaye shiba kuma ba sasanto naso ba idan bazaka iya ba zan kai gaba a bimin kadin dukan da sukai masa".

i ya gama cika shi cikin tsawa yace "dallacan kana bata min lokaci zaka taso ko saina figoka"?. A zabure Tanko ya mi'ke tun kafin ya d'ebi takalmi Habu ya jashi kiiiiii suka je gurin Sabi'u sannan ya dawo yana cewa Mudi "malam saura kai kake 'kwalalo min ido" shima jiki a sanyaye ya mi'ke suka fita ganin sun fara tafiya yasa Mudi cewa "ina zamu je"?. "Ka biyo mu man zaka gani ai" ya fad'a yana sake tisa 'keyar sa gaba har suke cikin kangon gidan nan juyowa Sabi'u yayi yana nuna musu gurin yace "Tanko wanne irin rashin imanin ne haka me Lami tayi maka zakai mata fayd'e gashi ka zama silar mutuwarta"?. A wannan lokacin tsabar firgici Tanko har saida ya 'kwaru muryarsa a sha'ke da'kyar yace "ni kuma amma Allah ya isa na sharri zaku min ina ruwa na da ita me tamin zanyi mata haka aiko bazan yarda ba saina kai ku gurin me gari". A fusace Habu ya sha'ki wuyan rigar Tanko yana naushin sa yace "sharri ma kace zamuyi maka tsinanne asararre wallahi yau saika amsa laifinka ko kaima ka ba'kunci lahira ka gano abinda ake gani" ya karasa maganar yana sake dam'ke wuyan Tanko wanda idonsa suka fito waje. Ganin Habu na neman yi masa illa yasa Sabi'u cewa "ka sake shi Habu kada kaji masa ciwon da zamu zo shari'a ta kada mu" saida habu ya gwara kan Tanko da bango yaga ya fad'i baya motsi sannan ya rabu dashi yana huci ya maida kallon sa kan Mudi da yake rarraba ido alamun rashin gaskiya ya bayyana a fuskarsa 'kiri 'kiri. Kamar wanda zai fad'a masa ya kashe shi haka habu yai kansa gadan gadan yana cewa "kai kuma munafiki zaka fad'i gaskiya ko kaima saina tura ka suman kamar abokin naka? FA'DI MANA" yai maganar a tsawace. Jikin Mudi na rawa yace "dan Allah Habu ka tsaya ni bansan komai ba". Wani kallo yai masa na baka da hankali amma zan koya maka kafin yace "kace bakasan komai ba ko? Haka kace ko? Lallai yau saina bambance maka abinda ake kira da jaki sha duka" warto shi yai tare da d'uma shi da 'kasa yabi ya take ya hau jibgarsa da dukkan karfi sa ihu Mudi keyi yana neman agaji Sabi'u na tsaye da yake baida zafin rai kamar Habu amma bazai hana shi dukan nasu harsai sun amsa cewa eh. Jin da Mudi yai idan ya sake za'ai bashi yasa cikin wahala da numfashi da'kyar yace "dan Allah Habu ka tsaya zan fad'a maka gaskiya wallahi zan fad'i gaskiya karka kashe ni zaka 'balla min 'kafa" jin haka yasa da gudu Sabi'u yaje yana 'bam'bare Habu daga ruwan cikin Mudi yai dauke shi yai gefe dashi. Yana cewa "tsaya haka Habu yanzu zaiyi bayani" huci Habu keyi yana kallon Tanko dake kwance sharkaf kamar matacce a hasale yaje ya wanka masa wani irin gigitaccen mari me karfi sai ga Tanko ya mi'ke tsaye a firgice yana neman hanyar guduwa dam'ko shi Habu yai yana maka shi da 'kasa yace. "Gidan uban wa zakaje"? Idan kaga na barka ka fita anan to saidai ka fad'a min amsar tambayar danai maka meyasa kaiwa Lami fayd'e"? Zaka fad'a ko saina fasa ma kai"?. Ganin ya cakumo shi yana dunkule hannunsa zai kai masa naushi yasa jikin Tanko na rawa bakinsa na jini yace "zan fad'a dan Allah kamin hakuri wallahi zan fad'a maka gaskiya". Sakin sa Habu yai yana kallon Sabi'u yace "kasan Allah yaya Sabi'u bazan 'kyale su fita nan cikin hayyacin su ba indai basu fad'i gaskiya ba saina dau fansar abinda sukai mata kamar yadda kai ka fad'a a kofar gidan mu dan na jika" ya karasa maganar yana kallon Tanko dake ta goge jinin da ya 'bata masa fuska. 'Durkusawa gaban sa Habu yai yana sha'kar wuyan rigarsa 'kara Tanko yana cewa "Habu zaka yanka min wuya dan Allah ka sake ni zan fad'a maka". Habu bai sake shiba saidai ya sassauta ri'kon da yai masa fuskarsa a d'aure tamau yace "ina jinka". Jikin Tanko na 'barin tsoro bakinsa na rawa ya fara magana "dan Allah Habu kuyi hakuri ku yafe min na aikata muku kuskure tabbas nine naiwa Lami fayd'e ranar amma dan girman Allah ku dube ni da idanun rahma ku yafe min".......................... Takaici ne ya rufe Sabi'u yana kallon Tanko yace "kenan zargin mu ya tabbata kaine silar mutuwarta me tai maka zaka dau alhakin ta"?. Muryar Tanko na rawa yace "babu abinda tai min kawai naji haushi ne sabod

sai mun kai rahoto gurin 'yan sanda a zo garin nan a tsananta bincike duk wanda yake da hannu sai an hukunta shi". Tarar numfashinsa Sabi'u yayi "eh 'kwarai Habu wallahi baza mu yarda sai an bi mana kadin wanda yai sanadin yarinyar nan taya za'ai mata haka mu 'kyale kamar wacce bata da gata dole mu tashi musan abin yi amma me kace Baffah"?. Shiru yai duk damuwa ta addabe shi ya rasa inda zaisa kansa yaji dad'i yana matukar takaicin rashin yarinyar nan yayi kuka ya 'kara harya gode Allah mutuwa lokaci in yazo ba jira amma Ramatu ta cuceshi bazai ta'ba yafe mata ba a rayuwa................................ Tunanin sane ya katse jin Sabi'u na cewa "Baffah baka ce komai ba"?. 'Dagowa Baffah yayi yana kallon dukkan su biyun cikin nazari ya sauke ajiyar zuciya yana cewa "Sabi'u Habubakar Allah yai muku albarka ya albarkaci rayuwar ku da zuriyar ku na amince da abinda kuka ce kuma na yarda ku dauki mataki akan koma waye ya cutar da Lami kuyi bincike ni na amsa muku da yardata Allah ya taimake ku ya tona asirin wanda yai mata haka yasa bazai gama da duniya lafiya ba". Da sauri Habu yace "Amin Baffah daga yau yanzu idan muka fita zamu fara aikin mu Baffah ka taya mu da addu'a mu samu nasara matukar aka samu wanda yai mata wannan rashin imanin shima a take zamu kashe shi dan wallahi bai isa mu rabu dashi yaci bulus ba". "Kwarai Habu kayi gaskiya tashi muje yanzu ma kuwa" Sabi'u ya fad'a yana mi'kewa tarar zancen nasu Baffah yai "a'a Habubakar karku kuje kuyi abinda za'ai dana sani dan Allah ku bi a sannu kunji"? "To shikenan Baffah zamu kula Yaya Sabi'u zo muje" fita sukai Baffah daya bisu da kallo hawaye na zuba a idonsa yana farin ciki da samun su matsayin 'ya'yansa. Gidan da suka d'aukata sukaje dube dube suka fara amma dai basu ga wata alama ba jingina jikin bango Habu yai yana cewa "tsaya yaya Sabi'u nifa na kasa fahimta musamman yanzu da muka zo nan". D'agowa Sabi'u yai "kamar ya ban gane ba"?. Kallon daidai inda suka ganta kwance Habu yai yana cewa "ka duba man lokacin akwai alamomi sakamakon muna rud'e ya hana na tsaya amma wanda yai hakan yabar alamar wani abu kai baka gani ba"?. Shiru Sabi'u yai yana tunani zuwa wani lokaci yace "amma kai a ganinka waye zai iya yi mata haka a garin nan da kewayen mu waye shi". Rufe ido Habu yai ya kasa cewa komai abubuwa yake tunawa suna masa yawo a kunne ya riski zancen da Lami tayi da su Tanko lokacin zai fito harya tsaya ya saurari wani abu kamar inda Tanko ke cewa saiya sa tayi kuka da idonta tayi nadama. Da sauri ya bud'e idon yana kallon Sabi'u yace "yaya Sabi'u tabbas akwai wani abu ina zargin mutum daya wallahi shine kuma ko kaffara bazan ba shi ya aikata mata haka" "waye habu wa kake tunani a ina yake yanzu muje"?. Kallon Sabi'u Habu yai yana d'an d'aga kansa sama alamar tunani a hankali yace "Tanko ne yaya Sabi'u tabbas shine ba kowa ba" zaro ido Sabi'u yayi yana 'kure Habu da kallo yace "Tanko kuma? Habu Tanko dai da na sani d'an gidan malam Balah saurayin ta? Meyasa kake zargin sa"?. Ri'ke hannunsa Habu yai yana cewa "kwarai shi nake zargi kasan wani abu na ta'ba jin suna hira da ita shida abokinsa Mudi akan saita rabu da yaron nan Alpha ta aureshi saboda ta'ki amincewa ta shiga gida basu san ina la'be ba suke cewa zatai nadama da dana sani a rayuwar ta dan haka dole nace sune". "Habu ka tabbata kaji haka"?. "Eh yaya Sabi'u wallahi da kunne na naji lokacin da suke wannan maganar da ace bishiyar kofar gidan mu tana magana zata bada sheda". Kai Sabi'u ya jinjina "shikenan Baffah yace kada muyi abinda za'ai dana sani amma ba baza mu 'kyale ba yanzu muje mu same su" fita sukai kai tsaye dandali suka nufa sukai sa'a suna majalisar su harda Ilyah tsayawa daga gefe Sabi'u yai yana cewa "je kayo mana magana dasu" kai Habu ya d'aga yana karasawa yai musu sallama tare da baiwa kowa hannu suka gaisa yana kallon Tanko yace "kadan zo zamuyi magana yanzu" dafa 'kirji Tanko yai idonsa kamar zai fito waje yace "ni"? Wata uwar harara Habu ya sakar masa yana cewa "a'a ba kaiba ni" saroro Tanko yai jikin sa na 'bari yana kallon habu wanda takaic

ya faru an ganta ne"?.......... Tana rufe baki taga Sabi'u da Habu sun fito dauke da ita ihu ta saki tana cewa "na shiga uku na lalace yau ranar tonon asiri tazo Lami wanne d'an diban albarkar wanda bazai gama da duniya lafiya bane ya miki wannan aika la'ilaha illallahu kaito na dama banga wannan rana ba wannan wanne irin masifa ne da bala'i" hakuri su Salamatu ke bata duk da kowa jikin sa rawa yake aka nufo gida wasu na cewa a kaita asibiti wasu na cewa bata da rai. Kwantar da ita akai Baffah dake durkushe gabanta yana kallon fuskarta abubuwa da na masa yawo cikin kwakwalwa musamman maganar da sukai na zai kaita makaranta gobe ashe yarinyar nan burin ta nason ganin tayi karatu ta samu ilimi bazai cika ba hawaye ne masu zafi ke zuma daga idon Baffah wanda suke sauka saman goshinta gida kam ya cika da jama'a ya kaure da koke koke mi'kewa Baffah yai da'kyar yabar gurin yayin da masu wankan gawa suka dauketa domin mata sutura bayan su kammala akace ba damar kaita dare yayi saida safe haka tai kwanan keso. Washe gari da wuri bayan anyi sallar asuba aka mi'kata makwancinta kafin suka dawo zaman makoki da sauran mutane da ba'ki lokacin da aka dawowa da Ramatu zanin da aka lullu'bi Lami dashi nan sabon kuka ya tashi da bori har rirri'keta ake ana dankwafarta da lallahi da bata hakurin cewa addu'a zatai mata ba kuka ba. Tashin hankali wanda ba'a sa masa rana lokacin da su Musbahu suka labarin karyatawa sukai saida suka zo suka gani da idanuwan su Musbahu yayi kuka ya kara kamar mace balle mama da Naja'atu alpha kuwa tunda ya suma bai farfad'o ba sai a gadon asibiti ya ganshi kwance daure da ledar ruwa hannu yasa ya fisge yana tashi zaune tare da saukowa daga gadon yayo waje likita daya taho d'akin zai sake duba shi ganinsa ya fita sai layi yake yace "a'a ina zaka je baka samu lafiya ba please yalla'bai mu koma ka kwanta" ko sauraron sa alpha baiyi ba yai gaba da sauri likitan yabi bayan shi yana masa magiya. "Dan Allah ka saurare ni ka dawo ciki na duba ka". Tamkar da gunki likita ke magana haka Alpha yai banza dashi yaci gaba da tafiya batare da ya kalli kowa ba kasa nutsuwa doctor yai domin yasan waye alpha d'an babban mutum ne duk abinda ya same shi yanzu shi za'a tuhuma bai daina binsa ba har suka fito harabar hospital din anan ya hango mom din Alpha da sauri yaje yana cewa "hajiya dan Allah ki taimaka kiyi masa magana ko zai tsaya", kallon Alpha daya nufi hanyar fita a gate din hospital tayi tare da girgiza kai tace "karka damu doctor zan dawo dashi" tana fadin haka tabi bayansa itama da sauri taga inda ya nufa domin basu taho tare da abbansa ba. Tsaye ta same shi jikin wani karfe ya kifa kanshi yayi shiru tsayawa tai a bayansa tare da sauke ajiyar zuciya tace "Alpha" bai juyo ba kuma bai amsa ba 'kara matsawa tayi kusa dashi tana dafa shi tace "Alpha me ya faru"? Har lokacin shiru baiyi magana ba juyo dashi tayi tana rike hannunsa cikin lallashi ta soma tafiya dashi tana cewa "haba alpha kaifa musulunci ne ka dau kaddara komai yai zafi maganinsa Allah na sani Lami rayuwar kace kuma kana kaunarta amma wanda ya halicce ta ya fika sonta shiyasa ya kar'bi kayarsa kayi adduar ta samu rahma da haske a kabarinta shine yanzu abinda take bukata kuma kaunar daya rage ka nuna mata kenan kaji", Alpha tari dabai kama shiba baiyi ba ganin haka yasa dole ta 'kyale shi tasan baya cikin hankalin sa doctor na tsaye yaga sun shigo d'an sauke numfashi yayi yana cewa "kiyi hakuri hajiya nayi kokarin dakatar dashi bai saurare ni ba" kai ta girgiza "a'a babu komai doctor nasani muje ka mayar dashi ya kamata ya samu hutu na d'an lokaci" "to shikenan hajiya" doctor ya fad'a yana bud'e kofa ya shiga suka bi bayanshi. Anyi sadakar uku ba'ki wasu suka fara tafiya saura kadan suma bayan bakwai suka dauri niyya suka koma garuruwan su domin Baffah mai jama'a ne sosai. Zaune Sabi'u da Habu suke a gaban Baffah suna masa 'korafin abinda akaiwa Lami wanda basu san waye ba Habu ne ya fara magana. "Yanzu Baffah shikenan haka zamu zuba ido baza ayi binciken wanda ya aikatawa Lami wannan rashin imanin ba gaskiya baza mu yarda ba

ma nayi karatu" sauke ajiyar zuciya yai yana rike hannunta yace "karki damu kinji share hawayen ki insha Allahu gobe da kaina zan raka ki har islamiya gurin malam Haruna yasa sunan ki cikin d'alibai ki fara zuwa daga baya saina dinka miki inifon tunda kinga Alpha din yace a 'kara masa lokaci bai 'karasa gini ba saiki fara islamiyar kafin lokacin ina haka kike so"? Kaita d'aga tana murmushi cikin jin dad'i tace "shima yace min zanci gaba da karatu na bayan bikin nagode Baffah Allah ya saka da alkairi" "Amin karki damu" Baffah na barin gurin Lami da murnarta ta tashi itama tana shiga daki tace. "Babah gobe Baffah yace zai kaini islamiya" Ramatu dake daurin gyada soyayyiya sai tumurmusa take jin abinda Lami tace yasa zatai magana ta 'kwaru tari ta ri'ka jerawa har shid'ewa da'kyar tace "kawo min ruwa" fita Lami tai ta debo mata bayan tasha tana numfashi tace "Kika ce gobe Baffah zai kaiki islamiya? Heeeeh lallai kam yau ake yinta to bari kiji wallahi baki isa ki makaranta ba abinda na yanke kenan wacce kika je ki kai a wudil din ma ba'a son raina bane talle zaki min kowa na neman kud'i ni kuma saboda da mutuwar zuciya gaki nan rid'ad'a ina kallon ki saidai kici kisha kije makaranta? Tab garama kisawa kanki salama babu wata makaranta da zakiyi idan ba haka ba lokacin aurenki saidai a kaiki daki hororo ba kaya". Cikin kuka Lami tace "dan Allah babah ki barni nayi wallahi ina son makarant.................duka Ramatu ta kawo mata tana cewa "ubanki yahau baro🙊 ina magana kina musa min bazaki makarantar ba talle zaki kuma na fad'a zaki tashi ki dauka ki fita ko saina miki shege dukan da zaki kasa tashi shima malam din ina nan daidai dashi" mi'kewa Lami tai tana kuka ta dau farantin gyad'a ta bita Ramatu data bita da kallo tace "kuma saura kije ki zauna a guri daya idan kika dawo min da saura saikin gane" Lami dai bata sake tofa koda alif ba ta fice ta nufi matallata. Bata fara ciniki da wuri ba sai jikin magriba kasuwa ta bud'e bayan sallar isha Lami ta baro dandali ta sayar gyad'ar tas sai farantin kawai a hannun ta jin taku ana bin bayanta yasa da sauri ta waiga ganin mutum yasa tace. "Waye"? Shiru ba amsa a tsorace tasa gudu wanda shima ya rufa mata baya ga duhu ga matsatstsan layi tuntu'be tayi da dutse ta fad'i 'kara ta saki daidai ya iso waje da sauri ya toshe mata baki tare da kinkimar ta ya shiga wani kango da ita. A tsautsayi ya daka mata tsawar cewa ta masa shiru cikin mamaki Lami tace "Tanko kaine me nai maka ka sake ni" kallon ta yayi "oh kin gane ni ashe aiko saina tabbatar ban barki kin kai labari ba yau babu me cetar ki a hannu na yadda kika haramta min auren ki shima wancan mayen da kika wulakanta ni akan sa saina tabbatar bazai same ki ba". Cikin karfin hali Lami tace "Tanko wulakancin ya isa haka ka sake ni kuma wallahi bazan yarda ba gobe saina kai kararka gurin me gari" dariya yayi "ki kai karata gun wanne me garin? Basai na barki da rai ba balle ki kai labarin" jin abinda yace yasa ta fasa kara tana kai masa duka ta ko'ina shi kuma yana 'ba'bbaka dariya kamar zararre. Ramatu na zaune lokaci zuwa lokaci ta kalli hanyar kofar shigowa ganin shiru babu alamar ta yasa ta mi'ke tana daukar hijab tace "a'a ni kalau kuwa Lami yau bata dawo ba bata irin wannan daren a dandali bari muga" fita tai ganin yar ma'kotansu abasiyya ta taho yasa Ramatu cewa "ina kika baro lami ko tana can"? Kai abasiyya ta girgiza "a'a ta ma riga ni tahowa saidai in a wani gun ta tsaya" jin haka yasa Ramatu wucewa ta nufi dandalin tana zuwa layin taga farantin da kud'i a baje a gurin salati tayi tana tattare kud'in tare da daukar farantin cikin mamaki ta kalli gabas ta kalli yamma babu alamar kowa da sauri ta fito a layin kamar zata kifa ta koma gida hankali tashe tan kururuwa azo a cece ina Lami tai nan gari ya hargitse aka d'ebo fitilu ana haska ko'ina tace ga inda taga farantin gurin suka je suka fara haskawa har cikin kangon gidan aiko sai gata kwance sharkaf bata motsi jikin ta harda jini da alama fayde akai mata innalillahi wa inna ilaihi raji'un guri ya kaure da salati Ramatu dake waje jiki na rawa tace "me

TYPING 📲 SAT, MAR 23/24 Yusrah Musa Abubakar 💞🌹 maman little Zaran aunty. 💫 ANNURI WRITER'S ASS💫 HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY GIDAN KARBAR MUTANE HANNU BIYU 🌹🥀 DA ZAMAN LAFIYA ANNURI HASKE LEKA GIDAN KOWA KODA MAKIYA NA KALLON KA RAMIN KURA SAI 'YA'YAN TA KIRARIN MU KENAN. Ya mai nasiha ga alumma muso juna mu rike gaskiya amana dan gudun kuna mu raya zuminci hanya ne na aljannah makiyin zumunci baya kusanci ceto ba ga wassu baitukan soyayya maula na daga masoyiyar ka Yusrah ta dumus yar Musa. _______________________ Allahu dan isar bawan nan da ka Aiko shine Muhammad rasulullah daya sauko me sansa ka fad'i ba shakka zai karko albarcinsa bani basira me fad'i ka bani hikkimar sarrafa waka alhadi idan nayita bata ga buri aji dad'i a kara kankame soyayyar manzo na. 💋YUSRAH MS ABUBAKAR MUHAMMAD💋. 23~AR-RAFI'U The exalter 24~AL-MU'IZZ The giver of honour 12~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Khaidinah. 🌄THREAT ND TREASON🌄 Episode 23 nd 24 Bayan kwana biyar da faruwar haka Tanko ya dawo daga d'an yawon shashancin daya je ko hutawa baiyi ba Mudi ya munafirta masa cewa Lami fa ta dawo ya kamata suje su lallameta kafin wannan d'an birnin ya biyota idan sukai sa'a ta amince zata aure shi yarda yai da shawarar Mudi yace gobe zasuje. Washe gari da magriba suka je kofar gidan Baffah suka sa aka yiyo musu magana da Lami tayi mamakin ganin Tanko har mamakin nata ya'ki boyuwa ranta a'bace tuna wulakancin dayai mata a dandali kwanan baya tace "meye ya kawo ka Tanko ko 'batan kai kayi tun wuri ka saitawa kan ka hanya". Tanko na shirin yin magana Mudi yai gyaran murya yana cewa "haba Lami kamar baki le'ka birni ba zaki mana wulakanci sannan baki tsaya kinji abinda zan fad'a miki ba kawai kika yanke hukunci". A fusace Lami tace "baka da wani abu da zaka fad'a min wanda zaisa na saurari Tanko kamar yadda ya tozarta ni a gaban kowa nima tun daga ranar na zubar dashi a rayuwa dan haka ka barni dan Allah naje nayi rayuwa ta". Zata juya Tanko ya katse ta "haba Lami ki tsaya ki fahimce ni muyi maganar gaskiya nasan na aikata miki kuskure banyi dadai amma kiyi hakuri kinsan ina son ki". "Na sani kuma na gode da soyayyarka gare ni saidai ka sani ka makara domin na riga na hakura dakai Tanko dan haka ka kyale ni nayi rayuwa ta". "Bazan rabu dake ba Lami har sai kince zaki aure ni kin rabu da wancan shashashan tsigalallan birni". "Kada ka sake zagin sa". A hasale Tanko yace "na sake shi dambun uban sa wato kinje ya zuzzuga ki shine zaki min rashin mutunci" "ba rashin mutunci nayi maka ba Tanko kawai na nuna maka gaskiya ne kayi hakuri bazan iya aurenka ba na riga na hakura dakai dan Allah ka fahimta ka rabu dani". Kai Tanko ya jinjina "shikenan na barki har abada kuwa jeki abinki" yana rufe baki Lami ta fad'a gida da sauri kai Tanko ya jinjina yana jan tsaki yace "lallai yarinyar nan ta kira ruwa saina gwada mata rashin imani na dan ko yayanta Ilyah bai isa jada niba balle ita" cikin zuga Mudi yace "to ai mutumi na kaine kayi sake taya zaka bari yar wannan yarinyar ta ri'ka kallon cikin idonka tana zazzaga maka rashin mutunci baka falleta da mari ba wanda saita ga wuta ba wallahi kada ka hakura ka dau fansar wannan abun da tayi maka" "fad'a batawa Mudi ai dole na sanyata bakin ciki kamar yadda ta sanya ni dole na rama cin fuskar da tai min kuma ta hanyar da kowa bazai ji dad'i ba muje kawai Mudi yau saina kora sosai kaina yadau zafi" wucewa sukai Mudi na sake zugashi da bashi shawarar yadda zaiyi. Zaman Lami haka babu islamiya yana damunta tana son shiga tana tsoron masifar Ramatu ta kasa fad'awa Baffah gashi tun ranar da aka kawo ro'kon arzikin ta Ramatu ta sake bud'e mata wutar talla kamar jaka wai saita tara kud'in da zata sai mata kayan d'aki Baffah yayi fad'an har ya gaji ya 'kyale. Lami na zaune a kofar d'aki tayi tagumi Baffah daya shigo cikin rashin jin dad'in ganin ta a haka yace "Lami lafiya meya faru"? Hawaye ne ya zubo mata tana kallon shi tace "dan Allah Baffah na rokeka ka sani a makaranta ko ta islamiya ce ni

u keyi ransa duk babu dad'i amma sakamakon Salamatu tayi masa magana yasa dole yai shiru bai amayar abinda ke cin ransa ba. Baffah baice 'kala ba ya kalli Ilyah dake gefe kamar ba babu shi a gun yace "saura kai Ilyasu muna sauraron ka meye matsalar ka". 'Dan tsaki Ilyah yaja yana kau dakai kamar bazai magana sai kuma yace "ni bani da matsala kalau nake rayuwa ta idan akan haka ka tara mu ni zan fita dan ina da gurin zuwa daya fi min wannan zaman". Kaiii duk kallon sa sukai a hasale Habu yace "Allah ya wadaran ka Ilyah wallahi kaji kunya kayi asara wannan d'abi'ar daka dauko sam babu inda zata kai ka sai halaka tun wuri ka gyara kafin lokaci ya'kure maka". "Ban sako dakai ba Habu kada na sake jin bakinka yace min wani abu idan ba haka ba ran kowa da yake nan saiya 'baci" Ilyah ya fad'a tare da mi'kewa ya kalli Baffah dake binsa da kallo kafin yace. "Kaja masa kunne ya fita harkata kafin ayi 'batacciya sai nayi abinda kowa zaiyi danasani". "Yau d'an halak haka nake son ji karka ragawa kowa" Ramatu ta fad'a tana hararar Habu. 'Diban takalmansa Ilyah yai zai fita Baffah ya dakatar dashi "kada ka fita Ilyasu bamu gama magana ba ka zauna ban baka izinin tafiya ba". Batare da Ilyah ya juyo ko ya dakata daga tafiyar da yake yace "dama umarnin ka nake nema saika sani abu zanyi basan zauna ba na fita zaka iya sawa a taro ni". Da kallo suka bishi yana fita Baffah da gabadaya zuciyar sa ke masa zafi take masa shiru yayi ya rasa me zaiwa Ilyah ya dawo kan hanya addu'ar nan kullum yi yake ba fashi amma abun na Ilyah gaba yake saidai bazai 'kosa ba zaici gaba da nema masa shiriya................... "To nima dai zan tashi dan na gaji bacci nake ji" Ramatu ta fad'a tana mikewa ta shige d'aki tare da rufo kofa. Har lokacin Baffah yana shiru ganin yanayin yasa Sabi'u cewa "kayi hakuri Baffah mun 'bata maka rai ka yafe mu na dauka idan muka samu zama zamu fahimci juna ashe saidai mu fahimci damuwa munyi kuskure bansan me zamuyi yanzu ba na kasa gane komai". "Me zamuyi kuwa daya wuce hakuri da addu'a dan Allah Baffah kayi hakuri ka kwantar da hankalin ka insha Allahu komai zai setu" Habu yai maganar. Ganin dai jiya iyau Baffah baice komai yasa Sabi'u cewa "BAFFAH ka gafarce mu dan Allah idan mun saka a wani hali". 'Dagowa Baffah yayi yana kallon su tare da girgiza kai yace "Sabi'u Habu Allah ya muku albarka baku ta'ba 'bata min ku farin ciki nane ina alfahari da samunku ina fata ku kasance cikin farin ciki har abada Allah ya tsare min ku ya shiga al'amarin ku ya baku 'ya'ya da matan aure na gari yasa ku gama da duniya lafiya duk abinda kuka san zaisa naji dad'i kuna kokarin yi min Allah yasa kuma ku samu masu yi muku". "Amin Baffah mun gode sosai". "Karku damu kuje ku kwanta" mi'kewa sukai suna masa saida safe ya rage daga shi sai Salamatu da Lami kallon Lami yai yana cewa "kiyi hakuri ke ba'a tambayi taki damuwar ba ko"? Kai Lami ta girgiza tana share hawaye cikin takaicin abinda taga Ilyah ya masa tace "ka gafarce ni Baffah ka yafewa yaya Ilyah abinda yake maka ka bishi da addu'a ka masa fatan gamawa da duniya lafiya shine fata na". Kallonta Baffah keyi yarinyar nan za'a tona kafin a samu irinta zai wahala shiyasa koda yaushe yake farin ciki da samunta matsayin 'ya gareshi sake kallonta yayi yana cewa "kada ki damu indai wannan shine burinki zan cika miki tashi kije ki kwanta" mi'kewa tayi tana masa saida safe ta tafi, numfasawa Salamatu tai tana kallon Baffah tace. "Malam na sani kana cikin damuwa a gidan nan mun gaza gyara zamantakewar mu badan bazamu iya ba sai rarrabuwar kai nayi tunanin a yau zamu magance matsalar mu amma sai naga abun yaci tura dan Allah malam kayi hakuri" kai Baffah ya girgiza "babu komai Salamatu tashi kije Allah ya mana sutura" Amin tace tana mikewa itama ta shiga d'akinta aka bar iya Baffah a tsakar gida yana sa'ka da warwara ya dad'e kafin ya mi'ke yana daukar buta yai alwala ya shiga d'akinsa ya fara nafila yana rokon daidaituwar al'amari a tsakanin zaman zuriyar gidan sa. MRS AL'AMEEN AHMAD CE 😘 MAI TAMBARIN YMA DUTSE 🏞️🏔️ JIGAWA STATE.

"nifa na gaji bacci nake ji, meye ne na tara mu haka abinda ban ta'ba gani ba sai yau ko wata sabuwar tsirfarce ta samu"?. Ba wanda ya kula Baffah dake kallon sauran yace "to alhamdulillahi ina godiya ga Allah daya nuna min wannan rana duk da banyi tunani ba na sani zakuyi mamaki zakuyi ta tambayar zuciyar ku meya faru akai kiranku ba komai bane dama na tara kune akan naji meke faruwa meke damunku kowa ya fad'i matsalar abinda ke ransa ina sauraron ku Salamatu mu fara daga kanki domin kece uwar gida kece babba"?. 'Dan shiru Salamatu tai tana tunani na 'yan mituna kafin ta d'ago tana kallon kowa tace "eh to gaskiya nikam ta bangare na babu komai ina wa kowa kallon kima da mutunci yara kuma na rikesu daya bana bambantawa ina yabawa da nagartarsu da kyakkyawar tarbiyyar da suka samu a gurin malam bani da bakin godiya gareka saidai nace Allah ya saka da alkairi kayi mana komai matsayin ka na me gida baka ta'ba gajiyawa damu ba ta bangaren abinci sutura harda kud'in kashewa na ihsani ka biya dukkan komai nauye nauyen dake kanka ka sauke ka karemu mu da karfinka da jarumtar Allah fatana a koda yaushe Allah ya kyautata ka kamar yadda ka kyautata mana" ta karasa maganar tana share hawaye. "Amin nagode sosai Salamatu da shedar arziki da kikai min ina da ya'kinin cewa ko bayan raina zan samu yabo a gareki" juyawa yai saitin Ramatu yana cewa "Ramatu saura ke na dawo gareki kema meke damunki me yake faruwa akwai abinda ake miki wanda bakya jin dad'in sa". Gyara zama Ramatu tai "nikwa ni akewa abinda raina baya so dan duk gidan nan babu wanda aka rainawa hankali kamar ni Kowacce bola aka d'ebo ni za'a lodawa saboda an tsane ni bansan me nai maka ba gara daka za'bi a zauna aji matsalar kowa sannan Ilyah ma yana da matsala domin munafikan yaran ka Sabi'u da Habu sun ware shi suna nuna masa 'yan ubanci komai su biyu suke babu ruwan su dashi". Wani kallo Habu yaiwa Ilyah yana cewa "shine yace miki ba ruwan mu dashi sau nawa muna binsa yana zamewa ko abinci da kike ganin muna ci mu biyu ga Ilyan nan ki tambaye shi har gobe idan zamuci sai mun masa magana amma yace Allah ya sauwake to ya kike so muyi iya so muna nuna masa baya gani kema bakya gani bari kiji wata magana daga yau baza mu sake........................... Katse shi Baffah yai "Habubakar bari kayi shiru haka Ramatu uwa ce gareka". "Ah dole malam ka gama 'kwarkwance su cewa su wulakanta ni kuma yanzu dan kar nace da hannunka shine harda wani kayi shiru ni uwarsa ce tab Allah ya suturu bu'kwui inji kishiyar 'konanna nikam ban haifeshi ba yaje can kabari ya nemi uwarsa na haifi wanda na haifa". Kowa kallon Ramatu yake da mamaki duk da dama ba ba'kuwarsu bace amma cewar Habu ba d'anta bane yaje ya nemi uwarsa a kabari bai kamata ba bata kyauta ba. Baffah yaji zafin hakan da tace amma ya share cikin kaiwa zuciyarsa nesa yace "Ramatu wannan shine abinda yake damunki sun ware Ilyasu a cikin su babu ruwan su dashi haka ne"?. "Eh haka ne basa kaunarsa kuma idan sharri na musu ko suna ganin na musu karya ka tambaye su basa kaunar Ilyah sam". Kai Baffah ya jinjina "shikenan naji matsalar ki bari nayi magana dasu" kallon Sabi'u yayi yana cewa "Sabi'u meye matsalar ka matsayinka na babba cikin 'ya'yana kaine jagoran gida". Fara magana Sabi'u yayi "ni Baffah damuwa ta rashin biyayyar da Ilyah yake maka da zama cikin samari yan shaye shaye da yake bugu da 'kari kullum idan muka ce yazo muci abinci ko kallon arziki baya mana matsayin mu na 'yan uwansa baida kamar mu a duk fadin duniya ko me zaiyi saiya yi shawara damu Baffah ka fahimtar dashi ka farkar dashi ka tuna masa matsayin mu a gunsa". Yana rufe baki Ramatu ta wurga masa harara tana cewa "dama har wani matsayi kuke dashi a gurinsa in kuna tunanin kuna da mahimmanci ku daina Ilyah ba sa'an shirmenku bane abinci kuma bazai ci daku ba wannan doka tace dana kafa masa har abada". Cikin 'bacin rai habu yace "to saime dan kin hana shi hakan bazai rage mu da komai b..................... "HABUBAKAR kayi shiru dan Allah ka bari Ramatu uwace a gunka" Salamatu ta fad'a tana d'aga masa hannu huci Hab

ganar yana yin wajen inda yai parking da motar da sauri Auwal ya bishi yana rike shi yace. "A'a Alpha kada kayi haka dan Allah mom bazata ji dad'i ba ka bari mu koma gida saika fada mata nima zanyi maka rakiyar ka nutsu" shiru Alpha yai ya kasa magana Auwal dake kallon shi yace "shiga muje" kaiya girgiza "bazan iya tu'ki ba" "ok bani key din shiga mu tafi" bashi yai yana shiga Auwal ya tada mota suka wuce zuwa gida. Har lokacin mom tana zaune a gurin ganin sun shigo da yanayin da Alpha yake ciki yasa ta fahimci basu sameta ba zama sukai mom dake bin Alpha da kallo tace "baku samesu ba"? Kai Auwal ya d'aga "eh mom sun tafi da binsu zaiyi amma na hana nace ya bari mu dawo gida yaje daga baya" kai mom ta d'aga tana kallon alpha tace "kaga auta na kayi hakuri in Allah ya yarda wannan yarinyar zaka aureta bari Abbanku ya dawo zan sanar masa sai musan me za'ai" shidai Alpha yana shiru baice 'kala ba Auwal daya mi'ke yace "ai mom wannan soyayyar tasu irinta ake so kaso mutum tsakani da Allah Alpha yana burgeni nima inaso ya aureta domin ta kasance farin cikin sace Allah ya tabbatar da alkairi" Amin mom tace tana sake kallon fuskar Alpha wanda ya shiga mood altering kawai baya cikin hayyacin sa dan girgiza kai tayi tana masa addu'ar samun nutsuwa a zuciyarsa Ramatu kam suna tafe tana zazzaga mata bala'i har suka hau mota bata daina kumfan baki ba kowa a motar sai mamaki yake Lami tari da bai kamata ba batai ba har suka sauka kowa a garin kallon yake ana ta tsegumin Ramatu taje ta taho da 'yarta haka suka shigo gida Baffah na zaune kan tabarma a kofar d'akinsa gefen sa Habu ne da Sabi'u suna hira sai ganinta sukai kamar an jefota ga Lami a bayanta ko kallon inda suke batai ba ta wuce d'aki karasowa gaban su tai tana kallon Baffah zatai magana sai kuma tana fashe da kuka tare da durkusawa. 'Dagowa Baffah yayi yana kallon ta tausayi da damuwa fal a ransa yace "Lami kiyi hakuri da irin uwar da kika samu ki dau kaddara ki jure wata rana sai labari kuma duk abunda zatai miki ki bita mahaifiyar kice kada ki sa'bawa umarninta kinji insha Allahu zaki samu nasara" kai Lami ta d'aga tana mi'kewa tace "nagode Baffah na gode da samun ubah na gari irinka me share hawayen 'yarsa". "Karki damu Allah ya miki albarka" Amin Baffah Lami ta fad'a tana wucewa da kallo suka bita duk su ukun tsaki Habu yayi yana cewa "Wai dan Allah Baffah yanzu haka zamu zuba ido mu bar yarinyar nan tana cin ba'kar wahala kamar ba a gurin uwarta take ba gaskiya nifa babah Ramatu ta kaini bango zan dau mataki akanta". Gyara zama Sabi'u yai "eh kayi gaskiya Habu dole mu gyara zaman gidan kamar ba mafad'i Baffah koda ace baka raye iyakaci kenan balle kana nan gamu amma ace gida ya lalace dole mu canza al'amarin gidan nan zamu zauna gabadaya yau da dare mu ji matsalar kowa mu gyara zaman mu kaji Baffah". Kai Baffah ya d'aga "to naji zancen ku kuma na amince domin nima ina son hakan ina kaunar ganin ahlina cikin farin ciki ina son naga suna walwala musamman yarinyar nan Lami ina jin tausayin ta a raina har bansan yadda zan kwatanta muku ba na amince kuyi komai kun cancanta ku 'ya'ya ne na gari". Kai Habu ya d'aga "shikenan Baffah idan anyi sallar isha zamu samu zama dukkan mu don magance damuwar gidan nan kowa ya fad'i abinda ke ransa". "Kwarai Habu kayi gaskiya haka za'ai Allah ya kaimu daren" Sabi'u yayi maganar yana mi'kewa yace "lokacin dawo da dabbobi gida yayi Habu taso muje" tashi habu yai suna fita yayin da Baffah ya bisu da kyakkyawar addu'a cikin jin dad'in samun su dayai matsayin 'ya'yansa nagartattu. Bayan sallar isha kamar yadda suka tsaya haka suka shigo suna shimfida manyan tabarma guda biyu Baffah ya zaune suma suka zauna ga Salamatu da Ramatu Lami na gefe kad'an da Baffah saida suka nutsu kowa yai shiru Baffah yace Sabi'u ya bud'e musu taro da addu'a. Duk hannu suka d'aga Sabi'u yana jero addu'o'i suna Amin Amin harya gama suka shafa sannan Baffah yace. "Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu". Duk amsawa sukai "Amin alaika salam wa rahmatullahi wa barakatuhu". Kafin Baffah yace Ramatu tayi farat tace

Musbahu yana daga zaune yace ""Naja'atu sake ta su tafi ki daina jawo wa mamanki zagi Lami zata dawo" Najat na kuka tana kallon sa tace "Abba bazan iya barinta ta tafi ba bana so tayi nisa dani mun saba" kai Musbahu ya girgiza cikin lallahi yace "kinga Najat nasani zata dawo ki bari su tafi" sakinta Najat tayi kamar gaske Ramatu na janta da gudu Najat ta kuma rungume ta". Zaro ido Ramatu tai tana cewa "ke anya wannan yarinyar ba 'yar shan jini bace yau nake ganin jaraba zaki saketa mu tafi ko sai naci malafar kan uban ki" takaici ne ya kama Musbahu lokaci guda ya mi'ke yana zuwa gaban Ramatu yace "Naja'atu ki saketa kinji ki daina sa tana ja miki alkaba'i" "Abba dan Allah ka 'kyale na bisu garin su". Ture hannunta Ramatu keyi tana cewa "uban wa zaki bi? Amma dai ba niba tabdijan lallai yarinyar nan baki da hankali garin mu zaki bimu? Aiko wallahi da sai kin yabawa aya za'kin ta" ta karasa maganar tana kallon Musbahu tace "kai marar zuciya kace ta sake min 'ya". Kallon yadda Najat ke kuka harda shid'ewa take yayi kafin yace "Naja'atu ki saketa idan na isa dake idan kin dauke ni a mahaifi" d'agowa Najat tayi zatai magana Musbahu ya dakarta da ita "karki magana basai kince komai ba ki sake ta" ganin ta 'ki sakinta yasa Musbahu ya daka mata tsawa tare da rike hannun ta yana 'bam'bare ta da 'karfi daga jikin Lami kafin ya kalli Ramatu yana cewa. "Ta sakar miki 'ya sannan ita ba mayya bace zaki iya tafiya". Wata uwar harara Ramatu ta sakar masa tana cewa "dallacan rufe min baki duk bakai ne sila ba na fad'a mayya kuma gidan ka kai kaso nazo tunda ka ta'bo ni idan ka cika d'an halak daga yau baku ba Lami ko tunanin ta kukai ban yafe muku ba" tana fadin haka ta ja Lami fuuu suka fita yayin da tabar su Musbahu tsaye cikin tsananin mamakin ta lallai Ramatu batasan san halacci ba batasan me kyautata mata ba. Da gudu Najat ta shige d'aki tana daukar waya ta kira Alpha bai d'aga ba a gigice ta sake kiransa nan ma dai no answer zata danna kira na uku taga ya biyo baya da sauri ta d'aga cikin kuka tace. "Hello Alpha dan Allah ka taimaki Lami ga babarta nan yanzu ta zo har garin nan ta tafi da ita kayi wani abu dan Allah Alpha kada ka bari ta tafi da ita". A firgice Alpha ya mi'ke tsaye daga zaunen da yake cikin mamaki yace "what ta tafi ko suna gidan naku"?. "A'a basa gidan mu ta tafi da ita yanzu dan Allah kayi sauri karsu shiga mota". "Ok shikenan karki damu bari naje" yana katse kiran da gudu yabar palor ya shiga bedroom yana dauko key din mota gabadaya ya fita hayyacin sa zai fita daidai yayan sa Auwal ya shigo saura kadan su gwaru da sauri Auwal ya matsa gefe yana kallon sa cikin mamaki ganin ya nufi mota yasa yabi bayansa yana cewa. "Kai Alpha 'kalau kake ina zakaje"?. Bai kalli Auwal ba yace "tasha zanje yanzu zan dawo". Da sabon mamaki Auwal yace "tasha amma me zakayo kake irin wannan saurin haka"?. Alpha na tada mota yace "wani abu zanyo Lami ce zata tafi garinsu zanje na dawo da ita". Zaro ido Auwal yai "ka dawo da ita kuma akan me sai kace wanda ka aureta". Alpha bai tsaya sauraron sa ba fuuu ya d'ebi mota da mugun gudu ya fita a gidan kai Auwal ya jinjina yana shiga cikin gidan ganin mom dinsu tsaye yasa ya karasa zaiyi magana ta katse shi. "zancen me kuke da Alpha ina zaije naji kana hana shi"? Zama Auwal yai yana sauke ajiyar zuciya yace "wai budurwarsa Lami ce zata koma garin ku shine zai bita bansan me zaiyo ba gaskiya Alpha ya zauce da yawa". Kai mom ta girgiza tana cewa "to nikam me zance Alpha yayi nisa a son yarinyar nan fatana da addu'a ta kullum shine Allah yasa rabonsa ce idan ya rasa ta a rayuwa bansan wanne irin hali zai shiga ba". Mi'kewa Auwal yai yana shirin fita a parlon yace "bari nabi bayansa ko a mashin ne" mom batai magana ba har ya fita samun guri tai tana zaman jiran dawowar su. A tasha ya samu Alpha yana ta duba motoci duk ya had'a gumi karasawa yai yana cewa "ka gansu ne ko sun tafi"? Kai Alpha ya girgiza "a'a ban gansu inaga saidai naje mu tafi da Najat ta raka ni garin idan ban ganta ba hankali bazai ta'ba kwanciya ba" ya karasa ma

an kwatance. "Kana jina kayi shiru ko? Amma bari na gama idan na d'ebo maka yan sanda zakai bayani". 'Dan kallon gefen da take Musbahu yayi yana cewa "ki kwantar da hankalin ki dama Lami ba daukota nayi dan na raba ta dake ba karatu zatai kuma tunda bakya so shikenan muje ki tafi da kayarki gida" washe baki Ramatu tai jin abinda yace tace "uhum d'an gari ba d'an garari ba muje yanzu ta had'a kayanta mu tafi kaima baka fi jin dad'i ba amma abu kamar naka kabi ka kanainaye saboda kwadayi da son zuciya" suna tafe tana masa bala'i mutane sai kallon ta suke suna mamakin a inda Musbahu ya samota. Suna shiga gidan ta gansu zaune suna karyawa salati ta saki tana cewa "Lami ahh dole ki 'ki zama kauye kiyo birni inda zaki ci abinda kike so tabdijan to maza taso daga yau maganar cin abu mai dad'i ya 'kare zaki koma garin da kika fito kauye inda kika fi wayo". Duk d'agowa dukai Lami data zaro ido waje cike da tsananin mamaki take kallon Ramatu yayin da mama tace "baiwar Allah wace ke daga ina me kike anan"? Hararar ta Ramatu tai tana cewa "a lallai kam samun gu harda zage zage ai ba dole saikin sanni ba wacce nazo gurinta ita ta sani". Kallon Lami mama tayi taga ta sunkuyar dakai tana share hawaye wato inta fahimta babarta ce wacce Musbahu yake bata labari mafad'aciyar nan mai jawo fitina kara kallon Ramatu mama tayi tace "kiyi hakuri karaso ki zauna". "Zama? Zama fa kika ce? Dama shi nazo yi banzo da niyyar ko kallon arziki nayi muku ba dan haka ki zuba min ido kawai shine naki kija bakin ki kiyi shiru" maida hankalin ta kan Lami tayi tana cewa "ke kuma dan ubanki da kika tsaya sauraron mu zaki tashi ki dauko kayan ki mu tafi ko saina fasa miki jiki da duka shashashar yarinya kawai". Mi'kewa Lami tai cikin damuwa tana shiga d'aki hawaye na zata hado kayanta Naja'atu dake ta bin Ramatu da kallo tace "dan Allah ki 'kyale mana ita anan meyasa zaki raba mu". Wani kallo Ramatu tayi mata "ke kuma asuwa kare da gudun layya ki bari nayi da tsofin ki dan ko kallo su d'in ma basu ishe niba kin gane". Kuka Naja'atu ta fashe dashi cikin takaici tana kallon Ramatu daidai Lami ta fito da kayanta itama tana kuka tazo gaban Musbahu tare da durkusawa cikin kuka ta soma magana. "Abba zan tafi dan Allah kuyi hakuri zamana daku idan na ta'ba muku rai ku gafarce ni ba lallai mu sake had'uwa ba a rayuwa amma ina fata kada ku manta dani zan tafi mama ku yafe ni" ta karasa maganar da tsananin kuka sosai kasa cewa komai Musbahu yayi sai kallo da yake bin Lami dashi cikin tausayawa tasowa mama tayi tana zuwa ta d'agota tare da share mata hawaye tace. "kada ki damu Lami ki daina kuka kinji ai bamu rabu ba tunda zaki auri Alpha wata rana zaki dawo kusa damu mu zauna tare iya rai da mutuwa tashi ku tafi ki kasance me wa uwarki biyayya kada ki sa'bawa umarninta in Allah ya yarda zaki zamo cikin nasara". Mi'kewa Lami tayi tana goge hawayen fuskarta da d'an murmushi kadan tace "nagode mama Allah ya saka da alkairi irin ri'kon da kika min". Kai mama ta girgiza "karki damu kinji Allah ya tsare". Karaso Ramatu tay tana fisgar kayan hannun Lami ta figeta tana cewa "ke dan 'kwal ubanki bariki nace ku nuna min kun bar ni a tsaye so'ko'ko ya 'kawar bora suna ta karanta miki kalaman tsiya wallahi baki isa ki aure a garin nan ba ko ke mayya ce uban Alpha zaki aura ba Alpha ba zaki zo mu tafi ko sai nayi miki duka" ta karasa maganar tana jan hannunta fuuuuu sukai waje, fashewa Najat tayi da kuka da gudu ta biyo bayan su ta rike hannun lami tana cewa. "Dan girman Allah na roke ki kada ku tafi ki barta anan Lami ki tsaya". Janta Najat keyi ta tirje ta'ki bari Ramatu ta tafi da ita cikin masifa Ramatu ta juyo tana cewa "ke sakar min hannun 'ya dan buhun ubanki ko tare aka haife ku"? Yau nake ganin mayyar yarinya zaki saketa ko saina ham'bare ki". 'Kin sakinta Najat tayi ta 'kankame Lami tana kuka sosai mama na kallon su itama sai hawayen take ta kasa magana. "Dake nake kika tsaya kina kallo na ko nayi miki kama da gyatumarki ne kizo ki janye min wannan mayyar 'yar taki data hana mu tafiya" Ramatu ta fad'a tana kallon mama.

cikin zaure ya samu me anguwa da tsirarun mutane sunzo gaida shi zama yayi bayan sun gaisa yace "dama naji wata magana ne a bakin mutane shine nake so na tabbatar wai jiya an kawo wata mata gidanka ta kwana"? Kai me anguwa ya d'aga "eh shakka babu zahiri jiya nikam ina barci ma aka tashe ni nayi mamaki dana ganta harda rauni a goshi wai ana ihun barawo aka rad'e ta ba'a sani anyi tunanin barawon ne shine aka kawo ta nan ta kwana kafin yau ayi bincike a kanta dan ni tsoro ma ta bani da fari, baka ji zagi iri iri ba a bakinta da diban albarka sai loya ashar take kamar ba musulma ba". Shiru Musbahu yayi na d'an lokaci kafin yace "zan iya ganinta"? "Eh ba matsala zaka iya Bismillah muje tana kewayen bangaren gidana domin ban bari ta kwana cikin gidan ba domin yanzu rayuwa ba tabbas mutane ba abinda yarda bane kar naje da dare ta tashe tayi mana wani abu ta gudu shiyasa nasa aka kulle ta amma muje ka ganta" mi'kewa sukai suna zagayawa Musbahu na binsa yana mamaki a ransa saida yaje ya tabbatar kamar a mafarki ya ganta zaune akan tabarma tana karyawa ga bandeji a goshinta kai ya jinjina yana cewa "Ramatu dama nasan haka zata faru zargina ya tabbata" d'agowa Ramatu tai tana kallon sa tace "dama kasan haka zata faru meh? annamimi shiyasa ka dauko min 'yata gashi nan a garin biyoka na dauke ta wani d'an Allah tsinen ya buga min sanda jiya wallahi ka sani bazan ta'ba yafe maka ba Allah ya isa ce zata rabamu" da mamaki mai anguwa dake gefe a tsaye yace "amma dai tana da ta'bin kwakwalwa ko idan ba zararre ba babu wanda zai ri'ka magana kamar haka" tun Musbahu baiyi magana ba Ramatu tace "tsohuwar kace me ta'bin kai ba niba dama wa ya sako dakai harka dauka in banda yawon gulma wanda ya cuce ni nake wa magana ba kai d'an gayyar sod'i ba bai shafe ka ba dan haka kaja bakin ka kayi shiru idan kuma ka matsa zakaga tashin hankali in kuma akan wannan d'an iskan tuwon da kokon da kuka kawo min ne saika fad'a na biyaka donni ba matsiyaciya bace irinka😲" tofa wai ikon Allah sai kallo fad'an daya fi karfin ka akace ka mayar dashi wasa me anguwa mamaki ne ya rufe shi harya kasa magana sai ido da yake binta dashi lallai matar nan ba 'yar arziki bace da yasan abinda zata saka masa dashi kenan wallahi da bazai karbeta jiya ba saidai ta kwana a layi ko tasan inda dare yai mata. Katse masa tunani Musbahu yayi da cewa "dan Allah me anguwa kayi hakuri ta sanadi nane da duk haka bata faru ba kai da baka santa ba kaine zakaji mamakin abinda datai maka wannan halin nata yana daya daga cikin butulci irin nata................. Yana rufe baki Ramatu tace "tsohon ka ubanka Saboh shine butulu ba niba" kai me anguwa ya jinjina yana cewa "tabdijan Allah ya sauwake kada Allah ya kara hada ni da irin ki Musbahu ta tashi ku tafi" me anguwa ya fad'a cikin takaici mi'kewa Ramatu tai tana sake kai lomar tuwon tace "basai ka koreni ba wata tsiyar ce a gidan naka badan kana me anguwa anacin na haram ba 'beran masallaci ma bazai fad'a maka babu ba" daukar kofin kokon tayi ta karasa shanyewa kafin ta d'ure wainar a leda tana cewa "ga gidan ka nan na bar ma saika dafa ka cinye dama in banda kaddara me zai kawo ni garin balle nazo gidan ka wannan me ba'kin idon ne ya jawo komai" tari me anguwa bai sake yiba har suka fita suna tafe tana cin waina a layi ga kafarta ba takalmi kuma ko a jikinta gajiya Musbahu yayi ganin sai kallon sa mutane keyi yace "dan Allah kibar cin wainar nan a layi nan fa ba karkara bace ki bari sai munje gida" harararsa tayi "to ubana dama an fad'a maka idan naje gidan naka zama zanyi ba arziki ne ya kawo ni ba" bai bi takan maganar da take fad'a ba yaci gaba "haba Ramatu gaskiya baki kyauta ba tsakani da Allah yanzu Saida kika biyo yarinyar nan da kinyi hakuri ma da anyi musu hutu zan mayar miki ita..................... Katse shi Ramatu tay "au haba jimin munafiki a gidan uban wa harda zaka mayar min ita to bana so na hutar dakai kuma kasa Allah a ranka ban yafe maka wannan ciwon da aka ji min ta sanadinka ba" ta karasa maganar tana sake kaiwa lomar waina Musbahu ikon Allah kawai yake kallo dan gaskiya fitinar Ramatu tafi karfin gab

garin ina ruwa na da wani barawo da kuka biyo wallahi Allah ya isa ban yafe muku ba" mamaki ne ya kama su wani daya furmutso ya le'ko cewa yake "ga barawon can fa an kama shi yana hannun matasa ita kuma wannan me take anan naga an kewaye ta ga jini a gaban goshi"?. Wata uwar harara Ramatu ta sakar masa tana cewa "au tambaya kake zakuyi bayani duk sai kun had'u da masifa bazan ta'ba yarda ba tunda kukai min rauni". "Kunga kamar naga bata hayyacinta ku tafi da ita gidan me anguwa ta kwana da safe ayi komai" wani da yake rike da bindigar mafarauta ya fad'a yana kallon sauran mutanen. Kallonsa Ramatu tayi "ubanka ne baya hayyacinsa amma ni nasan abinda nakeyi" wanda ya bugeta kam yana gefe ya kasa magana shi wallahi da yake a rud'e yake ganin yai kamar naminji ya daka "baiwar Allah tashi muje a raka ki gurin me anguwa" mi'kewa Ramatu tai tana cewa "uban gurin me anguwa zaku rakani dama gurin sa akace muku nazo ni gurin Musbahu nazo wani ri'kekken d'an mafiya mai sace yaran mutane da sunan zasuyi karatu idan yaga kwana biyu abu ya tsirga saiya sayar maka da d'an ka shikenan idan kana jina ka fito da kai nake" mamaki ne ya kama kowa a gurin lallai kila ta samu ta'bin kwakwalwa dan haka babu wanda ya biyeta da'kyar suka lalla'ba suka kaita gidan me anguwa dan ta kwana kafin gari ya waye ayi bincike koda wanda ya santa. Washe gari Musbahu na zaune a irin gurin me sayar da shayi yaji ana labarin yaji wani na cewa "kai jama'a ban taba ganin mace fitinanniya irin wannan matar ta jiya ba ta zage sai zagin mutane take" dariya d'ayan yayi yana cewa "humm kai dai bari kawai nifa nafi zaton mahaukaciya ce" me shayi dake tafaman shekawa yana mikawa yace "tab ba wani hauka daya sameta wallahi in kaga irin haka dama hali ne a jikin rai wazai yi fatan ace wannan uwarsa ce Allah ya kiyaye" Wanda yazo yanzu ya zauna ne ya tari zancen da cewa "ai abokai babu abinda zai baka dariya kamar da tace wai tazo gurin wani d'an mafiya ne mai sace yara da sunan zai sa su a makaranta idan kwana biyu yaji anyi shiru saiya sayar maka da d'an ka" dariya suka sa Musbahu dake zaune jin abinda suke cewa yasa ya shiga tunani kodai Ramatu ce ta biyoshi yasan zata iya ba karamin aikin ta bane kar abu yai nisa ma ta jawo masa masifa magana taje gurin hukuma bari yaje ya gano da mamaki fal a ransa ya kasa magana mi'kewa yayi yabar gurin dan yaje ya tabbatar abinda yaji suna fad'a gaskiya ne. Gida ya koma ya samu mama a waje tana d'an ayyukan safe ganin sa haka yasa tace "lafiya naga kamar akwai wani abu da ke damunka"? Zama Musbahu yayi yana cewa "eh ba lafiya ba yanzu dana baro gurin baban Khairat me shayi naji wani zance wai jiya wata mata tazo tana neman gidan Musbahu d'an mafiya yana sato yaran mutane yazo ya sasu a makaranta bayan kwana biyu idan yaga iyayen yaran sun dauke kansu saiya sayar dasu shine tsoro ya kama ni kar naje ko Ramatu ce kinsan zata iya zuwa". Zaro ido mama tai cike da mamaki tace "tofa gaskiya ne ma itace tunda kaji tace Musbahu kuma yana sato 'ya'yan mutane ai kasan itace yanzu tana ina" sauke ajiyar zuciya yai yana cewa "tana gidan me anguwa naji suna cewa" "to mezai hana kaje ka gani idan ita dince nifa bana son gayyar fitina sai a bata yarta mu samu salama tunda abun haka ne" kai Musbahu ya girgiza cike da damuwa yace "ina son yarinyar nan ta zauna a guna tayi karatu bana son ta koma wannan 'kauyen" "to ya zamuyi bamu muka haifa mata 'yaba dole mu ha'kura mu taba kayarta inda rabo tunda ga Alpha zai aureta kaga dai zata dawo kusa damu" mi'kewa Musbahu yayi "to shikenan bari naje na gani Allah yasa ba ita bace" "Amin mama tace daidai ya fita su Najat sun fito a d'aki suka ce "wace abban mu ke cewa Allah yasa ba ita bace"? Juyawa mama tai tana kallon su tace "ba kowa kuzo kuyi mana kayan karyawa" karasowa sukai Naja'atu ta dauki wu'ka ta soma firar dankali Lami kuma ta tafi kitchen zata dora tunkuyar shayi" Yusuf dake tsaye kusa da mama yace "to ni kuma me zanyi" kallonsa mama tayi "me zakai kuwa kana namiji aikin mata ne amma zauna ka taya ni d'aurayar kwanuka" kujara yaja ta roba yana zama suka fara. A kofar gida

a iyaka dashi babu shi ba 'yata har abada ehe". Ci kanki Baffah baice mata ba tayi hanyar fita da sauri da wasu ru'babbun takalma a 'kafarta da kallo Baffah yabi ta baice mata kar kije ba ko dawo ko bada yawu na ba ya share ta tayi gaban kanta "malam bakace min komai ba"? Ramatu ta dakata tare da juyowa tana kallon sa dauke kai yayi daga saitinta bai tanka ba, "malam kana jina kayi shiru wato baka so naje na taho da 'yata ko"? Jin har lokacin yayi mata banza yasa tace "malam ko zakace daga wudil idan na dauko Lami na zarce gidan mu wallahi bazan fasa ba sai naje ballantana baka tanka min nikam nayi gaba malam sai ayi zaune ayita jiran tsamani" tana kaiwa nan tayi gaba. Shiru Baffah yayi yana sake kallon kofar gidan gashi magriba ta kusa ya tabbata kafin taje anyi sallar isha ba sanin anguwar tayi ba kawai saboda neman rashin zaman lafiya ta d'ebi kafa ta tafi........................ "BAFFAH" jin an kira sunan sa yasa ya d'ago ganin Sabi'u yayi tsaye da murmushi a fuskarsa yace "zauna man" zama Sabi'u yayi yana cewa "Baffah ga tsire inji Habu yace a taho ma dashi daga kasuwa ba yanzu zai taho ba ni kuma ga kayan marmari na sayo maka Baffah kasha" kallon Sabi'u Baffah yayi yana cewa "to sannun ku da kokari Allah ya muku albarka ya 'kara bud'i ya haskaka lamarin ku" "Amin Baffah kuma na had'u da malam Yahuza yace na gaishe ka" "ina amsawa sosai Allah yai albarka" mi'kewa Sabi'u yayi yana cewa "Amin Baffah" kafin ya dauki buta ya d'ebo ruwa yana mi'kowa yace "lokacin sallah yayi Baffah" kar'ba yai cikin jin dad'i yace "Allah yayi albarka abun da kuke min Allah ya baku 'ya'ya masu hali irin naku su rama muku Allah yasa su faranta muku" "Amin Amin Baffah mun gode da addu'ar ka garemu" "a'a ba komai Sabi'u jeka maza kayi alwala ka taho masallaci kar lokaci ya 'kure" to Sabi'u yace yana shiga d'akin Salamatu itama ya bata nata sannan ya fito yana daukar butar da sauri jin ana neman shiga sallar. 'karfe sha biyu da kusan rabi na dare Ramatu na cikin garin wudil tana bulayi tayi nan tayi can ta rasa inda zata sa kanta da wani mutum suka had'u da sauri tace "dan Allah kasan wani Musbahu"? Kai ya girgiza "ban sanshi ba zaki iya karawa gaba" yana fadin haka yai gaba da harara Ramatu tabi shi tana cewa "ji min mitsiyaci kada Allah yasa ka sani shashasha kawai mai ba'kin hali" cigaba tayi da tafiya sai tambaya take kowa yace bai san shiba takaici ne ya kama Ramatu ga gajiya ga yunwa harda bacci take ji ganin ta rasa mafita ga jama'a sun fara raguwa a layi sai ihun karnuka yasa ta samu wani bakin shago ta zauna tana zafga hamma ta kalli gabas ta kalli yamma. Tsaki taja tana cewa "wannan wacce irin ba'kar jaraba ce ace idan mutum yazo gari baida kowa shikenan ya zama bola ba Wanda zai kula ka balle yaji matsalar ka ya taimake ka bari na tsaya na kwana anan din kar nayi gaba na had'u da kare gari na wayewa zan cigaba da cikiya................................ Ihu taji an kurma da karfi ana cewa "ihuuu jama'a ku fito 'barawo ku bishi gashi can yayi ta nan ku dauko abin duka haba da sauri Ramatu ta mi'ke tsaye tana gyara daurin zani tace "tofa yau nake ganin bankad'a iri iri wanne irin barawo kuma........ji tayi ana gashi can ku harbeshi kada fa ku bari ya tsere kallon gurin tayi aiko ta hango barawo yana cin gudu ana binsa ganin ya nufo wajen inda take yasa da sauri tayi gaba a guje taje shan kwana a bisa tsautsayi ji kake gammm!!!! Tayi karo da mutum tuni tayi baya rim ta fad'i cikin azama mutumin ya d'aga kokarar dake hannunsa ya buga mata a goshi yana saki ihu yace "kuzo da sauri ga barawon na kama shi" 'kara da kururuwa Ramatu keyi tana cewa "shikenan mitsiyaci ya kashe ni ya fasa min goshi Allah ya tsine maka bankad'adde mugu azzalumi". 'Duuuu jama'a sai tittid'owa suke kamar anyi kiranye tuni aka cika guri baka jin komai sai hayaniya wani daya dalle Ramatu da gitila irin ta kamun 'barayin nan yace "kai abin mamaki mace ce ai? Ke kuwa me zaki sata a daren nan kina mace"?. Haushi ne ya kama Ramatu ganin zai raina mata wayo tace "sata? nayi maka kama da 'barauniya tsabar mugunta kun fasa min goshi daga zuwa na

e nema masa auren Lami ba haku yai ba. Abokin Tanko Mudi wanda ba'a ganin tsakanin su shi Tanko ya samu yana fad'awa matsalar sa yace kuma ya bashi shawara Mudi yace masa kawai suje su samu Lami idan suka hure mata kunne tuni zasu rusa ala'kar ta da d'an binnin saiya aureta Tanko ya yarda haka zaiyi idan ya samu ya shawo kanta saiya lalla'ba ya saki Karime tunda d'akin sa daya ne. Lokacin da Tanko ya samu iyayen sa da wannan maganar sunyi mamaki kuma ransu ya 'baci cikin fad'a Delu tace "a lallai Tanko ka raina mana hankali wa ma naji kana zaka aura Lami ko? To wallahi ko Ramatu ce baka isa ba aidai itace ta haifi Lamin ko? gaskiya Tanko ka cika mara tunani Lamin data za'bi birni ta share ka ta manta dakai shine yanzu saboda baka da zuciya kai kuma kake kokarin rufa mata asiri bayan ta tona maka kai kuma sakarai kawai". Shiru yai yana sauraren su malam balah shima da haushi ya gama cika shi yace "kai Tanko kada ka kuskura naji ka sake firta sunan Lami a gidan nan baka da hadi yanzu da ita ko mutuwa zakai baka isa ka auri Lami ba kuma abinda na yanke kenan" tashi kaba mutane guri shashashan banza shashashan wofi" tashi Tanko yai yana fita a majalisar su ta matasa masu shaye shaye yan iskan gari yaje ya zauna ba sukuni kowa yana harkoki suna ta busa haya'ki amma shi yayi shiru ransa a mugun'bace. Ta'bo shi Mudi yai yana bashi sigarin dake kunne yace "mutumi na kadan busa ko zaisa ka kadan ji dama dama" kai Tanko ya girgiza batare daya kalli Mudi ba 'kara matsowa kusa dashi Mudi yai yana yin kasa da murya saboda Ilyah na gurin yace "aboki na ko akan maganar Lami ne su baba sun amince"? Kai ya sake girgizawa yace "taya zasu amince sai fad'a suke min da ihu wai ban isa ba kuma wallahi idan kaga ban aure taba to numfashi nane ya yanke domin ina son ta bazan yarda ta auri wani bayan niba ko meye zai faru har kisa zan iya yi" kasa da murya Mudi yai yana cewa "kaga Tanko ka daina d'aga harshen ka dole ne na taya ka cika burinka ka shirya gobe zamuje gurin ta muji ta bakinta in ta amince saika dauketa ku gudu kaje can wani gari ka aureta daga baya kamar shekara biyar sai ku dawo nasan duk tsiya idan kuka dawo baza suce komai ba dole su barku kuyi rayuwar ku wai mutum da ransa da lafiyarsa a hani shi jin dad'i"?. Tsaki Tanko yai "gane min hanya makaho yaso gulma amma ai su ba komai suke ganewa ba nabar haka a gigin tsofa ke damunsu amma zan saita musu zama" kai Mudi ya d'aga "yauwa aboki gaskiya suna takura maka gara ka nuna musu kaima na zamani ne d'an duniya ne shiyasa ni nake murna da nawa suka gangara tun ba yanzu ba gashi ni kadai suka haifa ba wa ba 'kani ga gadon gonaki sai fanjan fanjan nake da kud'i kaima ina maka fatan haka" kai Tanko ya jinjina yana cewa "idan mutum ya'ki mutuwa sai a 'karasa shi" dariya Mudi yayi yana cewa "kai mutumi na kana wuya ina binka da fetur haka ake so ka nuna kai d'an zamani ne me zama kan uwar d'an yaro, kaga karbi haya'kin nan ka d'an ja zakaji dad'i" karba Tanko yai yana sawa a baki Mudi ya sake dauko wata ya kunna. Kwana uku da zuwan su Musbahu Ramatu ganin babu Lami babu alamarta yasa tace "malam nifa kwana biyu banga Lami ba ina taje ne"? Kallonta Baffah yai "au sai yanzu zaki tambaye ni inda take duk da baki lura ba? Ta bi ubanta sun tafi" so'ko'ko Ramatu tayi tana kallon Baffah tace "waye kuma ubanta bayan kai"?. "Musbahu ranar da suka zo ro'kon arzikin ta yace an kusa komawa makaranta kuma yaransa sun damu da rashin ganinta shiyasa nace kawai ta shirya su tafi". Zaro ido Ramatu tai tana mi'kewa tsaye tace "meeehhh😲 sun tafi kuma? Wai komawa gurin sa ta sakeyi kenan lallai Lami ta raina min hankali tabdijan wallahi bazai yuwu ba sai naje na taho da 'yata bana son harkar gidadanci dan yaga wancan karon daya dawo da ita na share shi shine yake neman tashin hankali aiko ya sameshi tunda ya ta'bo ni". 'Daki ta wuce tana masifa ko kayan jikin ta bata sauya ba du'kun du'kun haka ta dauko kud'i ta fito tana cewa "malam nayi wudil zan taho da 'yata tunda naga idan na zuba ido za'a raba ni da ita ayi min haifi in mora ina zuwa zan wuce ofishin 'yan hisba sai an man

HMS ABUBAKAR. 21~AL-BASIT The extender 22~AL-KHAFID The abaser 11~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Sajidinah. 🌹🥀🌹🥀🌹🥀🌹 🌄DISCONTENT🌄 Episode 21 nd 22 Wata daya tsakani Musbahu da baban alpha suka zo nemawa masa auren Lami Baffah yayi farin ciki yayi godiya ga Allah ya kara yayi addu'a da fatan alkairi da sanyawar albarkarsa da samun zuriya ta gari sannan ya ro'ki Baffah akan zai tafi da Lami su Naja'atu sun damu ta koma tunda hutu ya rage saura sati daya a koma Baffah kuwa dad'i yaji a take yace ta dauko kayan ta su tafi itama Lamin taji dad'i sosai da sauri kuwa ta had'a komai bata ta shirya ta bisu suka tafi. Bayan tafiyar su Ramatu ta dawo batasan me ake ba hakkinta na uwa itama dole ya fad'a mata tasan abinda ke faruwa bazai biye halinta ba zata wuce yace. "RAMATU" da sauri ta waigo ganin kaya turus a gaban Baffah yasa ta washe baki tana cewa "na'am malam gani nazo ne"? "Eh magana zamuyi" kamar an jefota yaga taxo ta zauna tana le'ken babbar ledar dake gaban sa yace "to malam gani nazo in kaji kira an samu amma banda kiran dan sanda". Shiru Baffah yai yana kallon ta ganin baice komai ba tace "malam ka kira ni kuma kayi shiru"?. Sauke ajiyar zuciya yai yana cewa "ina fata yanzu kam zaki fahimce ni duk da nasa ke baud'addiyar mace ce wacce ba'a gane inda al'kibilar ki take amma ya zama dole na fad'a miki yau dazu bayan fitar ki Musbahu yazo tare da wani mutum wanda d'ansa yake son Lami sunzo nema masa aurenta kuma na basu duk da banyi shawara dake ba amma ya kika ce kema mahaifiyar tace kina da hakki a kanta ga dai kayan da suka kawo nan da kud'i". Zaro ido Ramatu tai gani kud'i daure a kyaure dami guda baki washe tayi tana cewa "ayya malam ai bakai laifi ba meye a ciki basai kai shawara dani ba ai kaida kaya mallakar wuya ne" ta karasa maganar tana dauko 'kwallelan goro daga cikin ledar ta soma garza tana cewa "yaushe zasu sake dawowa ne nifa ban gane cewa mutumin nan yana son Lami ba saiyau kace gara daya dauke ta suka tafi gashi harda abin arziki ta samo saurayi d'an birni" kai Baffah ya jinjina lallai kam wato idan akace mutum nada son zuciya sai a hankali yayi mamakin ganin yadda Ramatu ta amince Shi dai farin cikin sa daya Lami zata bar kauyen nan taje ta zurfafa karatun ta tayi ilimi ta cika burinta. "Malam me kake tunani"? Ramatu ta fad'a tana sake cewa "malam aban nawa kason zan rabawa dangi" . Cikin mamaki Baffah yace "kason me"? Kud'in dake gefe ta nuna tana cewa "garin su Mariya zanje in an jima nasan kayan lambu sunyi na saro Lami ta fara min talle" "telle kuma"? Baffah ya fad'a yana kallon ta "eh talle saita tara kud'in da za'a saya mata yan kayan d'aki da kayan katako" "a'a indai dan wannan ne ki barshi ni zanyi mata komai". Daina cin goron Ramatu tayi bakinta daya sauya kala zuwa ja ta bud'e shi tana cewa "amma dai malam zilama ce tasa kace haka"? Wani kallo Baffah ya mata tare da maimaita kalmar "zilama"? Ba kunya Ramatu tace "eh zilama nace kake dashi malam bada zilan zilan irin taka ba da had'ama taya zakace kaine zakai mata kayan d'aki dan karka bani ko sisi shine kace wani kaine zakai mata to wallahi bazan yarda ba domin nice nayi na'kuda na haifeta na fika iko da ita wato dan ka je ka sayi ru'babbun Kaya shine kace a barmaka ragamar komai a hannun ka". "Ramatu meyasa ko kadan baki da tunani? Ni kike cewa haka? Bansan ranar da zaki hankali ba shiyasa kullum nake godewa Allah da bai sa Lami tayo halinki ba" mi'kewa Ramatu tai "malam me kake nufi kenan karya nayi"?. Ransa a had'e yace "ban sani ba ban guri" wucewa Ramatu tayi tana cewa "wallahi kome zai faru bazan yarda malam ehe idan kuma ba haka ba saidai a fasa auren" Baffah bai sake kulata ba ya tattare kayan da kud'in ya shiga d'aki. Nan labari ya kardad'e gari ko'ina sai gulma ake wai Lami tayi saurayi d'an birni zata koma can tabar rayuwar kauye lokacin da labari ya iske Tanko hankalin sa ya tashi haka nan yaji yaji bayaso ta auri wani nan ya fara shiga da fita ya rasa inda zaisa kansa yaji dad'i dan haka ya yanke shawarar zai samu iyayen sa suj

min afuwa ita fa mahaifiya tace bazan iya jure fushinta a kaina ba hakan barazana ne ga zuciya ta da nasan abinda zai faru kenan bazan bishi ba zanyi ta hakuri ina zama cikin duhun jahilci na😔. Kallon ta Baffah keyi cikin tausayawa da rashin jin dad'in ganin yadda take kuka kamar ranta zai fita ya shiga jin wani irin d'aci na masa yawo a makoshi kirjinsa na zafi a fusace ya mi'ke yana zuwa kofar d'akin Ramatu yace "ke Ramatu kina ina? Caraf Ramatu ta bankado labule tana cewa "ga yar mutum biyu jikar mutum hud'u me ya faru ake nema na"? Ran Baffah a 'bace yace "kinsan Allah Ramatu ranki zaiyi mugun 'baci akan yarinyar nan sam babu d'igon imani a tare dake saikin kashe ta da 'kuncinki da kike sanya ta ciki to bari kiji yau kam kin kaini bango kibi a sannu zan iya yin komai". Shewa Ramatu tai "ahayye nanaye yau ake yinta tofa ran maza ya 'baci lallai malam wato nan din me kake son nunawa zakasa nayi abinda banyi niyyar yiba Lami ce nace na sallama ta yadda ta za'bi tabi bare to yanzu ma haka ta dauka baren ya fini ta koma gunsu nace babu ni babu ita har raina haka abin yake babu kuma wani abu da zai canza". "Haka kikace ko Ramatu"?. Tana kad'a kai kamar zata hau bori tace "eh nace hakan malam, meye ko kana tunanin zanji tsoron kane? Nasan karshen abun bazai wuce kace zaka sake niba kuma ni yanzu dama haka nake so na samu 'yanci na nayi yawo a gari naci uban kowa na taka na murshe na wanke biyar na tsoma goma na fantama duk inda raina yake so" shiru Baffah yai na d'an wani lokaci kafin ya juya yana kallon Lami da har lokacin take kuka yace. "Ramatu idan har baki yafewa Lami ba nima bazan ta'ba yafe miki abinda kikai min ba a rayuwa zaki ga karshen ki shiyasa nake miki kashedi tun wuri ki tuba ki canza kafin lokaci ya'kure miki". Yana juyawa Ramatu taja tsaki tana cewa "wa'azi da zaka gane da ka dena dan wallahi babu abinda zaka fad'a min yai tasiri a raina ko yasa na sauko daga halina har abada muje zuwa koni ko kai". Baffah babu yadda ya iya haka yayi ta lallahin Lami da fad'a mata magana me dad'i har yayi sa'a ta daina kukan ta saki ranta suka fara d'an zance yana matukar jin kaunar yarinyar da tausayin ta a ransa yana ganin bai kyauta mata ba daya auri Ramatu ta kasance uwa gare ta duk saiya tattara laifin ya dorawa kansa. Satin d'aya da dawowar Lami aka daura auren Tanko tayi kuka ta kara harta gode Allah domin a dandali a gaban mutane yaci mata mutunci yace tabi son zuciya da kwadayi ta za'bi zaman wudil a kansa yanzu ya cireta a shafinsa lokacin da Ramatu taji harda dariya haka ta tusa Baffah a gaba da baka'ken maganganu wai ga abinda ya jawo nan batai karatun arziki ba ga wanda take so yayi aure yanzu a saiya ji'ka ta yasha. Wudil zaune Naja'atu take tare da wani saurayi suna hira da murmushi a fuskarsa yace "wai nikam ba kuyi magana da Lami ba sai yaushe zata dawo nifa ina kewarta sosai duk na shiga damuwa" itama murmushin tayi tana cewa "hum Alpha kenan kaifa ina jin Lami bazata dawo ba domin dam bada amincewar mahaifiyar ta tazo ba inaga ta koma garin su da zama". "Da gaske kike Najat"? "Wallahi da gaske nake Alpha zanyi maka wasa da tunani ne". "To amma wayar dana bata fa idan na kira bata shiga kullum a rufe me yasa"? "Oh ai dama bata tafi da ita ba tana gidan mu sai bayan tafiyar ta ina gyaran d'aki na ganta" dafe kansa yayi yana cewa " to yanzu idan zan ganta ya zanyi garin zaki raka ni ko kuwa? Gaskiya ina son ta da aure ba yaudara ba shin zaki iya taimaka min"?. Murmushin jin dad'i naja'at tayi tana cewa "me zai hana ni kaina alpha ina son zaman Lami a kusa dani mun riga mun saba bana jin dad'i yanzu da bata nan". "Ok shikenan karki damu zanyi magana da abbanku duk abinda yake akwai zaki ji" "to nagode sosai alpha" mi'kewa yayi yana mata sallama itama ta mi'ke suka fita tare kowa ya wuce gida. MRS AL'AMEEN AHMAD CE 😘 Sai mun sake had'uwa a gaba masoya na masu yabo gareni godiya 💖💕💚 sosai sosai godiya. Think before you do 🤨. #Vote #comments #share #fallow. yusrahmusa65@gmail.com MAMAN LITTLE ZARAN AUNTY 💃👌👍. YUSRA

diya na fita Asad ya kira wayar Mami saidai bazata iya tashi ba balle ta dauko haka yai miss call kusan biyar tana ji ba damar dauka har shi yai zaton ko fushi tai dashi ya bari sai dare ya hau online nan ma ta saba suyi magana bai ganta ba dole ya hakura zuwa wani lokaci. Basu baro asibiti ba sai kusan karfe sha biyu da rabi na dare suka dawo masarautar babu wani labari mai dadi game da Kimiyyah domin likita yace bashi da tabbacin zata sake rayuwa idan kuma ta rayu maybe zata samu tabin kwakwalwa lamarin daya susutar da kowa haka suka dawo jikin su a mace kowa da abin da Zuciyar sa ke fad'a masa tana sa'ka da warwara. Mu dawo 'kauye tushe da asalin kowa wanda baida 'kauye baida asali tsintaccen kan hanya ne🙄. Gidan ilyah zaune Bara'atu take a gaban kayayyaki tana ta lissafi da maimwitawa ta kasa total din kudin gashi tasan ba'kin sun kusa karasowa d'aga murya tai ta soma kwalla kira "Maimuna Maimuna kina ina zo dan Allah taho da sauri taki ta sameki" da saurin kuwa Maimuna tayo waje daga d'aki tana gyara daurin zani tace "lafiya Barah irin wannan kira haka duk kin hargitsa min ciki"? Dariya Bara'atu tai tana cewa "ke kam dai wallahi ba wuya kice an d'aga miki hankali dama lissafin kudin wannan shinkafar zaki taya ni da buhun wake biyar ga na gyad'a can Mara 'bawo buhu biyu ga barkono dan Allah muyi sauri da Ilyah ya dawo zai fara fad'a kin sanshi da hararrami" zama Maimuna tai suka soma lissafi har suka gama daidai Ilyah ya shigo yake tambayar nawa ne kudin ta fad'a masa ledar hannunsa ya mika mata yana cewa "na sanki da nawa kiyi sauri ki dafa musu kajin nan sun kira ni a waya yanzu sun kusa isowa" to Bara'atu tace tana karba shigowar Nafisa da markaden kayan miya ta aje tai d'akin su ganin Salmah zaune tana kwalliya yasa cikin mamaki tace "ke kuma ina zakije kike ca'ba wannan adon kamar zaki gasar kyau"? Dariya Salma tai tana cewa. "To da fa ina zanje amma tun wancan satin nake fad'a miki saurayi na zaizo ko"? Tabe baki Nafisa tai "au kuma shi kikewa wannan kwalliyar lallai kina da aiki karshen ta mummuna ne me tumbi har kika tsaya bata lokacin ki wajen shafe shafe kamar d'an shugaban kasa ne zaizo gurin ki" had'e rai Salma tai "kuma saikin zagar min shi eh naji koma maye ni ina son kaya na in fitsari banza ne kaza ma tayi inta isa" dariya Nafisa tai tana cewa "ai yarinya ni yanzu na wuce tunanin na auri dan kauyen nan na karfi mahaifi na babu mai kudin sa a halin yanzu a garin nan kinga kuwa ai na tserewa sa'a" mikewa Salma tai tana cewa "haka mukam bamu fi karfin auren d'an garin muba kema zaki sauke domin ba d'an birnin da zai soki" zaro ido Nafisa tai "haka kika ce" daidai Salma tadau hijab zata fita tace "eh haka nace" tana fadin haka tai waje zama Nafisa tai ita kadai sai magana take "hum Salma kenan zaki sha mamaki bari Allah ya kaimu lokacin bikin zakiga irin mijin dazan aura nasan har abada babu wacce zata samu kwatankwacin sa a kauyen nan" karasa maganar tana fad'awa kan katifar su. Haka nan Amatullahi taji son ziyara a ranta dan haka ganin ba abinda take yasa ta mike tana debar ruwa ta shiga wanka shaf shaf a yan mintuna ta kammala shiri ta fito tana shiga d'akin umma tace "umma ina son zanje ziyara gidan baba Ilyah da Baba Rakiya kuma zan d'an biyo ta gidan su Fatima mun dade bamu hadu ba" d'agowa Binta tai tana kallon fuskar Amatullahi saidai tayi murmushi kawai tana mayar da kanta tace "to ki gaishe dasu saikin dawo" to Amatu tace tana fita a zauren gidan ta hadu da malam Habu zai shigo cikin mamaki yace "Mamana ina zuwa" d'an sauke kaitai tana murmushi tace "zanje gidan baba Ilyah da gidan baba Rakiya saina biyo ta gidan su Fatima" shiru yai kamar zaice mata a'a saidai bazai hanata zumunci ba dan haka yace "to shikenan Mamana Allah ya tsare min ke saikin dawo karki dade" "to baba bazan zauna ba yanzu zanje na dawo" kai ya d'aga mata ta juya ta fita a gidan shi kuma ya shiga ciki iya sallama yai tun bai sauke sallamar ba A'i ta dauko kwaryar garin tuwon da aka niko tana direwa gaban sa tace. "Malam ga garin tuwon ka nan gaskiya na gaji kullum ace kaine da girki bayan kayi casa ka g

bazai ta'ba dukan Kimiyyah koda ma ace jininsu bai had'u ba" "ku dai yanzu baza kuce komai ba mu jira komawa gida koma mene ya hada su ai gaskiya zata fito" kowa na magana a gurin amma tunda suka zo Makiyyah batace ko alif ba saida ido take binsu da kallo yayin da Zuciyar ta tashiga kakkarwa domin a kaf zaratan samarin hudu Asad ne taji ya kwanta mata take son shi amma yau d'aya ta shiga kokwanto domin a ganinta koda yana son mace ya aure ta zatai matukar shan wahalar da ba'ai zato ba balle wacce ta kasance matar cushe aka 'ka'kaba masa ita wannan dama washe gari saidai ta waye shi a lahira domin zai tura ta bacci na har abada. Batun Mami kuwa lokacin data shiga gurin da sauran matan suke tun kafin tayi magana Sultana Hadizah ta katse ta da cewa "babu abinda zaki ce min Hauwa gaskiya baki sa'ar haihuwa ba Asad bashi da tarbiyyah ko kadan yanzu me Kimiyyah tai masa dan tsananin tsabar tsagwaron mugunta irin tasa ta soja yasan ko namiji yaiwa wannan dukan iyaci kenan balle ita mace to wallahi bazan yarda ba ko kidau mataki ko na dauka da kaina dan na fahimci da sa hannun ki Asad yake duk abinda yaga dama a masarautar nan" mamaki ne sosai ya kama mami ba iya ita kadai ba harda sauran cikin rashin jin dad'in cin mutuncin da Sultana Hadizah kewa Mami yasa sultana Fatima cewa "amma dai gaskiya maman Khaldiyyah baki kyauta ba meye laifin sultana Hauwa'u a ciki zaki mata irin wannan wulakancin kamar wata bare ko baki santa ba kya yi kokarin ku fahimci juna ai ko amma daga xuwa baki bari tace komai ba kika hau fad'a gaskiya ki bata hakuri" a zabure sultana Hadizah tace "wa zan bawa hakurin bayan nice akai wa ba daidai ba wallahi I won't" ba sultana Fatima ba hatta abiyar sultana Hadizah taji babu dad'i itama saida ta magantu "haba ke kuwa maman Khaldiyyah ki bari mana dan Allah meye laifin ta a ciki ai baku bari ta farfad'o munji mai laifin ba ko"? Mikewa tsaye sultana Hadizah tai tana huci tace "waye mai laifi kuwa a cikin kowa ya sani bayan tantirin d'an nata da bataso a ta'ba niko fad'a ya zama dole tunda aka ta'ba min 'ya kuma wallahi bazan yarda ba 'kiris nake jira ta mutu na doka shi a kotu" ta karasa maganar tana jijjiga kamar wacce zasuyi dambe ba Mami data haifi Asad ba hatta sauran sultana Fatima da sultana Aisha sunji mugun rashin dad'in yadda Sultana Hadizahn ta rufe ido take ciwa Mami cin mutunci kamar bata ta'ba ganin taba ko irin bata santa ba" juyawa Mami tai zata fita a d'akin saida taje bakin kofa sannan ta juyo itama ba wuya idonta yai ja tana kallon sultana Hadizah tace "kiyi hakuri da komai duk ma abinda zaki fad'a min na bakar magana dole na dauka tunda d'ana ya miki laifi saidai ina son kisan wani abu you should stop spreading news with unreal source, be sure before you spread that's the right ba kuma ina nufin Asad bashi da laifi bane a'a amma mu jira farfad'owarta na barki lafiya Allah ya tashi kafad'unta" Mami na kaiwa nan tai waje cikin 'kunan rai da jin zafin kalaman da sultana Hadizahn ta fad'a mata amma ta 'kudura a ranta data koma zata samu Asad ya fad'a mata komai abinda ya hada su. Tun kafin su 'karasa gida Mami zazzabi ya rufeta da'kyar ta iya karasawa part dinta ta kwanta bayin dake mata hidima basu sani ba saida Rabi'at taje kai mata madara ta ganta kwance cikin katon bargo tana makyarkyata da sauri ta karasa tana cewa "subahanallahi ranki ya dade meya faru"? Jin bata amsa mata ba yasa ta fita da gudu domin kiran mutane tare da jakadiya suka shigo d'an kwalinta a hannu tace "ranki ya dade sannu baki da lafiya Allah ya 'kara sauki yanzu wa zan kira miki ko me martaba"? Kai Mami ta girgiza alamar a'a sannan muryar ta na fita da'kyar tace "jakadiya ki duba drawer ki dauko min magunguna" da sauri jakadiya ta mike jiki na rawa tace "to ranki ya dade" duba drawer tai ta debo su gabadaya daga kwancen Mami ta nuna mata wadanda zata ballo mata ta hada da ruwa ta bata saida tasha jakadiya ta tattare ta mayar inda ta dauko tana zuwa gaban ta tadurkusa tace "ranki ya dade ko akwai wani abu dazan miki"? Kai Mami ta girgiza "a'a nagode jakadiya zaki iya tafiya" "to ranki ya dade Allah ya sauwake" jaka

ni irin juyawa kan Mami keyi hajijiya na dibanta baya tai luuu da sauri Ajeeb ya taro ta yana cewa "sorry Mami kiyi hakuri" muryarta a hankali tace "ina Sultana Hadizah"? rike hannunta Ajeeb yai "muje na kai ki" fita sukai suka bar saura mikewa Ameer yai yana zura hannun sa cikin aljuhu ya fara zagaya gurin dakatawa yai yana d'aga kansa sama yace "nifa na kasa ganewa"? Kowa kallon sa yai da mamaki cikin alamar tambaya Annur yace "kamar ya"? Komawa Ameer yai ya zauna yana cewa "kamar yadda nace maka abun tambayar anan shine me Kimiyyah taje yi part din Asad me ya kaita laifin me tai masa wannan tambayar na bari a raina nake ta so mu koma na tambayi Asad" kai Annur ya jinjina yace "haka ne Ameer tunanin mu yazo daya wallahi nima abinda ke raina kenan Asad nada zuciya amma a banza Asad bazai yiwa Kimiyyah irin wannan ba'kin dukan mutuwar ba" da sauri Khaldiyyah tace "ya Annur nima abinda nake tunani kenan" kallon ta Annur yai yana cewa "wai ke ni sa'an wasan kine ko tare aka haife mu fad'a min inji yawancin lokata kina min shishshigi duk ranar dana rike ki ni kuma saina miki dukan shiga 'kabari😲" zaro ido Khaldiyyah tai baki bud'e take kallon sa dariya sauran suka ri'ka yi kamar ba Kimiyyah ce ke ICU ba. Waya Ajeeb ya dauko daidai zaiyi making call yace "to ai mutumi na in kaji kare yana shinshina takalmi hausawa sukace dauka zaiyi" wani kallo Annur yaiwa Ajeeb cikin had'e rai yace "meeeh d'an sake fad'a domin ban jika sosai ba"? Da sauri cikin tsokana Ameer yace "cewa yai in kaga kare yana shinshina takalmi hausawa sukace dauka zaiyi to nan din ma haka abun yake" sakon harara ya samu daga Annur yana cewa "kai kuma ban sako dakai ba saboda haka can you be quiet🤫" sannan yana kallon Khaldiyyah wacce ta kau dakai yace "ke da gaske ne"? Shiru tai ta kasa bashi amsa wanda hakan ya tabbatar masa wato da gaske son shi take tabb lallai ta kira ruwa bata da lema cire lips yai yana maida kallon sa kan Ameer wanda ya dage gira zaiyi magana jin Ajeeb na waya yasa yai shiru. Da mamaki suke kallon Ajeeb daya dage yana zazzagawa Asad fad'a cewa duk suna hospital bayan shine ya daketa amma ko leko su baiyi ba balle ya damu da halin da take ciki tsit Asad yai yana sauraron sa saida ya bari ya tsaya sannan yace "ka gama" shiru Ajeeb yai cikin takaici yace "ban gama ba" tsuka Asad yai yana cewa "ok continue Abba, ba kira na kai kamin fad'a ba mezai hana kazo ka kama ni da duka I think zaifi wannan ihun da kake min" da karfi Ajeeb yace "ASAD" "what up Ajeeb"? Asad yai maganar slowly cikin 'kulewa Ajeeb yace "wallahi idan muka dawo masarautar nan saika gane Allah da girma yake" Ajeeb na rufe baki Asad yace "ok what do you mean? wato so kake kace min ni bansan shiba kaine zaka nuna min ya sheik" "kasan Allah ko Asad ka jira dawowa ta saina baka mamaki" tsaki Asad yai yana cewa "me kake cewa ne magana kake ko bakin ka ne a haka? Meyasa lokacin da kazo ka tarar ina duka ta kaima baka rufe ni da duka ba, ka godewa Allah da sauran kwanan ta a gaba amma da yanzu na kaita kabari" haushi ne ya gama cika Ajeeb yace "maimakon ka risina kayi nadama ai haka kace ko"? Kai tsaye Asad yace "eh nace hakan idan akwai wani abu da kake tunanin zaka iya ina jiran ka babu tantama akan bugun danai mata" cikin alamun tambaya Ajeeb yace "me"? Cikin son tura masa haushi Asad yace "akuya zaka cewa me ba mutum ba" rai bace Ajeeb ya sakar masa ashar yana cewa "uban akuya zan cewa me wai Asad meke damunka ne" "babu kaga wani abu sa'banin hankali a tattare dani"? "Ban sani ba" "kada Allah yasa ka sani banza uban yan shishshigi kada ka sake kira na idan kuma ba haka ba daga nan inda nake zan saito ka da bindiga na harbeka" zaro ido Ajeeb yai yana cewa "ji d'an iska inka fasa harbi na kaci ubanka" d'if yaji Asad ya datse kiran tsaki yai yana aje wayar kafin ya soma magana. "Lallai ma Asad da tsaurin rai yake ji fa yadda yake magana hankalin sa kwance kamar wanda ya daki itace kuma na kirashi yana gasa min magana amma bari na barshi da Abban mu koma gida zanga da yadda zai Kare kansa" d'aga kafada Ameer yai yana cewa "da yadda ake karewa mana kaifa a banza Asad