TASKAR NOVELS
الذهاب إلى القناة على Telegram
3 386
المشتركون
لا توجد بيانات24 ساعات
-67 أيام
+2030 أيام
أرشيف المشاركات
3 386
nadan mintuna kafin ya bud'e baki cikin zazza'kar muryarsa da baiyi magana da ita ba tun dazu yace "Amjadd will you work for me if I ask you"? Sake dukawa Amjad yai yana cewa "Allah ya taimake ka Allah daukaka ka zanyi kowanne irin aiki daka sani amma ranka ya dade kamin bayani da hausa dan nafi fahimta ba sosai nakejin turanci ba" ya karasa maganar muryar shi na rawa saboda tsoro domin dazu a gaban sa ya fara dukan Kimiyyah jikinsa ma rawa yake kuma yana sauraron me zaice masa can ya tsinkayo muryarsa yana cewa "batu ne akan stockyard dina ina son ka kula min dashi kafin na dawo ya zama tamkar ina nan kuma koda Ajeeb ne ban amince ya shiga wurin su ba kaji abinda nace"? Da sauri Amjad yace "eh ranka ya dade za'ai yadda kake so Allah ya tsare ka ya dawo dakai lafiya" "Amin" ya fad'a can kasa kafin cikin taku ya wuce da sauri Amjad ya mike yana jan trolley yabi bayansa har mota da wadanda zasuyi masa rakiya zuwa airport batare da sanin kowa ba ko bankwana da kowa ko tunanin halin da Kimiyyah take ya wuce airport daga nan jirgi ya d'aga dashi zuwa Marshall islands.
Ummmhh😘😘 SAFE JOURNEY ALIYU ASAD🌹🌹.
To yau kam anan zan tsaya sai idan Allah ya kaimu gobe a'a ba gobe ba sai jibi oh sorry it was a mistake ba jibi ba sai gata zaku samu typing kuyi hakuri kada ku gajiya da halina ni haka nake bani da haushin kowa😅🤣😂.
Mrs AL'AMEEN AHMAD CE 😘 ta kowa.
Sannan ga wata sanarwa idan kuna so na yi muku typing gobe tofa saina ga sama da mutum dubu sunyi comments 😂😂😂😂 idan kuwa ba haka ba nayi fushi saina huci kafin na d'ora ehe bazan fatse aiki na nayi muku typing ba ku turo min sticker 🤗😜 duk wacce ta sake turo min sticker saina debo mata yan committee ko na kaita ofishin 'yan hisba 🤣😅🤣😂😅.
Jinjina nake a gare ku masoya abokan arziki fatan samun rahmar ubangiji da amincin sa a duk inda kuke bazan ta'ba mantawa daku ba.
Naja'at Musa Abubakar
Zarah Musa d'an Adam
Hafsat Harees
Salmah Hayat
Suwaiba Yusuf
Fatima Idris
Khadija A Yusuf
Saudat Yusuf
Zainab Sunusi.
Mrs Al'ameen Ahmad ce ke gaida ku 🌹🌹💍💍🌃🌆🌃🏙️.
YUSRAHMS WE WILL MEET AGAIN 🤗.
Tofa a'a abun yayi ashe ana son posting irin wannan comment haka na wani ma ban samu damar karantawa ba sai hakuri amma maganar gaskiya kun bani mamaki ai bansan haka littafin nan keda farin jini ba ya tara masoya da yawa masu min fatan aikairi TO IDAN KINJI DAD'I KO KAJI DAD'I KAI SALATI D'ARI GA MANZON ALLAH SAW RANAR JAMA'A ZAKA SAMU WANI HASKE RANAR ALKIYAMA WANDA DA ACE ZA'A RABAWA ABIN HALITTA ZAI ISHE SU SHIGA ALJANNAH🌲.
TYPING 📲 FRI 01 March 8:18AM Yusrah Musa Abubakar na karaso kuzo kusha story.
💎ME KAMAR SARKI 💎
ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY.
YUSRAH MUSA ABUBAKAR)(Maman little Zaran aunty 😘)(*).
🕌
🕌 🕌
🕌 🕌 🕌
🕌🕌🕌🕌🕌🕌
🕌 🕌
🕌 🕌
🕌🕌🕌🕌🕌🕌
📿📿📿📿📿📿
🕋🕌🕋
It's Friday don't forget to recite suratul al-khaf may Allah open the door of success for all of u may Allah accept our du'as may Allah bless nd help us Amin 👏.
Dedicated to
MR HAUSA EBOOKS 📚
📚📓📒📕📖📗📘📙📕📔
STORY AND WRITTEN BY
✍️Yusrah Musa Abubakar maman little Zaran aunty 😘.
07~ AL-MUHAIMINU
The dominator
08~AL-AZIZ
The almighty.
4~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Khaifina.
💎Me kamar sarki 💎
By
🌹 Yusrah Musa Abubakar Mrs Al'ameen Ahmad ce 🌹.
🌄 VIXENS ND ABSENT MINDED🌄
Episode 07 & 08
Lokacin da Mami ta isa asibiti duk suna zaune shiru sauke ajiyar zuciya tai tana cewa "ya jikin na Kimiyyah fatan babu abinda ya sameta"? Kai Ajeeb ya d'aga "eh Mami muna dai fatan hakan amma har yanzu bamu da wani gwarin gwiwa akan komai domin tana ICU likitoci suna iya bakin kokarin su ganin sun ceto ranta amma dai abun yaci tura Mami kita addu'a Allah yasa kada ta silar Asad ace Kimiyyah ta mutu" wa
3 386
daya ta kasa nutsuwa kuma tasan ba magana zaiyi ba amma dai tace "Asad mai Kimiyyah tai maka kake kokarin kashe ta meya kawota part dinka ya naga harbi a hannunka"? Shiru yai kamar kurma kuma dama haka take tunani rike hannunta yai yana fita da ita saida ya mayarta har part dinta kafin ya dawo ya cire bullet din hannunsa ya nad'e hannu yana tattare kayayyakin daya tarwatsa domin tun daga parlor ya soma dukanta har harabar part dinsa Saida ya gama sannan ya mike yana shiga bedroom ya cire kayan jikinsa ya shigo toilet saboda sanin irin zafin Zuciyar sa yasa ba mace ko daya da take aiki a part dinsa mazan ma sai taka tsantsan suke.
Ruwa mai matukar sanyi yake kwararawa jikinsa idanuwan sa a rufe hannunsa nakan kyakkyawan pink lips dinsa ya ma rasa mai tazo yi part dinsa uban waye ya turo ta mai take nema har ta samu damar shiga d'akin sirrin sa tai amfani da na'urarsa ta tura sako ta goge masa abubawa masu mahimmanci wanda yadau tsawon shekaru yana tarawa yau daya tasa yayi losing dinsu duka bude idonsa da har lokacin babu fari ko kadan yai tare da furzar da zazzafar iska ya dunkule hannunsa ya kaiwa mirron toilet din naushi take ya tarwatse ko'ina numfashi ya sauke cikin zafin Zuciya bad temper yafi awa biyu yana tsaye shower 🚿 na zubar ruwa a kansa kafin ya daura towel ya fita zama kawai yai gaban mirror yana zubawa had'ddiyar kyakkyawar fuskarsa ido mikewa yai a gurin yana komawa kan katafaren katon bed dinsa Wanda ya 'kawatu da kwaliyar zinare kwanciya yai yana kallon sama tare da lulawa cikin tunani har ya bata lokaci a haka karfe daya da rabi tayi bai sani ba kuma a yau yake son komawa domin isham ya kirashi a waya tun jiya ya yi masa albishir cewa ya kusa gano abinda ya dade yana nema amma yau d'aya Kimiyyah ta wargaza masa tanadin dayaiwa shekaru da dama runtse ido yai da karfi tare da cusa yatsunsa cikin lallausan gashin kansa tuni yaji ransa ya kara baci fiye da da jiyake dama zai hadu da Kimiyyah yanzu babu abinda zai hana ya d'aga bindiga ya harbe ta, tashi zaune yai a tsakiyar gadon yana tan'kwashe kafafunsa kamar daga sama idanuwan shi suka sauka akan wani photo wanda ya kasance anyi shi da dadewa zai kai shekara sha takwas sau'ka gadon yai yana zuwa gaban photo yasa hannu ya dauka yana kallo ko ba'a fad'a ba shine ya dauki wata karamar yarinya a hannunsa zatai shekara biyar da uniform a jikinta yana murmushi ita kuma tana dariya kuma da gani photon a waya akayi shi ya bayar aka wanka fuskar yarinya kadai yake kallo a ranshi yana tunanin shi da ita har abada bazai sake ganinta ba domin dama bai santa ba saidai yana fatan ya sake haduwa da ita ko sau daya ne a rayuwar sa aje photon yai yana barin wurin yaje ya fara tattara kayansa yana sawa cikin trolley ya zuge kafin yayo alwala yasa kaya yai salla ya shirya cikin kayan soja anan tsantsan asalin kyansa ya kara bayyana fili 'karara gaskiya ya matukar haduwa fad'a batawa fita yai a bedroom din,
yana yin hanyar wata kofa da aka rubuta STOCKYARDS anyi masa launin golden sai haskawa yake kamar ba rana ba password ya rubuta kafin kofar ta bud'e ya shiga iya ganinka dabbobin daji ne kamar gidan zoo fili ne mai girma an kawata shi da ado kyansa baya faduwa saidai hasashe wani 'katon 'ka'k'karfan zaki na ganinsa ya nufo shi yana kukan su na zaki da matukar gudu yana zuwa gabansa ya taka wani irin burki mai burgewa dukawa Asad yai yana shafa gashin zakin cikin so can ya jiyo kukan wata 'yar karamar giwa yana dubawa yaga har tazo inda suke amma babarta tana d'an nesa dasu itama shafa jikinta yai a yau baiji sanyi a ranshi ba sai yanzu daya shigo nan mikewa yai zakin🦁 na biye dashi ya soma zagaya gurin yaga lafiyar su kafin ya fito yana fita a part din nasa gabadaya yayi tunanin zuwa gurin Mami saidai yasan ba lallai itama ta zauna ba maybe ta bisu asibiti yana tsaye a katon katafaren kofar shiga fadar mahaifin sa yasa anyi masa Kiran wani bawa wanda ya kasance duk masarautar shi kadai ne jininsu yazo daya gano Asad din tsaye yasa shi karasowa da sauri cikin girmamawa ya du'ka yana cewa.
"Ka gafarce ni shugaba na ka kira ni ne"? Kallon sa Asad yai
3 386
aga nesa.
Ya nufi wata iriyar kyakkyawar kofa mai she'ki zaka iya jiyo kururuwa da ihu na mace tana kuka cikin tashin hankali da dana sanin abinda ta aikata.
Sanye yake cikin kayan sojoji kana ganinsa balarabe sak fari ne tarr kyakkyawan jarumtaccen sadauki wanda ba kamarsa a karfi kwarjini fuskarsa kamar ba'kin hadarin da yake gaf da zubar ruwa ransa a mugun 'bace idanuwansa sunyi ja kamar rana taje faduwa cikin tsananin bacin rai da tsantsan fushi yake kallon fuskarta da saitin inda yatsunsa suka fito da 'karfin gaske cikin taku yake yin wajen inda take kwance ganin ya kuma nufota kamar zakin daya hango nama yasa a zauce ta yunkura cikin dimuwa da gigita tana neman hanyar tsira daga hannun sa wani irin dan'ko gashin kanta yai yana jawo ta baya tare da wurgi da ita ta bugi jikin wasu kafaffun karafina tayo kasa ji kake tim ihu ta zunduma tana dafe kanta saiga jini ta hanci yana malala ko a jikinsa ya sake dan'ko wuyanta yana mikar da ita tsaye ya kuma sharara mata wani marin daidai Ajeeb ya bud'e kofar katafaren gate din part din yaga abinda ke faruwa da mugun gudu ya karaso yana cewa.
"Kai ASAD🦁 are you out of your sense baka da hankali ne ka sake mata wuya saika kashe ta mitai maka? ka bari fa nace ka sake ta" ko inda yake bai kalla ba balle yasan wai mutum ne ke masa magana sai kara matse wuyan nata da yake idanuwan ta duk sun fito waje sunyi jawur jini kuwa sai ambaliya yake ta hanci da baki ganin da Ajeeb yai idan ya zuba masa ido zai kasheta yasa da karfi ya soma kokawar kwaceta muryar Asad da tsananin fushi yace "AJEEB let's not get into this😠😡" shima Ajeeb cikin fushi yace "I won't spare you bazan 'kyale ka kashe ta ba wallahi ka saketa nace" a banza Ajeeb yake magana domin ko sauraron sa Asad baiyi ba kokarin kwatar ta Ajeeb keyi amma maimakon yai nasara sai ya jawo Asad din ya sake mata mugun rikon daya fi nada a susuce Ajeeb ya zaro pistol 'karamar bindiga dake aljihun wandon Asad ya harbeshi a hannu ko zai sake ta tuni jini ya wanke hannun amma tsabar tsaurin rai Asad bai sakar mata wuya ba "innalillahi wa inna ilaihi raji'un" abinda Ajeeb yake maimaitawa kenan cikin azama a guje ya fita ya nufi sashin mahaifansu dan yasan banda su ba wanda ya isa ya dakatar da Asad daga yunkurin kashe Kimiyyah duk bayin dake aiki a part din Asad kuwa kowa ya shiga taitayinsa sun rasa abinda yake musu dad'i tsoro ya hana suje su fad'a yanzu kuma sun san dole a hukunta su akan haka.
Dukkan ahlin gidan a gigice suka shigo domin mai martaba ko takalmi babu a kafarsa tsabar tashin hankali Mami dake gaba ganin halin da Kimiyyah ta shiga na rai ko mutuwa yasa da gudu taje tana kasarawa ta wanka masa mari sau biyu tare da fashewa da kuka tana rike hannunsa dake wuyan Kimiyyah tace "Asad ba ita ya kamata ka kashe ba nice ka saketa Asad ka rike nawa wuyan innalillahi wa inna ilaihi raji'un Asad ka sake mata wuya kada ka kashe yarinyar nan bazan yafe maka idan ka zama silar mutuwarta" ta karasa maganar tana sake jan hannun sa da karfi jin kukan da take da abinda tace yasa Asad sakin wuyan Kimiyyah tilas ba hakura ba hannunsa na tsiyayar jini inda Ajeeb ya harbeshi da bindiga Kimiyyah kam yana sake mata wuya ta 'kame tare da zunduma uban ihun tsananin azaba kafin ta yanke jiki ta fad'i kasa da sauri sukai kanta yayin da Mami ta fad'a jikin Asad tana kuka sosai.
Gaba daya jikin 'yan gurin rawa yake an rasa mai kwarin gwiwar cewa komai sai salati da ake ganin yadda Kimiyyah ke wata iriyar mi'kar tana sankarewa irin na mai 'ka'karin mutuwa hankali tashe Ajeeb yace "Abba muje asibiti dan Allah karta mutu" kasa magana mai martaba yai sai mikewa kawai dayai ya bar gurin da sauri Ajeeb da Ameer suka dauketa suna fita sauran suka bi bayan su har lokacin Mami bata daina kuka ba ta kasa shiru ga jikin ta sai rawa yake kamar maijin sanyi ko mai zazzabi da'kyar ta d'ago tana kallon fuskar jarumin d'an nata da har lokacin yana cikin mood altering ganin jini duk ya bata mata jiki yasa ta kalli hannun sa zaro ido tai ganin harbi da sauri tasa hannu cikin aljihunsa ta dauko wani d'an karamin towel fari ta daure masa hannu gaba
3 386
RI HASKE LEKA GIDAN KOWA KODA MAKIYA NA KALLON KA RAMIN KURA SAI'YA'YAN TA. TAKEN MU KENAN.
Dedicated to
MR HAUSA EBOOKS 📚
📚📚📚📚📚📚📓📓📓📓
WHAT'S APP NO: 234 8160983083
Chat with me at always banda kira idan kasan kai na miji ne only female kawai 💝💚.
✍️ Yusrah Musa Abubakar story and written dedicated to my mum mama na ta kaina Allah ya kara girman matsayi ya kiyaye min ke mama na Amin 👏.
05~ AS-SALAM
The source of peace and safety.
06~ AL-MUMINU
The guarantor.
Manzon Allah saw
Ya mai nasiha ga alumma muso juna mu rike gaskiya amana dan gudun kuna mu raya zuminci hanya ne na aljannah makiyin zumunci baya kusanci ceto ba.
4-Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Shahidina.
Wa alam anan nasra ma'as sabri😔 wa annal faraja ma'al karbi😢 wa anna ma'al usri yusrah🤗🌹🌹🌹.
🗣️🗣️🗣️👏AYI HAKURI IDAN AN SAMU TYPING 📲 ERROR🚨 MATSALAR KEYBOARD NE 🤓.
🌄 EMPIRE ND RESEMBLANCE 🌄
Episode 05 & 06
Babbar masarauta ce wacce ta shahara mai cike da dunbun tarihi da kafaffiyar daula da jajurtattun sarakuna wadanda sukai zamanin nika kuma har yanzu ake mulkin ta kamar da masarautar nada girma da tsari wanda bayan emire Aliyuddeen Abdulmalik mai mulkin ta ya kwanta dama sai babban d'ansa alhassan Aliyuddeen Abdulmalik yahau kuma ya jajirce kamar mahaifin sa har izuwa yau.
Emire Alhassan Sun kasance 'yan biyu ne shida d'an uwansa Alhussain kamar su daya sak ba'a bambance su kamar ma harta baci kuma da suka tashi haihuwa kowa Allah yake arzuta shi da 'yan biyu kuma masu kama daya saidai mai martaba Alhassan nasa dukka maza ne matansa biyu Princess Hauwa da princess Fatima suka haife su rana daya abin al'ajabi d'aya ta haihu da safe daya da dare farin ciki a wannan rana baya musaltuwa kuma abin sha'awa ya sanya musu sunan mahaifin sa marigayi Aliyuddeen duk su hudun sunan su Aliyu Aliyu an dauki lokaci mai tsawo a masarautar ana bikin murnar haihuwar su 'kasashe daban daban yanki iri iri anzo domin karrama Emire Alhassan da iyalan sa sai hussain shi kuma nasa 'yan mata su ma hudu 'yan biyu suna rayuwa ne cikin mulki daula da sarauta ga ilmi saima ka gansu kyawawa zarata masu kwarjini da aji.
Kuna ina ku fito ku kashe 'kaikayin idanuwan ku Kai tsaye ya kamata mu leka mu ganewa idanuwan mu abin yake faruwa cikin wannan kasaitacciyar masarauta💍👑.
Zaune suke a wani irin kyakkyawan siritaccen 'kayataccen parlor suna da yawa samari da yan mata kyawawa farare tarr jawur dasu sun gaji da kyau ta ko'ina sun hadu saidai ko tari babu a parlon kamar masu zaman makoki sunkai kusan minti talatin a haka kafin a samarin daya ya d'ago yana kallon na kusa dashi dake ta aiki cikin laptop yana cewa.
"Ajeeb wai ina Asad ne tun shigowar mu banga yazo ba lafiya dai"? Batare daya d'ago ba yace "gaskiya ban sani ba domin nikam tun asuba muka rabu dashi a masallaci maybe yana part dinsa ko kuma gurin su Mami" ya karasa maganar tare da dagowa ya kallo yan matan yana cewa "ga Khimiyyah ma ban ganta ba uwar shashanci ai dama halin su daya da Asad din" dariya Ameer yai dan kowa a masarautar yasan jinin su baizo daya ba har bayi idan ka tambaya zasu ce maka haka.
'Daukan waya Shaukiyyah tai zatai Kira da sauri Khaldiyyah dake gefen ta tace "ke me zakiyi"? Kai tsaye tace "oh Asad zan kira naji inda yake"? Zaro ido Shaukiyyah tai da mamaki tace "ki kira shifa kikace? kin manta laifin da kikai masa jiya kenan zai miki dukan mutuwa Mami ta hana shi shine kuma yanzu kanki na rawa kike son taso mutuwa daga bacci ko? Allah ya taimaka mukam yan kallo ne da sannu yayin daya sauya miki halitta" ta karasa maganar tana kallon Annur wanda shi kuma hankalin sa sam baya kan maganar da suke Ameer yace "ai dakin barta taje ina tasan yana tattare da ita" shiru Shaukiyyah tai tana kallon su daya bayan daya domin ita badan sun tuno mata ba ta manta da tai masa laifi jiya.
Mikewa Ajeeb yai yana cewa "bari mu gani tsaya naje part dinsa" fita yai ya barsu duk inda ya gifta du'ka masa bayi suke cike da girmamawa tun d
3 386
e "Amatullahi me akai miki kike kuka"? Jin tambayar datai mata yasa wasu sabbin hawayen sake gangarowa da sauri tasa hannu ta goge bude baki tai kamar zatai magana ganin Bintan na tsaye a kanta tana jiran amsa sai kuma ta kasa cewa komai a karo na biyu Binta tace "mamar gida tambayan ki fa nake me akai miki kike kuka"?.
Kai Amatu ke girgizawa da'kyar tace "umma shin bazan iya taimakon baba ba"? Da mamaki Binta tace "kamar ya"? Cigaba Amatu tai da cewa "umma zan koma gurin su Abba Bashir 'kanin ki na fara kasuwanci domin na taimaki baba wannan damuwar dake damunsa na gaji da gani bazan iya ba a iyasani na mahaifi na mutum ne me annurin fuska amma yanzu koda yaushe baya ciki walwala ki tuna yadda ya ri'ka kula dani ya taso dani a cikin gata ya bani komai da nake bukata a rayuwa idan na zuba ido yaci gaba da zama a haka na yaudari kaina na cuci kaina bazan iya yafewa kaina ba umma ina bukatar taimako" ta karasa maganar cikin kuka sosai wanda ke fitowa daga asalin ainishin cikin Zuciyar ta".
"Kinga mamar masu gida kiyi hakuri haka kinji karki jawo hankalin mutan gidan a kanmu" rufe bakin umma keda wuya caraf sukaji A'i na cewa "aikin banza kenan rigar bayan salla meyi ake cewa tai shiru kar muji za'a boye mana ko saurayi tayi ko kuma wani laifin tai ba'a so mu sani iye a fad'a min domin idan baku fad'a ba kun barni cikin zulumi" juyawa Binta tai tana kallon A'i dake wanke kwanuka batare datai magana ba tace "Amatu tashi ki koma kinji ina zuwa" mikewa Amatu tai tana shiga kamar yadda umman ta umarce ta.
Tabe baki A'i tai tana cewa "oh ni Indo yanzu Binta abin har yakai ga haka kin fara hurewa yarki kunne dan ta raina ni ina matsayin matar ubanta saboda kina kishi dani".
Kallon ta sosai Binta keyi cikin mamaki wato ta fahimci A'i ba 'yar neman zaman lafiya bace wa ya sako da ita har zata dauka..........
Katse mata tunani A'i tai "dake fa nake Binta"? Wani kallon umma ta kuma aika mata dashi batare datai magana ta wuce uzurinta dariya A'i tai tana cewa "ahahaha hayye kai ni yar gidan baba gaskiya akwai tantirai a gidan malam Habu gashi kuwa sun fara bayyana Allah ya tonu asirin su suna shirye shiryen zuwa gurin boka to naji ku sai ku sake shiri ku taka a sannu idan ba haka ba yanzun nan na garzaya na sanar da mai gari" ko kula iskar ta umma batai ba balle tasa ran ta mayar da ita mutum kawai aikin gabanta take.
🥀🌻MRS AL'AMEEN AHMAD CE 😘 MAI TAMBARIN YMA DUTSE 🏞️''YAR MUSA JIKAR ABUBAKAR MAMAN LITTLE ZARAN AUNTY 💃.
Mrs Al'ameen Ahmad ce mai tambarin yma dutse sabuwar duniya 🌍new world new life 🌌 and new style 👌.
🌹 Yusrah Musa Abubakar ta kowa ce kuma ni I have no girman kai if you are fushi dani tofa you are just 'batawa kan k lokaci 🕐.
Manzon Allah mai Makkah mai birni da 'kauyuka.
A gaskiya naji dad'in comments dinku yan uwa matukar jin dad'i da yadda kuka gwada kauna ga littafin nan hakan da kukai ya faranta min kuma na sake samun sabon confident na gwarin gwiwa daga gare ku kuma albishirn ku insha Allah zan dage kamar yadda kuka bukata naga kullum nayi muku posting koda kadan ne ngd da yabawa💖💕👏.
Wannan page din naku ne yan uwa ina matukar kaunar ku soyayya ta a gare ku bata kwatantuwa hasashe bazai ta'ba iya hangowa ba Allah ya bar mu tare.
Ibrahim Musa Abubakar
Ummi Musa Abubakar
Salim Musa Abubakar
Yusrah Musa Abubakar
Naja'at Musa Abubakar
Fatima Musa abubakar
Aishat Musa Abubakar
Abubakar Musa Abubakar
Abdullah Musa Abubakar.
Banda kamar ku duk fadain duniya ku nake kallo naji dad'i kune jini na kune dangi na kune ahli na kune abun faharin na.
To 'yan uwa mu tsaya mu kwana anan sai mai duka ya kaimu gobe ya bamu aron rai da lafiya zanyi muku.
Think before you do 🚨
Be good be kind people will like u.
YUSRAHMS
Mrs Al'ameen Ahmad maman little Zaran aunty 😘😘😘.
👌 Till we meet.
TYPING 📲 Thu 9:48AM Feb may Allah open the door of success for all of u.
💎ME KAMAR SARKI 💎
💫 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫.
HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY GIDAN KARBAR MUTANE HANNU BIYU DA ZAMAN LAFIYA ANNU
3 386
ar kike gorantawa wani meye a gidan naku wacce tsiyar ce fad'a min" mikewa Bara'atu tai ta fara masifa ta zazzaga bala'i irir iri wanda yasa sauran yan matan gidan fitowa da sauri Nafisa ta karaso tana cewa "wanne d'an hauren ne ya ta'bo ki umma? Gaskiya mu mun gaji da wannan maula da ake zuwa mana hakan ma bai isa sai anyi cin mutunci to wallahi bazamu dauka ba"..............
Tana rufe baki taji saukar zazzafan mari a fuskar ta Wanda yasa ta fasa Kara tana durkusawa a gurin ta fashe da kuka da sauri Ilyah ya fito wanda duk abinda ake da yana ji bai fito sai yanzu da aka mari yar lelensa cikin fad'a ya soma magana.
"Wai Habubakar wanne irin wulakanci ne wannan ka zagi mata ta ka goranta mata ka shigo gidana kai tsaye ba neman izni na duk hakan bai ishe kaba saika marar mun 'ya to yanzu kam ya isa haka na gode zaka iya tafiya ba an baka abinda kazo nema ba" a fusace malam Habu yace "yaya Ilyah yau ni kake fad'awa haka a gaban matan ka da 'ya'yan ka nagode kuma ka nuna min iya matsayi na" jan hannun Amatu yai suka fita yana fita Bara'atu taja tsaki tana cewa "wallahi ko kadan bakai sa'ar dan uwa ba haba inaga da baka fito ba saidai a debi gawata yadda ya zuciya ya hauro dinnan tsaki Ilyah yaja yana huci yace "ni na rasa me yake damun sa saikace nine dora masa talaucin duk yabi ya addabe ni tunda karayar arziki ta same shi ya hana naji dad'i amma zanyi maganinsa kodan yanzu ma alhamdulillah nasan shi da zuciya watakila bazai sake zuwa gidan nan ba ni kuwa haka nake so kuyi sauri ku gyara kajin nan a dafa su in anjima zanyi manya baki wanda nake sarar kaya a hannun yan kauyukan nan nake sarar musu daga binni zasu zo dan Allah ku tsara abincin nan sosai" ya karasa maganar yana komawa d'aki ta tafar sauke Habiba amaryar Ilyah batace saidai tana mamakin bakin hali irin na Ilyah ace kana da wadata d'an uwanka baida shi Amma saidai ka wadata bare ka barshi yana yarfe gumi yana aunar abinci a shago da kasuwanni Allah ya sauwake ta fad'a a ranta tanajin takaici da nadamar aurensa haka Nafisa ta share fuskar yatsunsa kuwa d'as a fuskarta sun fito hakan yasa ta dau alkawarin daukar fansan.
Malam Habu na fita daga gidan Ilyah yai nufin zuwa gidan dayan yayan nasa Sabi'u yai sa'a kuwa ya same shi a kofar gidan sa zaune mutane sun kewaye shi irin masu neman na kayan miyar nan ganinsa cikin jama'a yasa bayan yayi sallama sun gaisa ya nemi su d'an ke'be can nisa da mutane suka tafi karkashin wata bishiyan kuka malam Habu yasan da kamar wuya amma zai gwada kokarinsa yana fatan yakai nasara "ina jinka Habubakar ya akai ne na ganka duk a hargitse"?.
Ran malam Habu a bace yace "yanzu tsakani da Allah yaya abinda matar yaya Ilyah tai min tayi daidai yanzu shi daya goya mata baya bayan yanajin irin cin fuskar datai min ya kyauta min kenan ya kyautawa Bappan mu"?.
"Meya faru ne Habu meya hada ku me kaje yi gidan"?.
A hankali cikin nutsuwa malam Habu yai masa bayanin komai kai Sabi'u ya jinjina yana cewa "ai indai Bara'atu zatai yafi haka ba kirki gareta ba ta maganar kane dan talaka bai iya samun waje ba amma babu komai karka damu za'a biya mana ina maman namu take nawa ne kudin ai na fad'a maka duk wata matsalar ka idan ta tashi ka rika zuwa kana fad'a min ka kyale Ilyah indai ba harkar zumunci bane yanzu ka wannan maza da sauri kaje ka biya mata" karba malam Habu yai cikin jin dad'i da kaunar yayan nasa Wanda yake share masa kuka a duk sanda ya kawo korafin sa bai ta'ba nuna gajiwa ba ya mike yana sake masa godiya da fatan alkairi kafin yaje ya rike hannun Amatu suka wuce da kwarin gwiwa ya mayar da it's makarantar ya biya mata komai sannan ya shiga cikin gari dayake makarantar ba a garinsu take ba kusa da kauyen sune saida aka tashi ya biya ya dauketa suka tafi gida.
Sauke ajiyar zuciya Amatu tai tare share hawayen fuskarta bayan ta dawo daga tunanin da take ta sani mahaifin ta mutum ne na 'kwarai mai kyawawan halaye sannan ya na son farantawa ahlin sa amma babu ta gama mamaye shi sauke kanta kasa tai ganin Binta ta zo wuce wa dan kada taga cewa kuka take, Amma me tuni ta hango ta tun daga nesa Saida tazo saitin ta tac
3 386
cin tsufa" fuskar Aisha cike da damuwa tace "to ya zanyi Amatu rashi ne yasa nasan da baban mu nada shi duk haka bazata faru ba" sauke ajiyar zuciya Amatu tai tare da jinjina kai tace "haka ne amma dan Allah a rika ragewa aikin na yawa" dariya Aisha tai tana cewa "shikenan babbar aunty za a kiyaye kaka mai kamar uwa hajiya Hauwa's mai zamani" dariya sukai Amatu na mata hararar wasa tace "meye na Kiran suna na haka babu ko dan kara"? Har lokacin fuskar Aisha da fara'a tace " kakar mu na tuno duk da bamu Santa ba Allah sarki hajiya Hauwa naji mutuwar 'yar tsohuwar nan" maida hankalin ta kan littafi Amatu tai tana cewa "to ta zamuyi wanda ya fimu sonta ne ya karbeta duk wata kulawa da kauna da zamu gwada mata bayan nasa ne shike iko da kowa" sauke ajiyar zuciya Aisha tai tana kallon Saude data fito a d'aki tana mata kallon mamaki na ke kuma yaushe kika shigo mikewa tai tare da nufar ta yayin da Jamila ma ta mike tana daukar kayan miyar ta tafi gidan ni'ka.
Shiru Amatu tai tana kallon kowa da komai gida babban gida amma yanayin tsarinsa da gyara gashi babanta nada dangi amma duk laifinsa suke gani wai ya zauna kara zube ba sana'a yasa rashin zuciya gashi ya tara iyalai shiru tai ta nutsa cikin tunani lokacin da baban ta yaje gurin yayansa ya bashi kud'i zai biya mata ta zana jarrabawa ya hana dan rufe ido tai maganganun da kawu Ilyah ya fad'awa babanta na mata yawo a kunne daga lokacin data tambayi kudin jarrabawar.
Cikin mamaki shigowar malam habu ganin Amatu zaune tana kuka yasa ya karaso da sauri yana d'ago ta tare da goge mata hawaye cikin lallahi yace "Mamana kukan me kike ba na raka ki har makaranta ba meyasa kika dawo" Amatu na shashshekar kuka tace "baba wai malamin yace ban bada kud'i ba wannan shekarar ma bazan zana jarrabawa ba saidai na jira yan ajin baya" dafe kai malam Habu yai yana kallonta yace "kiyi hakuri Mamana kinji taho taso muje gurin yaya kila yau tunda yaga dake yaji tausayin na ko aro ya bani kudin nan na biya miki" rike hannunta yai suna fita daga gidan suka shiga dayan daya kasance gidan yayansa da sallama ya samu matansa zaune suna gyaran kaji gefe ga yara can suna ta fama da kan saniyar da sukai dafgensa abu yaji ya tsirga masa mai d'aci amma ya daure bayan sun gaisa yace "ko yaya na nan"? Da'kyar suka bashi amsa a wulakance ganin ko shi yayan nasa Ilyah yadda yake masa kenan yana tutture shi babbar matar ce ta budi baki tace "eh kamar dai yana ciki karasa ka duba".
"Karasa ka duba"? Malam Habu ya tambaya cikin mamaki yana juyowa ya kalleta a gadarance tace "eh haka nace ko kana tunanin muna aiki akwai wanda zai tashi maka wahala bayan kai kazo nema" ran malam Habu a 'bace yace "Bara'atu kinsan abinda kike fada kuwa" wani kallo tai masa tana cewa "ni nasan abinda nake cewa domin ni a hayyaci na nake ina ci ina sha banda matsalar komai saidai azo inuwa ta a ra'bu a fake kai kuwa fa tun karayar arziki ta same ka kullum kana yawon maula a gidan kamar duk kauyen nan mune muka fi kowa arzik..................
"BARA'ATU!!!😡 Malam Habu ya fad'a cikin tsawa wanda hatta yaran dake zaune gefe suna cin nama saida suka tsorata nuna ta yake da yatsa idonsa yai ja na bacin rai yace "Bara'atu ki iya bakin ki a kaina wadatar da mijin ki yake dashi baki isa kice zaki wulakanta niba domin uban mu daya dashi baki San wahalar saba kawai kin ganshi a saurayin sa kika aure shi kuma shine kike neman zagi na"? Tabe baki tai tana cewa "eh ai isa nai" malam Habu zai magana suka jiyo muryar Ilyah na cewa "ke Bara'atu ke dawaye ne anan nake jin hayaniya haka"? Mikewa tai tana shiga d'akin sa ta dade kafin ta fito tana sake wuce su ta shiga wani wuri da alama dakin ajiyar abinci ne sai gata ta fito da daurin leda tana cewa "dama maula ce abinda ya kawo ku shi kanshi ya fahimta gashi nan garin kwaki ne yace a baka koda gishi kwa tsama kuci" ta karasa maganar tana aje masa a gaban sa kafin ta koma ta zauna.
Cikin fushi malam Habu yai bol da wannan ledar garin ya tarwatse yana huci yace "ai dama d'an talaka bai iya samun waje ba wato ke harkin manta irin ke wahalar da kika sha a gidan ku yanzu kin samu guri h
3 386
ayen fuskarta tadau bokiti tana yin waje.
"Malam gaskiya nifa ban gane anyi gabas da kare ya zanyi magana Dala ta musa min kuma kana jinta baka dau mataki ba ko tsoron ta kake domin labari yazo min idan bana nan nayi tafiya wai wannan abar mai kamar ta'barya har ka zauna tana maka masifa to wallahi bazai yiwu ba gaskiya da sake idan baka gyara ba zan karbe kudade na dana baka kake juyawa" jin barazanar da Asabe ke masa yasa cikin rarrashi yace " kiyi hakuri hakan bata ta'ba faruwa ba karya ake min har nine zan tsaya sauraron wannan abar kibar wata magana kawai ke kadai nake so da Bahijjan ki" dariya Asabe tai "da gaske kake"? Cikin nuna an gama dashi an shanye shi yace "kwarai Asabe da gaske nake " hade rai Asabe tai tana cewa "to ni ban yarda ba baka nuna min a zahiri ba saika saitawa wannan agwagwar matar taka hanya idan kuma ba haka ba daga yau baka sake mora ta sisi kaji na fad'a maka" jiki na rawa cikin tsawa Balarabe yace "ke wai Dalah wacce iriyar bulkuma ce gidahuma bance ki wuce ki fara aiki ba so kike ki silar auren ki yanzun nan kinsan halina sarai ni ba ba'kon ki bane" a damuwance Dalah ta wuce ta barsu a gurin da harara Balarabe ya bita yana cewa "ke kam Dalah kinyi asara mace sai bakin hali yadda fuskar take haka Zuciyar take wuluk da baki da mugun hali nayi da nasanin auren ki Dalah dole ce tasa nake zaune dake amma a juri zuwa rafi wata rana tulu zai fashe" yana fadin haka ya fita yana sake babbaka fad'a kamar bazai ta'ba shiru.
Yayin da Asabe tasa Dalah a gaba tana sheka dariya kamar zata kifa harda hawaye tace "to ya kikaji irin salon nawa Dalah kenan na fad'a miki baza ki iya ja dani ba bakisan wace ni Asabe ba suna a kawai kikeji amma daga yanzu ina fata sunan ya zauna a Zuciyar ki har abada domin nayi alkawarin saina 'kuntata miki daga yanzun kin fara shan dandanon azaba dake da 'yarki a hannu na mu zuba mu gani waye zai nasara saina kaiki kasa" dagowa Dalah tai tana kallon Asabe da jin maganganun da take fad'a saidai batai mamaki domin tun lokacin da Balarabe zai aureta mutane ke tausaya masa suna koka mata cewa zai auro mata masifa Asabe tsiya ce mai lasisi gashi kuwa abinda ake fad'i ya tabbata.................... "Meye kike kallo na maiya"? Muryar Asabe ce ta katse mata tunani danne damuwa da bacin ran dake cin ta Dalah tai tana kankaro murmushi tace "Allah ya shirye ki domin ke abar tausayi ce daga ranar da duniya ta juya miki baya zaki bayani" dariya dariya Asabe tai "ahayye nanaye yau ake yinta lallai kam Dalah kina lokacin yanzu har kece zakice kina tausayin wani? Ta fad'a tanai mata wani kallo na tsantsan rashin mutunci Sai kuma ta sake bushewa da dariya tana cewa amma kinci abinci a kanki shin kina duba mudubi kuwa kodan ina za'a samu darajar mudubi bayan komai bai wadata ba har kice zaki wa wani gori tirrrrr anji kunya 'yar ba'ki ai labari ya same ni tun bayan na auri Balarabe cewa ke maiya ce yar mayu jikar mayu iyayen ki korar maiya akayo musu daga wani tsinannan kauye suka dawo nan suka addabe mu wato da dare baban ki har kura yake zama ko🙊? Daidai Indo ta shigo da bokatin ruwa ta dire asabe dake binta da kallon banza tace bance kayan Bahijjah zaki wanke ba yar gwana jikar maiya Asabe take Aiko mata da mugayen kalaman da take fad'awa uwar ga tsinuwar Balarabe a kanta kuka kawai take kamar ranta zai fita bangare na Zuciyar na adduar Allah ya kawo mata sauyi cikin rayuwarta.
Amatu na zaune a kofar d'akinsu tana duba wani littafin addua Jamila na gefenta tana gyarawa A'i kayan miyar abincin saidawar su ta kalli yadda Aisha ta shigo jikinta duk a jike shakaf da gumi alamar daga aikatau take tana haki da sassarfa ta iso inda suke tana zama sai haki tace cikin tausayawa Jamila yace "sannu Aisha Allah dai ya rufa mana asiri ya kawo mana canji a rayuwar mu" murmushin karfi hali Aisha tai tana cewa "amin Amatullahi me kike dubawa ne"? Murmushi Amatu tai batare data d'ago ba domin ita ba ma'abociyar 'kure mutum da kallo bace tace "sannu Aisha kiji yadda kike haki fa dan Allah idan aiki yafi karfin ki kina ragewa wannan gajiya fa da kuke dibawa jikin ku zata tambaye ku sai loka
3 386
kadaddiya mai hana zaman lafiya da ke nake mai idon d'inya kina ina ko saina shigo d'akin na cillo waje dake zakifi fahimtar abinda nake fad'a".
Shiru yaji ba'a amsa ba a hargitse yace "Dalah ke Dalah kina jina kikai banza saboda ga d'an iska yazo yana magana ko"? Da sauri Asabe ta fito daga dayan dakin cikin munafirci tace "ayya malami na ango na uban yayana meya faru ne bansanka da fushi ba" Balarabe na jijjiga kamar mace yana huci yace "ina Dalah take"? Dad'i fal ran Asabe tace "ai bata taje anguwa ba" "anguwa uban wa ta tambaya har ta samu damar fita"? Kar dakai Asabe tai tana dariyar cin nasara zata hada bom yau a gidan tace "au wai dama bata fad'a maka ba ta fita? Ganin bai magana ba ta d'ora "gaskiya malam bakai dacen mace ba ashe dama ba tambayar ka take ba Amma kullum saita fita" "kullum ina take zuwa"? Balarabe ya fad'a bud'e baki Asabe tai zatai magana Dala ta shigo da sallama da kwano a hannun ta Wanda da sauri Asabe tace "ka gani ko maula taje anguwa ta na nunawa mutane kasawar ka cewa baka iya rike mu baka iya ciyar damu gaskiya malam kai maganin ta kullum fa haka take wannan yawon kamar taci kafar kare".
Bai saurari Asabe ba sai Dala daya zubawa na mujiya kafin a tsawace yace "Dala uban waye ya fasa a gari na nemi Indo har yanzu aka goranta min a majalisar zaman mu ki fad'a min"? Da mamaki sosai Dala tace "innalillahi wa inna ilaihi raji'un malam wallahi ba sani ba" a hasale yace " baki sani ba? Karki maida ni wani gailo man an fad'a miki cewa duk wani siddabu da kike a gidan nan da asirce asirce ban sani ba zuba miki ido nai dake da matsiyaciyar 'yar taki naki domin gadon ki tayo gadon tsiya da bakin hali ina Indo din itama dan kambun ubanta? Ke Indo kina ina"?.
Da gudu Indo ta fito daga d'aki tana sharar hawaye ta tsuguna a gabansa jiki na rawa wanda asabe a nata 'bangaren ji take kamar ta taka rawa dan murna burinta ya cika lallai Marka aikinta mai kyau zata sake dagewa harsai ta fitar da Dalah daga cikin wannan gidan ya zama daga ita sai yayanta ta wanda biyar ta tsoma goma....................
Tunanin tane ya katse jin tsawar da Balarabe ya daka yana kaiwa Indo duka yace "dan bantan uban ki dan darar ubanki dan 'kashin singallin uwarki yau saikin barmin gida na kore ki bani bake har abada Indo ki kama gabanki'.
Kukan takaici da damuwa Indo ta fashe dashi tana sake durkusawa sosai ta soma bashi hakuri da batasan laifin datai masa ba ace uba na garine amma ya tsani yarsa ya rikajin duk duniya ba wanda baya son gani sai ita, "baki ji me nace bane zaki tashi a gabana ko saina fasa miki baki" yai maganar yana kai mata harbi da kafa jan kujera Asabe tai tana zama tare da zubo musu ido bakinta har kunne tace "malam kayi hakuri ka kyale ta tana mace idan ka koreta yanzu ina zataje duniya zata shiga karshe ta dirko cikin shege kuma ta dawo ta haife maka shi a gida" a zafafe Balarabe yace "Allah ya sauwake saidai ta nufi gidan marina amma ba gida ba dan ni na sallama ta" "to yanzun dai kayi hakuri na fanshe ta da sharadin zata rika yi mini duk wani aikin gida kama daga shara wanki wanke kwanuka aikin abinci kai inaso Bahijjah ma ta huta Indo ta dawo fita min da abincin sayarwa ta" ta karasa maganar tana sakarwa Indo muguwar harara.
"Wannan shi kike bukata"? Balarabe ya tambaya jiki na mazari d'aga kai Asabe tai "eh hakan ma yayi daga yau ka zama sarki ni gimbiya Indo da Dala bayin mu ko me kace"? Da sauri ya amsa mata "eh na amince na amince ba damuwa dama ai bayin ne aikin jakuna ne ya dace dasu" murmushi Asabe tai yauwa bari a fara yanzu ke Indo dauki bokatin san kije yanzu ki kawo min ruwa ke kuma Dala saiki dora mana tuwo".
Cikin takaici Dala tace "baki isa ba Asabe kinyi kadan a gidan nan kikazo kika sameni dan haka baza ki min mulkin mallaka ba" zaro ido Asabe tai tare da fashewa da dariya tace "au ashe har yanzu da d'an saurin karfin ki Dalah lallai kam na jinjina miki" sai kuma ta hade rai cikin tsawa tana kallon Indo tace "ke kuma ubanki kike jira da bazaki tashi ki fara abinda nace miki ba idan kin debo ga wankin Bahijjah can ya na jiran ki" mikewa Indo tai tana sake goge haw
3 386
dashi kuna yan'kare masa hakori da wayon 'kauye shi kuma ba rowa yana baku kud'i kuna bushasha amma yanzu dan karaya ta same shi kuke masa dariya gaskiya kun zama bulutu masu manta kyautar jiya ku sake tunani".
Tsam Tanko ya tsomo baki "to kai Sadi indai ba munafirci da shishshigi ba meye naka a ciki waye baisan bakin talaucin malam Habu ba saifa ba'ko wanda mota ta sauke amma indai d'an gari ne haifaffan kauyen nan yasan malam Habu fa'kiri ne a fa'kiran ma shine ogon yan rashin wadatuwa da komai" dariya Mudi yai yana cewa "haka nefa Tanko kila yanzu inka latsa shi bashi da biyar tasa rabon da yaga kud'i harya manta saidai ya hango su daga nesa a hannun wani yayi fatar ina ma shine kila biyar tasa bazai kuma mallaka ba" dariya suka bushe da ita harda masu rike ciki wanda malam Habu yaji zafin dariyar amma ya danne kamar bai damu ba yace "ba dani kuke ba da wanda ya jarrabe ni kuke" "waye ya jarrabe ka" Mudi yai maganar yana kuma shekewa da dariya "ban sani ba 😠" malam Habu yace yana daure fuska.
Sadi dai da baya jin dad'in abinda ke faruwa yace "dan Allah malam Habu kayi hakuri" cikin nuna rashin damuwa malam Habu yace "ba abinda ya bata min rai kasan su ba komai suke ganewa ba" "maye bama ganewa"? Tanko ya fad'a yana dauko sigari akan farantin gaban Mudi zai kunna wuta da sauri malam Habu ya tashi tsaye zai tafi yace "kune abin tausayin amma kun kasa ganewa Allah ya ganar daku" da sauri Tanko da Mudi suka ce "Amin inda gaske kake idan kuma ka fada ne dan ace kai malami ne na Allah Zuciyar ka a wanke take nan kuwa ba'ki 'kirim take aniyarka ta bika" malam Habu dai bai kuma sauraron suba yai gaba domin sun kore shi sakamakon wannan sigari da Tanko ya kunno.
Sadi daya bi malam Habu da kallo harya 'bacewa ganin sa yace "kai jama'a rayuwa a gaskiya ina tausayawa mutumin ace kullum rayuwar ka ba sauyi kome a ta'ba kamar me bakin iyaye saiya narke" tsaki Mudi yai yana cewa "kai dallacan wa ya fad'a maka malam Habu abin tausayi ne? Ai talauci da rariyar hannu yanzu ya fara gani ba ya nace saiya iya rike gidan saba muje zuwa waye mai nasara" cikin mamaki Sadi yace "ban gane meye abinda kake cewa ba kamar akwai abinda ka sani game dashi"? Murmushi Mudi yai mai ma'ana yana sake kure Sadi da kallo yace "karka damu haka malam Habu zai Kare rayuwar sa kamar 'beran masallaci bazai ta'ba samun wadata ba" "wai me kake cewa ne Mudi lafazin ka ya nuna da akwai wani abu da kake shiryawa" dariya Tanko yai yana cewa "malam Sadi karka damu wannan ba shafin ka bane mu tsaya iya haka kada ka sake neman binciken wani abu gare mu" shiru Sadi yai duk hankalinsa bai kwanta ba yace "amma da akwai wani abu da kuke boye min"? Har hada baki sukai wajen cewa "karka damu damu" sauke numfashi Sadi yai yana cewa "to meyasa bakwa so na sani"? A zafafe Mudi yace "to kai munafikin banza me kake so ka sani bayan wanda ka sani"? Sadi bai damu da zagin mudi ba ya kalli Tanko yana cewa "to me kuke boyewa" kafada Tanko ya d'aga "babu abinda muke boyewa kaga abu sa'banin hankali ne a tattare damu"? Kai Sadi ya jinjina yana cewa "kwarai ba abu daya ba da yawa kuke boyewa kuji tsoron Allah idan da hannun ku akan bawan Allahn nan ku kyale shi yaji dad'in rayuwar sa dan Allah" harararsa Tanko yai yana fadin "ka damu da kanka kaima ka kashe wutar dake gabanka kafin kai kokarin kashe ta wani" mikewa Sadi yai yana cewa "indai kune silar durkushewar malam Habu gaskiya kun cika azzalumai makiya a garesa amma ba damuwa akwai Allah zai saka masa" Sadi zaibar wajen caraf Tanko ya rike masa riga yana cewa "to ba kaji sirrin mu ba kada ka fad'awa kowa idan tsautsayi yasa ka fitar da zancen nan zakaga yadda ake wasan tsutsa a rana" cikin takaici Sadi ya fisge daga rikon da Tanko yai masa yana jan tsaki yabar gurin aka barsu iya su kadai sai zu'kar hayaki suke kallo d'aya zakai musu kasan su 'kware a wannan fannin.
Balarabe na zuwa cikin gidan shi ya bankad'a labule yana cewa "munafika ina kike fito yau asirin ya tonu kin gama yawa mitsiyaciya mai farar 'kafar dama zaman hakuri nake dake komai nawa a sace hakan bai ishe kiba harsai kin fad'awa duniya hali na ban
3 386
ce ko daya ba balle har ya samu 'ya'yan kaga babu wanda ya kai shi talauci ko akwai"? Ya karasa maganar yana kallon malam malam Tanko.
A zabure Mudi yace "wannan kuma dani kake malam Habu eh ban rike mace dayan ba amma ai ina da abinda me mata da yawan baida shi kud'i gonaki da yawa da kuma filaye ba abinda wani shege zai fad'a min" kai malam Habu ya jinjina yana cewa "kayi kokari Mudi kuma ka tabbata mai fad'a da cikawa ni kaina naga haka amma saidai duk kud'i na da wadatar da nake dashi bai amfane niba domin kuwa nasan d'ai d'ai ne a majalisar nan wanda bai bina kud'i kuma bazan biya ba naci na lahira haka nake ni haram din ma nemanta nake" duk zaro ido sukai suna bin malam Habu da kallon mamaki kafin Balarabe yace "amma dai malam Habu gaskiya kana da idon akuya uban Isyaku ne fa amma a idon sa kake ci masa mutunci" kai malam Habu ya girgiza bai kalli saitin da Isyaku yake ba saiya kalli idanun Balarabe yana cewa "ka fad'i gaskiya Balarabe idon akuya gare ni, kuma kowa ya shaida haka tunda kwanan baya har kama ni akai zanyi kwartanci da 'yata kaga ina kunya anan"? Dafa kirji Balarabe yai idon sa kamar zai fito waje na mamakin a ina malam Habu yasan wannan maganar bayan a iya gidan sa abin ya faru daga shi sai matarsa sai kuma yarsa ya kashe mata warning karta fad'awa kowa ya akai malam Habu ya San.........
Katse mata tunani malam Habu yai ta hanyar cewa "ko kana tantama ne naga kamar ka shiga shakkun magana ta" dawo da kallon sa Balarabe yai kan malam Habu kafin ya kalli kowa da yake gurin gashi sun subo masa ido alamar neman karin bayani yasa cikin takaici da borin kunya yace "wanne tsinannan ne ya fad'a maka"? Hade rai malam Habu yai yana cewa "kana mamaki ne"? A fusace Balarabe yace "Allah ya kwashewa wanda ya fad'a maka Allah ya tsine masa ya hada shi da masifu iri iri" amin Amin duka guri ya kaure gyara zama malam Habu yai yana cewa "ai Balarabe duk gurin ba wanda bai san haka ba kawai suna boye maka ne suna nuna basu sani ba amma a zahirin gaskiya ta hannun sha'ki'kin ka muka samu labarin" "waye wani sha'ki'ki na"? "Ai bani zaka tambaya ba malam Balarabe ka tambayi yan gurin mana na dai fi tunanin ba ni kadai ne mai ruhi anan ba" mikewa Balarabe yai yana cewa "to duk Wanda ya fad'a ma Allah ya tsine masa albarka ya d'ora masa mugun ba'kin talauci" yana gama fadin haka ya karkade rigarsa yai gaba yana tafe ya na masifa a layi.
Tanko ne yace "gaskiya malam Habu baka kyauta ba dan me zaka ce masa haka kuskure aka samu" wani kallo malam Habu yai masa yasa cewa " ka jira ni kaima ban gama dakai ba akwai tsakin mu da tsakuwa dakai dan wallahi nafi karfin wulakancin kowa a cikin ku" Mudi cikin haushin gorin da malam Habu yai masa dazu yace "ah kafi karfin wulakancin kowa Kam tunda ka samu shiga yayan matarka yana binni shine yake turo maka kud'i shiyasa kakewa kowa kallon hadarin kaji" kai malam Habu ya d'aga "ai hakan ma arziki ne wani ya samu yayan matar tasa ya ri'ka turo masa kamar ni din idan zai iya na isa ne" "ka isa kuma"? Tanko yai maganar cikin 'kulewa malam Habu bai damu da tunzurar da Tanko yai ba yaci gaba "eh na isa ne harna wuce inda ake tunani kuma a gabaki dayan majalisar nan babu wanda ya isa kamo kafa ta arziki badan ruwa da yaiwa babban zakara duka ya dawo d'an tsiyako ba" cikin ba'a Mudi yace "au au ba wani ruwa daya daki babban zakara ka dawo da arzikin naka mana watakila tunkaho da gadara daka fara nuna mana ne Allah ya jarrabe ka da talauci da rariyar hannu ya kwace kudin" "wa ya fad'a maka jahili"? Malam Habu ya tambaye shi yana kallon yadda Mudi ya zuro masa ido "rai bace Mudi yace "ka fad'i komai malam Habu lokacin kane dan banyi karatu ba kake goranta min kaima ba wayon Kane ya baka ba" caraf Sadi dake gefe tun dasu yana son yai magana sai yanzu yace "wai ku dan Allah meyasa kuke haka? Matukar malam Habu yazo gurin nan baza kubar shi ya huta ba waye ne keba da talauci ko arziki?" Ganin sunyi shiru yaci gaba "gaskiya yan majalisar nan ku gyara malam Habu fa ba karamin mutum bane ba abin rainawa bane ya kamata kusa hankalinku guri daya lokacin da yake da abin hannu kullum kuna li'ke
3 386
ko ya Nasuruddini a kujerar ka auwalun ne kai marar sani ya Wanda bai ta'ba hanawa masu nema ba, nabiyul huda da kaine aka bud'e kullalle rahmarka ta isarwa wahallalle da makalalle ka sada bayi da Allah zuwanka shalele badon dakai ba ba'a san azumi da zakka ba, ka saita bayi akan hanya ta Islama a koyarwar ka harda ladabin sanya takalma abinci kwa kar aci shi sai ansa hannun dama Bismillah ayi baza'a ci harda shed'an ba.
03~ AL-MALIK
The king
04~ AL-QUDDUS
The holy.
🚨 Think before you do 🚨
💃💃💃💃
🏞️ ''yar Musa jikar Abubakar Muhammad ta kowa ce🙈.
Till we meet masoya sai naji comment dinku koda ma ace zanci gaba gobe ngd.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Mrs Al'ameen Ahmad ce.
Barkan mu da kwana masoya yan uwa makaranta da marubuta inaiwa kowa da kowa fatan alkairi da samun rahmar ubangiji.
Yusrah Musa Abubakar maman Fatima ilham little Zaran aunty little Zaran Abba.
💫ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY GIDAN KARBAR MUTANE HANNU BIYU DA ZAMAN LAFIYA MAI DOREWA ANNURI HASKE LEKA GIDAN KOWA KODA MAKIYA NA KALLON KA RAMIN KURA SAI 'YA'YAN TA.
👑ME KAMAR SARKI 👑
Dedicated to
MR HAUSA EBOOKS📚
📚📔📖📘📙📗📔📝📚
Daga ✍️alkamin YUSRAHMS marubuciyar👇
Yarima Abdulmalik
Rayuwa biyu
Safriyyah
Husnah ko Badiyat
'Dan millionaire
Haskena sauban
Dama kece
Kowacce 'kwarya
Mina-umer
Royalty
A gidan talaka
Zuciyar Aliyu and now👇.........
💞🌹💃Me kamar sarki💞🌹💃
2-Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Mujahidina.
YUSRAHMS#
🌄 SESSION ND REACTION 🌄
Episode 03 nd 04
Bayan sallar la'asar rana tayi lis ta tafi faduwa almurun magriba ya fara bayyana malam Habu ya fito daga d'aki zai fita waje da sauri A'i ta tare shi tana cewa "malam kud'i na fa da nake binka gaskiya ka bani nima kwanakin nan na shiga talauci" kallon yadda take jijjiga malam Habu yai kamar wacce ke shirin dambe dashi kafin ya budi baki yace "bani dashi" zai sa kai ya fita ta kuma shan gaban sa "malam gaskiya nifa na gajiya kullum da anyi magana kace baka dashi sai kace kai talauci ya wasa ka tashi ka nema ka'ki nidai bazan iya ci gaba da irin wannan rayuwar ba ehe" "bani hanya A'i" malam Habu ya fad'a cikin tsawa da nuna fushi wanda da sauri ta matsa gefe tsakin takaici yai yana ficewa yayin da A'i ta rakashi da harara tana cewa "haka dai ka iya mutum yai magana aga zafin sa wannan bakin talauci haka wallahi bazan iya ba malam ka dawo ko me za'ai ayi ko hatsin daka noma ne saika warar mun na kud'i na" ta fad'a tana komawa ta zauna.
Malam Habu majalisar zaman su ta manyan gari ya nufa tun daga nesa yake jiyo dariyar su da hayaniya wanda idan da sabo ya saba suna zolayar sa yana karasawa wani tsakatsakin mutum yace "a'a malam alhaji sir Habubakar mai arziki kamar da bakin kwarya kaga na baba mai ruwan nairori taka sannu d'an uwan malam Sabi'u na attajiri Ilyasu kaga d'an Baffah masu hannu da maiko sai kayi" nan kowa ya fara 'babbaka dariyar rainin wayo da mugunta sunsan ba'a malam Tanko yake masa.
Ran malam Habu ya baci amma saiya danne bai nuna ba ya zaune yana basu hannu suka gaisa caraf malam Mudi yace "ai na wuce ta gefen gonar ka dazu naga kuna ta aiki kaida yan matan ka yanzu kai malam Habu tsabar son kud'i maimakon ka dauki yan aiki mutum biyu maza kaje kana wahalar da yayanka gaskiya ba tsari abinda kake ka daina ko hakan ne zaisa kayi arziki"? Nan dariya suka washe da ita cikin bacin rai malam Habu yace "eh kuyi dariyar ku nikam lokacin dariya na ya wuce tunda har mahaifa na suka mutu suna tsine min kuma ban roki yafiyar suba shiyasa naga yanzu arziki har bina yake" ya fad'a yana kawar dakai a fuakace Tanko yace "nasan Dani kake malam Habu bada kowa ba duk gurin nan kowa yasan haka" kallon sa malam Habu yai yana cewa "au abinda ciwo ashe aina dauka baza kaji zafi ba? Kuma ni ai ban fad'i suna ba zarguwa kawai kayi, gara ni ina da arzikin 'ya'ya matan kuma alhamdulillah na godewa Allah yaya mata sun min komai wani kwa bazai iya rikar ma
3 386
ta jeki diba kiyi wanka kinji" kai Jamila ta d'aga tana goge hawayen fuskarta kafin ta wuce Binta ma barin gurin tai yayin da A'i taja kujera ta zauna tana masifa wanda har makwafta suna jiyo ta.
Wucewa d'akin sa malam habu yai bai kuma furta wata kalma ba suma su Aisha d'akin su suka shiga domin su huta gajiyar su ganin yau Saude batai musu abincin saidawa ba haka Jamila ta shirya tadau abincin saidawa ta fita har lokacin bata daina share hawaye ba Wanda saida ta sake shan matsa a d'aki A'i tana mata gargadin karta sake ta dawo mata da kwashen abinci.
Da sallama Binta ta shiga d'akin malam Habu Wanda yake kwance akan wata gajiyayyiyar 'yar katifa mai yanayi da tabarma ya rufe ido kamar mai bacci jin sallama yasa shi budewa tare da tashi zaune yai shiru kana ganinsa kasan cewa yana cikin matsananciyar damuwa ko ba'a fad'a maka ba aje kwanon hannunta Binta tai tana zama a gefensa tace "malam ga abinci" ganin yai shiru bai amsa mata ba tace "malam dan Allah kayi hakuri ka daina sa damuwa a ranka kada hawan jini ya kama ka arziki da talauci duka na Allah ba wanda aka haife shi da kud'i kowa a duniya ya samu a duniya zai barshi mai rai baya fidda rai da rabo".
Ganin jiya iyau bai tanka ba yasa tadan dafa kafadar shi tana cewa "malam lafiya"? Sauke ajiyar zuciya yai "eh lafiya Binta kada ki damu kalau nake" cikin tausayawa tace "to amma malam dan Allah ka rage yawan tunanin nan idan jari ne zan baka aron dubu goma ka saro koda mangoro ne kana saidawa" kai ya girgiza "Binta matsalar ba'a ni bane na kasa gane meke damu na kamar me rariyar hannu ko me na ta'ba bazai albarka ba sai kace mai bakin iyaye kuma kinsan wani abu Binta wallahi harna rabu da mahaifana babu ranar da zata fito ta fad'i basu ce Allah yamin albarka ba na d'ago ina matashi nayi tashen kud'i da manya manyan kasuwanci amma lokaci guda kud'i ya narke min a ka ba iya nawa ba harda na mutane dole filayen Dana mallaka da gonaki haka na rika d'agawa ina Saida su dan dole ina biyan mutane kudaden su tun daga wannan lokaci rayuwa ta juya min baya ban kuma samun kwanciyar hankali ba harwa yau Binta" ya karasa maganar yana dafe kanshi dake sara masa.
Goge hawayen fuskarta Binta tai tana cewa "kayi hakuri malam hakan ma jarrabawa ce kayi kokarin ciyewa sai Allah ya maida maka mafi alkairin sa" kai ya jinjina "na gode Binta hakan yasa naji dama dama ki kaimin ruwa bayi zan fito wanka yanzu" mikewa tai tana cewa "to malam kaci abincin kafin nan bari na dafa ma ruwan saboda naji kamar garin da dan sanyi sanyi" ta fad'a tana bud'e labule ta fita ganin Amatu tai zaune a kofar d'akinsu ta zuba tagumi naban tausayin tana kallon guri daya har zatai mata magana kuma saita fasa ta wuce aikin ta tana tausayawa ahlin gidan nan.
MRS AL'AMEEN AHMAD CE😘
Yusrah Musa Abubakar maman Fatima ilham )(little Zaran aunty)(
To reader's anan zan tsaya insha Allahu sai wanda yake damu ya bamu aron rai zuwa gobe idan naga comment naku shine zai tabbatar min da kuna bina ko a'a sai mu d'ora fata na a koda yaushe ku kasance cikin farin ciki.
Sannan ina son saidawa masoyana cewa Yusrah Musa Abubakar ta kowa ce ga mai bukatar magana dani👇
+234-816-098-3083
Chat with me, be with me at always my lovers, we will me again till we meet.
#✅OTE
#COMMENTS
#SHARE
#FALLOW.
Ina gaisuwa gareki gudan jini na 'yar uwata Naja'at Musa Abubakar banda tankar ki Allah ya kara hada kan zumuncin mu ya tsare min ke daga dukkan sharrin mutum da aljan Amin 👏.
💕📿Manzon Allah s a w📿💕
Ya mai nasiha ga alumma muso juna mu rike gaskiya amana dan gudun kuna mu raya zuminci hanya ne na aljannah makiyin zumunci baya kusanci ceto ba, azimu domin muntahal mukami a kara hau Dani makurar mukami a karfafa mini a dade ni kaimi na bayayyanar da sirri na zuciya ta sallim ala abban su nana Binta mafi cika da girma a duk halitta ai nuru babullah mafi nagarta dashi halittu suka samu gata, kofar shiga da fita nana Fadima ce rahmar halitta zahra'u arziki ce kai Fadima tsikar jikin jiki ce na mustaphal arabi sannu nana Binta, ya wanda halinsa ne tayar damai rauni d'abi'ar kace taima
3 386
a A'i amma dai baki adalci ba bafa mune mukai miki laifi kika saki guga ta fad'a yanzu dame zamu debi ruwan"? Cikin masifa A'i tace "oho miki ban sani ba damuwar kice kina da ruwa ko baki dashi bai shafe ni wannan ba matsala ta bace taki ce" cikin 'bacin rai Saude ta shako hijab din A'i nan suka fara dambe wanda ya riga ya zame musu jiki idan da sabo sun saba da sauri wata mace ta fito daga wani wuri dake fitar da hayaki tana cewa "haba ku kuwa dan Allah kullum kuna cikin fad'a ko karnuka basa abinda kuke gashi abin takaicin babu ruwan ku da wai yaranku suna gurin suna kallonku kada ku zama haka wata rana zakuji kunya" ganin ko sauraron ta basayi yasa ta shigq tsakanin su tana raba su amma ina Saude ta gama tukuikuye hijab din A'i tana cewa "babu ruwan ki Binta ki kyale ni naci uwarta" a hasale A'i tace "kici uwar ki dai dan wallahi baki isa ki zage ni na kyale kiba saina zubar miki da wadannan rubabbun hakoran" a fusace Saude ta kuma shako A'i sai saukar duka kakeji tim tim suna dambe wanda gabadaya sun gama luguiguice Binta wacce take kokarin raba su amma ta kasa tsawa suka ji ta bayansu.
"Kaiiiii kaiii meye hakan"!!!!? Basu saki juna ba kowa na huci suka juya suna kallonshi rai bace ya karaso yana cewa "wannan wanne irin shashanci ne wai filin ya'ki kuka maida min gida da kullum sai kunyi fad'a kamar karnuka to wallahi bazai yiwu ba tun wuri ku gyara halayen ku kafin na dau mataki har yanzu bakusan waye malam Habu ba inaga saina tuna muku watakila kun manta bana son hauka da d'anyen kai".
Sakin A'i Saude tai tana huci tace "wai malam dan kawai nace............katse ta malam Habu yai "na tambaye kine meye abinda ya faru tsakanin ku na gaji da halin ku bana son jin komai yanzu kam ya isa haka ni ba shashashan mai gida bane dole ku canza nafi karfin gidana kusa tunanin ku guri daya".
Gud'a da shewa A'i ta rafka kamar zata cire hanci tana cewa "ayyuririiiii ayyuri yuriiiiii kai jama'a ikon Allah sai kallo wato kai a hakan daukar ka kake kafi karfin gidanka ko malam Habu mai carbi? To wallahi bari kaji tin wuri garama ka daina fad'a domin idan yan kauyen nan sukaji zasuyi maka dariya a baki ne kafi karfin gidanka wajen zakwad'i da zance amma ai ba wata tsiyar kake bamu ba zama 'kalli 'kalular da saidai mu ciyar da kanmu sisi kana bamu ne saidai ka zuro ido kana nema a gurin anji jiki wallahi anyi asara" ta karasa maganar tana shigewa daki tacigaba da masifa iri iri yayin da tabar malam Habu tsaye guri daya kamar an dasa shi dan bakin cikin maganganun data fad'a masa.
Kuka Amatu ta fashe dashi tana shigewa d'aki a duniya ta tsani jin ana cin mutuncin mahaifin ta zata dau Kowacce irin magana amma banda wannan A'i daga cikin d'aki tace "Jamila kizo ki fita da abincin nan kada muyi kwashe dama kune zanbi na taho dake wannan tsinanniyar ta tare ni akan na jefa guga a rijiya" sak Jamila tai cikin kunyar maganganun da A'i keyi tana kallon su Aisha da Asma'u a hankali tace "Aisha dan Allah kuyi hakuri" murmushin dole Aisha tai tana cewa "karki damu babu komai" dundu mai zafi Jamila taji a bayan ta a firgice ta juya A'i ta gani tana huci kafin ta bud'e baki tai magana ta rufe ta da duka tana cewa "suyi hakurin uban ki shegiya wacce kare ya lashewa kurwa nidai ba gado na kikayo ba mitsiyaciya" da gudu Binta ta fito jin dukan bana karewa bane tazo tana janye A'i dake d'irkar Jamila kamar ta samu jaka tace "haba A'i dan Allah yanzu wannan dukan da kike mata bakya tsoro ki tara mata jini a ciki me tai miki baki barta da yunwa da gajiyar aiki ba kinzo kina sake dora mata wani ciwon" hura hanci A'i keyi tana hararar Jamila dake kuka kamar ranta zai fita tace "wallahi kadan kika gani indai juninki a saranci zakici na jaki a guri na sarai kinsan hali na" ta karasa maganar tana kai mata wani dukan da sauri Binta ta tare cikin takaici tace "wai dan Allah A'i meye hakan"? Hannu A'i ta d'aga "kinga Binta ba ruwan ki ina ce 'yata ce koma me nai mata ki 'kyale ni" shiru Binta tai tana kallon A'i cikin mamaki kafin tace "Allah ya huci Zuciyar ki" d'ago Jamila tai tana cewa "kinga Jamila daina kuka maza dauki baho akwai ruwa a randa
3 386
ai ya girgiza mata "a'a mama na jeki gida baki da lafiya Allah ya sauwa'ke karki damu kinji" numfashi ta sau'ke a hankali kafin tace "to shikenan baba sai kun taho" "yauwa mama na Allah ya albarkaci rayuwar ki" cikin jin dad'in addu'arsa a duk sanda yai mata tace "amin baba nagode" juyawa tai tana nufar Fatima wacce ke tsaye tana jiranta kafin suka fita daga gonar suna gangarawa kan hanya suka fara tafiya.
Cikin naci Fatima tace "ke Amatu nifa na 'kosa baki fad'a min mafarkin me kikai ba" kallon ta Amatu tai "ai nace zan fad'a miki" "to ina jinki".
Saida Amatu ta kuma sauke numfashi kafin a hankali ta soma magana "Fatima mafarki nai wai gani a wani irin guri mai shuke shuke da kyan gani abin kwatance gurine daya wadatu da furanni kala kala ina sanye da alkyabba fara tarr nasha lalle kafa ta takalmi ne mai kyau da tsada wuya na da sar'ka ta gwal fuska ta da kwalliya a gefe da gefe na akwai bayi a baya na akwai bayi sun tsaya tun kafin na shigo gurin shi kuma tsaye yake a gaban wani guri wanda ruwa yake 'bubbuga an zagaye gurin da fulawoyi masu kyan launi a hankali na isa gareshi ta bayansa batare daya sani ba na taka wani dutse ina son nakai daidai tsayinsa daga bayansa nasa hannuna na rufe masa idanu wanda inajin sautin murmushin daya sakar min kafin ya rike hannuwa na yana bude idanuwansa ya juyo gare ni yana d'aga ni sama daga kan dutsen bai ajiye ni ko'ina ba sai a wani gurin shimfidadden carpet mai taushi wanda ya 'kawatu da kayan 'kawa na ado da abubuwan sha iri daban wanda ban ta'ba gani ba zama mukai yana rungume dani da muryar sa mai za'ki yace 'ina tsakanin sonki mata na banda kamar ki ina fata mu kasance tare' murmushi nai wanda yaja hankalin sa har ya shafo beauty points dinta daya lotsa sakamakon murmushin da nai bude baki nai zanyi magana ya sunkuyo yana d'ora bakinsa akan nawa kawai daga haka naji umma tana tashi na ban cigaba ba har bacci na koma bayan sallar asuba ko zan dora daga inda na tsaya amma a banza banyi mafarkin komai ba kinji abinda yasani farin ciki kuma ni kaina bansan dalili ba".
Sauke ajiyar zuciya Fatima tai kafin ta fara dariya tana cewa "gaskiya ne "kawata kenan mafarkin yarima d'an sarki kikai kuna tare kin zama matar sa"? Kai Amatu ta d'aga tana cewa "eh" cigaba Fatima tai "kai ai mafarki yana da abin mamaki sai kikaji dama gaske ne amma bamu sani ba ko zai zama gasken nan gaba" kai Amatu ta girgiza "taya zai zama gaskiya Fatima wannan gurin har na 'kare rayuwa ta bazan ta'ba ganin saba" cikin tsokana Fatima tace "to kika sani ko Sa'adu d'an gidan mai gari zaki aura" hade rai Amatu tai "kinga ki daina hada ni dashi kin manta kwanan baya uwarsa har gida taje ta tsiyata umma ai ko d'an gwal ne Sa'adu bazan aure Shiba" dariya Fatima tai tana cewa "nima da wasa nake Sa'adu da ba ganin girman manya yake ba kuma ba abun kunya bane ya ci mutuncin ki ubansa ya sani amma ya dauke kai da d'an wani ne da kinji bakinsa na shela 'kauyukan kusa damu ma sai sunji labari" tabe baki Amatu tai tana cewa "yabi dai a hankali duniya ta ishi kowa riga da wando wanda bai zota bama jiran sa take balle wanda yake cikin ta".
Tare suka shiga gidan daya kasance da mata uku Kowacce da aikin da take matar dake bakin rijiya tana jan ruwa ne ta juyo tana cewa "Ke Amatu ya na ganki ke kadai ina sauran a ina kika baro su Jamilan ga tallar abinci na jiran su"? Aje kwanon hannunta Amatu tai tana d'an kallon wacce tai mata maganar kafin tace "suna can basu gama aikin ba" sakin gugan A'i tai tana rike kugu tace "kuturun ubancan lallai malam da wargi yake wato ke da yake mai ido da kwalli ce kina kai abinci kika dawo amma tawa 'yar da yake bata da gata tana can rana na gasa mata baya wallahi bazai yiwu ba bari na dauko hijab na na bisu gonar na taho da 'yata da kaina" d'aki ta nufa tana bala'i "wannan muguntar har ina 'ya'ya mata ba maza ba a dauke ku aikin garada cikin rana ba wani amfanin arziki za'a samu ba dandani haukaci kafin shekara ya kare sai dai aune za a kashe min 'ya da aiki to wallahi bazata sa'bo ba".
Ganin ta saki gugar ta fad'a ga babu mai ruwa a gidan yasa Saude data fito daga d'aki tace "hab
3 386
tsaye tare da rike bayan shi alamar ciwo yake masa sharce zufan fuskarsa yai yana kallon 'yan matan yace.
"Wai ni kam Aishatu ina kuka baro Mamana ne har yanzu me take a gida bata zo ba gashi munci 'karfin aiki ko yau ma zazzabin ne"?.
Ya tambaya yana zama cikin gajiya sosai kallo d'aya zakai masa kasan cewa talauci ya gama samun gurin zama a jikin sa d'agowa wacce ya kira da Aisha tai itama ta jike shakaf da gumi cikin alamun gajiya da yunwa tace "wallahi baba ban sani ba har muka taho nidai ban ganta ba amma bana ce ba ko Asma'u ta ganta kai Asma'u ta girgiza tana cewa "a'a nima bamu hadu ba".
Kai baba ya jinjina yana cewa "to ikon Allah, Allah yasa dai lafiya mama na bata zo ba na damu akan zazzabin nan nata mara jin magani gashi duk d'an kudin hannu na ya 'kare, baka dashi a d'aka baka dashi a waje masu kudi sunai ma kallon ka 'ki tashi ne ka nema kai jama'a Allah rufa mana asiri dai" ya fad'a cikin damuwa sosai tare da mikewa yana daukar wukar ya koma bakin aikin sa da kallo 'ya'yan nasa suka bishi cikin tausayawa domin sun san waye uban su matukar yana dashi baya hana iyalinsa yana wadata su da komai amma babu tai masa katutu.
Tafe wata zu'ke'kiyar kyakkyawar zazzafar budurwa 'yar kimanin shekara ashirin da biyu take dauke da fanteka a kanta bata kallon kowa bata kallon komai sai hanyar da take bi wacce ciyawa tai kwance lif akai daga bayanta taji ana 'kwala mata kira da karfi "AMATULLAH ke AMATU ki tsaya".
Dakatawa tai batare data juya ba har wacce ke kiran ta karaso tana d'an haki tace "haba Amatu kamar wacce kika fara kurmancewa ina ta kiran ki sai yanzu kika jini" fuskarta dauke da wani kyakkyawan siritaccen murmushi tadan juya manyan fararen idanuwanta kafin da murya mai dad'in sauraro tace "haba Fatima kinsan na jiki bazan 'kyale kiba" sauke ajiyar zuciya Fatima tai tana cewa "amma na tambaye ki wani abu"? Ta fad'a tana mamakin yadda taga yau fuskar Amatu da murmushi mai kyan kwatance tacigaba "wannan murmushin ya nuna akwai wani abu daya faranta miki ranki idan na canka daidai"?. 'yar dariya Amatu tai tana cewa "kinga sauri nake zanje gurin su baba ki bari idan na dawo zan fad'a miki" kai Fatima ta d'aga tana cewa "ai dama na taho ne dan na raka ki" "to shikenan muje.
Wucewa sukai Fatima da mamaki ya gama cika ta da annurin da take gani a fuskar 'kawar ta ta yasa ta kasa hakuri tace "Amatu nifa na kasa fahimta dan Allah ki fad'a min miyasaki farin ciki haka"?.
Sauke ajiyar zuciya Amatu tai tana cewa "kinsan abinda ya bani mamaki? wani irin mafarki nai wanda na kasa fassara shi to me ma zan kirashi? Ki fad'a min Fatima na kasa yarda da komai na dauka da wasa ne amma al'amarin yafi gaban tunani na kullum da kalar mafarkin da zanyi kuma dai duka daya ne ki bani shawara ina neman mai bani agaji a tare dani".
"To aini Amatu ban fahimce kiba magana kike min a hagunce kinga ki samu nutsuwa daga baya sai kimin bayyani kamar naga ki d'an shiga wani yanayi"? "Eh yanayi na shiga Fati kinsan daren jiya nayi mafarki......... Katse ta Fatima tai harda zaro ido tace "mafarki Allah yasa ba mummuna bane" sun kusa gonar Amatu tace "ke kam 'kawata bakya cin moriyar zance ai bance komai ba tukuna" dariya Fatima tai "eh kuma fa haka ne bari nai shiru kawai ina jinki".
"A'a mun riga da mun karaso ki bari saimun tashi zan fad'a miki" Fatima zatai magana sukaji muryar baba na cewa "mama na a ina kika tsaya ne kin barni a fargaba nayi tunanin ma ko zazzabin ne bai sake kiba" kallon fuskar sa tai sau d'aya ta kawar dakai gefe jin hawaye na shirin zubo mata da'kyar muryata na d'an rawar kuka tace "eh baba nasamu sauki ga abinci umma tace a kawo muku" "to mama na Allah ya miki albarka ke Aishatu kuzo maza ga abinci kubar aikin nan" tasowa sukai suna zuwa inda suke 'karkashin bishiyar mangoron dake cikin gonar suka zauna Amatu na gefe tana kallon su tana kuma goge hawayen dake zuba mata na tausayawa mahaifin ta da 'yan uwanta bata yarda sun ganta ba har suka gama zasu koma bakin aiki ta tashi taya su baba ya dakatar da ita.
"Mama na me zakiyi ne" cikin ladabi ta amsa masa "aikin zan kama muku mu karasa" K
3 386
TYPING 📲 {mon Feb 12/2024 9:05} ¥ÚSRÀH MÚSÃ ÃBÚBĀKÅR 💎💎💎💎🌹💎💎💎💎🥀💎💎💎💎
👑ME KAMAR SARKI👑
WHATSAPP: 234 816 098 3083
yusrahmusa65@gmail.com
(*()*) (*()*) (*()*) (*()*)
A*W*A
ÀÑÑÙRÌ WRÌTÉR'S ÃSSÕÇÌÅTÍÔÑ 💫.
DEDICATED TO👇
👉🌹MR HAUSA EBOOKS📚
📔📕📗📘📙📖📓📒📝📗📙📘📕
CEO FAUNDER OF TASKAR NOVELS 💃💃💃💃💃.
May Allah bless u, may Allah protect u nd ur household from all calamities🤲 may Allah open the door of success 4u may Allah accept ur du'as Amin.
In the name of Allah the most benefits and the most merciful ALLAH (SWT) THE MOST HIGH DOES NOT SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPTS ONLY WHAT IS PURE, whoever you ask, ask Allah whoever you need assistance, seek Allah's assistance WE LOVE OUR NABEEY (ANNABI S A W) NO SUCCESS WITHOUT HIM HE'S THE LIGHT OF EVERY DARKNESS HE'VE NO LIMIT PEACE BE UPON HIM AMIN👏.
💫ANNURI WRITER'S ASSOCIATION💫
Haske 🌃 leka gidan kowa birni da kauye koda makiya ba kallon ka ramin kura sai 'ya'yanta.
I'm here to make u happy💃 educated and🤗 domin nifa i have no girman kai if you are fushi dani to wallahi you are just 'batawa kan k lokaci🙈.
Fallow my WhatsApp channel DUNIYAR NISHA'DI HAUSA NOVELS WhatsApp.com
Please fallow the DUNIYAR NISHA'DI HAUSA NOVELS. on my WhatsApp channel https://whatsApp.com/channel/0029VacB0We0wajwN160HO2y
👆Kuyi join wannan Link din domin shiga Duniyar nishad'i ku d'ebi nishad'i yadda ya kamata 😘🤩🤣.
Wannan page din naka ne dan uwa rabin jiki ha'ki'ka kai na dabam ne ina fata Allah ya dafa maka ya kareka daga sharrin miyagun ma'kiyanka, ina fatan alkairin Allah yakai maka duk inda kake a fadin duniya.
YUSUF KING___SKEEBOY 👑👑🎧🎧🎤🎤🎶🎵🎙️🎹 SHATAN RAPPER REAGAN RB RAP DA KUMA HAUSA HIP HOP YAYAN ZAINAB KALAR CAMERA 📸📸 DA NA'IM🥁🎻 💃💃😘.
🗣️🗣️🗣️Ranar kuce masoya maza kada kuyi sanya muyi rausaya 'yan uwa mu taho da baya baya💃💃 mune muke shagali😘😂 ranar mu tayi haske.
Zarah Musa d'an Adam
Naja'at Musa abubakar
Maman Khaleel
Hajara Abla's Glam
Rabi'at bichi
Chep~melody
Batullah Abdullah
Fatima Musa abubakar
Samirah Ahmad
Aishat Yakubu.
Da sauran wadanda ban fad'a ba kuma ba domin mantuwa ba dukka ina gaida ku tare da fatan alkairi gare ku a duk inda kuke Allah ya zama garkuwar ku Amin.
Dedicated to
MY MOTHER {😘mama😘💕}.i love u with all my body and 💓 heart bani da wanda ya fiki mama na ina tsakanin son ki Allah ya 'kara ja min kwanan ki mama na Allah ya tsare min ke Amin.
🚨🤔 Think before you do 🤨
Always be watchful don't take risk don't try to get lost try to protect your life 🌌 always.
Yusrah Musa abubakar maman Fatima ilham (little Zaran aunty).
YMA JIGAWA DUTSE 🏞️
Da anyi kiran Jigawa har wani tunkaho nakeyi ana maganar Jigawa har wani canza salo nakeyi Jigawa jihar muce abun faharin mu ce an sanmu akan zaman lafiya ba'a sanmu da rigima ba 💞.
🏞️Mai alfaharin jiha tace ko ina nake inda zan zarce a cikin Nigeria 🇳🇬 muke da gada mun taka kan dutse birnin daraja daya batse ga haske 🌃 ga adon dutse 🏞️🏔️.
💞AR-RAHMAN💞
The exceedingly compassionate
💞AR-RAHIM💞
The exceedingly merciful.
1~Allah humma salli wa sallim ala sayyadina Muhammadin sayyidil mursalina📿.
#ASTONISHED
#EMPIRE
#LOVESTICK
#INSIDER
#EMBELLISH.
🌄 MARVEL DREAM🌄
Episode 01 nd 02
Lokaci ne na damuna yanayin gari kullum da hadiri ga koren ciyawa daya mamaye ko'ina iya ganin ka amfani yayi matukar kyau a wannan yankin wanda ya kasance 'karamin 'kauye ne Wanda ya batse da mutane iri daban daban duk inda kasa kallon ka mutane ne burjik a gona suna ayyuka.
Wani farin mutum dake ta faman yanke gero da wata filleliyar wukar sa ne lokaci zuwa lokaci yakan kalli hanya da kuma sauran yara guda uku 'yan mata dake taya shi aikin tare geron ganin abinda yake son gani shiru yasa ya mike
3 386
jera ta zauna tana masifa wanda har makwafta suna jiyo ta.
Wucewa d'akin sa malam habu yai bai kuma furta wata kalma ba suma su Aisha d'akin su suka shiga domin su huta gajiyar su ganin yau Saude batai musu abincin saidawa ba haka Jamila ta shirya tadau abincin saidawa ta fita har lokacin bata daina share hawaye ba Wanda saida ta sake shan matsa a d'aki A'i tana mata gargadin karta sake ta dawo mata da kwashen abinci.
Da sallama Binta ta shiga d'akin malam Habu Wanda yake kwance akan wata gajiyayyiyar 'yar katifa mai yanayi da tabarma ya rufe ido kamar mai bacci jin sallama yasa shi budewa tare da tashi zaune yai shiru kana ganinsa kasan cewa yana cikin matsananciyar damuwa ko ba'a fad'a maka ba aje kwanon hannunta Binta tai tana zama a gefensa tace "malam ga abinci" ganin yai shiru bai amsa mata ba tace "malam dan Allah kayi hakuri ka daina sa damuwa a ranka kada hawan jini ya kama ka arziki da talauci duka na Allah ba wanda aka haife shi da kud'i kowa a duniya ya samu a duniya zai barshi mai rai baya fidda rai da rabo".
Ganin jiya iyau bai tanka ba yasa tadan dafa kafadar shi tana cewa "malam lafiya"? Sauke ajiyar zuciya yai "eh lafiya Binta kada ki damu kalau nake" cikin tausayawa tace "to amma malam dan Allah ka rage yawan tunanin nan idan jari ne zan baka aron dubu goma ka saro koda mangoro ne kana saidawa" kai ya girgiza "Binta matsalar ba'a ni bane na kasa gane meke damu na kamar me rariyar hannu ko me na ta'ba bazai albarka ba sai kace mai bakin iyaye kuma kinsan wani abu Binta wallahi harna rabu da mahaifana babu ranar da zata fito ta fad'i basu ce Allah yamin albarka ba na d'ago ina matashi nayi tashen kud'i da manya manyan kasuwanci amma lokaci guda kud'i ya narke min a ka ba iya nawa ba harda na mutane dole filayen Dana mallaka da gonaki haka na rika d'agawa ina Saida su dan dole ina biyan mutane kudaden su tun daga wannan lokaci rayuwa ta juya min baya ban kuma samun kwanciyar hankali ba harwa yau Binta" ya karasa maganar yana dafe kanshi dake sara masa.
Goge hawayen fuskarta Binta tai tana cewa "kayi hakuri malam hakan ma jarrabawa ce kayi kokarin ciyewa sai Allah ya maida maka mafi alkairin sa" kai ya jinjina "na gode Binta hakan yasa naji dama dama ki kaimin ruwa bayi zan fito wanka yanzu" mikewa tai tana cewa "to malam kaci abincin kafin nan bari na dafa ma ruwan saboda naji kamar garin da dan sanyi sanyi" ta fad'a tana bud'e labule ta fita ganin Amatu tai zaune a kofar d'akinsu ta zuba tagumi naban tausayin tana kallon guri daya har zatai mata magana kuma saita fasa ta wuce aikin ta tana tausayawa ahlin gidan nan.
MRS AL'AMEEN AHMAD CE😘
Yusrah Musa Abubakar maman Fatima ilham )(little Zaran aunty)(
To reader's anan zan tsaya insha Allahu sai wanda yake damu ya bamu aron rai zuwa gobe idan naga comment naku shine zai tabbatar min da kuna bina ko a'a sai mu d'ora fata na a koda yaushe ku kasance cikin farin ciki.
Sannan ina son saidawa masoyana cewa Yusrah Musa Abubakar ta kowa ce ga mai bukatar magana dani👇
+234-816-098-3083
Chat with me, be with me at always my lovers, we will me again till we meet.
3 386
miki ban sani ba damuwar kice kina da ruwa ko baki dashi bai shafe ni wannan ba matsala ta bace taki ce" cikin 'bacin rai Saude ta shako hijab din A'i nan suka fara dambe wanda ya riga ya zame musu jiki idan da sabo sun saba da sauri wata mace ta fito daga wani wuri dake fitar da hayaki tana cewa "haba ku kuwa dan Allah kullum kuna cikin fad'a ko karnuka basa abinda kuke gashi abin takaicin babu ruwan ku da wai yaranku suna gurin suna kallonku kada ku zama haka wata rana zakuji kunya" ganin ko sauraron ta basayi yasa ta shigq tsakanin su tana raba su amma ina Saude ta gama tukuikuye hijab din A'i tana cewa "babu ruwan ki Binta ki kyale ni naci uwarta" a hasale A'i tace "kici uwar ki dai dan wallahi baki isa ki zage ni na kyale kiba saina zubar miki da wadannan rubabbun hakoran" a fusace Saude ta kuma shako A'i sai saukar duka kakeji tim tim suna dambe wanda gabadaya sun gama luguiguice Binta wacce take kokarin raba su amma ta kasa tsawa suka ji ta bayansu.
"Kaiiiii kaiii meye hakan"!!!!? Basu saki juna ba kowa na huci suka juya suna kallonshi rai bace ya karaso yana cewa "wannan wanne irin shashanci ne wai filin ya'ki kuka maida min gida da kullum sai kunyi fad'a kamar karnuka to wallahi bazai yiwu ba tun wuri ku gyara halayen ku kafin na dau mataki har yanzu bakusan waye malam Habu ba inaga saina tuna muku watakila kun manta bana son hauka da d'anyen kai".
Sakin A'i Saude tai tana huci tace "wai malam dan kawai nace............katse ta malam Habu yai "na tambaye kine meye abinda ya faru tsakanin ku na gaji da halin ku bana son jin komai yanzu kam ya isa haka ni ba shashashan mai gida bane dole ku canza nafi karfin gidana kusa tunanin ku guri daya".
Gud'a da shewa A'i ta rafka kamar zata cire hanci tana cewa "ayyuririiiii ayyuri yuriiiiii kai jama'a ikon Allah sai kallo wato kai a hakan daukar ka kake kafi karfin gidanka ko malam Habu mai carbi? To wallahi bari kaji tin wuri garama ka daina fad'a domin idan yan kauyen nan sukaji zasuyi maka dariya a baki ne kafi karfin gidanka wajen zakwad'i da zance amma ai ba wata tsiyar kake bamu ba zama 'kalli 'kalular da saidai mu ciyar da kanmu sisi kana bamu ne saidai ka zuro ido kana nema a gurin anji jiki wallahi anyi asara" ta karasa maganar tana shigewa daki tacigaba da masifa iri iri yayin da tabar malam Habu tsaye guri daya kamar an dasa shi dan bakin cikin maganganun data fad'a masa.
Kuka Amatu ta fashe dashi tana shigewa d'aki a duniya ta tsani jin ana cin mutuncin mahaifin ta zata dau Kowacce irin magana amma banda wannan A'i daga cikin d'aki tace "Jamila kizo ki fita da abincin nan kada muyi kwashe dama kune zanbi na taho dake wannan tsinanniyar ta tare ni akan na jefa guga a rijiya" sak Jamila tai cikin kunyar maganganun da A'i keyi tana kallon su Aisha da Asma'u a hankali tace "Aisha dan Allah kuyi hakuri" murmushin dole Aisha tai tana cewa "karki damu babu komai" dundu mai zafi Jamila taji a bayan ta a firgice ta juya A'i ta gani tana huci kafin ta bud'e baki tai magana ta rufe ta da duka tana cewa "suyi hakurin uban ki shegiya wacce kare ya lashewa kurwa nidai ba gado na kikayo ba mitsiyaciya" da gudu Binta ta fito jin dukan bana karewa bane tazo tana janye A'i dake d'irkar Jamila kamar ta samu jaka tace "haba A'i dan Allah yanzu wannan dukan da kike mata bakya tsoro ki tara mata jini a ciki me tai miki baki barta da yunwa da gajiyar aiki ba kinzo kina sake dora mata wani ciwon" hura hanci A'i keyi tana hararar Jamila dake kuka kamar ranta zai fita tace "wallahi kadan kika gani indai juninki a saranci zakici na jaki a guri na sarai kinsan hali na" ta karasa maganar tana kai mata wani dukan da sauri Binta ta tare cikin takaici tace "wai dan Allah A'i meye hakan"? Hannu A'i ta d'aga "kinga Binta ba ruwan ki ina ce 'yata ce koma me nai mata ki 'kyale ni" shiru Binta tai tana kallon A'i cikin mamaki kafin tace "Allah ya huci Zuciyar ki" d'ago Jamila tai tana cewa "kinga Jamila daina kuka maza dauki baho akwai ruwa a randa ta jeki diba kiyi wanka kinji" kai Jamila ta d'aga tana goge hawayen fuskarta kafin ta wuce Binta ma barin gurin tai yayin da A'i taja ku
3 386
shikenan baba sai kun taho" "yauwa mama na Allah ya albarkaci rayuwar ki" cikin jin dad'in addu'arsa a duk sanda yai mata tace "amin baba nagode" juyawa tai tana nufar Fatima wacce ke tsaye tana jiranta kafin suka fita daga gonar suna gangarawa kan hanya suka fara tafiya.
Cikin naci Fatima tace "ke Amatu nifa na 'kosa baki fad'a min mafarkin me kikai ba" kallon ta Amatu tai "ai nace zan fad'a miki" "to ina jinki".
Saida Amatu ta kuma sauke numfashi kafin a hankali ta soma magana "Fatima mafarki nai wai gani a wani irin guri mai shuke shuke da kyan gani abin kwatance gurine daya wadatu da furanni kala kala ina sanye da alkyabba fara tarr nasha lalle kafa ta takalmi ne mai kyau da tsada wuya na da sar'ka ta gwal fuska ta da kwalliya a gefe da gefe na akwai bayi a baya na akwai bayi sun tsaya tun kafin na shigo gurin shi kuma tsaye yake a gaban wani guri wanda ruwa yake 'bubbuga an zagaye gurin da fulawoyi masu kyan launi a hankali na isa gareshi ta bayansa batare daya sani ba na taka wani dutse ina son nakai daidai tsayinsa daga bayansa nasa hannuna na rufe masa idanu wanda inajin sautin murmushin daya sakar min kafin ya rike hannuwa na yana bude idanuwansa ya juyo gare ni yana d'aga ni sama daga kan dutsen bai ajiye ni ko'ina ba sai a wani gurin shimfidadden carpet mai taushi wanda ya 'kawatu da kayan 'kawa na ado da abubuwan sha iri daban wanda ban ta'ba gani ba zama mukai yana rungume dani da muryar sa mai za'ki yace 'ina tsakanin sonki mata na banda kamar ki ina fata mu kasance tare' murmushi nai wanda yaja hankalin sa har ya shafo beauty points dinta daya lotsa sakamakon murmushin da nai bude baki nai zanyi magana ya sunkuyo yana d'ora bakinsa akan nawa kawai daga haka naji umma tana tashi na ban cigaba ba har bacci na koma bayan sallar asuba ko zan dora daga inda na tsaya amma a banza banyi mafarkin komai ba kinji abinda yasani farin ciki kuma ni kaina bansan dalili ba".
Sauke ajiyar zuciya Fatima tai kafin ta fara dariya tana cewa "gaskiya ne "kawata kenan mafarkin yarima d'an sarki kikai kuna tare kin zama matar sa"? Kai Amatu ta d'aga tana cewa "eh" cigaba Fatima tai "kai ai mafarki yana da abin mamaki sai kikaji dama gaske ne amma bamu sani ba ko zai zama gasken nan gaba" kai Amatu ta girgiza "taya zai zama gaskiya Fatima wannan gurin har na 'kare rayuwa ta bazan ta'ba ganin saba" cikin tsokana Fatima tace "to kika sani ko Sa'adu d'an gidan mai gari zaki aura" hade rai Amatu tai "kinga ki daina hada ni dashi kin manta kwanan baya uwarsa har gida taje ta tsiyata umma ai ko d'an gwal ne Sa'adu bazan aure Shiba" dariya Fatima tai tana cewa "nima da wasa nake Sa'adu da ba ganin girman manya yake ba kuma ba abun kunya bane ya ci mutuncin ki ubansa ya sani amma ya dauke kai da d'an wani ne da kinji bakinsa na shela 'kauyukan kusa damu ma sai sunji labari" tabe baki Amatu tai tana cewa "yabi dai a hankali duniya ta ishi kowa riga da wando wanda bai zota bama jiran sa take balle wanda yake cikin ta".
Tare suka shiga gidan daya kasance da mata uku Kowacce da aikin da take matar dake bakin rijiya tana jan ruwa ne ta juyo tana cewa "Ke Amatu ya na ganki ke kadai ina sauran a ina kika baro su Jamilan ga tallar abinci na jiran su"? Aje kwanon hannunta Amatu tai tana d'an kallon wacce tai mata maganar kafin tace "suna can basu gama aikin ba" sakin gugan A'i tai tana rike kugu tace "kuturun ubancan lallai malam da wargi yake wato ke da yake mai ido da kwalli ce kina kai abinci kika dawo amma tawa 'yar da yake bata da gata tana can rana na gasa mata baya wallahi bazai yiwu ba bari na dauko hijab na na bisu gonar na taho da 'yata da kaina" d'aki ta nufa tana bala'i "wannan muguntar har ina 'ya'ya mata ba maza ba a dauke ku aikin garada cikin rana ba wani amfanin arziki za'a samu ba dandani haukaci kafin shekara ya kare sai dai aune za a kashe min 'ya da aiki to wallahi bazata sa'bo ba".
Ganin ta saki gugar ta fad'a ga babu mai ruwa a gidan yasa Saude data fito daga d'aki tace "haba A'i amma dai baki adalci ba bafa mune mukai miki laifi kika saki guga ta fad'a yanzu dame zamu debi ruwan"? Cikin masifa A'i tace "oho
