cookie

Sizning foydalanuvchi tajribangizni yaxshilash uchun cookie-lardan foydalanamiz. Barchasini qabul qiling», bosing, cookie-lardan foydalanilishiga rozilik bildirishingiz talab qilinadi.

avatar

مكتبة بحر الأطلس نيجيريا

WANNAN CHANNEL DIN YAKUMSHI DUK WASU ABUBUWAN SHEIKH ABDUL JABBAR KABARA/ DUK MEBUKATA YA DANNA LIKE DINMU TA TELEGRAM

Ko'proq ko'rsatish
Mamlakat belgilanmaganTil belgilanmaganDin & Maʼnaviyat71 359
Reklama postlari
999
Obunachilar
Ma'lumot yo'q24 soatlar
Ma'lumot yo'q7 kunlar
Ma'lumot yo'q30 kunlar

Ma'lumot yuklanmoqda...

Obunachilar o'sish tezligi

Ma'lumot yuklanmoqda...

Follow the مكتبة بحر الأطلس نيجيريا channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Va5kyfOA2pLJPhVNfk11
Hammasini ko'rsatish...

Document from Ashiru Abdullahi
Hammasini ko'rsatish...
SHARAR FAGE AKAN TAUHIDI FROM HUKUMULLAHI.mp37.70 MB
Photo unavailableShow in Telegram
Sako Daga Sheikh Abduljabbar Kabara! "Kusan kalmomin da za kuyi amfani dasu wajen nuna farin-ciki da godiyar ku ga Allah bisa nasarorin da yake baku ko zai baku anan gaba. "Ku kiyayi habaici ko izgili ga kowa ya-yin nuna farin-ciki kada Allah yayi fushi daku ya barku da kawunan ku.
Hammasini ko'rsatish...
Tabbas ta tabbata cewa a lokacin da Sarkin Yakin Shehu Dan Fodio yake raye, Wato Sheikh Muhammad Nasiru Kabara babu wani mahaluki da yakai shi sanin tsantsar Larabci a duk fadin Afrika. Domin tabbatar da hakan, dubi Wannan kasida da shehin Malamin yayi ba tare da amfani da wani harafi mai digo ba. Misali Babu ج خ غ ف ق ث ض ظ ن ت ب ي ش ز ظ ة ذ Ga baitukan nan a kasa: 👇👇👇 أعلى سلام لأعلى الرسل إعلاما وأكرم الرسل أحلاما وإسلاما. Mafi daukakan Aminci ya tabbata abisa mafi daukakan manzanni wajen shiryar da bayi , kuma mafi darajar manzanni wajen nauyin hankali da miqa wuya ga Allah. محمد أحمد المحمود حامده المملأ الروح أسرارا و أحكاما. Abin yabo ,mafi yabo, sha yabo kuma mai yabo, Abin cikawa ruhi da sirruka da hukunce-hukunce. أحدو مدائحه عسى أحوط لها لدى إله الورى المعطاء إكراما. Ina koro yabonsa yalla ko na sami kyauta daga wajen ubangijin Al'arshi don girmamawa. ما أرسل الله أعلى سرمدا أحدا كأحمد العلم المعلوم إعلاما. Allah bai aika wani mutum guda tamkar Ahmadu (s.a.w) ba,wannan da shine Tsauni (tsakanin tsikwankwani) kuma sananne wajen sanarwa أولى لكل علا أدلى لكل ملا أحمى كلاما و أولى الدهم إكلاما. Mafi cancanta da duk wata daukaka mafi kusa ga duk wasu mutanen , mafi katanguwa wajen zance kuma mafificin daukacin mutane wajen iya furta kirari ga Allah. طه الطهور الرد المحاص كل ردى أحاط سورا على الإسلام أهراما. Daha tsarkakakke daga duk wani Aibu mai halakarwa kuma mai shafe duk wata halaka,ya gewayar wasu rayuka na Sharifai da waliyyai abisa musulunci a matsayin katangu. مدح المكرم حمد والكرام لهم لئالئ المدح إملاءا و إحكاما. Yabon abin girmamawa godiya ne ga Allah, su kuwa manya suna da gwalagwalan yabo a haqqinsa (s.a.w) don roqo da Neman cikawa da kyautata kammalawa daga Allah. عسى أحل على الأمداح أوسطها أطاول المادح السحار أحلاما. Ina ma dai kuma na kusanta abisa jirgin yabo in sauka tsakiyarta , in Shallake mai bege a garjin dare wajen mafarki أطول مادحه ما سال سائلهم مه مه و مهمه هاء طاول اللاما. In shalkake mai yabonsa a duk sanda matambayinsu yayi tambaya, duk inda ma ta kaya HA'UN CE ta Shallake LAMU . وهو المحال له لسعد طالعه وطول طائله والحاسم الهاما. حام حماه رعاه الله أكمله وصل الملاح ولاح الراح إلهاما.
Hammasini ko'rsatish...
abu tanima ,to da wane dalilin bukhari zerusa hadisi dan mursali ne bayan ga mursalin a sahihin sa ina salafawa, 23 bukhari be taba ruwaya gun ibrahim ibn dahaman ba, sanda yarasu ko kusan haifar bukari ba'aiba Duk sadda bukhari ze rawaici hadisin ibn dahaman za'aga akwai rawi 2 a tsakanin su ,misali bukhari hadisi na 892, 1117, 1185, dik in anduba za'aga akwai ratar mutum 2 tsakanin ibn dahaman da bukhari , amma ahaka bukhari yace ibn dahaman yabiya mai hadisi, aduba hadisi na 421, 1107, 1613, diz za'agani bukhari yana cewa yaji gun ibn dahaman , ina salafawa , 24 bukhari 4369 Ismail bin abi uwais , dan uwansa, saidil makburi , abuhuraira, hadisin abinda yafaru tsakanin Annabi Ibrahim da Allah , da babansa ranar alkiyama , asharadin bukhari bayasa hadisin isma,il bin uwais a littafinsa seyanada mutabaa , to akwai wata hanyar hadisin a sunanu kubura ta nasa,i 11375, ga isnadin , ahmadu , hafsu bin abdullah , babansa , Ibrahim bin dahaman, Muhammad bin abdurrahaman , saidil makburi , abuhuraira, nasa,i yakora hadisin Annabi Ibrahim na alkiyama, inka duba bukhari 3350 zakaga lafazin iri dayane dana bukhari, to da wannan isnadin na nasa,i ibn hajar yace bukhari yayi mutabaa yasa hadisin isma,il bin abi uwais a sahihinsa , to inda matsalar take a isnadin nasai akwai Muhammad bin andurrahaman bin abi laila , anyi ittifaki daifi ne , kuma shikadai yarawaito hadisin , se bukhari yacireshi yasa abdurrahaman bin abiziibin shikuma amuntaccene ,to da wannan magudin bukhari yashigar da hadisai 2 cikin littafinsa , 4369, 3350, ina salafawa , Jauful Farah 132,133 #makonsheikhabduljabbarkabara Kahfi world media
Hammasini ko'rsatish...
KALU BALE DARI DA Dr ABDULJABBAR YAYWA MALAMAN MAJA 3 Yau zamu kutsa da salafawa cikin ilimin musdalahul hadis , Allah yasa sugane karatun , balantana su iya amsa kalu balan da akai musu , akwai wani hadisi na abuhuraira da Dr Abduljabbar yay sati shida yana karatu akan sa , in har hadisin ya tabbata abuhuraira yafada to dukkan hadisan daya rawaito sun samu matsala dan baza'a karbesu ba , in kuma hadisin yarushe to abuhuraira ya tsira ,manyan malaman hadisi sunaso ta karfi sesun rusa hadisin , albarkar bahasi yau da gobe Dr Abduljabbar yagano hadisin nan fa ya inganta abuhuraira yafada ,ga lafazin hadisin Abuhuraira yace Annabi yace magana indai mekyau ce , kuyi aiki da ita ko ban fadaba na fada , Mahallin rigimar ( ko ban fadaba na fada) 17 Abuhuraira yakirkiri wannan hadisin dan yasamu damar kirkirar hadisai, malamai sun hadu akan maudu'i ne hadisin , malam yatabbatar sahihine a sharadin bukhari da Muslim , tabbas Abuhuraira yafada, yakamata salafawa kuzo ku kwaci malaman ahlussunna , 18 jauzajani yace yahaya bin ma,in yace zindikaine suka kirkiri hadisin , albani alittafin sa da'ifa , shima ya maimaita abinda jauzajani yace yahaya binma'in yace , amma in an koma , al maudu,at na jauzajani za'aga da isnadi yakawo maganar , shikuma albani se yadatse isnadin ,saboda albani yabi isnadin yagane jauzajani kagawa yahaya maganar yayi, isnadin kagaggene , kuma duk dawaninu na yahaya , guda 5 babu maganar aciki , kuma duk maganar da yahaya yayi za'a sameta anan, dan haka salafawa kuzo ku kwaci albani , da jauzajani munka masu da karya dumudumu, 19 albani yace da bukhari da abuhatimin razi , sun fadi illar hadisin , isnadin bukhari , ibrahim ibn dahaman ,ibn abi ziibin , sa'idul makburi, Annabi s a w , wannan isnadin babu abuhuraira , bukhari yace amma yahaya bin Adam isnadin sa shine, yahaya bin adam , abusa,idil makaburi , Abuharaira , Annabi s a w , se bukhari yace yahaya kuskure yayi babu abuhuraira a hadisin , dan haka a gun bukhari hadisi mursaline yarushe tunda babu sahabi a isnadin, albani yace shikuma ibn abi hatim ,yarawaito daga babansa abi hatim , bassamu bin Khalid, shuaibu bin isihak , ibn abi ziibin, sa,idil makburi, babansa , Abuhuraira, abuhatimin yakora hadisi , akarshe yace sikatu basa dan gana wannan hadisin zuwa kan Annabi s a w , jama'a bukhari yasa Annabi a hadisin yacire abuhuraira, abuhatimin ya cire sunan Annabi yasa na abuhuraira, abuhatimin ya yadda abuhuraira yafadi hadisin amma be yadda Annabi ne yafada mai ba ,bukhari ne yake ta kokarin cire sunan abuhuraira saboda kada akamashi dayiwa Annabi karya ,malam yace dud duniya babu wanda ya isa yahada lafazin bukhari da na abuhatimin razi, kuma albani karya yake dayace abuhatimin yasoki hadisin ,abuhatim tabbatar wa yayi abuhuraira yafada , kuma karya yayiwa Annabi s a w , dan haka salafawa munajiran amsa, 20 lafazin da bukhari yakawo takan ibrahim ibn dahaman shi kadai yaka daita dashi , yadatse lafazin (Annabi yace ko nafada ko ban fada ba )kuma shine mahallin rigimar,sannan ya datse sunan Abuhuraira, duk dan yarusa hadisin , kuma shikadai yayi haka a marawaita , ina salafawa suke kuzo ku kwaci bukhari, yayi ha,inci , 21 Albani yace dalilin daya sa hadisin ibrahaim ibn dahaman yafi na yahaya bin Adam inganaci , saboda dan dazon amuntattu dasuka rawaici lafazin ibn dahaman, nan albani yana goyan bayan bukhari ne akan lallai se ance babu abuhuraira a hadisin , malam yace ko mutum daya be rawaici lafazin ibn dahaman ba , ina salafawa , 22 bukhari yarusa hadisin ibn dahaman saboda mursaline ,maana tabi'i daga Annabi s a w babu sahabi shi ake nufi da mursalin hadisi , malam yace mursalin hadisi ba matsala bane agun bukhari saboda akwai a sahihul bukhari, wani lokacin ma yana fifita mursali akan muttasili, muttasili , shine hadisin da sahabi yaji daga Annabi s a w , to bukhari yana fifita mursali akan muttasili wani lokacin, misali hadisi na 5275 a bukhari ikirima yace yaji hadisi daga gun Annabi s a w , ikirima tabi'i ne bega Annabi s a w ba , kuma shima bukhari malamin dayace yabiya mai hadisin , bukhari beyi zamani dashi ba , sunan sa
Hammasini ko'rsatish...
KLUBALE ƊARI GDA DR. ABDULJABBAR YA YI WA MALAMAN MAJA. 7-Sheikh Dr. Abduljabbar ya ƙalubalanci malaman maja a kan cewa Anas Bin Malik bai taɓa yi wa Annabi SAWA) Hidima ba, kuma in sun isa su kawo masa hidimarsa guda ɗaya daga bakin wani sahabi da ya ce ga shi ga Anas Bin Malik ga Annabi, Anas Bin yana yi wa Annabi (SAWA) Hidima, ko kuma an yi wani abu da Anas Bin Malik shi Sahabin yana wurin, ya zama dai Hidimar Anas Bin Malik ta samu shaida daga bakin wani Sahabi, malam ya saɓa misalai da hidimar wasu daga sahabbai, a bakin Sahabbai ƴan'uwansu. Amma har yau tsit Jauful Farah-112. 8-Sheikh Dr. Abduljabbar ya ƙalubanci malaman Maja a kan cewa duk hadisan da "Anas Bin Malik" ya zantar da su, wanda suka taɓa mutuncin Annabi (SAWA), ya faɗesu ne a lokacin da manyan Sahabbai duk sun ƙare, ya rage daga shi sai ƙananun Sahabbai da tabi'ai, wato lokacin ƙarshen ɗabakar uku da ɗabaƙar huɗu, har da ɗabakar biyar ma, wanda har yanzun nan salafawa ba su iya kawo Hadisi guda ɗaya da Anas Bin Malik ya zantar mara kyau a lokacin manyan Sahabbai irin su imamu Ali (A.S) da Sayyadina Abubakar ba, har yau tsit. Jauful farah 92-93 9-Sheikh Abduljabbar ya ƙalubalanci salafawa a kan cewa Annabi (SAWA) bai san Anas Bin Malik ba, in kuma ya sanshi a kawo masa ta yadda aka yi ya sanshi, ko kuma inda Annabi (SAWA) ya ambaci sunan Anas Bin Malik ma. har yau tsit Jauful fara -111 10- Sheikh Dr. Abduljabbar ya ƙalubalanci Malaman Maja a kan faɗin Anas Bin Malik cewa, wai lokacin da Annabi (SAWA) ya dawo daga Khaibar ya tsaya a wani guri mai suna "Saddal Rauha,i", Sheikh Abduljabbar yace a Duniya ma gaba ɗaya babu wani wuri mai Suna "Saddal Rauha'i", kuma har yanzu tsit. Jauful Fara91 11- Sheikh Dr. Abduljabbar ya ƙalubalanci malaman Maja a kan cewa, duk hadisan da suka taɓa Mutuncin Annabi (SAWA) a yaƙin khaibar Anas Bin Malik ne ya ruwaitosu shi kaɗai. Misali: Anas ya ce, wai Annabi (SAWA), ya yi sukuwa a Doki har zani/kwarjallensa ya kwaye, Anas ya ce ya ga cinyar Annabi fara tas (Wal'iyazubillahi), kuma wai Annabi ya ba wa wani daga cikin sahabban sa wata kuyanga mai Suna Safiyya, daga baya aka faɗa wa Annabi cewa Kuyangar nan fa kyakykyawa ce, kawai sai ya ce ya fasa bayarwa, kuma wai Annabi ya tsaya a hanyar dawowa, ya tsayar da ayarin Sahabbai ya angwance da safiya har na tsawon kwanaki Uku. Sheikh Abduljabbar ya ce Anas Bin Malik shi kaɗai ya ruwaici wannan hadisin, in kuma akwai wani Sahabi ko da guda ɗaya ne da shi ma ya ruwaici wannan Hadisi a kawo masa sunan wannan Sahabi. Har yau tsit. Jauful Fara 87 12- Sheikh Dr. Abduljabbar ya ƙalubalanci Malaman maja a kan Mas,alar Isra'i da Mi'iraji, ya ce tabbas Ƙur'ani ya bamu labarin an yi Isra,i wato daga masallacin Annabi (SAWA) zuwa Masallacin Ƙudus, tabbas wannan gaskiya ne, kuma Annabi (SAWA) ya je ya yi gáni da Allah (SWA) har ALƘUR'ANI ya ba mu labari, amma batun wai an tafi da Annabi (SAWA) Sama, an je sama ta ɗaya, an ce waye? Ya ce jibrilu ne da Annabi, aka ce an aika masa ya zo ne? Suka Amsa da "an aika", sannan wai aka buɗe, haka har aka je sama ta Bakwai, wai Annabi (SAWA) ya haɗu da Annabawa da Mala'iku, malam ya ce wannan duk ba a yi ba, saboda karo da tufka da warwarar da take cikin Hadisan, in kuma akwai wanda zai iya haɗe karon da hadisan suka yi ya zo ya gwada haɗesu. Har yau tsit. Jauful Fara. 57-58 13- Sheikh Dr. Abduljabbar ya ƙalubalanci Malaman maja a kan cewa Anas Bin Malik shi kaɗai ne ya ruwaito cewa Mala'ika jibrilu da Annabi (SAWA) sun tafi sama, ma'ana miiraji, Malam yace babu Sahabi ko ɗaya da ya san da maganar Mi'iraji, in kuma akwai shi a kawo. Har yau tsit. 109 14- A cikin Sahihul Bukhari Hadisi mai Lamba 5610, za a ga isnadi kamar haka "Ibn Ɗahaman, Shu'uba, Ƙatada, Anas, daga Annabi (SAW)", a nan Bukhari ya kuma canjawa, ya kawo wani Isnadin kamar haka "Hisham, Anas Bn malik, sai Malik bin sa'a sa'a.
Hammasini ko'rsatish...
Sheikh Abduljabbar ya ce wannan hadisi ne maudhu'i, ya ce babu wani Sahabi wai Malik bin sa'a sa'a, ba a taɓa yinsa ba, kuma a wurinshi aka ciri Maganar Mi'iraji, sannan duk inda aka ga Isnadi wai Anas daga "Malik Bin sa'a sa'a", za a ga Anas Bin Malik ya ruwaitar da Hadisin ne a ɗabaƙar uku, a lokacin akwai sauran Sahabbai, amma kana komawa ɗabaƙar 4 zuwa 5, za ku ga kawai Anas Bin Malik yana cewa Annabi (SAWA) ya faɗa masa, kuma duk Duniya Anas Bin Malik ne kaɗai ya san "Malik Bin sa'a sa'a". Har yau tsit, babu wanda ya taɓa kawo wani Sahabi da ya san Malik Bin sa'a sa'a. 15- Sheikh Abduljabbar ya ƙalubalanci Maja a kan hadisin da Anas Bin Malik ya ruwaito, cewa wai Annabi (SAWA) zuwa yake kofar gari ya tsaya, in bai ji kiran Sallah ba kawai sai ya afka wa mutanen garin da yaƙi, a Hadeethin ne Anas yake ba da labarin cewa wai an je wani gari aka tsaya, kawai sai aka ji wani mutum yana kiran Sallah, sai aka fasa yaƙin aka dawo gida, Dr. Abduljabbar ya ce wannan karya ne, babu dole a Addini, in ji Allah, babu wani yaƙi da Annabi (SAWA) ya je don ya ji kiran Sallah wai aka fasa yaƙin, babu shi a duk yaƙe-yaƙen da Annabi ya yi, in kuma akwai Yaƙin a kawo. Har yau tsit. Jauful farah 90. 16- Sheikh Abduljabbar ya ƙalubalanci Majar Duniya a kan cewa Anas Bin Malik shi kaɗai ne ya ruwaito cewa Annabi SAWA yana kwanciya da matansa su 11, a wata ruwayar su 9 wai a cikin Sa'a ɗaya da Rana da Dare ma haka yake yi, wai da wanka ɗaya, kullin ta Allah haka yake yi Sheikh Dr. Abduljabbar ya ce duk Sahabbai Anas Bin Malik ne ne kaɗai ya san da wannan hadisin, in da akwai Sahabi ɗaya tal da ya sani a kawo shi. Har yau tsit. Rayuwa Bayan Mutuwa 21. KAHFI WORLD MEDIA #makonsheikhabduljabbarkabara
Hammasini ko'rsatish...
Boshqa reja tanlang

Joriy rejangiz faqat 5 ta kanal uchun analitika imkoniyatini beradi. Ko'proq olish uchun, iltimos, boshqa reja tanlang.