ch
Feedback
TASKAR NOVELS

TASKAR NOVELS

前往频道在 Telegram

Download all kind of hausa novels,musics videos and movies

显示更多
3 386
订阅者
无数据24 小时
-67 天
+2030 天
帖子存档
baro Mamana ne har yanzu me take a gida bata zo ba gashi munci 'karfin aiki ko yau ma zazzabin ne"?. Ya tambaya yana zama cikin gajiya sosai kallo d'aya zakai masa kasan cewa talauci ya gama samun gurin zama a jikin sa d'agowa wacce ya kira da Aisha tai itama ta jike shakaf da gumi cikin alamun gajiya da yunwa tace "wallahi baba ban sani ba har muka taho nidai ban ganta ba amma bana ce ba ko Asma'u ta ganta kai Asma'u ta girgiza tana cewa "a'a nima bamu hadu ba". Kai baba ya jinjina yana cewa "to ikon Allah, Allah yasa dai lafiya mama na bata zo ba na damu akan zazzabin nan nata mara jin magani gashi duk d'an kudin hannu na ya 'kare, baka dashi a d'aka baka dashi a waje masu kudi sunai ma kallon ka 'ki tashi ne ka nema kai jama'a Allah rufa mana asiri dai" ya fad'a cikin damuwa sosai tare da mikewa yana daukar wukar ya koma bakin aikin sa da kallo 'ya'yan nasa suka bishi cikin tausayawa domin sun san waye uban su matukar yana dashi baya hana iyalinsa yana wadata su da komai amma babu tai masa katutu. Tafe wata zu'ke'kiyar kyakkyawar zazzafar budurwa 'yar kimanin shekara ashirin da biyu take dauke da fanteka a kanta bata kallon kowa bata kallon komai sai hanyar da take bi wacce ciyawa tai kwance lif akai daga bayanta taji ana 'kwala mata kira da karfi "AMATULLAH ke AMATU ki tsaya". Dakatawa tai batare data juya ba har wacce ke kiran ta karaso tana d'an haki tace "haba Amatu kamar wacce kika fara kurmancewa ina ta kiran ki sai yanzu kika jini" fuskarta dauke da wani kyakkyawan siritaccen murmushi tadan juya manyan fararen idanuwanta kafin da murya mai dad'in sauraro tace "haba Fatima kinsan na jiki bazan 'kyale kiba" sauke ajiyar zuciya Fatima tai tana cewa "amma na tambaye ki wani abu"? Ta fad'a tana mamakin yadda taga yau fuskar Amatu da murmushi mai kyan kwatance tacigaba "wannan murmushin ya nuna akwai wani abu daya faranta miki ranki idan na canka daidai"?. 'yar dariya Amatu tai tana cewa "kinga sauri nake zanje gurin su baba ki bari idan na dawo zan fad'a miki" kai Fatima ta d'aga tana cewa "ai dama na taho ne dan na raka ki" "to shikenan muje. Wucewa sukai Fatima da mamaki ya gama cika ta da annurin da take gani a fuskar 'kawar ta ta yasa ta kasa hakuri tace "Amatu nifa na kasa fahimta dan Allah ki fad'a min miyasaki farin ciki haka"?. Sauke ajiyar zuciya Amatu tai tana cewa "kinsan abinda ya bani mamaki? wani irin mafarki nai wanda na kasa fassara shi to me ma zan kirashi? Ki fad'a min Fatima na kasa yarda da komai na dauka da wasa ne amma al'amarin yafi gaban tunani na kullum da kalar mafarkin da zanyi kuma dai duka daya ne ki bani shawara ina neman mai bani agaji a tare dani". "To aini Amatu ban fahimce kiba magana kike min a hagunce kinga ki samu nutsuwa daga baya sai kimin bayyani kamar naga ki d'an shiga wani yanayi"? "Eh yanayi na shiga Fati kinsan daren jiya nayi mafarki......... Katse ta Fatima tai harda zaro ido tace "mafarki Allah yasa ba mummuna bane" sun kusa gonar Amatu tace "ke kam 'kawata bakya cin moriyar zance ai bance komai ba tukuna" dariya Fatima tai "eh kuma fa haka ne bari nai shiru kawai ina jinki". "A'a mun riga da mun karaso ki bari saimun tashi zan fad'a miki" Fatima zatai magana sukaji muryar baba na cewa "mama na a ina kika tsaya ne kin barni a fargaba nayi tunanin ma ko zazzabin ne bai sake kiba" kallon fuskar sa tai sau d'aya ta kawar dakai gefe jin hawaye na shirin zubo mata da'kyar muryata na d'an rawar kuka tace "eh baba nasamu sauki ga abinci umma tace a kawo muku" "to mama na Allah ya miki albarka ke Aishatu kuzo maza ga abinci kubar aikin nan" tasowa sukai suna zuwa inda suke 'karkashin bishiyar mangoron dake cikin gonar suka zauna Amatu na gefe tana kallon su tana kuma goge hawayen dake zuba mata na tausayawa mahaifin ta da 'yan uwanta bata yarda sun ganta ba har suka gama zasu koma bakin aiki ta tashi taya su baba ya dakatar da ita. "Mama na me zakiyi ne" cikin ladabi ta amsa masa "aikin zan kama muku mu karasa" Kai ya girgiza mata "a'a mama na jeki gida baki da lafiya Allah ya sauwa'ke karki damu kinji" numfashi ta sau'ke a hankali kafin tace "to

👑ME KAMAR SARKI👑 WHATSAPP: 234 816 098 3083 yusrahmusa65@gmail.com (*()*) (*()*) (*()*) (*()*) A*W*A ÀÑÑÙRÌ WRÌTÉR'S ÃSSÕÇÌÅTÍÔÑ 💫. DEDICATED TO👇 👉🌹MR HAUSA EBOOKS📚 📔📕📗📘📙📖📓📒📝📗📙📘📕 CEO FAUNDER OF TASKAR NOVELS 💃💃💃💃💃. May Allah bless u, may Allah protect u nd ur household from all calamities🤲 may Allah open the door of success 4u may Allah accept ur du'as Amin. In the name of Allah the most benefits and the most merciful ALLAH (SWT) THE MOST HIGH DOES NOT SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPTS ONLY WHAT IS PURE, whoever you ask, ask Allah whoever you need assistance, seek Allah's assistance WE LOVE OUR NABEEY (ANNABI S A W) NO SUCCESS WITHOUT HIM HE'S THE LIGHT OF EVERY DARKNESS HE'VE NO LIMIT PEACE BE UPON HIM AMIN👏. 💫ANNURI WRITER'S ASSOCIATION💫 Haske 🌃 leka gidan kowa birni da kauye koda makiya ba kallon ka ramin kura sai 'ya'yanta. I'm here to make u happy💃 educated and🤗 domin nifa i have no girman kai if you are fushi dani to wallahi you are just 'batawa kan k lokaci🙈. Fallow my WhatsApp channel DUNIYAR NISHA'DI HAUSA NOVELS WhatsApp.com Please fallow the DUNIYAR NISHA'DI HAUSA NOVELS. on my WhatsApp channel https://whatsApp.com/channel/0029VacB0We0wajwN160HO2y 👆Kuyi join wannan Link din domin shiga Duniyar nishad'i ku d'ebi nishad'i yadda ya kamata 😘🤩🤣. Wannan page din naka ne dan uwa rabin jiki ha'ki'ka kai na dabam ne ina fata Allah ya dafa maka ya kareka daga sharrin miyagun ma'kiyanka, ina fatan alkairin Allah yakai maka duk inda kake a fadin duniya. YUSUF KING___SKEEBOY 👑👑🎧🎧🎤🎤🎶🎵🎙️🎹 SHATAN RAPPER REAGAN RB RAP DA KUMA HAUSA HIP HOP YAYAN ZAINAB KALAR CAMERA 📸📸 DA NA'IM🥁🎻 💃💃😘. 🗣️🗣️🗣️Ranar kuce masoya maza kada kuyi sanya muyi rausaya 'yan uwa mu taho da baya baya💃💃 mune muke shagali😘😂 ranar mu tayi haske. Zarah Musa d'an Adam Naja'at Musa abubakar Maman Khaleel Hajara Abla's Glam Rabi'at bichi Chep~melody Batullah Abdullah Fatima Musa abubakar Samirah Ahmad Aishat Yakubu. Da sauran wadanda ban fad'a ba kuma ba domin mantuwa ba dukka ina gaida ku tare da fatan alkairi gare ku a duk inda kuke Allah ya zama garkuwar ku Amin. Dedicated to MY MOTHER {😘mama😘💕}.i love u with all my body and 💓 heart bani da wanda ya fiki mama na ina tsakanin son ki Allah ya 'kara ja min kwanan ki mama na Allah ya tsare min ke Amin. 🚨🤔 Think before you do 🤨 Always be watchful don't take risk don't try to get lost try to protect your life 🌌 always. Yusrah Musa abubakar maman Fatima ilham (little Zaran aunty). YMA JIGAWA DUTSE 🏞️ Da anyi kiran Jigawa har wani tunkaho nakeyi ana maganar Jigawa har wani canza salo nakeyi Jigawa jihar muce abun faharin mu ce an sanmu akan zaman lafiya ba'a sanmu da rigima ba 💞. 🏞️Mai alfaharin jiha tace ko ina nake inda zan zarce a cikin Nigeria 🇳🇬 muke da gada mun taka kan dutse birnin daraja daya batse ga haske 🌃 ga adon dutse 🏞️🏔️. 💞AR-RAHMAN💞 The exceedingly compassionate 💞AR-RAHIM💞 The exceedingly merciful. 1~Allah humma salli wa sallim ala sayyadina Muhammadin sayyidil mursalina📿. #ASTONISHED #EMPIRE #LOVESTICK #INSIDER #EMBELLISH. 🌄 MARVEL DREAM🌄 Episode 01 nd 02 Lokaci ne na damuna yanayin gari kullum da hadiri ga koren ciyawa daya mamaye ko'ina iya ganin ka amfani yayi matukar kyau a wannan yankin wanda ya kasance 'karamin 'kauye ne Wanda ya batse da mutane iri daban daban duk inda kasa kallon ka mutane ne burjik a gona suna ayyuka. Wani farin mutum dake ta faman yanke gero da wata filleliyar wukar sa ne lokaci zuwa lokaci yakan kalli hanya da kuma sauran yara guda uku 'yan mata dake taya shi aikin tare geron ganin abinda yake son gani shiru yasa ya mike tsaye tare da rike bayan shi alamar ciwo yake masa sharce zufan fuskarsa yai yana kallon 'yan matan yace. "Wai ni kam Aishatu ina kuka

Testing channel chat ID retrieval

Good Day

This is a long post that includes multiple paragraphs of text. It might be overwhelming for users to see the entire content at once, so we will use a "Read More" break. Here is the rest of the post that will be hidden after the "Read More" link is applied.

Baba Zubairu Wanda akewa lakabi da Zubairu Rocket da shi taci Karo a zauren,Yana ganinta kamar yaga Mutuwa ya Bata fuska kamar zai mareta,ganin Haka ta zuge jakar makarantar ta wacce take ta buhun Leda ce ta dakko Naira dari a ciki ta Mika Masa tace gashi aci goro Baba,Baki ya washe hakoran Nan Jajir dasu yace yawwa Ilham Yar albarka an dawo? Sannu kinsha Rana,kwana Nan dai zan samu na siyo katuwar mota na dinga kaiku makaranta a ita,Dariya Ilham tayi Sabo da kowa yasan irin karyar Zubairu wacce yake Harbo ta kamar Rocket, dariya tayi tace Baba Rocket Ina gaisuwa Zubabu, Yana washe Baki yace Baki fa da kirki 'yata, tana dariya tace Alhaji zubairu Rocket yace Inshaallah bana zan keta hazo,ke nifa bazan daina sa Rai da tafiya ba sai na tabbatar an Gama Arfah,Ilham tace Haka yake ta wuce ciki shi Kuma yayi waje. Tana shiga ciki Anty Halimatu ta zuba mata Harara tace munafuka shigo Mana sai wani rabe rabe kike Yi, kizo kici Abinci ki Fara aiki yau baza ki Islamiyya ba,sabo da dama Kun san Zubairu ba son karatun Boko da Islamiyya yakeyi ba don yafi son Makarantar Allo nice nayi muku gata Amma da tuni an tura ku almajiranta, mata da almajiranta?Ilham ta tambaya,Anty Tace kwarai kuwa Wlh garuruwa da yawa akwai Almajirai Mata yanzu Ana turasu can Garin da Malam suna Zama cikin matansa da Zaku dage ko kudi ai sai ki samo mana da yawa kiyi aikin karfi, Baki Ilham ta tabe tace ga Yaranki Nan su Bilkisu su ai da kina sonsu bakya Zancen su sai Ni da bakya kauna. Halimatu duka ta rufe Ilham dashi tace Dan ubanki Ina Kanwar Uwarki Uwa Daya uba daya kike maida min magana? Ni sa'arki ce? Kai ta girgiza mata tace Amma Baki da girma a idona wlh bazan boye Miki ba kin cuceni da yawa bani da aiki sai na Bauta Miki na samo muku kudi ke da wancan Dan Iskan Mijin naki makaryaci Zubairu Rocket sai harbo karya. Halima idonta ya canja kala sabo da kalamn Ilham sun mata ciwo tace ubanki ne makaryaci,Oho miki, To wlh ki mike aikin Neman kudi yanzu Kika Fara. Mikewa Ilham tayi ta dauki abincinta taci sannan ta zauna tare da gyara gidan da ko Ina su Kuma yaranta sun tafi Islamiyya. Washe Gari juma'a da Sassafe ta shirya cikin Kayan gwanjo na Riga da wando sabo da ita Ilham Dole fa sai ta Zama yar gayu bata sa kayan Hausawa ko kadan sai na Bature Amma Halimatu murna takeyi kudinta ya huta Kaya Yan gwanjo dari uku ta ishi Ilham, da Sallah Bata tunanin ta girma ta Hana ta Babu ruwanta gaba Daya ta lalace bata da kunyar kowa burinta harkar Gayu kawai Ilham tace Ni mutanen birni suna birgeni kawai ta Dole so nake na Zama Yar gayu Nima sabo da Haka nake yawan kallon fina finai a kauyenmu gidan Wata Amarya Haule. Hijab Karami ta daura a saman Riga t-shirt da Jean blue trouser Data sa tayi kyau dake dama Ilham Kyakyawa ce ta karshe. Ita dama bata kwalliya a fuska sai powder da jambaki kawai take sawa irin na Yan birni sai tayi kyau, katon tire ta dauka ta nufi kasuwa wacce Ranar Juma'a take ci. Tana shiga kasuwar duk an santa kowa ji kake Ana cewa Ze Golden Girl ce, Wajen Idi me nama ta Karasa Yana ganinta yace Ze..ze..irin shegiyar Nan na Karasa Masa Golden Girl tana yarfe hannu Kamar Yar Raps, yau da me Zaki Fara ne? Tace Kitse Mana,kasan a kauyuka da yawa sunfi son kitse busashe akan Nama sabo da sunce idan ka yanki kadan ka jefa a Miya to yafi nama dadin Miya. Idi yace Wai kinji shegu a radio naji rannan Wai masu sai da kitse a kasuwa su daina sabo da wani kitsen ba a San daga Ina ake kawo shi ba Wai wani ma na Alade ne, Dariya Ilham tayi tace Kai Dalla kyale su makaryatan banza Ana Basu kudi suna watsa labarin karya ai wlh wutarsu daban ce,mutane ba kudi idan ba a Sha miyar kitse ba ta me...

8/6, 12:44 AM] Sis Asma: 🔰🔰'YAR KWANGILA🔰🔰 COPY BY ZAINAB BUTALAWA BISMILLAH ALHMDLLH Ina matukar farin ciki da Allah ya kawo mu sabon Novel dina,Allah yasa mun Fara a sa'a Kuma Allah yasa mu Gama lafiya Ni Mai rubutawa da masu karatu. Ina gaisuwa fans Dina a duk inda kuke da Wanda na sani da Wanda ban Sani ba. Pls Sharhi nafi bukata fans,ba sai Wanda zasu siya ba harda Wanda baza su samu dama ba indai kun karanta Free pages. NA KUDI NE RASHIN SA'A cmplt Dari Uku 300 ne TA GYARU cmplt Dari Uku 300 ne 'YAR KWANGILA Dari biyu 200 ne Zaku iya siya ta Bank,accnt Number Kamar Haka: 2177560408, Yahaya Garba Muhammad, Zenith Bank. Zaku iya siya ta Hanyar tura katin waya MTN Sms ko ta Whatsapp a Wannan number 08033933642. Zaku Iya yin Transfer Kati ko Vtu a wannan number 09032409668. 'Yan Niger ga number da Zaku nema ga masu bukatar Siye. +227 90 79 59 39. 'YAR KWANGILA IS DEDICATED TO DR RABIU MUSA KWANKWASO. 1 FREE PAGE Official By AsmaBaffa Page na Farko naku ne ZAINAB GARBA BUTALAWA. MARCYCOOL ADALA FLOWER AIDA MAMAN TASNEEM FREE PAGE. 2019 Makarantar secondary ta Gomnati Dake kauyen Fulani rigar Arma a karkashin jahar Yobe, Malam Yusufa ne a ajin Yana koya musu darasin turanci English, yace da fatan kowa ya gane? maza da Mata Suka daga hannu sama tare da Furta ae mun gane,Malam Yusufa yace tunda an gane to Cikinku wace ko waye zai fada min sunan tsohuwar mace da turanci? Tsohuwar mace da turanci waye zai fada Mana Muji? Kowa a ajin yayi Shuru tsit kake ji an rasa me fada. Can daga kusan karshe baya wata Kyakyawar budurwa fara da ita Amma ba Kar Kar ba,ga kyau iya karshen kyau da sura Allah yayiwa wannan yarinya da baza ta wuce 17yrs ba suna Ss3, Hannu ta daga malamin yace Ilham yau kece Zaki bamu amsar kenan? Budurwar Ilham tace ae nice ta furta da gadara ita irin me sani ta san komai, Mikewa tayi tsaye Amma tayi Shuru Bata fada ba,malamin yace a kwashe Mata da tafi tun kafin ta fara,Haka aka dinga tafawa Ilham. Malam Yusufa yace muna jinki Ilham ya sunan tsohuwar da turanci,Ilham tace Dan ubanku duk nasan gidajenku kowa akwai tsohuwa a gidansu Amma Baku san sunanta ba Kuna asarar kudin Tara,Malam Yusufa yana washe Baki yace yawwa Yi musu fada wlh kin birgeni, Sai da Ilham ta Gama zagin yan ajin sannan tace badan halinku ba sunan tsohuwa da turanci shine Expire Lady, dukul Malam Yusufa yaji, yace Sha shashar banza fice min daga class, Dariya student Suka dinga yiwa Ilham, Ilham ita a Dole Yar gayu ta waye ta wani yarfe Hannu Kamar me wakar Raps tace Yusy Man, Da bulala ya bita ta zura da gudu,ya samu kofar ajin da bulalarsa. Bayan Malam Yusufa ya fita Malam Barau ya shigo malamin Biology, ya Gama Darasinsa a karshe yace babu tambaya? Ilham ce ta daga hannu sama tace Ina da ita Malam, Murmushi Malam Yayi irin ta birgeshi tana ganewa,yace Yi tambayarki Ilham,Ilham tace Malam ka manta sunana Ze(the) Golden girl, tana sagale hannu tace Sunana Ze Golden Girl, Dariya aka dinga Yi sannan tace Malam tambayata Wai ta Ina ake Haihuwa ne? Duk gamu an haife mu Amma bamu San ta wacce Hanya Muka biyo ba,bakin ciki ya Kama Malam Barau yace ta gemun Ubanki Yar iskar yarinya Fuuuu ya fice Daga class,ita kuwa Ilham dariya ma ta dinga Yi tace gaske ne ta Gemu ake Haihuwa. Bayan an tashe su sun fito zasu tafi gida Uniform Dinta gashi me Tsafta yasha guga Amma Kuma duk maho da dinki a jiki wannan Alama ce ta su talakawa ne sosai, cikin Fushi ta fito shi yasa ko kawayenta bata kula ba sai gidansu. Wani Rubabben gidan kasa ne Wanda rabinsa katangar Kara ce,Ko murfin Kofa Babu kamar ginin zai rufto kowa yaga wannan gida yasan talauci ya samu gindin zama. Baba Zubairu Wanda akewa lakabi da Zubairu Rocket da shi taci Karo a zauren,Yana ganinta kamar yaga Mutuwa ya Bata fuska kamar zai mareta,ganin Haka ta zuge jakar makarantar ta wacce take ta buhun Leda ce ta dakko Naira dari a ciki ta Mika Masa tace gashi aci goro Baba,Baki ya washe hakoran Nan Jajir

DUBAI PART 1 Hausa Novel Document By Fauziya Tasiu Umar,Oum Hairan https://taskarnovels.com.ng/novel/dubai-part-1

BARIKI GADO NAH Hausa Novel Document By Oum Aphnan https://taskarnovels.com.ng/novel/bariki-gado-nah

BARIKI GADO NAH Hausa Novel Document By Oum Aphnan https://taskarnovels.com.ng/novel/bariki-gado-nah

JARABABBEN NAMIJI SABON SALO Hausa Novel Document By Oum Aphnan https://taskarnovels.com.ng/novel/jarababben-namiji-sabon-salo

SUGAR MUMMIES Hausa Novel Document By Oum Aphnan https://taskarnovels.com.ng/novel/sugar-mummies

YAR KWANGILA Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/yar-kwangila

AUREN MU Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/auren-mu

MA AIKACIYAR GOMNATI Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/ma-aikaciyar-gomnati

DUK INDA TA FADI Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/duk-inda-ta-fadi

MAFARKIN FARIDA Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/mafarkin-farida

CIRANIN AMANA Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/ciranin-amana

TA GYARU Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/ta-gyaru

ADDU'AR KAWA Hausa Novel Document By Asma Baffa https://taskarnovels.com.ng/novel/addu-039-ar-kawa